Showing 6001 words to 9000 words out of 39216 words
Chapter 3 - ZULFAH Complete Book 1&2 By Oum Maheer Miss Green.txt
 ahankali mubi komai asannu,indai motace ni zan siya miki tunda nima kaina me arziƙi,masu iya magana sunce kafin ai ɗaran akan ƙwanɗi."
Duk da abin ya yiwa Hibba daɗi amman sai ta tsuke fuska ta haɗe ƙafa ɗaya kan ɗaya,tana ji azuciyarta dama ta kashe Zulfah ta huta da jaraba.
Wayar Hajiya Raihana aka bugo,ta ɗaga tana ce wa"ok!to ku bita yanzu yanzu kada ku sake ta ƙara tserewa awannan karon don yadda na gama da uwarta itama dole ne tabi sahu."
tana gama wayar ta kalli Hibba,wacce itama kallonta kawai take da mamaki,tana jiran amsar tambayarta sai kuwa Hjy Raihana ta ce"nasan kina da tambayoyi da yawa,amman kuma ayanxu ba zaki samu amsarki ba,har sai burina ya cika don wannan karon so nake ayita taƙare."
Sai danayi kuka na me isata sannan na kamo hanyar gida,ammanfa duk wanda ya ganni yasan tabbas ina cikin matsala,ni daman ba ƙiba ba sai na ƙara figewa tamkar wata figaggiyar kaza.
ahankali nake tafiya acikin motar,amman gabana sai faɗuwa yake ni narasa me yake damuna,amman dai nasan hakan bazai rasa nasaba da kukan dana sha yanzu ba,don rashin uwa babbar ƙaddara ce arayuwa,ni dai yanzu bani da me bani shawara sai benezar,tare mukayi makaranta tun daga matakin farko amman daga baya kowa ya cigaba da karatunsa aƙasar da yake so,don anan burikanmu sun banbanta,ita ƙasar Australia ni kuma Oman don haka kowa ya kama gabansa ammanfa kullum muna manne a waya chart,vedio call da sauransu.
Ahankali na fara fuskantar wata mota na bina abaya,amman ban tsaya ba nayi dauriyar cigaba da tuƙina gabana yana cigaba da faɗuwa.
Tun suna bina ahankali har suka fara yi da ƙarfi,duk yadda nakai da gudu da motata kasawa nayi sai da suka kusa cimmini,Allah ya taimakeni na shige cikin go soluw,abinda na tsana kenan amman awannan karon sai gashi go slow ɗin yayi min amfani awannan lokacin,sai da muka daɗe sannan masu bada hannu suka sallamemu,amman sai na rasa wacce hanya ma zanbi?gashi kuma na rasa yadda zanyi in ɗaga waya in kira dady na.
Wata hanya nabi,ammanfa sai dana bi nake nadamar bin hanyar saboda babu kowa tsit sai ƴan motoci jefi jefi,ai kuwa sai ga motar nan da take bina ta ƙara biyoni,tsoro ya bayyana aruhina da kuma gangar jikina,nayi saurin ɗaukar wayata don kira Dady na,bugu ɗaya ya ɗaga ban bari ya fara magana ba na ce"Dady wasu ne suke bina,don Allah Dady ina kan titin bayan banki wanda kake da hannun jarin nan?"tsit na kashe wayar.
A haukace Malik ya ajje glas cup ɗin da hjy Raihana ta zubo masa sanyayyan zuɓo wanda yasha kayan haɗe haɗe,halastacce da baragurbi don daman ta saba bin bokaye da malamanta.
Tana gani ya tashi afirgice kuma baice mata komai ba yasa tasha gabansa ta magantu.
"haba Dadyn yara ina kuma zaka daga dawowarka?."
fuzgar da wata muguwar iska yayi amman baice mata ƙala ba,ya fice da mugun sauri har yana haɗawa da gudu,saboda ya samu ya buga waya don akaiwa ƴarsa gudum mawar gaggawa saboda ba ƙaramin son ƴar tashi yake ba.
hjy Raihana ta bishi da sauri amman bata cimmasa ba,,ta ɗanyi dariyar yaudara don tasan yau ta ƴar gwal ɗin tasa ta ƙare,sai dai wata Zulfan amman ba wannan ba,yadda ta tsani ahalin Jiddah abin har ya ɓaci,saboda haka ma su kansu iyayan Jidda da ƴan uwanta,sai da tasa aka cire musu tunanin Zulfah baki ɗaya suji su manta da itama adoron ƙasa,saboda haka basu neman Zulfan itama bata nemansu.
Hankalinsa ya tashi sosai,ya shiga goge Zufa yana gani duhu duhu alokacin da komai ya faru,don suna bin bayan waɗannan mutanen kuma gashi da alamar sun kusa cimmata,harbin motarsu akeyi amman tsaf sunƙi tsayawa sai faman harbin iska suke,ita kuwa Zulfah duk iya tserenta yau kasawa tayi,musamman da take tauraruwar ƴar sukuwar doki,amman kuma yau kasawa tayi saboda yau cikr take da nauyin zuciya dana jiki dana ruhi.
Karon farko kenan daya kasa taimakawa ƴarsa,bata neman wani awajensa ta rasa ba musamman asanda ta rasa mahaifiyarta,sai gashi yau yana ganin ƴarsa cikin halaka amman kuma ya kasa taimaka mata ɗin,don duk harbinsu da akeyi baisa sun tsaya ba,sai ƙarawa motocinsu iska da sukeyi su dole sai sun cika burinsu na kashe Zulfah.
Da mugun gudunsu suka kamota,harbin motarta kawai sukeyi sun harbi sama da rabin glashin murfin motar,dauriyarta da jarumtarta duk suka ƙare kawai daga ƙarshe ta gangara cikin rami ne mugun zurfi da kuma duhu,wanda yake nan agefen titi ganin ta faɗa rami yasa sukayi wata muguwar dariya suka wuce da mugun gudu.
Mutuwar zaune Malikh yayi,ya kasa koda motsa ɗan yatsansa don ganin abinda ya faru,kuka da hawaye suka kasa fitowa daga ƙwarmin idanuwansa,ya samu shuɗewa ta wasu awanni ji yake tamkar mafarki yake yi wanda yake shirin farkawa amman ya kasa farkawar saboda tsoron mafarkin.
Ƴan sandan sunyi yunƙurin bin waɗannan mutane amman ganin halinda Alhaji Malikh ya shiga yasa suka kasa aiwatar da komai,don kiran ambaton Allah yake yi jikinsa sai wani irin kyarma yake yi da tsuma,idanuwansa kuwa sunyi wani irin mugun yi ja tamkar idon jini.
Sosai abin ya basu tsoro,da sauri suka tsaya da motarsu dai dai inda abin ya faru.
Amman babbansu ya bada doka akan atsare wannan titin da waɗannan baragurbin suke,don atantance su waye sukayi wannan aika aikar,sannan ya tura musu da nombar motar.
Kasa fitowa yayi daga cikin motar,sai wani irin haki yake yana danne saitin zuciyarsa,sosai ƴan sandan suka tausaya masa suka kasa bashi baki akan wannan babban lamarin,don duk wanda ya ƙwana ya tashi agarin yasan irin bala'in son da Malikh ke yiwa ƴarsa.
Ɗan sanda ɗaya ne yayi ta maza ya matso kusa dashi,ya dafa kafaɗarsa cikin faɗuwar gaba ya ce"mu musulmi ne Alhaji,kuma baza muyi biris da ƙaddararmu ba,kuma daman asali yana can a lauhul mahfuz ka nuna juriya da jarumta azuciyarka,kayi ra kiran sunan buwayi gagara misali,shine ke taimakon mara ƙarfi da kuma mara jarumta,inna lillahi wa inna ilaihi raji'un,shine abinda ya kamata ka dinga ambato ba riƙe zuciyar da ba tada ƙashi ba,don komai zai iya faruwa da ita daga nan ka mutu ka cewa Allah saboda ƙaddarar daya yi maka ka kashe kanka da ciwon zuciya?,kaga ka zama me butulcewa Allah tunda babu abinda Allah bai yi maka ba,ka taso acikin ahalinka wani kuwa yana can bulayi duniya akufai,baisan iyayensa ba?bai san ƴan uwansa ba?wani kuma babu abinda Allah bai bashi ba,amman a ƙaddararsa sai ya hanashi haihuwa,kuma yana so amman haka yake haƙura,to kai me zai sa baza ka yi wannan haƙurin ba"?.
Sosai Alhaji ya dawo da kafatanin linzamin ganinsa zuwa ga wannan ɗan sandan,sai yaji ya samu wani kyakkyawan hope saboda haka sai ya fara kiran sunan Allah,kawai sai yaji ya samu ƙwarin gwiwar fitowa ahankali,ya fata takawa sannu sannu duk da juriya da dauriyar da yake son arowa amman kana ganinsa zaka gane,maraunaci ne akan abinda yake so ba shida jarumta ko ɗaya ta wannan sashen.
Da sauri ya yi baya ganin har an fara fito da motar Zulfah daga cikin wannan ramin,baki ɗaya motar tayi wani ƙwasa ƙwasa,alamu sun nuna wanda yale cikin motar babu makawa bazai fito da ransa ba,mota ma tayi haka ballan tana mutum?.
Bai san sanda wani mugun jiri ya rinjaye sa ya faɗi awajen ya fad'i tamkar matacce.....✍
MRS GREEN CE.
domin chart dani kai tsaye 07068606171
*_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 SEPTRMBER._*
_1-ƘWAI A BAKA...!!!🥚_
👇🏽
*(Ummu Affan)*
_2-NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA...!!!🫗_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*
       _ZULFAH_🍏
👇🏽
*Ummu maher(mrs green)*
_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_
Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank
Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽
07068606171
Ƴan Niger zasu turo katin Moov ko Airtel ta wannan number.
08104335144
*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa*
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
07068606171
08179523215
Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽
2K
sati biyu
3k
idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.
Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
_*Typing🤳🏼*_
_*🍏....ZULFAH....🍏*_
         Na
_*®UMMU MAHER(MRS GREEN)*🍀_
   *TEAM🔥GAWURTATTU 🤟🏻3*
_*AREWABOOK🤳🏼*_
ZULFAH::https://arewabooks.com/book?id=64ff0277d73b80a18ea59540
   _*Page∆4*_
........Wani irin kuka mahaifin Zulfah ya fara,dukkanin ƴan sandan jikinsu ya yi sanyi sosai acikinsu ma sai da wasunsu sukayi kuka,saboda sunfi kowa sanin yadda ya ke matuƙar son ƴarsa wato Zulfah,zai iya sadaukar da komai nasa saboda ƴarsa wacce matarsa mafi soyuwa aransa,baya ɓoye son da ya kewa Zulfah agaban kowa shiyasa da damar mutane idan suna neman wani abu agunsa suke haɗawa da yi masa kirari,Baban Zulfah kuma uba nagari zaki majinginar Zulfah.
ko da a tv ne kuwa wannan kirarin ake yawan yi masa kuma duk yawancin kamfaninsa da sunan Zulfah ya ke buɗewa,ko gajiya da sanya sunan bayayi saboda son ƴarsa da ya keyi,sai gashi rana ɗaya Allah ya aiko musu da wata mummunar ƙaddara,wacce take baraza da rayuwarsa don mutuwar Zulfah tamkar mutuwarsa ce.
      ¢¢¢¢¢¢¢¢¢¢
a hankali Zulfah ta buɗe idonta wanda ya yi mata wani irin mugun nauyi,babu ciwo ko ƙwarzane ajikinta saboda alokacin da hatsari ya same ta har ta faɗa cikin wannan babban ramin mai mugun hatsari,yadda kasan an cillo ta daga cikin wannan ramin ta riƙe wani ƙarfe ta dinga sauka a hankali har ta koma cikin wani ɗan ƙaramin lungu,tana murnar tsiran da ta samu sai me kuma???wani ƙaton kumurcin miciji ta gani acikin wannan ramin ta kurma wani uban ihu wanda yasa hankalin kowa ya dawo wannan ramin,nan da nan Abee mahaifin Zulfah ya taso tamkar mahaukaci ƴan sandan nan suka riƙe sa,aka kirawo masu agajin gaggawa suka fito da ita a sume tamkar matacciya,amman abinda ya bawa kowa mamaki bai wuce yadda suka ga Zulfan ba,saboda babu ko ƙwarzane ajikinta alamu dai sun nuna ce wa wani abin ta gani ta tsorata.
Abeey da hjy Innah dasu ta fara cin karo,sun rafka uban tagumi suna kallonta dukkanin nutsuwarsu da komai na su yana ga Zulfah,idanun hjy Innah sunyi jajir alamar tasha kuka har ta gaji,ta juya da kallonta kan mahaifinta shima dai kusan halinda Innar ke ciki shima haka ya samu kansa,ammanfa nashi ma har yafi na Innar don shi jijiyoyin kansa sun tashi sunyi raɗa raɗa dasu.
tausayinsu taji ya ɗarsu a zuciyarta,waɗannan mutanen biyu wato Innah da Abinta sune mafi soyuwa arayuwarta,dasu ta tashi ta buɗe ido sune kominta arayuwa sai kuwa Murash-sha ƴar uwarta kuma aminiyarta,ayanzu ma tayi mamakin rashin ganinta amman tasan hakan bazai wuce rashin amincewar mahaifiyarta ba,don sam momin murash-sha ta tsaneta sosai ko gaisuwa bata haɗasu,daman ita Zulfan ba ma'abociyar gaisuwa bace,dona girman kanta sai dai kai babba ka zubar da girmanka ka durƙusa har ƙasa ka gaisheta amman ita tafi ƙarfin gaisuwa.
 ahankali na buɗe bakina wanda ya yi min nauyi na ce"Abeey na".da sauri ya juyo yana kallona,ya ƙaraso inda na ke har yana haɗawa da tuntuɓe. ya shafa gashin kaina yana kuka ya ce"Zulfah kin tashi?me yake yi miki ciwo?me kike so"?.duk alokaci ɗaya ya yimin wannan tambayoyin?ita kuwa Hjy Innah ce wa tayi"ƴar nema duk kin sanyamu acikin tunani da zullumi".sai ta fashe da kuka sosai har da majina don tana masifar sona ni da kaina na tabbatar da hakan.
ana ta zuwa dubani duk da babu abinda ya ke damuna yanzu,don na warke baki ɗaya amman sarai Abeey na ya hanani sakat don ko tafiya zanyi sai yace min wai inyi a hankali.har ranar da za'a sallameni Hjy Raihana bata zo ba,rannan muna zaune ni da Murash-sha Hjy Innah kuma tana sallah ta idar tana jan cazbaharta wato carbi,sai mukaji sallamarta kamar daga sama ita da ƴarta Munirat.
tasha wata uwar ƙwalliya tamkar za tazo gidan biki,wani leshi ne ajikinta ɗan ubansu don faɗar kuɗinsa ma ɓata bakine saboda yadda ya tsaru,ya fitar da kyaunsa na asali da zallar zunzurutun kuɗinsa,tayi ɗaurin ture kaga tsiya daman kuma ita wannan ɗaurin shine ainihin ɗaurinta indai ba abaya ta sanya ba.
Munirat ma tayi kyaunta sosai,tana sanye da wasu ƙananun kaya masu shegen kyau wando jeans me ruwan zaiba,da kuma farar tishet wacce tayi bala'in kamata,ga uban atachment da ta sanya akanta wato gashin doki,don su daman gashin uwarsu sukayo.
Kallo ɗayan danayi musu na kauda kaina ina yi wa Murash-sha magana don ta haɗamin ruwan tea babu madara.ina jinsu suna yimin sannu a wata murya a dausashe,tamkar waɗanda aka yi wa dole Hjy Innah tayi musu kunnen uwar shegu,don sam taƙi jini hjy Raihana saboda yadda take son taga bayanta,don ta rabata da ɗanta daman bata gaida Hjy Innah ba saboda haka nima ban amsa sannunta ba,don gani nake duk wanda zai muzantawa Innah sai inda ƙarfina ya ƙare,don haka da suka gaji da zamansu suka nemi hanyar tafiya.
Inajin Hjy Innah tana ce wa"Innah ta gaida ash-sha dama babu wanda ya gayyaci kaza zuwa hanyar rafi,shisshigi da ƙwala kai afaranti kina tafe kamar wata uwar mata sai munafunci fal ciki".
tas taji abinda surukar ta tafaɗa mata amman ta danne,sai dai Munirat taso ta dawo ta zubawa kakarta rashin mutunci,don ita duk wanda zai taɓa mata uwarta sai ta yayyagashi ko wanene kuwa,saboda haka da sauri Raihana ta riƙeta tana ce wa"kul ɗinki Munirat!saboda kinsan halin munafuncinra,sai ubanki ya dawo ta haɗamai munafunci ƙarya da gaskiya ta faɗa masa,shi kuma ya hau kai har ya nemi yin hukunci akan hakan,banda ma yanzu na sanya mlm na zaune ya rufe masa baki da abinda zai faru da yanzu ba'ayi hirar ba,saboda haka barni dasu dukkansu nasan matakin da zan ɗauka akansu,don wannan son da ubanta yake mata take wani kallon mutane ɗai ɗai ba?to ki rubuta ki ajje sai na mayar dashi mummunar ƙiyayyar da zata sanya ma ya cire ta acikin ƴaƴansa baki ɗaya.
dariya suka sanya ita da mahaifiyarta sannan suka wuce.
   
         ¢¢¢¢¢¢¢¢¢
*ALIYU*
     da ƙer aka samu aka fito da mahaifinsa,saboda sai da ita da kanta ita Zulfan taga dama sannan ta rattaba hannu aka sallami mahaifinsa,abin ya ƙona masa rai ranar yayi kuka sosai har ya gaji ya share hawayensa,ranar yayi kukan rashin babu yanzu saboda talauci aka yi musu haka?gashi abinda ma yafi ƙona masa rai shine.
 
   da ƙer ya samu ɗan sandan daya shige masa gaba sukaje har gidansu Zulfah,sai da suka ɓata wajen awa uku suna zaman jiran zuwan Zulfah sai da akayi musu manya manyan screening sannan suka ga Xulfah yadda kasan zasu ga wani sarki ko shugaban ƙasa,amman don ganin mutum ɗaya akayi musu wannan cin mutuncin,donshi aganinsa babban wulaƙanci ne saboda sam baiga amfanin yin hakan ba?don zasu ga wannan ƴar tayin ƙwailar yarinyar dako hannunsa zai kai faɗin ƙugunta,amman akanta suka fuakanci tozarci me girma wanda ba'a taɓa yi masa ba.
a hankali ta fara takowa har tazo inda suke,ta zauna awata rantstsiyar kujera tana yi musu wani irin banzan kallo wanda ko kashi tagani sai haka.
jin munyi shiru mu dukanmu babu magana,kuma da alamu ba zata tanka mana ba yasa ɗan sandan nan ya ce"ranki ya daɗe dama wannan saurayin na rako wajenki,don ya nemi alfarma kuma ya baki haƙuri akan abinda ya faru da laifin da mahaifinsa yayi miki".
Ƙala bata ce ba,ta cigaba da danna wayarta ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya sannan ɗan sandan ya ɗan taɓani ya ce"Aliyu kayi magana mana"?.
da baiyi magana ba da ko zamu ƙwana awajen bai isa na kallesa bama ballantana ma har inyi wata magana,don ɗaura aniya azuciyata akan cewa indai har bata yi magana ba to nima bazance ƙala ba.
   da ƙer na fara magana kamar me ciwon baki na ce"kiyi mana alfarma a sake shi".
Da sauri naga ta ɗago don bata zata zan faɗi ƴar gajeriyar magana haka ba,tayi zaton zan tsugunna ina yi mata fadanci tamkar dai yadda sauran mutane suke mata don ƙwaɗayin abin hannunta,ni kuwa ko xata bani dala da gauron dutse bata isa inyi mata hakan ba,don bana neman komai awajenta face wajen Allah sarki gagara misali.
  abinda ta faɗa ne yasa nayi saurin kallonta da wani irin mugun kallon da bansan ya fito ba,ta ƙara zaro idonta masu mugun ƙyau da haske ta ce"are u ready or not"?...............✍🏻
MRS GREEN CE.
domin yin chart danj kai tsaye 07068606171
*_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 SEPTRMBER_*
_1-ƘWAI A BAKA...!!!🥚_
👇🏽
*(Ummu Affan)*
_2-NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA...!!!🫗_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*
       _ZULFAH_🍏
👇🏽
*Ummu maher(mrs green)*
_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_
Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽
0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank
Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽
07068606171
Ƴan Niger zasu turo katin Moov ko Airtel ta wannan number.
08104335144
*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa*
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽
08104335144
07068606171
08179523215
Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽
2K
sati biyu
3k
idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.
Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
_*Typing🤳🏼*_
_*🍏....ZULFAH....🍏*_
         Na
_*®UMMU MAHER(MRS GREEN)*🍀_
   *_TEAM🔥GAWURTATTU 🤟🏻3_*
_*AREWABOOK🤳🏼*_
ZULFAH:: https://arewabooks.com/book?id=64ff0277d73b80a18ea59540
   _*Page∆5*_
..........Aliyu ya sunkuyar da kansa ƙasa,ya kasa ko da ɗaga ɗanyatsansa tunani kawai ya ke aransa saboda yarinyar ta bashi mamaki me tsananin gaske,wulaƙanci da tuzarci yau dai tayi masa shi mutum ne me girmama na gaba dashi,sam baya yarda araina sa shima kuma ba shida raini ko kaɗan,duk da yake yana talaka bai taɓa zuwa wajen wani me kuɗi neman wani abuba,abinda ya sani shine kawai aikin kanikancin da yake kullum da safe ya fice sai yamma,shi dai aganinsa ko da me mahaifinsa ya yi mata bai cancanci wannan tozarcin da cin mutuncin ba.
da sauri Zulfah ta miƙe tana yi musu wani irin wulaƙantaccen kallo,yadda kasan idanuwanta zasu fito daman kuma gasu manya,da sauri na sunkuyar da kaina don sam bana son ganin mummunan fuskarta,don duk kyaunta da ake ko ɗawa ni to muninta nake gani,bansan na furta wata kalma ba sai da ta fita,biyo bayan tuno da mahaifina danayi acikin mummunan hali.amman kuma sai dana faɗa na ke dana sanin faɗin hakan.
duk da haka bata tsaya wani abuba ta wuce abinta,tana wani karairaya tamkar zata tsinke,don yadda kasan ƴartsana me remote haka









