Showing 12001 words to 15000 words out of 39216 words

Chapter 5 - ZULFAH Complete Book 1&2 By Oum Maheer Miss Green.txt

ranar tarihi,ƙamshinsa da ƙwarjininsa suka kusa nitsar da ita acikin wannan hali,da sauri ta fara gaishesa cikin nutsatstsiyar muryarta wacce take cike da kamala da kuma raunin,irin raunin ƴa mace wacce ta rasa rabin farin cikin rayuwarta.
cikin nutsuwarsa mai ƙara sanya ta acikin nishaɗi ya ce"lfy ƙlau murai ya kike?"
sunan da yake faɗa mata kenan,alokacin yarintarta wato 'MURAI' ita kuma Zulfah ya ce mata 'MY FAH'.
sosai taji daɗin sunan ta sunkuyar da kanta cikin nutsuwa ta ce"lfy ƙlau Yaya Bilal".
bai ƙara magana ba yayi shiru,daman kuma shi mutunne mara magana sosai magana ɗaya biyu yayi shiru,wannan yana ɗaya daga cikin abinda yasa yake ƙara burgeta saboda tana masifar son namiji me jan ajinsa.
tun daga wannan maganar basu ƙara magana,hjy innah tana shigowa ta ce"a'a ke muraisa dawo gaba malama,zan zauna kusa da mijina uwar iyawa".


da sauri Murashsha ta gimtse fuska kuma taƙi tashi,Bilal ya yi dariya sannan ya ce"no babu komai Murai tashi ki koma gaban,tunda kinga matata uwar gidana ta fiki matsayi".sosai ran Murassha ya ɓaci,ta buɗe bakinta kamar za tayi magana sai kuma ta fasa,sai kuwa Hjy innah ta ce"da kada ki fasa mana zauna uwar ƴan rashin kunya,yo idan bakiyi ba ai sai Allah ya kama ki tunda uwar kima taci ta ƙoshi take ganin mutane da wani irin kallo na ƴan tsibbu".


cikin takaici Murassha ta ce"haba hjy innah ki daina haka fa,ta yaya zaki dinga zagarwa mutum uwa agabansa".banza Innah tayi mata suka cigaba da hirarsu da Bilal,abin kuwa ya ƙonawa murassha rai daman ita Hjy innah haka take,sai ta ƙona maka rai tazo kuma tana hirarta,taso ta barta kusa da yaya Bilal ta shaƙi mayen ƙamshinsa da ta daɗe bata ji ba.amman wannan fitinanniyar tsohuwar ta rabasu,anya ma kuwa wannan tsohuwar za ta bari ayi auren?don itama taga kamar tafi son haɗa Zulfah da Bilal ɗin,in kuwa haka ne aƙwai babbar ƙura don ko wacce irin macece zata iya yaƙi da ita indai kan Bilal ne,don ya zama jini da tsokarta wannan dalilin yasa ko da suka isa gida bata ƙara magana ba ta wuce sashensu cikin baƙin ciki,tana zuwa ɗakinta ta faɗa kan faffaɗan gadonta ta saki wani irin kuka me ciwo da ƙuna.




¢¢¢¢¢¢¢¢¢


*ALIYU*


sosai ransa ya ɓaci da abinda Zulfah tayi mishi,gashi tayi masa asarar ɗan neman kuɗin da yake don su rufawa kansu asiri,shi kaɗai nr namiji agidansu sauran ƴan uwansa duk mata ne,saboda haka ko wani nauyi yanzu yana kansa ƙwanansu biyu yanzu basu ɗora girki ba,kamar kullum yau ma gidan babu abinda aka ɗora,Aliyu ya kallo ƴar ƙaramar ƙanwarsu me shekara biyar hawaye yaji yana son zubo masa da sauri ya share hawayen saboda sam baya son su gane yana cikin wani hali,ya dubi mahaifiyarsa ya ce"Umma kuyi haƙuri da jarabtar da ta samemu in sha Allah komai zaizo da sauƙi,kuma duk me haƙuri yana tare da riba yanzu zan fita in ɗanyi buga buga in samo mana ɗan abin kaiwa baki."


Umma ta ce"to Aliyu Allah yayi maka albarka ya baka abinda ka ke nema duniya da lahira,kuma insha Allah nan gaba komai zai zama labari don ni dai ina ji ajikina wataran zaka zama wani a wannan duniyar tamu".ɗan murmushi ya yi sannan ya ce"amin Ummana".ya shafa kan ƙaramar ƙanwarsa ya riƙo hannunta suka fita sai tsalle take don yanzu tasan za ta samu abinda zata sanya acikinta,yaro kenan yasan me basa shiyasa akeson mu zama masu son yaranmu da ƙaunarsu,ammanfa kada ka bari sansu ya rufe maka idanu ka lalata abinka da kanka.suna fita ya duba aljihunsa naira hamsince dashi, saboda haka ya wuce da ita wajen me ƙosai ya siya mata na hamsin ɗin sai tsalle take tana murna,shima kallon yarinyar yake tausayinta fal ransa ya saka azuciyarsa kuwa duk halin da zai shiga arayuwarsa ba zai taɓa bari suyi ta zama da yunwa ba,ya saki wani irin tsaki a fili yana jin wata iriyar muguwar tsanar Zulfah duk itace ta sanya su acikin wannan halin,kusan ƙwana biyar bai fita aiki ba sai ya ƙara jin tsanarta ta ƙara cika maaa zuciya,sannan ya ƙara ɗaukar aniyar rama duk abinda tayi masa cikin ruwan sanyi da kuma salo.




¢¢¢¢¢¢¢


*ZULFAH 2*


da daddare har mun fara barci ni da mahaifiyata kawai sai naji jiniya,ma'ana motar ƴan sanda kuma bata tsaya a ko'ina ba sai a ƙofar kangon gidanmu daga nj har mahaifiyata muka tsorata,duk da ita ba gane komai take ba amman na lura ba wai haukacewar duka tayi ba,aƙwai sauran wasu sauran ƙwalitis ajikinta.
kai tsaye macen ƴar sanda ta shigo mana tana zare ido ta ce"ke ce Zulfah"?.


da sauri na ɗaga kai na alamar eh'sai kuwa ta ce"ok you are under arest".


ban samu damat ce wa komai ba ta sanya min amƙwa,idanuwa suka kawo ruwa ina ce wa"don Allah ki faɗamin laifin dana yi muku"?.bata ce min komai ba ta tisa ƙeya ta gaba muka tafi,zuciyata cike da baƙin ciki dama ana haka kawai kana zaman zamanka ƴan sanda suzo su kama ka?ba tare da an tabbatar da laifinka ba?lallai kuwa aƙwaj matsala babba a ƙasarnan wato indai kai ba kada ga ta sai ayi ta juyi da kai?tamkar wainar masa?".


ina hango mahaifiyata ta biyosu tana nuna ni tana kuka tana rirriƙeni,amman ko ajikinsu suka hamɓareta suka wuce dani duk da daddare ne bai hanani gane Bala ba,wanda yake cikin motar ƴan sandan goshinsa duk bandeji gashi goshin ya ƙato rum dashi,ga idonsa na dama a tashe sai bankamin harara yake yana wani irin abun yana nutse damtsan hannunsa tamkar zai dake ni,sai alokacin hankalina ya ƙara tashi wato dai Bala abinda zaiyi min kenan?ya so yimin fyaɗe don na ƙwaci kaina kuma yazo ya kaini ƙara?to me hakan yake nufi?.


Tun daga yarintata har zuwa wannan lokacin ban taɓa riskar kaina a matsanancin baƙin ciki ba irin na yau,tabbas Bala ya kai maras mutunci ni da ya kamata in kaishi ƙara saboda lalatamin rayuwa daya so ya yi,shi kuma ashe har ƙara ya kaini don ya cimin mutunci saboda yaga ba nida wani gata?to ni na yarda da Allah kuma shine zaiyi min maganin komai.


muna zuwa aka ɗanyi rubuce rubuce sannan aka sanya a bayan kanta idanuwana sai wani zafi suke min,cike da barci da kuma takaici ƴan sandan wajen sai kallona suke kallo irin na ƙurulli,don ko samun damar ɗauko ɗanƙwalina banyi ba,gashina ya bazo ta ko'ina yadda kasan aljana duk da bana samun damar gyara jikina saboda rashin gata amman hakan bai sa na disashe ba,don da ina samun damar gyara da ba ƙaramar fara bace ni saboda yadda siffata da kuma halittata take,komai nawa abin burgewa ne duk da ayanzu ina da shekara ashirin,kuma na gama cika budurwa komai nawa cike yake ɓam,sai dai rama da ƙashin wuya shima duk na rashin gata ne.


Ina da matsakaicin tsayi,ni ba doguwa ba ni ba gajera ba sannan fara ce ni sosai,rawn face ne dani ba doguwad fuska ba,wacce aka ƙawatata da siririn hanci da ɗan ƙaramin bakina,idanuwa manya ne sosai waɗanda aka ƙawata su da zara zaran gashin ido,idona yafi kala dana turawa don ƙwayar idona ba baƙa bace brown kala ce,ga gashin gaban goshina ya ƙwanta luf luf,tunda na taso ake kawowa rayuwata hari amman Allah bai taɓa bawa wani sa'ar lalatamin rayuwa ba,saboda na dogara da Allah shine me kariya aduk inda kake.


ƴan sandan suka yimin tambayoyi na amsa musu duk abinda ya faru,sukayi ƴan rubuce rubuce sannan sukace mu jirayi zuwan oga saboda case ɗin babba ne,don case ɗin fyaɗe ba ƙaramin babba bane shi kuwa Bala tuni idonsa ya raina fata don yaji ance sai oga yazo,gashi yaji labarinsa ba shida mutunci ko kaɗan ko gidanku ɗaya dashi idan kayi laifi sai an yanke maka hukuncin daya da ce,tuni cikinsa ya ɗuri ruwa ya fara ƙulli ji kake ƙuuuuuuuuu alamar zawayi.......✍🏻😄




*MRS GREEN CE*




domin chart dani kai tsaye 07068606171


*_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 SEPTRMBER._*






_1-ƘWAI A BAKA...!!!🥚_
👇🏽
*(Ummu Affan)*




_2-NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA...!!!🫗_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*




_ZULFAH_🍏
👇🏽
*Ummu maher(mrs green)*




_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_


Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽


0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank


Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144


Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽




07068606171


Ƴan Niger zasu turo katin Moov ko Airtel ta wannan number.


08104335144


*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa*
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144
07068606171
08179523215


Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽


2K
sati biyu
3k


idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.




*Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼*
_*🍏ZULFAH🍏*_
_page 8_


_@🫰🏻Ummu Maher_
*{MRS GREEN}*






_*please kuyi following ɗin littafin Zulfah on arewabookstore🫰🏻*_
ZULFAH:: https://arewabooks.com/book?id=64ff0277d73b80a18ea59540
________________________
*GAWURTATTU 3*




_*AMMA ARAB!AMMA ARAB!!AMMA ARAB!!!*_


_kai daga jin sunan kasan sunan ya amsa sunansa,AMMA ARAB ta kawo muku wani supplement na gyaran jiki mai sanya daɗi da ƙamshi AMMA ARAB gidan ƙamshi_


*MUSUK*
*MADARAR TURARE*
*KAJIJI*
*ROT*
*SANDAL*
*HUMFUR*
*SANDAL FLASK*
*SANDAL WUD*
*AALUT*
*GAF-GAF*
*JANNAMI*
*ƘWALAKCA*
*MAHAHABSUFYAN*




*WANNAN SHINE GRP ƊINA NA WHATSAPP,KI ANTAYO SABODA KADA AYI BABU KE*
👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
https://chat.whatsapp.com/BrUXmBHnDN6KUJYnkBDT7S


*ADDRESS👇🏻👇🏻👇🏻*
Zaria road kwankwasiyya sabon gari dangwauro house number 224


*AƘWAI WANI SUPPLEMENTA NA GYARAN JIKI DA TAZO MUKU DASHI KE DA KANKI IDAN KIKA YI ZAKISAN EH LALLAI ZAKI GIGITA ME GIDA,KINSAN MAZA SAI DA ƘAMSHI DUK MATAR DA BATA SAYI WANNAN SUPPLEMENT ƊIN BA TO AN BARTA A BAYA*


*AƘWAI BABBAN MAGANI NA INFECTION,WANDA ZAI DAWO MIKI DA MARTABARKI NA ƳA MACE,ZAI CIKO MIKI DA NI'IMARKI KI KOMA ƳAR GATAN MEGIDA*


*AƘWAI BABBAR KAMBASA,TA TURARA KAYA HAJIYA KI BUƊE BAKIN ALJIHU KI JIƘO DA ƘAMSHI,KINA ZAMA AN SAN KIN ISA MACE HAJIYA DON AMMA ARAB TA SHARA SOSAI WAJEN KAWO MUKU KAYAN GYARA NA MATA*


*AƘWAI SABULAN GYARAN JIKI SUNE KAMAR*


*MULATO SOAP*
*FACE CREAM*
*FACE SOAP*
*MULATO WHITENING LOTION*
*HAIR GROW OIL*
*HAIR GROW CREAM*
*KAR-KAR OIL*
*MINT LEAVE OIL*
*ANTI PIMPUS SOAP*
*AƘWAI SABULUN NANKARWA*


sannan ina harkar👇🏻👇🏻👇🏻👇🏻
*ABIN BUKI*
*ABINCIN OFFICE*
*SNACK*


KAMARSU👇🏻👇🏻


*WAINAR MASA*
*SINASIR*
*MEAT PIE*
*CINCIN ƊAN LAUSHI*
*CUP CAKE*


DA DAI SAURANSU.
AMMA ARAB GIDAN GYARAN AURE😄👏🏻




_ZULFAH 1_




...........Ji tayi kamar ana kallonta,da sauri ta ɗaga lulu eyes ɗinta tana kallom wanda ke mata wannan kallon tsaf ɗin,don ita arayuwarta ta tsani kallo sosai saboda hakama bata fiya son fita ba saboda kallon da maza ke binta dashi tamkar waɗanda basu taɓa ganin mata ba.
ganin shi take kallo da rinannun idanuwanta yasa yaji wani irin abu ya tsarga masa tun daga kansa har zuwa tafin hannunsa,ya ƙaraso wajenta cike da fara'a ya matso kusa da ita zai zauna.


da sauri na miƙe tsaye ina ƙare masa kallo,kallon tas nake masa ma'ana kallon baka isa ba shima kallon nawa yake,a maimakon ɗazu da annuri yanzu kuwa fuskarsa ta canja alamu sun nuna cewa tabbas yaji haushin abinda nayi masa,kallon kyama nake binsa dashi saboda ni gani nake don yaje ƙasar waje ne zai nunawa mutane ya koyo iskanci ko kuwa me?ahankali na buɗe bakina na fara magana cikin tsiwa.


"look Bilal,ya zaka zo ina cikin shaƙatawa ta ka nemi damar min rayuwa haba wannan wacce irin rayuwace wannan?".kasa magana Bilal yayi ya shafa ƙwantaccen gashinsa wanda ya ƙwanta masa luf,bai ƙara magana ba ya tashi ya fita duk ransa a matuƙar dagule,ko ɓangaren mahaifiyarsa bai shigo ba yazo wajenta amma da abinda zata saka masa kenan?haka ya wuce ɓangaren nasu cikin matsananciyar damuwa.


****
"Momi ki duba fa ki gani?ace yaya ya dawo amman ba zai fara zuwa wajenki ba?sai ya fara zuwa wajen wannan mara mutuncin?wacce bata ganin kan kowa da gashi?".
hajiya Maryam ta haɗiye wani irin ƙaton malulun daya tokare mata maƙoshi sannan ta ce"ni wallahi na rasa abinda yarinyar take dashi?da maza suke binta tamkar wata uwarsu?ki duba fa kiga yadda yaron nan mata suke binsa?yana wulaƙantasu amman tun yana can ya dameni da maganar wannan yarinyar,shiyasa yanzu sam bana zuwa sashen waccan fitananniyar tsohuwar,don daga ita har jikarta ba mutuncine ya ishesu................"
tana cikin maganar Bilal ya shigo,ransa duk a matuƙar jagule saboda yadda yaso ya samu Zulfah ba haka yaso ya same taba,tun dama ita Zulfah macece me yiwa maza ƙwarjini ba kowani namiji ne zai kalle ta kallon farko yace yana sonta ba,dole sai yaji ɗar ɗar da kuma haɗi da ɗan tsoronta kafin ya faɗi abinda ke ransa,idanma har kayi dauriyar yin maganar saboda tsare gidanta.


Hajiya Maryam ta ɗan tura bakinta gefe alamar ka ji dashi,wai an saci zanin mahaukaciya duk da tana cikin matsananciyar murnar dawowar tilon ɗanta namiji bai hanata fara faɗa ba tana ce wa.


"to sannu shanyayye! wanda uwar Zulfah ta shanye tun kafin tabar duniya,wallahi tallahi ka bani mamaki Bilal me akayi akayi wata Zulfah,da tun yanzu zaka banbantata dani kaf duniyar nan kana da wanda ya fini ne?da har zaka nuna min Zulfah ta fini?to ka buɗe kunnuwanka ka jini,tun kafin ubanka yaji cewa kana son Zulfah ka cirewa kanka sonta na dole,saboda nasan yana jin komai zaije ya garxaya ya faɗawa waccen fitinanniyar tsohuwar tazo ta fitine mu,don wallahi rufe idona zanyi inci mata mutunci,don idan tana tutiya da ɗanta ni Maryam bata isa tayi min da nawa ba,saboda haka ba gilin gilin ba tayi mai,kuma hawainiyarka ta kiyayi ramata don naga kanka yana rawa sosai sai na ɗoraka bisa hanya".


Nan dai Hajiya Maryam ta shiga faɗawa ɗanta illar auren Zulfah ta ƙara da ce wa"ubanta ma haka yasha wahala da uwarta,ta shanyesa sai abinda tace ya yi shi yake yi kai ko cewa tayi faɗa rijiya ka mutu zai faɗa saboda mugun halinsu a jini yake".shi dai bai iya ce mata komai ba ya tashi ya wuce ɓangarensa,yana jin wani irin mugun son Zulfah na ratsa masa ko ina na jikinsa,son maso wani ƙoshin wahala abinda ya faɗa azuciyarsa kenan,sai kuma wata zuciyar ta sanar dashi fa'idar yin haƙuri,yau da gobe sai Allah a haka yana gwaji Xulfah zata so shi.




yana shiga ɗakinsa,ya yi tsuru yana kallon ɗakin saboda hotunan Zulfah da akabi aka cire masa baki ɗaya,ya cika da mamaki sosai duk da yasan ba kowa ne zaiyi mai hakan ba banda mahaifiyarsa,babu yadda zaiyi da ita duk da yadda zuciyarsa ke yi masa wani irin ƙuna,ya dafa saitin zuciyarsa yana ce wa"ya Allah Ka sanyaya zuciyar mahaifiyata akan farin cikina Zulfah,ya Allah ka bani Zulfah ya Allah ka sanya mata sona ko yaya ne."ya faɗi hakan yana sakarwa kansa shower a banɗaki.




wayarsa ya buɗe tarr hoton Zulfah ya fito akan kyakkyawan screen ɗin wayarsa,tana murmushi tayi kyau sosai dimples ɗinta sun lotsa sosai,ya yi murmushi yana shafa dai dai fuskarta yana ji dama ace yanzu tana ƙwance a ƙirjinsa,ya rintse idonsa yana jin wani irin daɗi yana ratsa sa randa akace gashi ga zulfah sai ya ahayar da ita zumarda bata taɓa ɗanɗana ba saboda yadda yake sonta,da yake jinta ajikinsa ba wai iya son ƴan uwantaka kaɗai ba,a'ah harda wani irin gigitaccen son da bai san yana mata shi ba,tun tana ƙaramarta yake sonta amman bai nuna mata hakan saboda ko kallonta yayi sai yaji gabansa na faɗuwa.ayanzu abu biyu ya rage masa addu'ah sannan ya kama ƙafa da hjy inna saboda yasan yadda take sonshi da ƙaunarsa.yayi wankansa cikin jin daɗi da annushuwa ya fesa ƙwalliyarsa cikin ɗanyar shaddarsa drk blue kasancewarsa fari ba ƙaramin kyau yayi ba yadda kasan wani balarabe ya fito yana angiza wani irin ƙamshi mai sanyaya zuciya ya wuce wajen hajiya Innah.


********
Yana fita hjy innah ta shigo,ta kalle ni sosai sannan ta ce"haba haba fisabilillahi Allahu ya Allah,wannan yarinya ko ƴar bani na iya yanzu don Allah Zulfah meye laifin Bilalu?yaro da ɗan jan kunnensa kamar bature,ni sai dana nutsu ma naga duk kamar da ake cewa kunayi cutarsa akeyi,don yafi kyau da komai ke dai wannan cikon da kike yine yake ruɗarsu".ta nuna ƙirjina tana hararata,na gane abinda take nufi saboda haka ban tanka mata ba ban kuma tashi ba,har ta gama rigimarta ta wuce tana bankamin harara tamkar idonta zai faɗo.
tana wuce na ce"jarababbiyar tsohuwa kawai."




¢¢¢¢¢¢¢¢¢
*ALIYU*


a hankali yake tafiya yana tuna abubuwa da dama na rayuwa,ayanzu ƙarfin mahaifinsa ya ƙare shi ya kamata ya zama uba awajen ƙannensa,yana son cikawa ƙannensa burinsu na karatu amman ayanzu kaf ƙannensa babu mai zuwa makaranta,wannan abu yana matuƙar ci masa tuwo da ƙwarya,duk sanda zai fita bai wuce ya samo ɗan abinda za'a sanya a baki ba,kullum ƙoƙari yakeyi don yaga kaf ƙannensa basu nemi abu sun rasa ba,amma ya gaza yin hakan saboda halin rayuwa.


wajen wani abokinsa ya wuce a gareji,wanda yake aikin kanikanci yana zuwa ya sameshi yana aikinsa ya buɗe wata hamshaƙiyar mota yana gyarawa,yana hango Aliyu ya saki fara'a don Aliyu mutumin kirkine sosai kuma ya isa akirasada aboki nagari,don duk babunsa bai yarda ya yi roƙo yafi ganewa duk wahalar da zaisha yasha ta shi kaɗai,har ya samu ya kawo gida amman bai yarda da zubar da mutuncin kai ba.


Ahmad ya ce"a'ah yau su gadanga ne awajen namu?sannu da zuwa yau babban baƙo ne yazo min".ya faɗi hakan yana ɗakko masa gujera fara ta roba a cikin rumfa,na zauna ina murmushi na ce"haba Ahmad yanzh nine babban baƙon?".Ahmad ya ɗan murmusa sannan ya ce"haba Aliyu ai kai kullum baƙo kake awajen kowa,saboda kamun kanka da riƙe mutunci,yanzu Aliyu duk wanda ya ganka yasan kana buƙatar taimako musamman yadda kake da ƙannai masu yawa,saboda haka dole a tausaya maka".


na ce"dama Ahmad wata shawara nazo nema awajenka"?.


Ahmad ya ce"ba komai faɗi abinda kake son faɗa,a shirye nake da in baka shawarar da ta dace Aliyu don nima kana bani shawarwari kuma idan nayi amfani dasu sai inga sunyi sun zauna raɗau."dariya nayi sannan na fara faɗa masa abinda ya kawo ni ɗin...


sosai ya girgiza da jin abinda Aliyu ya faɗa masa,da sauri Ahmad ya ce"haba haba Aliyu da hankalinka da komai ka aikata haka?yaushe ka fara rashin tsoron Allah...........✍🏻.






*To kowacce shawara Aliyu yake nema?har Ahmad ya tsorata?sai a feji na gaba zakuji yadda aka haihu a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login