Showing 9001 words to 12000 words out of 39216 words

Chapter 4 - ZULFAH Complete Book 1&2 By Oum Maheer Miss Green.txt

Zulfah take sam ba tada jiki ko kaɗan sai dai tana da sura me kyau da duk wanda ya kalleta da idaniyarsa to sai ta burgesa.
ɗan sandan da mukazo tare ya kalleni da wani irin mugun takaici ya ce"uhm daman ance talaka yafi kowa faɗin rai,duk faɗin ran wannan yarinyar ashe aƙwai wanda ya dame ta?ka dubi halinda mahaifinka yake ciki?na tausaya maka na kawo ka wajenta shine zaka dinga magana a daƙile kana wani ciccinyewa?to wallahi a hakanma Allah yayi maka gyaɗar doguwa da ko wajen nan bazaka bari ba kai ma sai ta sanya an garƙame ka,bakasan ƙarfin ikon wannan yarinyar da faɗa ajinta ba"....tun kafin ya ƙarasa na ce"a'uzu billahi minashshaiɗanir rajim,yanzu har aƙwai me ƙarfin ikon daya wuce ubangiji buwayi gagara misali?to wallahi sajan audu ka tuba tun kafin ka riski hukuncin ubangiji,ai ni aganina babu wanda ya kai Allah ƙarfin iko da kuma izza,saboda komai da mukeyi a duniya yake kuma faruwa to ai da ƙarfin ikonsa ne,numfashinmu,lafiyarmu,tafiyarmu,buƙatar abinci,me kuɗi,talaka,duk Allah ne yayimu kai ɗaya sai dai wanda yafi yi masa ibada."
Sajan ya murmusa ya ce"mlm Ali zan dinga zuwa har gida don ɗaukar karatu saboda ƙwanyarka aƙwaita da ilimi".mukasa dariya muka koma office ɗin tamkar babu abinda ya faru,don daman ni ba mutum ne me ruƙo ba sai ka ƙuntatamin yanzu anjima kuma ka sameni a farinciki,sai kayi tunanin raina maka wayo nake kai na sanya ka a baƙinciki ni kuma akasin haka,to wannan ma baiwa ce daga Allah don duk mutumin da ba shida roƙo azuciyarsa to yayi ta godewa Allah don ya bashi baiwa babba.


abin mamaki tun muna hanya aka saki mahaifina,na rungumesa ina shafa bayansa aduniya ina masifar son mahaifina,duk da wata ƙaddara me girma tayi shawagi acikin rayuwarmu baki ɗaya,amman hakan bai hanani jin tausayinsa ba don ko ma menene tabbas shine ya haifeni.







¢¢¢¢¢¢¢¢
*ZULFAH 2*
duk sanda kuka ji ance zulfah 2 to ƴar mahaukaciya nake nufi don itama sunanta Zulfah don gashin tabon sunanta raɗau a hannunta,don ko da take ƴar mahauciya haka ta taso ta samu kanta mahaifiyarta na hauka amman kuma ga sunanta nan a hannunta.


Cigaban labarin Zulfah 2


tunda wannan mummunar ƙaddara ta samu mahaifiyata sai na shiga taka tsantsan da ita,don duk inda zani da ita nake tafiya ayi ta tsokanarmu da jifanmu akan hanya amman hakan baya damuna,don daman nasaba jin makamanciyar ire iren annan wulaƙancin daga jama'a manya da yara.
rannan muka tashi mahaifiyata ba tada lafiya,abinka da wanda ba shida gata sai naje wani chemist na kusa damu na shiga da sallamata.
sanda na shiga ko kallona baiyi ba,ya cigaba da sallamar mutane masu siyayya amman ni shiru,hakan bai dameni ba baj sanya kuma nayi zuciya na tafi ba,don me nema yana tare da samu saboda haka sai na jingina da ƙofar wajen ina ta kallon silin ɗin chemist ɗin,a zahiri sai ka ɗauka silin ɗin nake irgawa,amman ko kusa ba shi nake irgawa ba tunanin rayuwa kawai nake yadda take gwagwarmaya damu,ko su waye ƴan uwan mahaifina da mahaifiyata oho?.ina cikin tunanin ne naji ya ce"to ƴar mahaukaciya!idan kin gama tunanin kya shigo".


da sauri na bishi cikin shagon,ina buɗe kyawawan haƙora na kallon farko zaka gane ni asalin kyakkyawa ce,ƙazanta da rashin kula sune suka yi wa rayuwata babban giɓi,ba wanka har gwara ma wanki wani lokacin idan nayi wankin mota kan hanya anan nake samo kuɗi,sai inyi wata ɗaya banyi wanka ba har gwara ma mahaifiyata ina yi mata wani lokacin,don a hasashe na adacen baya ita mutunce mai matuƙar tsafta saboda yadda take son taji jikinta da wanka tsaf tsaf,saboda haka nake yawan yi mata wanka duk bayan sati.
Bala me chemist ya tsiramin ido sosai,yana kallon zahirin kyau yarinyar don Allah ya yi halittarsa awajen.ganin irin kallon da yake min na fara kuka wiwi tamkar wacce ya daka.
da sauri ya ce"ke me nayi miki da kike kuka"?.a hankali na ce mishi"babu komai Bala,taimako nake son kayi min don Allah mahaifiyata ce ba tada lafiya tun cikin dare,shine nake so ka rantamin magani anjima idan ta samu barci zan fita aiki sai in kawo maka kuɗin".
na faɗi hakan ina kuka sosai kukan tausayin kaina da mahaifiyata.


Bala ya kalleni sosai sannan ya ce"me yake damunta"?.


da sauri na ce"ciwon kai ne da kuma amai".


tunda na fara maganar ya fara rubutu sannan ya ce"kuɗin maganinki dubu ɗaya da ɗari biyar ne".
da sauri na ce"yanzu Bala a ina kake tunanin zan samo kuɗi har haka?sai inyi ƙwana uku ma fa ban haɗa haka ba,kuma da wannan kuɗin muke cin abinci".yana kallona sosai har na gama baice min komai ba bai kuma katseni ba.


juyawa ya yi a hankali ya fara haɗomin magungunan ya miƙomin,sai murna nake yi don na ɗauka ya barmin maganin ne sai naji yana ce wa"zan baki Zulfah amman kuma zan yafe miki kuɗin maganin ma duka amman da sharaɗi ƙwaya ɗaya idan har kin yarda".
da sauri na ce masa"ko menene zan yi maka Bala indai har zaka barmin kuɗin maganin ni kuwa a shirye nake dana yi maka komai".
da sauri naga yana murmushi tun ma kafin in ƙarasa maganata ya ce"to nagode Zulfah yanzu dai kai mata tasha magungunan sannan ki dawo zuwa anjima idan tayi barcin."da sauri na amsa masa da "na gode".yayi ɗan murmushi sanna na fita ina tafiya ina murna,duk wanda ya sanni yasan ina cikin farin ciki sosai ba kamar ɗazu ba dana zo chemist.
ina kai mata na bata tasha,ina kallonta ta ƙwanta a hankali kan ƴar yamutsatsiyar katifar dana tara kuɗi na sayo mana ita,tuni barci ya ɗauketa har da minshari,na zauna kusa da ita ina cikin matsanancin fasin ciki kana ganin fuskata kasan taf take da tsananin farin cikin samun lafiyarta.


sai dana ga barcin ya ɗauketa sannan na tashi a hankali na ɗan karo mata ƙofar kangon namu sannan na wuce wajen Bala,saboda alƙawarin da nayi masa na komawa bayan tayi barci.
Ina zuwa na sameshi ya fesa uban wanka,cikin wata red ɗin shadda taji aiki sai wangalemin bakinsa yake ya bulbula uban turare ɗan misra,daman kuma gidansa kusa da chemist ɗinne.
ina shiga ya ce"yauwa Xulfah har kin iso"?.na faɗaɗa fara'a ta na ce"eh na iso har tayi barcin ma".ya ce to muje daga ciki sai muyi maganar".da sauri na kallesa don tsaf da wayona kusan shekara 19 ace na nida wayo ai nayi asara,saboda haka na ce"a'a Bala duk maganar da zamuyi muyi ta anan ina ganin hakan zaifi mana baki ɗayanmu".
tuni ya haɗe baƙar fuskarsa baice min komai ba kawai sai naga ya rufe chemist ɗin ni kuma ina ciki,da sauri na fara magana har idanuwa na sunyi jawur na tashin hankali na ce"me kake nufi ne Bala?meye makomar hakan daka aikata"?.
Murmushin mugunta naga ya yi sannan ya tunkaroni ya ce"yau burina na wajen shekara biyar zai cika akanki.........✍🏻


MRS GREEN CE.


domin chart dani kai tsaye 07068606171


*_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 SEPTRMBER._*






_1-ƘWAI A BAKA...!!!🥚_
👇🏽
*(Ummu Affan)*




_2-NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA...!!!🫗_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*




_ZULFAH_🍏
👇🏽
*Ummu maher(mrs green)*




_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_


Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽


0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank


Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144


Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽




07068606171


Ƴan Niger zasu turo katin Moov ko Airtel ta wannan number.


08104335144


*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa*
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144
07068606171
08179523215


Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽


2K
sati biyu
3k


idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.






Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
_*Typing🤳🏼*_








_*🍏....ZULFAH....🍏*_






Na
_*®UMMU MAHER(MRS GREEN)*🍀_






*_TEAM🔥GAWURTATTU 🤟🏻3_*




_*AREWABOOK🤳🏼*_
ZULFAH:: https://arewabooks.com/book?id=64ff0277d73b80a18ea59540






*Tallah✍🏻✍🏻✍🏻*
GRP ƊINMU NA
*MU GYARA MATA*
https://chat.whatsapp.com/FZOmqzBp6w5IRfgnxJAt3y


Wannan GRP din mun bud'eshi ne don mufarka mata.
Gyara shine mace💋
Gyara shine ginshik'in mace💃🏼💃🏼💃🏼
*Zamu fara siyar da magunguna ingantattu kuma,Wanda zai dawo miki da martabarki ta y'a mace*


*ina mata masu fama da ciwon sanyi????*
*ina mata masu fama da bushewar gaba????*
*ina mata masu fama da zubewar nono???***
To ga dama ta samu,don kuwa munzo muku da magunguna na kwarai ingantattu,y'an gaske saboda haka yi maza ki antayo kada a barki a baya🖕🏻🖕🏻🖕🏻🖕🏻🖕🏻.


Sai an gwada a Kansan na kwarai........✍🏻


*_Page∆6_*




*ZULFAH 2*


.........da sauri na fara kallonsa kallo kuwa na nuna tsantsar mamakin abinda yake faɗa,mamaki da ruɗun abinda Bala ke faɗamin ya kusa zautar dani na sanya wani irin ihu,saboda kaina ƙiris yake jira ya rabe gida biyu tsabar tashin hankali.


ganin inason tona masa asiri yayi kukan kura ya cafkoni sosai,har muna jin numfashin junanmu ya wankamin marin da sai da yasa naga waɗansu taurari waɗanda sukayi min kama da wuta,sannan ya ciremin yalolon hijabina wanda dashi da babu duk ɗaya ne,saboda tsabar ƙoɗewar da ya yi har kana hango jikina,na sanya haƙorana duka biyu na gantsara masa uban cizo,yaji zafi sosai har yana yarfar da hannu da sauri na wuce don buɗe shagon,sai kawai naji ya janyomin gashina wanda ya sauka har gadon bayana,me shegen tsayi da kuma laushi don ma babu gyara.
ihu nake ina ta neman ɗauki,da alama babu wanda yake jina shi kuwa Allah Allah yake ya samu ya kai inda yake son kaiwar don cikar muradinsa,ni kuwa na sanya hannuwa na rufe jikina,ban tabbatar ina da ƙarfi ba sai dana ga irin artabun da muke sha ni da Bala.
Allah ya taimakeni na hango wani ƙaton ƙarfe me shegen tsayi,ai kuwa banyi wata wata ba na kafta masa akansa,nan da nan wajen ya fara ambaliyar jinj tamkar an buɗe famfo,ni kuwa tsoro da firgici yasa na hango wata ƙofa ta cikin shagon na buɗe da sauri na fito.
da sauri naja baya don ganin wacce take wajen,matar Bala ce da yaranta biyu sai kuka suke daga ita har yaranta,ashe dai shagon nasa ajikin gidansa yake don daman tun ba yau ba nasan matar Bala me suna Hafsat.
da sauri nayi gefe,kunya da kuma nadama suka ziyarce ni alokaci ɗaya tuni na sanya wani irin kuka na durƙushe awajen,kuka nake sosai kuma bani da niyyar dainawa, Hafsat ta sanya hannunta ta ɗagani a hankali sannan ta ce"kiyi haƙuri ki wuce wajen mahaifiyarki duk abinda ya faru a kunnena yake,sannan kuma don Allah ki rufa mana asiri kada ki faɗawa kowa,kuma ina fatan baiyi miki komai ba ko"?.
maganganunta suna isowa kunnawa ba tare dana shirya jin hakan ba na ce"babu abinda ya yimin".ban ƙara ce mata komai ba na wuce zuciyata tamkar zata fito waje,wai me yasa mutane da dama suka ɗauki ɗan adam ba abakin komai ba?kamar yadda Bala ya ɗauki rayuwa da zafi har yana son lalata mata ƴar rayuwarta,rayuwarda babu galihu acikinta?me yasa mutane da dama suke zuwar mata da ire iren waɗannan mugayen halayen na su?ko don sun ganta ba tada galihu ne?abin bai tsaya kanta bama har ya iso kan mahaifiyarta?duk da ba zuwa islamiyya take ba,amman tasha laɓewa ta saurari karatu da wa'azozi kala kala,amman bata taɓa riskar inda akace wannan mummunar ɗabi'ar ta cigaba da yaɗuwa ba.
a haka na ƙarasa wajen mahaifiyata,ina zuwa na same ta a zaune tana ganina tayi saurin tashi da sauri tana kallona sosai,aduk sanda taga na yi dare awaje sai naga damuwa ƙarara acikin ƙwayar idonta,amman bazata iya magana ba sai dai tayi shiru tana kallona cikin tsagwaron damuwa,wato mahaukaci ma yasan ɗansa kenan?.
a hankali na zauna na ƙwanta akan cinyarta,sai kallona take amman babu bakin magana,wannan rashin magana na mahaifiyata ba ƙaramin ɗaga min hankali yake ba,har gani nake ko dai daman can kurma ce?abin yana damuna amman babu wanda zan faɗawa,don babu wanda ya janyoni ajiki balle ma har in faɗa masa.


*BALA*


da sauri ya tashi biyo bayan ruwan da matarsa ta zuba masa,ya ajiye wata irin atishawa tamkar wanda aljanu suka shiga,ya kalli Hafsat wacce haryanzu kuka take,ƴaƴanta ma sai kukan suke daga bisani ya sunkuyar da kansa hannunsa na kansa yana tariyo abubuwanda suka faru.
wani irin mugun ɓacin rai ya ziyarce shi,dayaji bandeji ajikinsa shi dai yake sanyawa mutane bandeji ajikinsu idan sukaji ciwo,ammanfa shi sam baya son yaji shi an sanyq masa ajikinsa,don tun yana yaro ya tsani yaji bandeji ajikinsa rabonda ma yaji ciwon da za a sanya masa bandeji har ya manta.
Hafsat ta fara magana tana kuka sosai.


"wallahi Bala kayi asarae rayuwarka,kuma Allah ba zai taɓa barinka da wannan zaluncin da kaso ka yiwa ƴar mutane ba,azzalumi macuci wanda baisan mutuncin kansa bama ballantana yasan na wasu......"
da sauri ya shaƙo ta ya kawowa bakinta mari sai yaji an riƙo hannunsa,abin mamaki ɗanta ya gani me shekara goma kacal aduniya yana kallonsa yana kuka ya ce"Abba idan ka daki Ummanmu sai na rama mata."bai sake cewa komai ba yaja hannun mahaifiyarsa sukayi ɗaki.suka bar Bala yana kallonsu tamkar zaiyi kuka,ga baƙin cikin abinda Zulfah tayi masa ga baƙin cikin abinda ɗansa ya yi masa.


_*ZULFAH 1*_


Hajiya Innah ta ce"yauwa Zulfah kinga ashe ma yau Bilal zai dawo,to shine Babanki yace muje mu tarosa".bance mata ƙala ba na cigaba da danna wayata don sam bana son ina uzuri ayimin magana musamman ma na waya.ganin bance mata komai ba sai kuwa ta ce"Murash_sha ɗan bani wayarki in nuna mata hoton Bilalu wataƙil ta manta dashi ne".
Ina bidiyo call da wata friend ɗina kawai sai naga hannun Hjy Innah kan wayata wai don inga hoto.
da sauri na cire hannunta kan wayata na cigaba da dannawa,Hjy Innah ta kai maƙura ta ƙwace wayar daga hannuna sannan ta ce"ke wai wacce irin yarinya ce?ba'a isa ayi miki magana ba?".ina kallonta raina yana ƙara ɓaci na buɗe kyawawan laɓɓaina cikin shagwaɓa na ce"to grany me kike son na ce miki?ko dad ɗina da yake da babban matsayi bana zuwa taro sa balle wani Bilal?saboda haka a barni mana,kuje ku kawai ai ina ganin yafi ko"?.
ina faɗar hakan na wuce na karɓe wayata hannun Murash-sha na galla mata wata uwar harara,tayi gefe da sauri tana ce wa"bari in matsa nani na kar zomon ba,nima rataya aka bani".
tuni Hjy Innah ta hau fushi,murashsha kuwa ta dinga ƙel ƙela dariyarta,don tana masifar son ganin faɗan hjy innah da jikarta Zulfah.
Hjy Innah ta ce"oh ni na haifi jika,yarinyar nan gaba dukana zata koma yi maƙiya suyi murna,irin uwarki Murashsha don daman ba sanmu ake ba".
Murashsha tayi mata gwalo ta fice fit.
sosai Murassha ta tsantsara ƙwalliya,don murnar dawowar masoyinta abin sonta dom aduniya tana masifar son Yaya Bilal,sai dai duk kulawar da take bashi shi ko ajikinsa don ba ta ita yake ba,tunowa da hakan da tayi yasa taji tamkar ma kada ta fita don tarosa ɗin,amman tana cikin yin wannan shawarar mahaifiyarta ta shigo,da sauri ta ɓoye damuwarta zata fito sai kuwa ta ce"yauwa ba naga kina wani rawar ƙafa ba,ba gilin gilin ba dai tayi mai saura ki bari a tafi da waccen munafukar,kinga daga nan ke kin zama ƴar kallo sha sha wacce batasan inda ke mata ciwo ba".tana faɗar hakan ta fice,tabi mahaifiyarta da kallo kawai don arayuwarta ta tsani taji wani ya zagi Zulfah abin yana mata ciwo sosai,ta fice don taro masoyinta Bilal ......✍🏻✍🏻




MRS GREEN CE


domin chart dani kai tsaye 07068606171


*_GAWURTATTUN UKU🔥🔥🔥2023 SEPTRMBER._*






_1-ƘWAI A BAKA...!!!🥚_
👇🏽
*(Ummu Affan)*




_2-NA FAƊO DAGA BENE NA ZARCE RIJIYA...!!!🫗_
👇🏽
*Badi'at Mrs bukhari*




_ZULFAH_🍏
👇🏽
*Ummu maher(mrs green)*




_Littafi ɗaya;400_
_Littafi biyu;800_
_Littafi uku;1000_


Ga masu son tura kuɗinsu ta acc sai su tura a wannan acc ɗin👇🏽👇🏽👇🏽👇🏽


0037219728
Fatima Rabiu Sunusi
StanbicIBTC Bank


Sai ka tura da shaidar biyanka ta wannan no ɗin👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144


Masu tura kati kuma sai su turo screenshot na katinsu Mtn ta wannan no ɗin👇🏽




07068606171


Ƴan Niger zasu turo katin Moov ko Airtel ta wannan number.


08104335144


*GA MASU SON A TALLATA MUSU HAJARSU A DUKKANIN SHAFINMU na facebook,whattpad,telegram,youtube,group da status,zamu tallata muku ne akan farashi me rahusa*
10K ne kacal.
Sai ku tuntuɓe a numbobinmu kamar haka👇🏽👇🏽👇🏽


08104335144
07068606171
08179523215


Domin tallata muku hajojinku a cikin littafinmu na sati ɗaya ya kama👇🏽👇🏽👇🏽


2K
sati biyu
3k


idan kuma kanason har mu gama book muna ɗora maka ya kama
10k kacal.






Mun gode da zaɓar gawurtattu uku ako da yaushe.🙏🏼
_*Typing🤳🏼*_








_*🍏....ZULFAH....🍏*_






Na
_*®UMMU MAHER(MRS GREEN)*🍀_






*_TEAM🔥GAWURTATTU 🤟🏻3_*




_*AREWABOOK🤳🏼*_
ZULFAH:: https://arewabooks.com/book?id=64ff0277d73b80a18ea59540






_*Page∆7*_


...........a hankali Bilal ya fara saukowa daga matattakalar benen jirgin,yana farawa da addu'ah da kai ƙarshenta har ya sauko,lallai tsarki ya tabbata ga subhanahu wata'ala ubangijin da yayo mu,domin kuwa Bilal ya haɗa komai na kyau siffar jiki da kuma zati kallon farko zaka hango tsananin kamanin da sukeyi da Zulfah,a kallon farko ma zaka iya cewa yayanta ne wanda suke ciki ɗaya,sai dai kash!ɗan uwanta ne na jini sosai.




kallon familinsa yake yana murmushi mai bayyanar da zallar murna da kuma jin daɗi,murnarsa ke son komawa ciki saboda kuwa sam bai hango mutuniyar tasa ba,wacce yayi dawowar saboda ita don sam bai yarda ya ƙarasa sauran shekara ɗayar da ta rage masa ba acikin jerin gwanon shekara goman da aka ɗibar masa,ya nemi alfarma don a rage masa kuma ya gama course ɗinsa lafiya,sai dai kash!wadda ya dawo saboda ita ɗin da alamu sun nuna bata damu da dawowar tashi ba.
Murashsha ta tsura masa idanuwa sosai,duk motsinsa na kanta ganin ko kallon ƙurar da ta ƙwaso ta baiyi ba, yasa taji wani ƙaton mashi ya daki zuciyarta,da ciwo ace kaso wanda baya sonka son Yaya Bilal ya daɗe yana addabar zuciyarta,duk ɓoyewar da takeyi amman sai da mahaifiyarta ta gano ta,saboda uwa tafi gaban wasa saboda haka yasa mahaifiyarta ƙara tsanar Zulfah,a ganinta saboda Zulfan ne yasa bai son ƴarta don ita ma Murashsha ba baya bace wajen kyau.




tun kafin su gama gaisawa Murashsha ta yi saurin shigewa cikin mota,ta fashe da wani irin wahalallan kuka wanda yasa taji zuciyarta tana mata wani irin zafi,aduk sanda ta tuna irin son da Bilal ya kewa Zulfah sai taji atake ta fara jin haushin Zulfan amman ya zamar mata tilas ta cirewa kanta wannan tunanin,don a gaskiyar magana tana masifar som Zulfah don zata iya cewa tana cikin mutane biyar ɗin farko na rayuwarta,mahaifinta,mahaifiyarta,Innah,Bilal,sai kuma Zulfah.


tana cikin hakanne taji an buɗe motar,da sauri ta goge hawayenta tana murmushi ganin wanda ya shigo ne ya sanya ta ƙara nutsuwa sosai tana jin wani irin mugun farin ciki mai saurin tafiya da mutum,yau itace ga ta ga yayanta Bilal?tabbas yau itace rana ta farko cikin ranakun da ta ajje a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login