Showing 9001 words to 12000 words out of 53080 words
Chapter 4 - Wasa Farin Girki Cigaban Gidan Gandu Complete Hausa Novel By.txt
kwalliyah.
Ita kanta surayyah ganin nayi mata shiru yasa itama ta kama tura saƙonta a wayah,ni hakan ma yafimin da wanann zance nata.
Daddy yana shigowa tun kafin yah zauna na fito daga ɗakim ina haɗe fuska,kallona yayi da alamar damuwa a fuskarsa ganin yanayin dana ke ciki.
"Ƴar daddy mai yasameki haka?"
Kallon mommy nake wanda take zabgamin harara kaman idonta zai fito,hakan bai dameni ba saima ɗauke kaina danayi ina kallon inda mai sona yake wato daddy,
"Daddy inadai wai sameer ne yaƙara aure....."
Ina gama faɗin hakan hawaye ya fara zuba a idona,daman yau kam ai idon cike yake da hawaye.
Cikin razana da kaɗuwa daddy yafara magana ransa a bace,
"Aure kuma,daga aura masa ke kawai sai yahsake aure,ni naga ga mahaifiyarki nan ban sake mata abokiyar zama ba,sai shi ne zai wani yi miki kishiyah da yarintarki kawai dan ya bata miki rai"
Ina jin haka na sake rushewa da wani kukan ina ɗora kaina a kafaɗarsa.
Dan tsabar takaici dayah shaƙi mommy buɗe baki kawai tayi tana zubawa sarautar allah ido,dan kam abin yah fara bata mamaki.
"Kutt yanzu alhaji abinda zaka ce kenan,kana ganin tah baro gidanta ta dawo gida sai tijara takeyi da girmanta ,ba ƴar yayeba harda ƴaƴa biyu,da a ƙauyene ma tah kusa auren ƴarta shine kake wani rarrashinta harda ɗaure mata gindi dan kawai mijinta yah ƙara aure?,toh wallahi bazan yarda da hakanba,yau ɗinnan basai gobeba zata koma ɗakinta,idan kuwa tah kwana a gidannan akan wannan abin,toh kuwa zanyi fushi da itah"
Binta mukayi da kallo nida abban,wanda shima bai ji daɗin mommyn tace ba,saidai babu yanda zayyi tunda ta faɗi hakan toh bazata sanjaba tana nan akan bakanta.
Dadare na fara da kafafuna ina kiran daddyn,ganin hakanne yasashi ɗaga wayah ya ƙira sameer akan yazo yana son ganinsa,nikuma yah lallabani na tafi ɗaki kafin sameer ɗin yah ƙariso.
💎*Sameer a madubin gani*💎
Tun lokacin da saleemah tah bugamin ƙofar ta fitah ina jinta har tashin ƙarar motarta,wanda dama nasan sai hakan tah faru,abu ƙaramima take kaiwa ƙararsa bare kuma al'amari irin wannan.
Baccine ya ɗaukeni na wahala a wajen,dan kaina ji nake kaman zai sare gida biyu.
Sai can wajen magribane naji ƙarar buɗewar ƙofar dakinnawa,farouq ne ya shigo da kayan islamiyyah a jikinsa,kaina yah ɗale da sauri yana dariyah,nima wani sanyi naji yah jiyarci zuciyata,dan rabona da ɗannawa nayi ɗan kwana biyu,muna nan zaune sai kuma na tashi nayi masa wanka kafin najashi muka shiga madafar abinci.
Taliyar yara na yimasa,dan dama kowane yaro yana sonta,da farinciki kuwa yah karba ya nufi falo da gudu.
Nima bin bayansa nayi ina murmushi,sai surutu yakemin maganar bata fitah,wani nagane na bashi amsa wani kuma saidai kawai na kalleshi,*yara manyan gobe*
Waya tace tayi ƙara ina dubawa naga abban saleemah ne,nasan *za'a rina wai an saci zanin mahaukaciyah*
Ɗauka nayi tareda yin sallama cikin girmamawa,cewa yayi na sameshi idan anyi isha a falon sa,amsawa nayi da toh kafin na kashe wayar.
Wajen anty talatu (nanny ɗin farouq)nakaishi bayan yagama cin abincin nikuma na wuce masallaci.
Lokacin dana dawo anyi isha,farouq na dauka a motah muka nufi gidan su saleemah.
A falo nasameshi a zaune,saleemah tana gefensa idonta yayi luhu luhu,na ɗan ji tausayinta a raina amma kuma ta wani bangaren dama inaso tayi hankali,tasan ba kullum ake kwana a gadoba.
Zama nayi akan daddumar da take kasan falon tareda gaishe da alhajin. Dadai lokacinne itama hajiyah Fatima ta shigo fuskarta ɗauke da murmushi,daga gani alhaji Musa bai so shigowar ta ɗakinba saidai baice komaiba.
"Yawwa sameer ina jinka,yarinyah tah daho tana kuka wai tacemim ka ƙara aure,ɗazu ka faɗamata sannan kuma amaryar jibi zata taro,wani abu saleemah tayi maka ne"
"Babu abinda tayimin,sannan abinda tah faɗa gaskiyahne,nayi aure kwana uku da suka wuce,jibi za'a kawota m"
Ina gama faɗan hakan na basu labarin nima jinayi kawai an ɗaura auren bayan an gama ɗaura na ƙannena wanda naje nasu ɗaurin auren.
Jinjina kai alhaji musa yayi kafin yace,
"Yanzu yah ake ciki kenan,gida ɗayah zaka haɗasu?"
"Eh hakan nake da niyyar yi,dan a tsarina banason yin gida biyu gaskiyah"
"Ammma.........."
Hajiyah fatima ce tayi saurin katse alhaji musa daga maganar dayake son yi tace,
"Shikenan sameer munji duk abinda kace,munayi maka fatan alkhairi allah ya tayaka riƙo ya kuma baka ikon yin adalci a tsakaninsu,yanzu kaje ka jira ta,nasaka ta ɗakko zuhrah da kuma jakarta yanzu zata fito ku koma".
Har a raina naji daɗin yanda hajiyah fatima ta taƙaita maganar,dan har raina nake yaba irin halin dattako da sanin yakamata irin na hajiyah fatima,matar ta kwanta min a rai,ganinta nake tamkar mahaifiyata.
A hanyar mu tah dawowa gida kuwa babu wanda yayi wa wani magana tsakanin nida saleemah,dan ko kalllona batayiba,idonta yana kan titi,farouq kuwa yana kulata zata zabga masa harara shima dayaga hakak sai ya cigaba da wasansa a gefe ,ni dariyah ma tabani.
💎*Sameemah a madubin gani*💎
Mutane sai taruwa akeyi ƴan ina da biki,zuwa yanzu kowa yasan alaƙata da sameer,cewa ni ba ƴar inna hajara bace riƙeni tayi,saidai babu wanda yafaɗawa kowa su waye iyayena,kowa idan yagam kwakkwafin yaga bai gano komai na sai ya haƙura.
Ina jinsu suna tah hidimarsu da mutane a cikin gida saidai koh inda nake babu wanda yake zuwa barekuma ayimin tsokana irin tah amare.
Kaman yanda na faɗa nabada ɗinki kuwa haka akayimin,wannan duk hidimar surayyah ce,dan itah kadaice take shigowa ɗakin tah gama yimin tsiyah ta fice,tun da safe burgu yah kawota akan idan aka yini tah kwana washagari a tafi kaiwani da itah,hmmm lallai aure manya,zasu san sun sakani cikin masu aure kuwa.
Riga ce jah ta yadi mai tsada,saidai anyi mata ɗikin buɗaɗɗen wuyah,sai kuma tah matse kunkumi tah zuba a kasa ,lokacin dana faɗamata yanda za'ayi rigar bata so a yi irinta ba,amma yanda na bayar dole haka za'yi ina haka na kuma na fitah da kaina na kai ɗinkin.
~~keee mai taurin kai,koyaushe kina cikin karya mana doka koh,mun ce kinuna ƙin amincewar ki akan aurennana amma kikayi biris da zancen,idan san samune ki kawo mana jinin mijinnaki ana kaiki gidan,sauranki jinin guda uku ki hau kan karagar mulkinki,wanda dama lokaci yake jira,idan kuma kika ƙi aikatawa ............
Bazan aikata ba daman,karku bata lokacinku,koh kasheni zakuyi bazanyi abinda kuke so ba sai abinda nayi niyyah,tsarinku daban nawa na daban,sannan sau nawa nake faɗa muku banason kiran ruhina da kuke batareda ixinina ba zuwa duniyar mafarki,idan har kuka cigaba da aikata hakan,toh zan samo hanyar yin abinda bakwaso kodah kuwa yah zama koni koh ku ne.~~~~~
Tashi nayi daga kan gadon ina kallom rufin ɗakin wanda nagama kwanan na na ƙarshe a cikinsa,tareda tunanin mutanen mafarkinnawa,ruwa na ɗauko a gefena na fara sha saida na shanye shi tass,natsani ƙishirwar dasuke sakani ina ji,wayonsu shine su ɗaɗe dani a duniyar mafarkin har sai na buƙaci shan jini a wajensu idan inaso naji dadai,saidai sun makaro,domin na koyi fitowa daga wajennasu koda suna so koba su so,nasan hakan bai yi musu daɗiba saidan babu yanda zasuyi ne.
Bankoma bacciba sai ƙoƙarin hada canjin wajen aiki da nakeyi,dan burina shine ina zuwa can na nemi aikina na cigaba dayi.
Washagari tun da hantsi motoci guda uku suka tsaya a ƙofar gida,ina jin dirinsu na tuno da motar alhaji bala dana ɗauko,wanda jiyah nasa burgu ya mayar masa kayarsa,dan dama banida niyyar riƙeta din din,saboda bana ra'ayin mallake abinda ba nawaba,dama na taho da itah ne dan yaji haushi.
Wanka na shiga nayi,kowa idan zan wu ce sai bina yake da kallo,kome suke kallo oho.
Saida nagama shiryawa na saka rigar dana bayar akayimin,surayyah ce ta nace sai tayimim kwalliyah,hakanne yasa na barta tayimin amma kuma baƙi yafi yawa a kwalliyar,dan jam bakimma baƙiƙƙirin aka saka hakama gira da kwalli,bataso yamda na bata kwalliyar ba saidai yazatayi dani.
Muna cikin yine saƙo yah taddani cewar baba umaru yana ƙirana,
Abinda ya tsana kenan wannan wa'azinnasu na munafurci,banda munafurci sun san fah mutum ba sajawa zayyi a sakanniba imdai har girmansa bai canja ba,kawai a damu mutum da iyayi kawai.
Lifayar kayan da ɗauka na yane jikina dashi kafin na fito zuwa dakim baba umarun,a zaune yake akam dadduma yana jan carbi,sallama nayi ciki ciki tah dole,shima murmushi kawai yasan dan dole nayi sallamr ba da san raiba.
"Toh sameemah allah ya kawoki lokaci kema zaki ɗakinki kaman sauran ƴan uwanki,ina miki fatan alkhairi allah ya zaunar daku lafiyah ya baku zuri'a dayyaba,ina yimiki nasiha da ki bi mijinki sau da kafa,sannan yi nayi bari na bari,banda musu da kuma tairin kai,dan nasanki sosai,saidai naga kaman kwannan kinyi hankali kaman ba lokacin baya ba,dan haka a zauna lafiyah ........"
Surutunsa yake tayi ina jinsa,da ni mai saurin dariya ce ma dana tuntsure da dariyah,saidai kasshh ba komai bane yake sakani dariyah,yasakani a gaba yama wani surutu kaman ya samu yar shekara biyu,hmmmm.
Tun yana maganar a marmari har yafara gajiyah,rufewa yayi da addu'a,yana ƙara cewa na zauna lafiyah,inna rabice dake gefe take ɗan matse wata ƴar ƙwallah,tabbb lalllai mutanennan nifah suna bani mamaki,tashi nayi ganin innna rabi batada niyyar tashi nayi hanyar fita daga ɗakim ina yiwa baba umaru sallama,toh mezan tsaya nayi bayan yagama surutun.
A hanyah inna rabi ta isoni da ɗan sauri,batacemim komai ba dan itah yamzu abin yah fara daina bata mamaki.
Motar da aka kawo muka nufah,sauran motocin duk an cika su sai wanda zamu shiga nida inna rabi ce tah saurah.
A gidan baya muka zauna ina tsaƙiyarta itah da wata mata,wai naji suna kanwar iyah mai kalwace.
Maganganun da baba umaru yayi minne suke dawowa cikin kwanyah tah.
Me baba yake nufi ma tukunna,ai shikenan nayi hankali saina zauna a gidan sameer lafiyah?
Inaaaa hakan bazai taba yiyuwa ba,waisu nan a barikin sojoji,ai shiyasa aka haɗani dashi ana ganin babu abinda zan iyah,sai kuwa san ya kaini cikin gidansa,dan sai yah gagareshi samun kwanciyar hankali,ballanta kuma matarsa,dama naga rainine da itah,dan haka itah zan fara gyarawa zama tukunna,sai azo ta kan mazauannan gidan,duk wanda ya taboni koh bindiga ce shi ba sojaba saina saita shi.
Natsani zama da wasu,a gida ma zaman dole nakey ,shine harda suka min aure koh,hmmm bazance yasakeni na amma zanyi masa abinda dakansa zai gaji da zama dani.
Lallai basu san wacece sameemah ba,wasan yan zu za'a fara bugawa kawai.
Ina cikin tunani na saƙar zuci bansan lokacin da muka shiga garin porthacourt ba sai gani nayi mun doshi babban barkin sojojin mai kama da gari guda a girma,ko kalle kalle banyiba saboda wanann ba shine karona na farko a ganin barinkin sojojiba,naga wanda suka fi wannan ma girma da komai, sabani sauram mutanen ƴan tafiyar musamman ma wanda dama basu taba zuwa birni kaman hakaba.
Ba laifi yana da girma sosai dan saida muka ɗanyi tafiyah kafin muka zo bangaren gidajen manyan ma'aikatan.
Buɗe murfin motah kowa yayi yah fito yana tah wawware ido dan bawa idonnasa abinci.
Wani sojane ya taho yana wani taƙama da ƙasaitah,uniform ɗinsa na kalla kawai nasan wane muƙami ne dashi.
Murmushi nayi tareda cewa,lallai akwai aiki anan wajen sosai.
Lambar asusu:3131951977
Lambar waya:09035784150
Dan allah karki karanta koh karka karanta baka biyah kuɗin ba,domin akwai hakkina na naira jaka ɗaya(200) a kaknka koh akanki idan baki biyaba kike koh kake karantawa.
💎Sadi-Sakhna________✍🏼💎
*(¯'*•.¸,¤°'✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*'¯)*
💎•°• *WASA FARIN GIRKI* •°•💎 {cigaban gidan gandu}
💎11~12💎
Wuceshi nayi nice ma ta farkon shiga cikin gidan,saboda su sun tsayah ɗari ɗari da kuma bashi amsa,hannu yaɗaga mim akan meyasa na wuce,kallo ɗaya nayi masa dana juya kafin na wuce ciki.
Da sauri inna rabi tah taho ta riƙe hannuna tareda yimin kallon tah gaji da halina,ko a jikina sai ma ɗauke kai danayi.
Babban falone yayimana salllama yasha kayan alatu irinna ƙyalelen duniyah.
Wasu manyan matane masu kama da hajiyoyi a zaune akan kujerun ɗaya bangaren,mukuma muka zauna a wanda suke kallonsu.
Dayake kafin mu shigo inna rabi ta sakamim baƙin ƙyalle a fuskata dan haka bana ganin fuskarsu saidai maganar su kawai,tsinkayo maganar wata daga cikinsu nayi wanda take cike da gadara da kuma isa.
"Toh da farko masu kawowa amarya barkanku da zuwa,saidai ina son sanar daku cewa nan gidan saleemah ne dan ita aka zo aka samu,karkuga cewa wai dan itah tana ƴar uwar miji ta nemi yi mata iko koh gadara,toh hakan bazai faruba,dan itah kanta dukiyar da sameer yake da itah da kuma ɗaukakar da kuka ganshi da itah har kuka laƙaba masa ƴar ku,duk mallakin mahaifin saleema ne,yanzu amarya zata buɗe mana kanta mugani kafin kuma mununa mata ɗakinta,kafin sannan kuma........."
Jin maganar nayi tah isheni haka zuciyata da kunnuwana baza su iyah cigaba da jin irin wannan kalar rainin hankalin.
Saurin yaye alkyabbar nayi ina kallonta ido cikin ido,ganin ɗan razanar da tayi ne tanan kallon lallen dayake hannuna na hotunan ƙwari da majicai na baƙin lalle anyi musu ado da jan lallene yasata zare idanu,su kansu wanda suka taho tareda dani basusan mai yake jikinba sai yanzu,surayyah ce kawai ta sani,ɗauke alkyabbar nayi daga jikina gabaɗaya nayi wurgi da itah a ƙasa,hoton macijin dayake wuyanane yah fito fili,zanen kansa yana kwance akan kinrjina wanda akayiwa ɗinkin mai buɗaɗɗen wuyah.
Tun daga kan kwalliyar da take fuskata da kuma irin nau'ina lallen dayake jikina mutum zai ɗauka daga cikin duniyar ifiritai na bayyano.
Kallon saleema nakeyi wanda tayi suman tsaye,da alamun bata san waye a cikin gyalenba sai yanzu ta tabbatar da wa zatayi zaman wani abu wai shi kishi.
Mayar da kallona nayi kan wacce take feso magana sakkanni kaɗan da suka wuce,ganin kallon bazai isheta bane yasa na matsa har inda take ina ɗora ƙafa ta ɗayah mai tsinin takalmi a kan hannun kujerar da take kai,dan dama ni ban cire takalmina ba daza mu shigo.
Fuskata nakai har wajen fuskarta,dan baifi tazarar yatsa ba na bari a tsalaninmu,ɗaga girar hagun nayi tareda kanne ido ɗaya sannan nace ,
"Ke....mekika ce maimaita naji,bazanyi taƙama da abin gidannan ba?,ke wacecs toh a gidan?da har kika samu ƙwarin gwiwar fadamin hakan,toh bari kiji na faɗamiki,tun daga kan itah matar tasa da kuma shi babu wanda ya isah yah takani,barekuma wani can banzar bazara baƙo a gidannan,itah kanta wacce kikeyiwa wannan aikin wato matar gidam ta fiki sanin wacece ni,ke bakisan komai ba a kaina,dan haka ina jan kunneneki da idan goda wasa watarana kikazo gidannan kikayi zancena ,sai na cire harshe fiyattttt ma kuwa,.............dan haka yanzu zaki iyah nunamin ɗakin dazan zauna ɗinne koh kuma har yanzu baki shiryah faɗan suanan ɗakin ba?"
Tsayawa nayi na bata ɗan lokaci saboda ta samu damar jan numfashin da ta riƙe shi tun ɗazu,ga kuma gumi dayake keto mata,duk da sanyin Ac din ɗakin.
Da hannu ta ɗaga tah nunamin ɗakim da takasa cewa komai da bakinta.
Matsawa nayi daga kanta domin tasamu ta sha iska,murmushi nayi mata tareda miƙe hannuna nayi wata miƙa kaman hannuna zai balle gida biyu,juyawa nayi na kalli mutanen da muka zo dasu wanda suma sukayi tsitt suna bina da ido.
"Kuje su nuna muku ɗakin dazaku zauna dan wancan nawane,kuma bacci zanyi na huta dannagaji,idan kuma wata tazo tah tasheni hmmmm"
Jiyawa nayi nasake kallon matan da suke gefen saleema,
"Sauran kuma na tashi naji kun cigaba da watsawa wanda muka zo tare magana,wallahi ko mai gidan bai isa kwatarku a hukuncina ba,zai fi mukuma na tashi na samu kun bar gudan"
Saida na zare ido tareda haɗe fuska kafin na faɗi hakan,har na fara tafiyah na juyo na kalli surayyah wanda itama mamakinnawa takeyi,duk da tasan hakan kadanne daga halina.
"Ke kuma zo mutafi dakinnawa akwai abinda zan faɗamiki"
Da sauri tah tashi zata biyoni,inna rabi tagumi kawai tayi,ba ko gigin biyoni ba,dan yamzu itama tasan halina.
Muna shiga ta maida ƙofar ɗakin tareda cewa,
"Yanzu anty sameemah me kikayi haka kenan?ƴan uwan ogan mijinki ne fah,amma kika yi musu haka daga zuwamki"
"Toh yan uwansa ƴan uwanane,kema ba surutu na ƙiraki kiyimin na,yanzu dai ciro mun kaya a cikin wajen kayannan tukunna,sannan idan kin ciro ki je ki dubamin matannan,duk abinda suakyi kizo ki fadamin,dan ba yarda dasu nayiba,ƴan tuƙa tuƙa kawai"
Surayyan ta buɗe baki zata sake cewa wani abu nayi saurin shigewa banɗakin.
Dan banson yawan surutun yanzu,ina jin dariyarta a ɗakin har kuma tayi shiru.
Cika bahon wanka nayi na shiga na kwanta,gaskiyah nayi kewar ƙasar palastine dan rabona da danayi wanka na cikin baho tun ina can.
Saida na kusa awa guda kafin na fito daga bandakim,shima ina fitowa na samu surayyah ta fitomin da kayan,dan haka ina sakawa nabi lafiyar gado.
Bangaren masu aikin gidan aka kaisu dan shima wajene mai zaman kansa,sun mafi sakewa a canɗin akan dakina,dan wallahi babu da matar da zan kwana tunda bani na gayyatosu ba ai.
💎*sameer a madubin gani*💎
Tun dazu nake zaune ina aiki amma nagaza tabuka wani abin kirki,daga na fara tubutun da shigar bayanai sai na ajiye,ni kadai na jera tsuka tafi cikin kwando ina zaune.
Na rasa ma abin da yake min daɗi,ni kaɗai nasan irin ƙalubalen dana ke shirin fuskanta na rayuwa da sameemah a cikin gida guda,kirjina sai bugawa yake yi lokaci bayan lokaci.
Ga saleema tun lokacin dana daukota daga gidansu tah daina yimin magana,ko na kulata ma saidai ta bar wajen,abin duniyah duk yah isheni.
Sallama akayi tareda bugo ƙofar office ɗinnawa,ina ɗaga kai mukayi arba da Ahmad babban abokina wanda tare muka yi karatu da kuma tafiyah service a Russia.
Miƙomin hannu yayi muka tafa kafin yace,haba mutumina kana ango wanda za'a kawo masa amaryah yau amma kuma kake aiki,wai yama naganka da damuwa a fuskarka,kamata yayi yau ka yini cikin fatin ciki ai"
Hmmmm kawai nace,dannasan idan nayi masa magana ma bazai fahimta na sam,dan haka babu ma wani zancen tsayawa bata lokaci akan maganar.
Wasu abokan aikimmune suka sake shigowa,sai tsiyah suke min,dole babu yanda zanyi na ajiye aikin tareda ta fiya gida.
Gidan su Ahmad muka wuce,dan shine zai auri suhaila ƙawar saleema watan jibi.
A dakinnasa yada zango,akan zasu rakani zuwa dare,saboda nace bazan yi komaiba dan haka dole suka ƙyakeni tunda basu san dalilina ba na ƙin yin komai ɗin.
Wajen ƙarfe goma na dare muka shigo cikin gannawa kowa a cikin motarsa,nidai binsu kawai nake duk abinda suka ce,dan karsu gane halin da ake ciki.
Falon babu kowa kaman ba bu mutane a gidan,ɗakin saleemah muka fara nufa wanda yake bangaren dama yana kallon wanda sameema take ciki.
Nufar ɗakin saleema muka farayi tukunna amma ƙofar ta ƙi buɗuwa tah kulleta,ɗan jimm nayi kaman mai tunani kafin na koma inda su ahmad suke,ɗan yaƙe nayi wanda yah fi kowa ciwo.
"Ina ga tayi bacci kaman"
Ɗaga kai sukayi alamar sun fahimta duk da basu yarda da abinda nace ba,ƙarbar ledar dayake hannun ahmad nayi ina yi musu murmushi.
Fatan alkhairi