Showing 12001 words to 15000 words out of 74994 words
Chapter 5 - MATAR OGA NA COMPLETE DOCUMENT writing by UMMY AYSHA.txt
ita, Da tsaronta da kyau zaka samu lada .
Keeeyyyyyyyyy motar ta kwacema jameell sukai taga taga suka daki wata katuwar..
*Nace ba*
*Kina nan zaune kin buga tagumi kina tinanin taya zaki samu so da kulawa daga mai gida ko kuka kike kullum*
*To maza garzayo ki kwashi naki rabon cikin ikon Allah*
*Ba tallah ba daɗin baki zahiri ne anan* .
*Farko dai ni macace yar uwarku mai kishin ku,Matsala da dama mu mata muna fuskantar ta agidan auran mu,Duba da Irin yanda zamani ya lalace maza suna daukar matayen su tamkar bayi*.
*Kar in cikaku da sututu*.
Kisa tsoron Allah a lamarinki kiyi Addu'a sosai ki kai kukanki ga Allah kamin kifara amfani da Humrah sirri tah,in sha Allah in mijinki kanshi yakai kwakwa tauri sai kinga yanda zai sakko da makaman yakinsa ya baki kulawa da tarairaya in sha Allah kedai mallaki kayan mu na gyaran aure kisha mamaki da izinin Allah*
1Humrah sirri.
2Kwalaccam
3Turaran gaɓa 14
4Sahihin maganin mata da zayyi tsawon wata ɗaya jikin ki
5Maganin matsi mai balain kyau da zai rikita mai gida kuma wallahi azeem babu Haufi akansa kana baya saka kowane matsala cikin ikon Allah, na yarda da kayan aikina dan saina gwada zan baku.
6 Akwai sabulun kama ruwa da zai kawar miki da warin gaba,Ya matse ki,Zai tsayar da farin ruwa ,Ya miki maganin sanyi Dan zatin Allah,in baki shiryaba kibar kirana kana ina sake faɗa akwai tsada kunson abu mai kyau shike sayar da kanshi.
In kuma kayan kamshi kukeso na ɗaki mai sanyaya rai da zuciya gami da saukar da natsuwa ku kirayi UMSAD INCENSE
08028827241
❤️ *MATAR OGA NA* ❤️
*MALLAKI*
❤️ *UMMY AYSHA* ❤️
PAGE 7️⃣
Sukai taga taga suka kusan kaima wata katuwar bishiya duka kamin suka tsaya cak.
Ihu sosai Alh Adnan ke kurmawa dan ya hango mutuwa Rara ainin.
Jameel kau Hawayen dayake ɓoyewa ne suka sakkomai yasanya hannu ya share tare da kwantar da kanshi akan sitiyarin motar ya lumshe ido wasu na sake sakkomai, Lallai Alh Adnan mugune kuma akwai manufa akansa sannan bayason Aymah ko kaɗan, Tinda har yake zarginta. A ƙa'ida sharia kuma dama zargi ga aure ma ɓata auran yake baki ɗaya to miye Ribar wannan Auran miye kuma hukuncin sa.
Alh adnan .
Buɗe marfin yayi ya fito hankali tashe yana kallon jameel ɗin daya rufe ido.
"Kai Jameelu mutuwa kai ko buguwa kayi? ya karasa yana jijjigashi.
*Jameel*
A'hankali ya buɗe jajayen idanuwan shi ya sauke su akan bak'ar fuskar shi,kamin dakyal yana control din bakin sa yace. ciki na kemun ciwo".
*Adnan*
Kirji ya dafe yace "wai Allah nah jamilu har hankalina ya tashi! kai kayi sanadin mutuwata yanzu ai ba abinda zancemai saidai in'ce Allah ya tsinema albarka kaida iyayen ka,dan wlh yanzu nikejin daɗin duniyar nan, kana yanzu nike bukatar kara bunkasa dukiyata saboda baka daraja awajen kowa sai kana da kudin nan.
Jameel
Kai wallahi a irin yanda Jameel yaji a wannan lokacin jiyayi kamar ya shake shi zagin dayama iyayen shi har sai ya wulla shi lahira kamin ya barshi, Amma dayake akwai manufa akanshi sai baice komiba sai gyara zamanshi da yayi Yanajin sauyawar yanayin sa.
Alh Adnan.
Zaka iya kaimu gida koko? Ya tambayi Jameel.
Zan iya yace yana kallon katuwar bishiyar da barabon su daketa dan ba karamin bugawa zuciyar shi tayi ba da jin wannan mugun furucin Dayama iyalin sa.
Shiga yayi ya tuka suka tafi gida kai tsaye,bayan sun tsaya yace mai gobe zan koma bakin aikina dan banga amfanin zaman da zanba anan kwara in koma cen wajen yarana.
Allah ya kaimu yace yanayin ƙasa da kanshi.
Ameen Alh Adnan yace tare da fadin ko akwai wata magana ne?
Jamil ya sosa kai yace A'a?.
Tsayuwa ya gyara yace .
Kai jameel na yarda dakai kaji , saboda baka son raini shiyasa naji ka zama nawa fadaman duk abinda kake so .
Jameel yace ranka ya dade dama abinda zancema anan shine.
"Why not ka saki matar nan taka A ɓoye da Allah ya kamaka gobe kiyama da laifin ta,In yaso sai ka bani ajiyarta in killacema ita nida masu gadin nan naka,Bazatama taɓa sani ba balle ta samu hujja,Dama ba wata alaka ke tsakanin kuba balle abin ya zamana akwai kuskure, ko kuyi zaman da bai halattaba,In yaso sai kayi nesa da ita gabaki daya a rayuwar ka ,In lokacin bukatar ta ya tashi kazo ka dauketa tama rakiya tinda kace sama saboda Aikin ka ko ba haka ba?.
Adnan
"Haba jameel sai kace ƙaramin yaro da zakabani wannan shawarar ai som batai ba,Ai bana da wani hop da ya wuce ace igiyoyin auran ta na hannuna ,kaga ba ubanda ya isa ya rabani da abata abadan da iman,Amma yanzu nace in'baka naci uban gwari kenan .
Rai ɓace kuma a fusace jameel yace to ka sauke nawinta da Allah ya baka mana ya karasa cikin suɓutar baki.
Yimin shiru Jameel! zan ya koran ka wallahi ka sake shiga hurumina, ban baka fuska ba dan ka datsaman maganar da kakeso , Zan iya ɓatar dakai a doran kasar nan baki daya saboda ka fara sanin sirrina Da matata , Abinda naima Aymah bai zamema darasi ba ita da take matata,,Ban'faɗama maganaba dan ka rainani duk karsashin ka na fika,Kadai gani sanin sirrinane da tayi yasa na bata wannan dokokin da kwace duk Abinda yasata iya gayaman magana,Balle kai banza bazara dabaka tara 3k ta kanka ba ka kiyaye ko bakaji.
Naji jameel yace kanshi kasa zuciyar shi na suya amma tabbas saiya son yanda yayi yasanya ya saketa shikum daga lokacin zai fara nashi aikin,Kana duk abinda yamai zai rama, Dan wannan cin mutunci kesawa ko alaka da mutane bayayi saboda kar ayi La'akari da talaucin sa a kawomai raini.
Har ya juya zai shiga ciki kuma ya dawo yace na fasama tafiyar sai na cika lokacin dana diba,Anjima zan nemeka ka tsaya cen ya nunamai bayan part din Aymah.
Ohk Jameel yace yana juyawa yayi tafiyan shi.
Aymah kau tin sadda taji tashin motar sa ta tashi tayi wanka ta shirya tsab dan saita nunamai bai isa ya zauna da itaba , Daga nan office din kawar ta zata barrister Halima Garkuwa, ta shigar da kara dan dole court ta raba auran nan nasu bazata iyaba dan tana da hujjojin da zasu zame mata sheda.
Bayan ta kammala komi ta fara neman key din motar ta amma bata gani ba, Duk inda take sany rai babu A'hankali ta fara binciken wani a locar da take aje kayanta masu mahimmacin ci amma babu komi nata, Duk wani kuɗi ko takaddun kaddarata babu komi.
Kanta ta dafe cikin tashin hankali tana tinanin wayamata wannan illar.
Adnan".
Tabbas shine zai mata haka, A'Hankali ta fara nazarin yanda ta kamashi yanason daukemata waya, ,Sassanya murmushi ta saki tace kai suka shama kai,Kwashemun komi dakai bazai daukeni ya ɗaɗa da ƙasa ba dan na tsani dukiya saboda farin cikin mai itane kawai, Auran miji mai dukiya bashi da amfani ,Balle irin Adnan mai bala'in son kai,kwara ka auri wanda keda rufin asiri kutaru ku rufama juna asiri , kuma ya baka lokacin sa.
Mikewa tayi ta fita palo ta zauna dan ko girkin ma ta fasa dan ta riga ta fidda Adnan a ranta a matsayin miji.
Tana zaune suka dawo har sadda ya shigo suka hada ido ta kawar da nata shima ya ɗauke kanshi ya wuce kamin ya waiwayota yace .
A sama mun abinda zanci bai tsaya jintaba ya wuce war shi.
Murmushi tayi tana raka bayan shi da kallo.
Tsawon awa ɗaya kamin ya fito da computer shi a hannu da medical glass din sa yana sanye da jallabiya ya zauna ya fara aiki kamin yace.
Ɗan kawomin abincin ki haɗoman da lemu mai sanyi.
Mikewa tayi ta shiga kiching ta debo danyar shinkafa ta sanya a kula da tattasai da nama ta hadomai ta kawomi ta aje gaban shi tare da hakimce wa gefe.
Kallonta yayi kamar zai magana sai kuma ya fasa ya ajiye komi dan bala'in yunwa yakeji ya sakko ya fara bubbuɗewa .
Sosai hankalin shi ya tashi ranshi ya baci ya dakamata tsawa da fadin miye haka?
Banza tamai ya dinga magana ta kyaleshi kamin a fusace ya mike yayi kanta ta zaro karamar wukar da ke hannuta tace kana matsowa wallahi saina kasheka,Dan nidama ka riga ka kasheni kwara in kare rayuwata a gidan yari da wannan tsinannan gidan naka mai cike da bakin ciki da duhun jahilci.
Cak ya tsaya kamin ya koma ya zauna idon shi akan ta yana kuma hango gaskiyar abinda ta fad'a yace.
" Aymah zaki iya kashe mutum?.
"Aymah
Har abada, in'sha Allah Aymah bazata taɓa iya kashe mutum ba,in'kaga nayi kisa to dabbace mai haɗari itama zan kashe tane dan kare kaina daga cutar war'ta.
Adnan
Subhanallahi kina nufin ni a sahun dabbobo kika ajeni? mijin kine fa!.
Aymah
Adnan da girman Allah zan zagi ubanka ka sake kiran kanka da sunan mijina,Mijina na nan zuwa kwana kusa da ikon Allah.
Tsalle ɗaya ya buga ya kwasheta da mari tare da murɗe hannunta ya anshe wukar ya sake saukemata wani dai-dai lokacin da Baraka ta turo kofar tashigo,Ganin ta ko alama bai sanya Ya saurarama Aymah ba ya dinga kwallo da ita cikin palon nan kamar ya samu jaka.
Sosai Baraka ke kuka tana salati tanaso ta shiga tsakanin su amma yaki bata dama dan gabaki daya baya hayyacin sa.
Gigitatta tsawa ya dakamata data sata komawa gefe ta zube tana kuka Aymah kau duk uban dukan da yakemata, da jagwalgwala ta da yake zuciyarta ta ke k'ashe babu alamar hawaye a tattare da ita, Dan burin ta yayi ajalinta kawai ko ta huta da bakin cikin zaman da suke.
Ganin ya fita hayyacin sa yana dukanta kamar ya samu tsarar sa yasa Baraka watsawa da gudu ,Acen ƙarshen get din taga jameel zaune yayi shuru dan da gaske cikin shi ke ciwo bana wasa ba .
Wannan yaron zo zai kasheta tace cikin kuka.
Ido ya dan zaro yana kallon ta ta bugamai tsawa.
Aguje ya bita su duka suka afka dakin dai-dai lokacin daya sanya katon hannun shi zai kaima Aymah duka a ciki Jameel ya shiga tsakani ya kaimai wannan uban naushin daya sanya gabaki daya duniyar ta juyama Jameel din , Dan gabaki daya guntun ciwon da yakeji saida ya zame mai kamar na mai Naƙuda,Duk da yakai shi kasa amma iya kokarin sa yi yake dan kare Aymah daga wannan mugun dukan da ake saukemata.
Aymah kau tinda taga uban naushin daya sakar ma Jameel tayi tsaye cek bata sake gusawaba illah ido data zubamai yana duke rike da Cikin shi da hannusa na dama ɗayan kuma yanata kawomata waigi dan kar a sameta.
Cikin ihu tace.
Adnan kamasa raunifa
Cak shima Adnan ɗin da zai sake wanketa da mari ya tsaya yana kallon Jameel dafe cikin Sa sosai da duka hannuwa biyu, idon shi a kasa bakin shi kuma na digar da jini kaɗan kaɗan.
Jamilu!
Yace da ƙarfi yana tallabo shi.
Baraka kau kuka take sosai tare da kawar da kanta gefe dan tason sun ɓallomasu ruwa, Dan Jamil nada matsala sosai wadda suke Addu'a magancewarta da kuma neman budin Allah Dan su samu amasa aikin da zai samu lfy Amma kudin da yawa ga kuma yanayi.
Aymah kau kuka ta fasa tana fadin shikenn Adnan ka kashemin shi wallahi , Dan Allah waye shi dan waye? Adnan zan yafema komi bazan yafema kashemin shi da kayiba har abada, Wallahi sai na ƙarar da kaf abinda na malllaka domin kwatar masa hakkin Sa saboda inaji ajika yana da mahimman ci a Rayuwata,.
Adnan ya dakamata tsawa dan yayi tinanin zagin sa take dan som baiji kalma ɗaya acikin maganar taba da yake cikin kuka take magana kuma A hankali amma jameel kau dake cikin yanayi gabaki daya yaji kalamata kuma sunyi tasiri a A zuciyar sa,dan duk azabar da yakeji saida yaji tsaigar jikinsa na tashi sosai .
Kiyi wani abu akai man Adnan yace da ƙarfi ganin har lokacin Jameel din ya kasa koda motsawa.
Bazan iyaba muje mukaishi Asibiti tace cikin rauni tana share hawaye.
Gabaki daya dokar daya samata ya manta Ya ɗaukai ya sashi mota Suka bar Baraka data lafe gefe tana share hawaye Dayi masa Addu'ar samuwar lfy..
Kai tsaye FMC suka nufa Emergency.
Cikin gaggawa aka kwashe shi akayi dakin bada agajin gaggawa dashi.
Kimanin 30mnt wani Basamuden likita ya fito yana share gumi yace.
" gaskiya haniyar nan tasa tana neman fashemasa kuma hakan Babban illace ga lfiyar sa, Dan haka dole ake bukatar manyan kuɗaɗe dan ceto rayuwar sa, Dan ina tabbatar maku da cewa yanzu ko tsayuwa bazai sakeyiba muddum ba a tallafamasa anyi aiki yau zuwa gobe ba...
Nawa ne kudin? AYMAH ta tambaya.
Yace 90k ne.
Aymah da duk fuskar ta ke a kumbure ta kalli Adnan daya juya baya yana tsuke fuska Tinda yaji batun kudi tace.
" kaga abinda ka jawo ko,saika biyasu amishi tinda kaine sanadi.
Bazan biya ba yace cikin bacin rai ,Ni na haifesa,aikin da yakemun kyauta ne ba kudi zanbashi ba,ina kudin da akeba uwar shi da uban shi da bazasu biya ba.
Cikin mamaki ta kalleshi tarr da cewa" ɗan waye.
Kafada ya daga yace dan mai aikin kine da mai gadinki.
Ido ta zaro kamin tace kana nufin ɗan Baraka ne,shine tana gani bata biyomu ba?.
Afusace yace to Tinda munafukace ta ɗauke ni katon banza ai dole ta barmu da wahala, Wallahi biyar bazan badaba,wuce mutafi gida ki sanar da uwar shi tazo ta kama yaronta sutafi gida suyi na wanzamai, ai nima ina da yaran ko..
Kuka tasa tace Adnan kaji tsoron Allah, Ɗa na kowane fa sannan duk wanda yaji tausayin dan wani shima za'aji tausayin nashi, ka taimaka Dan Allah da manzon sa.
Ke dakata a ina kika haihu balle tausayin Ɗa da uwa ya shiga ranki? ko dai kina da manufa akansa ne bansani ba, dama kin saba kwalkwale yaron mutane ido na samiki .
Allah ya tsareni ya kareni, yakuma karemun mutuncina data abinda zan haifa nan gaba, Adnan bazan taba yafema sharrin da kakemun ba kuma in sha Allah zakagani akan abinda ka haifa.
Mari ya kawomata likitan dake tsaye yana kallon su ya rikemai hannu tare da faɗin.
" Haba Yallaɓai! macace fa , Dan Allah adaina saurin kai hannu ,zaya iya samun matsala kuma kaima Hakan zai zamema hadari mai girma nan gaba,Ko yanzu ka dubi fatar fuskar ta jibi kwanciyar jini idonta wanda ina da tabbacin mari ne.
Tsaki yayi yana faɗin ta wuce sutafi.
Bazanje ko inaba Adnan,Nice sanadin faruwar ciwon sa dan haka zan tsaya kai da fata naga na sauke nawin sa daya rataya kaina.
Dariya ya fashe da ita kamin cikin shammata ya fizge wayarta yace.
" wallahi duk hanyar jin dadin ki saina lalata,Badai dani kike fito na fito ba,To bazan bayar ba , haka kena bazaki bayar ba ,wuce muje wayanda suka haifesa suzo suyi jinyar kayan su.
Cikin rauni na ya mace ta durkusa har kasa tana mai hade hannayenta duka biyun waje daya tace'' Adnan! ,Dan girman Allah da manzon sa,Dan son da kakema annabi muhammad SAW kayi hakuri nabi Allah nabika,nakuma yarda da duk ƙudirinka,Kana nagama fito na fito dakai,sannan zan zauna a gidan ka har karshen rayuwata,amma kabani dama,ka kuma bani dukiyata,in bama yaron nan Amasa aiki,Bakason sharrin Ciwon nan nasaba ne, ya fashe A cikin sa zayyi sanadin lalacewar lfyr sa ta ɗa namiji.
Tsaki yayi yace aikin kenan kwartuwa,Da anyi abu namiji, lfiyar namiji mtssa.
Hawayen bakin ciki da tsanar shi ta share ta durkusa har kasa tace.
Ka bani duk umarnin da kakeso nayi Alkawarin yima koma miye.
Dariya ya saki yana samun wani ɗan sit ya zauna yace na yarda! sharaɗiin farko .
Kinyi Alkawari zakici gaba da zama dani a haka bisa umarnin dana baki.
Kuma bazaki sake magana na kusance ki ba.
Kana duk abinda nace zakibishi koko..
Kana miye tukuicina in'har na baki kudin ki kika bayar akamasa aiki?
Adnan na yarda ka bani kuɗin aikin sa,In yaso kaf dukiyar tawa ka rike nabarmaka ita halak malak, ko awajen Allah baka da laifi wallahi azeem na barma,Asibitina ma na baka takaddun ma acanzasu zuwa naka,Amma dai kabani abinda zan ceto ran sa...
Kallon ta yayi kallo mai cike da ma'anoni kamin yace da gaske?
Yess da gaske nake ta fada hawaye na zubomata.
Dr dake tsaye gefe yana latsa waya ya juyo yana kallon ikon Allah.
Adnan ya kalle shi yana faɗin bani pen da byro.
Bashi yayi yana ganin tsantsar Jahilcin Adnan amma baice komi ba.
Adnan yace in dai har hakane na amince.
Sannan daga nan zamuwuce dake kisanya hannuwa.
Da sauri ta daga kai Yayi wani dan rubutu ya tura aljihu tare da zaro Wayar shi yace ma Dr ya bashi Account number sa ?
Turasu inda zasu biya Yayi tare da zamun waje ya zauna ya zubama waje ɗaya ido.
Cikin lokaci akai komi aka gama da niyyar da Asuba zasu shiga dashi aiki.
Waji irin walwala da farin cikine ke bayyane a fuskar Aymah,cen ita dama mai taimakoce amma tafi samun farin ciki a yanzu data Taimaki Jameel.
Tafiya sukai likitan nan ya bisu da kallo zuciyar sa fal da tausayin Aymah,,ya lura ita kanta ba lfy ne da itaba dan layi kawai take , Amma baiga ta nemi ko paracitimol ba saima sadaukar da abinta da tayi akan wanda sukaji ance dan mai aiki da mai gadine, lallai ya Jinjinama ta kuma yanason yason wace ita waye Jameel waye Adnan. .
Adnan kau suna cikin tafiya zuciyar sa fal farin ciki ya dauki hanyar janbulo,kai tsaye gidan manager bank ɗin nan suka nufa, dakyal da taimakon Allah dana waya ya gano wannan gida.
Bayan yaje ya kirashi ya fito ya tarbesu.
Anan Adnan ke labartamai duk abinda ya faru Suka dinga dariya Aymah na kallon su kallo mai cike da ma'anoni.
Mutumin yace to Hajiyar taimako sai azo a rantama muna hannu ko Anan . Ya karasa yana mata kallon sama da kasa tare da bata wasu takaddu.
Murmushi tayi ta mike ta fara duba takaddun tare da kallon Alh Adnan da ke gefe yana murmushi kamin ta kalli manager ya dakamata tsawa yana fadin rantaɓamun ki bani.
Ajiyar zuciya ta sauke ta sanya hannu duk inda aka gwadamata, gabaki daya ta mayar dasu na Adnan din ,Kudin dake account dinta duka aka mayar dasu account din Manager dan yana nan kanbakan sa bazai hada dukiyarta data shiba wayan nan wata masana'anta zai samu mai mahimmanci ya gina.
Saida suka gama komi kamin ya jata suka