Showing 30001 words to 33000 words out of 45829 words
Chapter 11 - Amaryar Zayyad Complete Book By Rahma Kabir.txt
ya rufe ba ya zo ya zauna yana cewa.
Madam Zainab barka da safiya, amma lafiya na ganki wani iri.?
Safna ta miƙe ta isa gareshi fuska kwaɓa kwaɓa kamar zata fashe da kuka ta zauna a cinyarsa tana dubansa.
Sirrina kunnena ke mini ciwo duka biyun, na hagun nan ma ya toshe bana ji sosai da shi.
Ta ƙare maganar hawaye yana sauka a kuncinta, Zayyad y tallafo fuskarta da duka hannunsa cike sa tsantsar kulawa.
Subhanallahi ciwon kunne kuma, sannu ƙaunata Allah ya ƙara sauki. Ina ganin ki shirya yanzu mu fita tare inna sauke yara a makaranta sai mu wuce asibiti likita ya duba ki dan abinda ya shafi kai ba a wasa da shi.
Ya ƙare maganar yana manna mata kiss a leɓenta tare da share mata hawayen da hannu. A lokacin ne Ilham ta turo ƙofar ta shigo kamar an korota ba ko sallama, cikin tsawa Zayyad ya dakatar da hanzarinta.
Wannan wani irin shashanci ne zaki faɗo ba sallama.
Mamanmu ce tace in kiraka mun shirya.
Ai nasan kun shirya wuce ki bani guri, kuma ki ƙara shigowa ba tare da sallama an baki izinin shigowa ba, sai na gauraya ni da ke.
Ilham ta fice da sauri tana turo baki dan bata son ayi mata faɗa, Safna tace cikin sanyi.
Da ka yi mata haƙuri, kasan yara in sun shirya zuwa makaranta nan hankalinsu yake tafiya.
Hmmm Ƙaunata kenan, nafa tuna malamar makaranta ce ke, ya kamata ki ware lokaci kina yiwa yaran nan lesson a gida.
Sai ka sanar dasu tare da mahaifiyarsu su sani, dan ni ko wani lokaci suka zo banda damuwa.
Godiya muke Amaryar Zayyad, yanzu jeki shirya da sauri Allah yasa ma kin karya.
Bana jin yunwa sai mun dawo na samawa kaina abinda zanci.
Shiyasa naganki ba kuzari ai, da yanzu zance mu shiga daga ciki ba zaki taɓuka komai ba.
Waye ya gaya maka? ai kasan bana taɓa yarda ka ƙure mini gudu sai dai mu jera, kuma ko a yanzu zaka sha mamakin karatun da zan biya maka.
Safna ta faɗa tana 'yar dariya ta nufi ɗaki zata shiga, Zayyad ya yi dariya shima.
Iye lallai na auri daidai ni, Ko dai zamu gwada ne mu ga waye gwarzo a yanzu.
Ban yarda ba.
Ta faɗa tana shigewa ɗaki, Zayyad ya saki murmushi yana girgiza kai wato Safna ce daidai shi in dai a wajen sakin layi ne tana bashi haɗin kai yadda ya kamata, hakan kuma yana sawa tana ƙara samun gurbi a zuciyarsa, duk wani hanya da salo na kula da miji tana ƙoƙarin yi, wanda da ace ita ya aura tun farko baya jin zai iya ƙara aure sai dai in yana cikin ƙaddararsa, duk da bata gama gwanancewa a harkar gado ba amma tana iya ƙoƙarinta ganin ta faranta masa, abin burgewa duk yadda yazo mata da salon kwanciya tana jure masa ba tare da ƙorafi ko raki ba, saɓanin Rashida da komai nata bata mayar da shi mai muhimmanci, ya rasa wani iri tunani Allah ya ɗaura mata, ita baga girki ba baga shimfiɗa ba komai nata ci baya ne, ga rashin iya magana da rashin kunya dan sosai ta raina shi, ya tabbatar tarbiyyar Safna da bambanci da Rashida, hakan yasa Safna ta soma samun babban gurbi a zuciyarsa sama da Rashida. duk da yana sonta amma Safna ta fara cin galaba a zuciyarsa da babban matsayi.
Safna bata tsaya ɓata lokaci ba ta saka doguwar riga baƙa da aikin farin duwatsu, ta saka hijab har ƙasa kana ta ɗauki glass ɗinta ta saka wanda ya ɗan cika mata fuska, ba kwalliya a fuskarta amma tayi kyau Masha Allah, ta saka turare mai sauƙin ƙamshi a jikin kayanta ta fito riƙe da waya, Zayyad ya kura mata ido har ta ƙaraso tana cewa.
Na shirya mu tafi.
Zuwa asibiti har da tabarau matar Zayyad, anya kuwa zan yarda da wannan mugun wasan, salon wani ya gama kalle mini ke gaki dai ba kwalliya amma kinyi kyau sosai, gaskiya kin san sirrin ado yarinyar nan.
Matar nan dai zaka ce, kuma ina cikin mota waye zai ganni? kasan tun ina gida ina ƙaunar tabarau dan Allah karka hanani sawa.
Ta ƙare maganar cike da shagwaɓa, banko ƙofar da aka yi yasa duk suka juya, ita dai Safna sai da gabanta ya faɗi, Rashida suka gani a tsaye fuska a ɗaure tana dubansu.
Zayyad amma abinda kake yi kana kyautawa, yara sun shirya zasu tafi makaranta kazo nan ka shagala, idan ban shiryasu da wuri ba kayi ta faɗa da mita, amma gashi kusan minti nawa ka ɓata anan, ke kuma saboda baki san zafin haihuwa ba balle kisan darajar karatun yaran shiyasa kika tare shi saboda mugunta da son kai, ki cigaba da abinda kike yi.
Tana gama faɗar haka ta juya ta wuce kamar guguwa, Zayyad da Safna suka kalli juna.
Mu tafi kuma bana so ranki ya ɓaci akan maganganunta.
Haba Ruhi bakomai, nasan rashin fahimta ne kuma ita muka yiwa laifi sai ka bata haƙuri.
Ta ƙare tana ɗan murmushi, sosai maganarta ya burge shi wanda ya nuna tsantsar tarbiyya a ciki, tayi shi cikin tauna harshe da kuma kawaici da haƙuri, hakan yasa shi kasa magana ya wuce gaba ita ta bishi a baya har suka isa wajen mota. Sun samu yaran suna tsaye yace su shiga baya su zauna, sai Safna ta shiga ta zauna a gefen driver, Zayyad ya zagaya zai shiga gurin driver ya hango Rashida ta rungume hannunta a ƙirji tana kallonsu, saboda ya wanke kansa daga zargi sai ya wuce sashinta ya tsaya a gabanta yana cewa.
Safna ba tada lafiya tana fama da ciwon kunne shiyasa zamu fita tare, inna sauke yara na ƙarasa da ita asibiti.
Hmmm sai ku jira ni mu tafi tare nima nayi muku rakiya.
Yadda tayi maganar cikin haɗe fuska yasa shi yin shuru bai tanka ba sai ya juya ya koma ya shiga mota, ita kuma ta shiga ɗaki tana ciwon yarda da jin wani raɗaɗin zafi a ƙirjinta wanda tun sadda Ilham ta koma ta sanar da ita Zayyad ya korota kuma taga Safna zaune a cinyarsa, ba ƙaramin dukan zuciyarta maganar tayi ba, tsabar kwazzaba jiya ya gama naniƙarta har da sambatunsa amma kuma yaje yana mannewa Safna, bayan tasan magungunan da ta sha ba ƙaramin aiki suka yi mata ba dan sosai taga sauyawarsa saboda tuni duk wani fushi da yake yi da ita ya daina, dama rabonsu da juna tun kafin bikinsa da Safna sai jiya ta sauke kai taje ɗakinsa ta bashi dama, ta ɗauka zaita rawar ƙafa akanta duba da lokacin da suka ɗauka ba mu'amalar aure, duk da yana samu a gurin amaryarsa amma ta zaci irin da ne da yake yawan nane mata, shiyasa ta dage da yin gyara musamman magungunar da ƙawarta Kubura ta kawo mata daga niger, amma wai ya je sashin Safna ya shantake kamar an aiki bawa garinsu, tayi kwafa tare da ɗauko hijab ta ɗaura akan riga da siket ɗin atamfar dake jikinta, ta fito ta rufe ƙofa ta isa motar ta tsaya a ƙofar da Safna take zaune.
Malama sai ki fito ki bani guri na zauna.
Rashida miye kike yi haka ne? ki shiga baya mu wuce tunda ta riga ta zauna.
Amma kasan dai uwargida ce ke da gaban mota.
A naki ƙaulin ba, amma ko wacce tana da damar zama a gaba in dai mace tana da girki, kije ki ƙara tambaya.
To ai nice da girkin.
Ta faɗa tana tsuke fuska, Safna ba musu ta buɗe ta fito ta zaga ta zauna a baya ta gefen Zayyad, Rashida ta shiga ta zauna Zayyad ya tada mota suka wuce cike da takaicinta.
Bayan ya sauke su Ilham sai ya juya alakar motar zuwa asibiti, sun hau kan titi sosai Rashida ke cewa cikin sakin fuska.
Abban Ilham yaushe rabonmu daka fita damu unguwa a mota har na manta, ya kamata ace nima yanzu ka saya mini mota, kaga kaima ka huta da jigilar kai yaran nan makaranta.
To kai ki unguwa Rashida ai kamawa take yi, mota kuma a yanzu banda halinta sai dai kiyi mini addu'a Allah ya hore mini nan gaba na siya muku keda Safna.
Amma ai zaka iya siyan mini daga baya ka siya mata, ba dole sai lokaci ɗaya ba.
Hakane sai ki taya ni da addu'a.
Ya faɗa a takaice tare da gundura da maganarta dan ya kula Rashida tana da son kanta, Zayyad ganin Safna tayi shuru ya kalle ta yana cewa.
Safna kin yi shuru kamar ruwa ya cinyeki ko ciwon kunnen ne?
Uhum da sauƙi Alhamdulillahi.
To ko kina tunanin Allura ne.
Ni bana tsoronta saboda ni jaruma ce.
Allah ko? kar dai sai kin ganta ki saka mana kuka.
Ni ɗin? haba dai Sirrin Ruhi gaka a kusa dani mai zai saka ni kuka, na tabbatar har ayi a gama ba zanji zafinta ba, kuma kamata yayi a raba ruwan allurar biyu a yi mini rabi a maka rabi nasan zanfi samun sauƙi akan lokaci.
Taya za ayi mini rabi bayan ni ƙalau nake.
Ka manta da cewa wanda aka yi maka zai dawo yayi aiki a jikina.
Zayyad sai da ya kalle ta ta madubin saman kansa, ya ga shi take kallo tana sakar masa murmushi.
Na yarda amma da sharaɗi.
Ya bata amsa yana nuna mata yatsun hannun damansa guda huɗu.
Naƙi wayon.
Ta bashi amsa tana maƙe kafaɗa, Zayyad ya saki dariya har yana dukan sitiyarin mota, gabaɗaya sun shagala kamar su kaɗai ne a motar, Safna murmushi ta dinga saki ta mayar da dubanta gefen hanya, dan tuni ta gano jirginsa akan nuna mata yatsunsa guda huɗu da yayi, hakan yana nufin kusancin aure zai yi sau huɗu a dare ɗaya, karatu ne daga shi sai ita suka san kansa, Rashida kamar ruwa ya cinyeta dan ba ƙaramin ƙular da ita suka yi ba, hakan yasa ta kunna data ta hau online zuciyarta kamar zata fashe, sai ta koma tana dana sanin biyo su da tayi, dama gulma yasa tace zata je dan bata yarda asibiti zasu ba duba da bata ga Safna a wahalce ba balle tayi kama da mara lafiya.
*Kuyi haƙuri da wannan. Da kyar na jure typing ɗin a cikin daren nan*
[20/09, 8:03 pm] null: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/C2K7oAG7DtwAX8OnKUpxns
*AMARYAR ZAYYAD*
Na
©®Rahma Kabir MrsMG.
Wattpad @rahmakabir
Page 14.
Suna isa asibiti suka zauna a reception suna jiran likita da aka ce yana ward round, tuni aka tura file ɗinsu zuwa system ɗin doctor. Bayan kamar minti goma sha biyar sai gashi likitan ya ƙaraso, yana ganin Zayyad ya isa gareshi shima ya miƙe cike da fara'a suka yi musabaha.
Alhaji Zayyad Barka da safiya, kai ne da iyalin duka waye ba lafiya.?
Amarya muka rako.
To madallah Bisimillah.
Likita ya ambata ya juya zuwa office ɗinsa, Zayyad ya kalli Safna yace mata su shiga sai Rashida ta miƙe da nufin binsu.
Maman Ilham ki jiramu mu fito.
Cewar Zayyad daya katse mata hanzarinta, ya rasa wannan wani irin binbini take yi musu ko wace mace tana buƙatar sirri amma yaga Rashida sam bata da wannan tunanin. Da suka shiga likita ya tambayi Safna meke damunta, sai ta faɗa masa daga nan ya ɗaura da tambayarta yadda take ji a jikinta harma da yaushe rabon data ga jinin al'adarta, duk ta faɗa masa dan bikinsu saura sati ɗaya tayi wanka kuma bata ƙara ganinsa ba dan har ta soma ɓace lissafi, likita yayi rubuce rubucensa kana ya miƙa musu wata takarda yace suje lab za a ɗiba jininta ayi gwaji da kuma fitsari, Zayyad ya amsa kana suka fito yana gaba Safna tana binsa a baya har suka isa lab, ba ɓata lokaci aka ɗiba jininta tare da bata wata ƙaramar roba akan taje tayi fitsari, suka nuna mata bayi ta shiga ba jimawa ta fito ta basu suka amsa tare da cewa suje su jira zasu kawo result office ɗin likita. Bayan sun dawo suka zauna zuna jiran sakamako, Safna hankalinta yana kan tv Rashida kuma tana ta danne danne a waya haka shima Zayyad. Bayan wani ɗan lokaci sai ga nurse tace su shiga ɗakin likira dan har an kawo result ɗin, suka miƙe suka shiga tare da zama suna fuskantar likita.
Alhaji Zayyad ina tayaka murna da samun ƙaruwa dan sakamako ya tabbatar da Amaryarka tana ɗauke da juna biyu, dan haka zuwa nan da sati biyu zaku dawo dan tabbatar da kwanaki nawa yake. Wannan ciwon kunnen alamu ne na laulayi yazo mata a haka, Allah ya raba lafiya.
Ameen nagode likita sai a ɗaurata akan magani dan samun sauƙin ciwon kunnen.
In Sha Allah gasu zan rubuta sai kuje gurin biyan Kudi ka biya sai ku amsa magungunan a pharmacy.
Zayyad yayi godiya sosai, Safna kuwa taji daɗi sai dai abin yazo mata a ba zata bata taɓa kawo ciki yanzu ba, balle babu wani laulayi kamar amai zazzaɓi kamar yadda sauran wasu mata ke yi. Bayan sun fito Zayyad yace su jirashi a mota ya wuce gurin biyan kudi, daya gama dasu ya amsa magani kana ya fito suka kama hanyar gida.
Bayan sun ƙaraso gida Rashida kamar abin arziki ta juya tana cewa Safna.
Allah ya ƙara sauƙi yasa kaffara ce, zaki iya ɗiga Zaitun a kunnen shima yana maganinsa sosai.
Ameen ya rabbi nagode maman Ilham In Sha Allah zan saka.
Malama ba abinda zaki saka tunda likita yace ciwon kunnen da akwai dalili, ga maganinki ki tabbatar kin karya kin shasu, ina zuwa.
Ya ambata tare da miƙa mata ledar maganin, Safna ta amsa ta wuce, shi kuma suka jera da Rashida tana cewa.
Ya zaka ce kar ta ɗiga bayan kaima kasan yana maganin ciwon kunne, ko ba kaine ka taɓa siyowa ba lokacin da Aslam yayi fama da shi kace Hajiya tace a saka masa.
Hakane amma ita fa laulayi ne yazo mata a haka.
Dumm Rashida taji akanta kamar an buga mata guduma, nan take taji wani gumi ya soma damunta amma haka ta shanye yanayin da take ciki ta ƙaƙalo murmushi.
Ayyiriri kace har ta ƙunsa, Allah ya raba lafiya, lallai fa Zayyad ka zama Sharp shooter wannan abu da wuri haka.
Bana son sharri Malama, kema ina ce daga zuwanki wata guda kika ƙunsa, dan haka kin tabbatar da ni ɗin jarumi ne ina da lafiya.
Aiko ni shaida ce. To Allah ya inganta. Zaka karya anan ne ko kuwa?
Ta ambata tare da cire hijab ta aje saman kujera, Zayyad ya zauna yana cewa.
Ki haɗa tea mai kauri ki kawo mini arish da biredi, bana ma jin wani yunwa sosai.
To tace masa ta isa kitchen ta haɗo masa dan dama tun ɗazu ta soya arish ɗin haɗe dana 'yan makaranta, ta kawo masa ya karya suna hira kamar wani rikici bai shiga tsakaninsu ba, sosai Rashida taji daɗin yadda komai ya soma zama dai dai a tsakaninsu, tun dai jiya data ba shi haɗin kai, bayan ya gama ya ciro dubu ɗaya ya miƙa mata yana cewa.
Ki riƙe ko da kina buƙatar siyar wani abu.
Hmmm yaushe rabon da ka bani kuɗin kashewa sai yau, kodai duk murnan samun ƙaruwar ce.
Ki amsa kiyi godiya ba niman ba'asi ba, imma shine ai ya kamata dan haihuwa Alkhairi ne, balle ma kuma ba shi yasa na baki ba ra'ayi nayi.
To nagode a dawo lafiya.
Ta amsa ya wuce ɗakinsa ya ɗauki abinda zai ɗauka kana ya fito ya wuce sashin Safna wanda Rashida da harara ta bishi, kamar tana jira ya fita ta ɗaga waya ta kira mamansu tare da shiga ɗakinta ta rufe ƙofar ta ciki, bayan ta ɗauka suka gaisa ta ɗaura da cewa.
Mama wai Safna ciki gareta, yanzu muka dawo asibiti bata jin daɗi.
Ikon Allah abu da wuri haka to Allah ya inganta.
Mama ya zaki ce haka.
Rashida ai tunda aka ɗaura auren nan kema kin san ƙaddara ta riga fata dan haka kiyi haƙuri ki karɓi ƙaddara, sannan ke ya batunki har yanzu shuru ko.
Mama yaushe na cire implant din, ai da saura tukuna.
Gobe kya sake biye masa ai, gashi Amarya tana fara zuba ɗaya to ɗaya ne zai rage ta kamo ki, in kuma 'yan biyu ne to kun yi daidai kenan.
Mama madadin ki lallashe ni sai ki ƙara mini zafi.
Rashida ta faɗa cikin rawar murya, Maman tayi ɗan murmushi.
Ya kike so nace miki, to kiyi haƙuri in kin samu lokaci sai ki sake kira muyi maganar can da na fara yi miki jiya.
Yanzu ma ina da lokaci, kuma ina da kati muyi kawai ina jinki.
Rashida ta faɗa tana zama a gefen gadonta tare da tattaro duk natsuwarta suka shiga hira.
...
Zayyad yana shiga ɗakin Safna ya tadda falon ya ɗauki Ƙamshin turaren wuta, ya zauna yana shaƙar numfashi tare da fitarwa cike da samun natsuwa, Safna ta iya kula da sashin ta sosai ya ambata a cikin ransa, fitowa tayi daga ɗakinta tana murmushi.
Farin Masoyi har ka fito.
Eh amma kin karya kuwa?
Yanzu na gama gyaran ɗaki zan shiga kitchen.
To kin san dai ba ke kaɗai bace yanzu, ki kula da cin abinci dan Allah, sannan duk abinda kika ji kina son ki ci ki sanar dani zan aiko miki.
Nagode da kulawa ina Ƙaunarka masoyi.
Kamar yadda nima nake ƙaunarki, ga dubu ɗaya ki aje saboda tsaron lalura koda sa kati ko wani buƙatar in ta taso miki da gaggawa.
Ta ƙaraso in da yake zaune ta ɗago haɓarsa ta sakar masa kiss a goshi.
Yadda kake faranta mini Allah ya cigaba da faranta maka, ya ƙara maka buɗi da yalwar arziki mai albarka ya kuma tseratar da kai daga Haram.
Zayyad miƙewa yayi yana kallon kwayar idonta cike da tsantsar so da farin cikin kasancewarsu tare a inuwa ɗaya.
Ameen ƙaunata ina alfahari da samunki a cikin inuwa guda, Allah yayi miki albarka tare da abinda ke cikinki.
Ameen tace tare da rungumeshi tsam a ƙirjinta, shima runguneta yayi sosai kamar zai mayar da ita cikin jikinsa, suna jin bugun zuciyar junansu tare da shiga wani daular duniya wanda sai tsantsar masoya sune kaɗai suka san yadda yanayin yake, Safna ta sauke ajiyar zuciya ta sake shi shima ya saketa suna kallon juna.
Badan badan ba dana ƙi fita aiki yau na cigaba da kasancewa da ke, Safna kina yalwata mini duniyata da farin ciki Allah yasa zamanmu ya ɗaure a haka.
Ameen ta ambata ta kama hannunsa ta jashi suka fita har mota tayi masa rakiya, ya shiga ya zauna suna jifar juna da shu'umin kallo wanda su kaɗai suka sai irin karatun da suke aikawa junansu, ya tada mota