Showing 30001 words to 33000 words out of 44631 words
Chapter 11 - KUNDIN QADDARA BOOK COMPLETE By MJay.pdf
A hankali ta shiga diba tana bashi a darare, ita duk kunya ya kamata. Babba dashi ya zauna
yana bude baki tana bashi abinci, kanta na qasa take sa masa a baki, wanda garin yin hakan ta
kai cokali hancinsa. Nan da nan ta dago a tsorace, suna hada idanu taga yadda kwayar
shinkafa ta maqale masa a hanci. Ai sai tasa dariya, shima sai yasa dariya. Yasa hannu zai
goge da sauri ta kai nata ta share masa. Ita kanta ta bawa kanta mamaki. Bata bari sun qara
hada idanu ba ta kwashe kwanukan ta nufi kitchen dasu.
Saleem kuwa binta yayi da kallon sha'awa, a yanxu sai yake alfahari da Allah ya salota cikin
rayuwarshi.
Washegari da misalin 4:56pm na yamma suna hira da hafsah wadda itama tazo gida duba
Abbah, hafsah tayi tambayar duniya akan taybah ta gaya maya yanayin zamansu yanxu amma
taqi. Sirrin aure is better kept secret.
~"kuskuren da mukeyi yanxu knn, mu dinga ba kawaye labarin yanayin zaman auren mu which
is not right and is against our Islamic~~teachings.~ ~Our holy Prophet(PBUH) Warns us against
such act. Baida kyau ko kadan wanda yanxu an chanja salo harda first night ake bada labari.
Allah ya qanar damu gaskiya ya kuma shiryemu baki daya".
Suna cikin hirar tasu mai dadi kuwa wadda ta danganci yanayin zaman duniya, sai wayar
hafsah ta fara ruri. Da sauri ta dauki wayar cikin tsanani farin cikih tana cewa..."swthrt, kamn
kasan ina hira da bestiee kaine a raina". Hafsah ta fada tana wani kashe murya ana
nannarketa. "Yeah, gani zaune tard da bestiee nah, ka mata gaisuwa gata nan zan bata wayar". Hafsah ta
fada tana miqama taybah wayar.
Tana sa wayar a kunnenta aka mata sallama..."Salamu alaiki yaruwa".
Sandarewa taybah tayi a wurin, wannan muryar waye haka....."y...y..yy...ya...yaa fay...faysal!".
Ta fada a ranazaneh.
*©MSS MJAY*
[12/25/2016, 1:13 AM] Mss Mjayí ½í²…í ¼í¿½: WWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
*KUNDIN KADDARA*
WWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
Written by
*MSS MJAY*
In dedication to
*SEMBYY LUFF*
*39*
Taybah ta fada tana stammering......."Durln sis, ya kike"?. Faysal ya bata amsa.
"Yaa faysal, kana nan ashe, tunda ka tafi baka taba kirana bah. Why? Meyasa kamun haka?".
Ta fada muryarta na kuka alamun any moment from now zata iya barkewa da kuka.
"Sis, i have to do it that way, sometimes muna abu bada son ranmu bah, sai dan ya zama dole.
Nagode miki sister, you changed me, you changed my heart. And thanks to the charming soul
da take kusa dake, na rungumi KADDARAR da Allah ya daura mana, wanda kuma kece kika
fara qarfafa mun gwiwa har haka ta faru, nake kuma gani alkhairin dake tattare da tamu
KADDARAR. Allah ya bamu ikon cinye wasu in akwaisu".
Hawaye ne suke silalowa daga idanun taybah, tabbas a maganarshi babu qarya, komai ya fada
gaaskiya, dukda ita a nata bangaren al'amura da saura basu gama daidaita ba. Amma ta taya
yaa faysal cinye tashi KADDARAR. (Allah ya bamu ikon cinye tamu in tazo, cikin gidemai da
kuma daukaka darajar shi).
"Ma shaa Allah, naji dadin wannan lbrin daka bani bruh, i adore you a lot, thank you for being
yayanah. Allah qara danqon kauna tsakaninka da bestiee". Sun dauqi kusan 10mins suna waya
sannan sukayi sallamah, saura wata uku ya dawo gida gaba daya shima.
"Keh silly girl, yaushe kika sacema yayanah qalby?". Taybah ta fada tana kaima hafsah duka a
baya.
"Humm, bari kawai swthrt, Allah shine mai yanda yaso a duk lokacin dayaso. Yaa faysal na
zuwa Singapore ko kwana biyu beyi ba ya kirani yana kuka, kuka taybah ba dan kadan ba, that
is ranar daurin aurenku, ba abunda yake banda cewa shi knn ya rasa ki. Dakyar na samu na
kwantar mai da hankali. From that day onwards i do call him akai akai inji ya yake, ko three
months bamuyi a haka ba na fara developing feelings for him. Ba abunda ya qara burgeni dashi
kamar haqura da yayi ya rungumi KADDARARSHI which is the amazing part of it all. Cikin
hukuncin Allah soyayyah ta kullu tsakanin mu".
"Shine kika kasa gayamun koh?".
Haka dai suka cigaba da hiransu har zuwa lokacin da likita bokan turai yazo daukarta.
Kwanansu uku cif a garin jos suka juya abuja, da nufin saleem zaije bauchi wurin likitan ido ya
nema musu appointment. Bayan komawar tasu abuja abubuwa da dama sun faru, ciki harda
sabuwar kulawar da saleem yake bata, which to her is surprising, bata kuma nuna mai alamar
ta damu da dawainiyar da yake da ita balle yayi tunanin zata kula dashi itama. A kuma yan kwanakin nan da strange feelings saleem yake kwana yake tashi a kanta. Wanda
deep inside him yasan love ne, amma bayason yayi accepting wannan fact din.
A bangaren taybah kuwa tana ma saleem abubuwa a boye not wanting him to know. Misali, duk
tayi sallah saita mai addu'a. Ita kanta mamaki takeyi idan ta zauna tana zabgo addu'ar samun
cigaba wa saleem. Sai ta duba taga kuma da gaskiyarshi, domin sun zama daya, duk abunda
ya sameshi ya sameta, kamar yadda yanxu da abu ya sameta ya nuna kwarai shima ya shafa.
Don ko kadan baya nuna gajiyawarsa wurun bada kowane taimakon daya dace.
Da misalin 10:07pm na dare taybah ta fito wanka, ta zauna ta gyara jikinya a gaban madubi, ya
zura rigar baccinta wadda take coffee in colour na silk sai kuma tunani yayi awon gaba da ita,
har bata san lokacin da Saleem ya shigo dakin ba sai qarar kulle kofa, wanda yayi dalilin dawo
da ita daga duniyar tinanin data lula. Ta juyo a tsorace. Kallonta ya tsaya yi yana la'akari da gaba daya ta qara sanyi, tana kuma cikin
damuwa a lokuta da dama......"ke yanxu hankan ya fiye maki? Ki kulle kanki a daki kina tunani?
Waima kinga yadda kika lalace kuwa?". Wai daya fada saita komar da ganinta xuwa kan
madubin. Tanaso taga lalacewar wanda hakan ba karamin dariya yaba saleem ba. "Gaskiya idan kinaso mu shirya, to ki daina daga hankalinki, idan ba haka ba kuwa saina zuba
miki ido tunda baki amince da KADDARA ba".
Da sauri ta dubeshi tace..."Allah na daina damuwa akan lalurar baba, dukda dai ba zance
kwata-kwata ba, amma na barma Allah komai".
Kura mata idanu yayi, kasancewar tana fuskantar madubi yasa shi dafa jikin dressing mirrorn ya
sata a gaba..."toh fadamun matsalarki guda a gidan nan". Ta cikin madubi suke kallon juna, ita
tafi tsanar shishigewar da yake mata, ta kula tun ciwon Abbah yake wani makalewa kamar ya
damu da ita. Shiru tayi tana tunanin yanda zata fada mishi damuwart, ta san bazata iya ba, dan
haka a takaice ta bashi amsa..."Babu"
Dayan hannun nashi yasa ya zama ya kewayeta a jikin mirrorn din sannan ya kuma
rankwafowa daf da fuskarta yana cewa..."kin tabbata?". Gabanta ne ya shiga dukan uku uku!
Yayin da hancinta ya cika da kamshinsa mai saukar da natsuwa, sai dai a wannan lokacin sam
babu nitsuwar a tare da ita. Tsantsar zafin saleem takeji da zai iya bata mata rai, ya tozartata, sannan ya sa jikinta ya mace
a duk lokacin da taji kamshinsa, bare akai gajin muryarsa.
Cikin zafin rai da gajiya da al'amarinsa ta runtse idanu tace..."kaine matsalata yaa saleem, dan
Allah ka barni ka sarara min, bazan iya daukar komai a kaina ba yanxu yai min yawa. Ka rabu
dani kawai shine matsalata da kuma damuwata". Ganin yayi shiru yasa ta dago idanunta ta
dubeshi sannan cikin raunin murya tace...."Zaka iya?.....rabuwa dani?" Ta qarasa cikin murya
qasa qasa.
A hankali ya zuqi wani numfashi saboda abu na qarshe da ya kawo ma ransa kenan game da
abinda yake damunta, nan take idanunsa suka chanja launi. Duk da halin da maganarta ta
sashi a ciki, a tsanake yace...."Taybah, wannan wace irin magana ce kuma, daga ina ta fito
haka?". Just let me know, tambayata kayi ni kuma na baka amsa na kuma fada maka buqatata, zaka iya
bani abunda nake nema? Thatz the only thing i want to hear". Taybah ta bashi amsa a zafafe.
Cikin kaduwa da maganarta ya kai kansa ya hada gefen kansa da nata. Wani irin murda yakeji
cikin kirjinsa, ya kasa yarda wai abinda takeso kenan, baya iya kwatanto rabuwa da ita, balle ya
kwatanto idan ya rabu da ita zata kasance matar wani. Ina!.
Idanunsa a rufe ruf yace mata... "Taybah tambayata kike ko zan iya baki rayuwata. Ke ki bani
amsa zaki iya karbar rayuwata da hannunki?".
Zuciyarta ce ta shuga bugawa a guje, tamkar zata balle, shin da gaske abinda take ji gaskiya ne
ko kuwa kunnuwanta ne sukai mata qarya? Shin Dr. Saleem neh ya kwatanta ta da
kasancewarta rayuwarsa ko kuwa dai?.
Da sauri ta miqe daga kujerar ta fice daga kawanyar daya mata da hannayensa karfafa,
kasancewar ta daukeahi bazata ya sa ta samu nasarar kubucewa.
"Yaa saleem, bansan me karbe rayuwar mutum yake nufi ba, amma bana ko fata na ga wannan
ranar bare ya kasancd ta hannuna hakan zai auku. Ni dai fatana kawai ka barni in samu FARIN
CIKINAH(littafin HAFSAT RANO) kamar yadda idan na tafi kaima zaka samu naka FARIN
CIKIN". Kalamanta ne suka sa ya juyo da ifa tana fuskantarshi..."waya fada miki fitarki a rayuwara itace
FARIN CIKI a gareni?".
"Basai wani ya fadamun ba, da kunnenah naji kana cewa ka tsane ni....ka fada not only once
but lokuta da dama, wannan ta isheni hujja, dan haka na rokeka don son Allah.ya sahale mi......
Kafin ta kai aya ya toshe mata baki da nashi, kissing her soo deep and passionately, wanda ko
rufaida da sukayi auren soyayyah i don't think ya tabama irinshi, wannan karon babu alamar
lightly a al'amarinsa dan kuwa ko sassautawa ya kasa yi. Wannan ake kiea abunda jini da jiki
suka dade sunaso aka kuma samo. Saida yaga suna buqatar numfashi sannan yabar
sumbatarta. "Do you have any idea? Kinsan iyakar darrarakin dana dauka bana barvi sabida tsananin sonki?
Kinsan iyakar darrarakin dana bata bana bacci saboda begenki? Karki qara...." Ya fada fuskarta
na cikin tafukan hannayenshi..."koda wasa karki qara furta wannan kalmar, na haramtah miki
fadin ta". Cikin tsananin fushi ta fusge kanta tareda da goge bakinta, kamar wadda aka sama mugun abu
a ciki.
Kofar dakinta ta nufa cikin baqin cikin tareda bude ta sannan ta juya ta dube Saleem cikin bacin
rai....."Malam, get the hell out of my room". Taybah ta fada cikin fada
"Zaujatiyy...lis....".
"Now!". Ta qara fada ba tare data bari yakai karshen maganar shiba.
Sum sum saleem yaja kafafunshi da sukayi mugun sanyi yabar dakin.
*©MSS MJAY*
[12/26/2016, 2:55 AM] Mss Mjayí ½í²…í ¼í¿½: WWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
*KUNDIN KADDARA*
WWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
Written by
*MSS MJAY*
In dedication to
*SEMBYY LUFF*
*40*
Tana ganin yadda kwalla suka taru a idanunsa, suna shirin zuba, tayi saurin kawar da kanta
gefe, donma karta karaya, duk da taji nauyin abinda ta masa. Don ita kanta ta kasa yadda duk
girman Saleem da kuma haduwarshi da kwarjininsa ta iya dubansa tayi masa yadda taga dama.
Amma, tafison yangane kurenshi, ya kuma dau darasi, saboda nan gaba sai yayi tunani sau
goma kan ya maimaita haka.
Yana shiga falo ta tura kofar dakin, ta sulale a bayan kofar ta bude sabon fagen kuka, wannan
bana kunci bane, wannan kukan na tsananin son mijinta ne.
Dukansu biyu ba wanda ya runtsa a darwn, gashi shikam yanada tafiya suleja washegari
saboda wani aiki da zasuyi washegari.
A yadda suken kuma ta tashi tun sassafe ta tsara musu lafiyayyen abin karyawa, ta ajiye masu
a table sannan ta fada wanka. Yau kam ta shirya cikin wata shadda lilac dinkin doguwar riga har
qasa daya sha aiki mai stone work. Koda ta fito yayi daidai da fitowarshi shima a shirye, zama
yayi sannan tayi serving dinshi itama ta zuba nata. Saida suka gama karyawar ne ya dubeta kasa-kasa don ta kula tunda suka zauna cin abincin
yaqi yadda su hada idanu......."Ni zan wuce Azare saboda wani aiki, sai xuwa jibi In shaa Allah
zan juyo". Maganar ta daketa kwarai, amma ta danne ta ce...."Allah ya kiyaye hanya". Ta mike
tana kwashe kwanukan kan table din. Waima yaya za'ayi zai yi tafiya, sai yanxu da zai tafi shine zai sanar da ita, kuma tafiyar ma bata
wuni ba har kwanaki biyu? A wani bangaren zuciyarta ko tuhumar kanta takeyi......."Bake kika
koreshi ba, ai yayi qoqari daya shaida miki ma". Haka dai ta wuni a kwance kamar wacce kwai
ya fashewa a ciki. Wani qarin abin haushin ma shine, wayarta a hannunta ta wuni amma harta
tashi kwanciya ko missed call din saleem daya bata gani ba. Gashi fushi da zuciya sun kai mata
cafka ba zata iya kiranshi ba.
*2dayz later*
Tana zaune cikin wani swiss lace dinta yellow mai adon peach zaren daya turu, doguwar rigace
data kamata daga sama zuwa kugi, sannan ta sake daga kasa. Ta sha daurinta tana kallonta a
Cbeebies.
Wajen hudu ne na yamma ta tsinkayi sallamarsa cikin muryars mai taushi da kuma ratsa zuciya.
Gaban tane yayi wani mumunar faduwa, sai kuma ta fara neman abinyi, data rasa ne ta daure
ta amsa sallamar.
"Sannu da dawowa". Ta fada a hankali. Ita dai bata ji lokacin daya amsaba bata kuma damu ba
ta wuce kitchen danta sama mai abunda zaici.
Binta yayi da kallo yana hadiyar yawu.
Ya gama dinner amma shiru har lokacin babu zancen taybah zata qara fitowa. Dafe kanshi yayi
cikin tsananin damuwa sannan ya nufi dakinta.
Yana murda kofan cikin sa'a ya hango ta kwance kan gado ta rufe ido tana bacci, wanda alal
haqiqah ba bacci takeba illa zurfi a tunani da begen mijinta.
Bata ankara ba kawai taji kamshin turarenshi a kusa da ita, kafin tayi yunkurin yin wani abu
kuma ya haye gadon tareda fara kissing dinta ba sassautawa.
Taybah tayi iya yinta ta kwace kanta amma ta kasa, because not a kissing kawai abun ya tsaya,
hannayenshi na aiki ne a ajikinta, sending sparks of electric shocks into her, aii nan da nan
taybah tayi falling, going deep into kissing him, kissing him back more widely than yanda yake
kissing dinta. Love binds it all, tana sonshi yana sonta, but kuma aii yasha fadamata ya tsaneta.....Dammit!
Gashi yanaso yasa tayi loosing control dinta.
Da sauri ta riqe hannunwanshi da suke qoqarin shiga cikin bra dinta. Sannan ta takarkare ta
danna mashi wani zazaffan cizo.
Ba shiri ya saketa, yana kallonta itama tana kallonshi, sannan cikin sauri ta tureshi tareda
miqewa tana gyara nytie dinta daya sabule. Bai damu da abinda ta mishi ba sai cewa
yayi...."Zaujatiyy, what do you want? Me kikeso ne a tare dani, shin har yanzu bakiga alaman
nayi nadama ba? Maida kanta baya tayi tana kallonshi cikin daurewar kai sannan tace.."Nadama? Ai a iya sani na
mai laifi da rarrashi aka sanshi, bada shirya tafiya ba without telling that particular person or
even bothering to call and ask after her...ko kuwa duk suna cikin nadamar?".
Juya idanunsa yayi cike da damuwa yace.."ke kanki kina rudewa, ke kika nuna kinfiso in rabu
dake, a tunanina hakan shi zai kawo miki kwanciyar hankali, shi yasa na janye miki amma
yanxu i can't take it anymore, i really can't".
Ba tare data qara cewa komai ba ta bude kofan toilet ta shiga abinta ta barshi tsaye a wurin.
Sum sum ya fice daga dakin nata ya nufi nashi cikin tsananin damuwa.
Washegari ma breakfast kawai ta hada mai ta koma daki abinta, wanda shi kuma hakan ya
hanashi jin dadin cin abincin. Sai da yamma neh daya dawo ta lura da yanda taji masa rauni a
baki, gaba daya sai taji wata irin kunya da nauyi sun kamata gameda tausayinshi.
Dukda bata cemasa komai ba a lokacin. Saida ta bari ya nufi dakinshi bayan ya gama dinner
sannan ta miqe tabi bayanshi.
Motsin bude kofar dakin ne yasa ya juyo, singlet ne a jikin sa da wando ruwan kasa mai haske(
Tan color) mai laushi, da alama yayi wanka kaya yake sawa. Da sauri ta juya zata koma yayi
saurin cewa..."come in".
Sai kuma ta juyo ta isa kusa dashi a sanyaye bata ce komai ba bata kuma yi abunda ya kawota
ba. Ganin haka yasa saleem ya gama qare mata kallo kafin yace..."yaya dai?" Hade da daga
girarsa cikin alamar tambaya.
Baiyi aune ba, kawai yaga tasa yatsanta akan labbansa data ji masa ciwo, wani ointment ne a
hannunta ta shiga shafa masa a hankali da yatsunta masu laushi. Mamaki neh ya daskarar
dashi na wucin gadi. Zata sauke hannunta yayi saurin riqoshi ya hada da dayan zuwa kirji.
"I love you zaujatiyy, i love you a lot. Ki yadda dani ina sonki more than anything dana taba so.
Ki soni mana taybah koda kashi daya ne cikin kashi goman son da nake miki". Ya fada hawaye
na silalowa daga idanunshi.
*©MSS MJAY*
[12/27/2016, 12:53 PM] Mss Mjayí ½í²…í ¼í¿½: í ¼í¾ˆí ¼í¾ˆWWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
*KUNDIN KADDARA*
í ¼í¾ˆí ¼í¾ˆWWW.HAUSAEBOOKS.COM.NG
Written by
*MSS MJAY*
In dedication to
*SEMBYY LUFF*
*41*
Shiru tayi kawai suna kallon juna ta kasa cemai komai banda kallonshi da takeyi kawai. Ba
kuma karamin duka maganar daya gaya mata ya mata ba.
"I know, nasan na cutar da ke in every way possible. Amma dan Allah kiyi haquri ki gafarta min,
kiyi haquri mu daidaita kuma na janye duk wani abu dana fada. Inaso ki sani lokacin nan banda
yanda zanyi ne, i was helpless".
Zuciyarta cike taf! Da tausayinsa da kuma son ta amince da shi,sai dai kawai ta tuno abin daya
fada mata to her face, not only that to his friends ma sai taji ranta ya qara baci.
"Naji uzirinka, tunda kai bazaka iya nisanta dani ba,