Showing 27001 words to 30000 words out of 54969 words

Chapter 10 - ZAMAN TASHA COMPLETE BY UMMY AYSHA.pdf

10 Jul 2025

4017

ilimin an ce dai ko kana da kyau yakama ta ka kara da wanka.
A'bangaran waka kam ban sake yiba, dan Baba yace ko zanyi waka saina kammala saukar,
Alkur'ani na na biyu ,dan nayi sauka ta farko inada shekara sha biyar,nazo na fara tishi daga
farko, haka kam akai su rafel sun zo harsun hakura sun'daina zuwa..
Baba yasawoman wani katon banki yace daga yanzu Moopy in kinyi d'inki kidinga zuba ku d'inki
anan kinji ko?

"Nace Baba kwara in baka ka ƙara kayi hidimar gida ko?

Baba yace karki damu Moopy a'bunda nike samu sun ishemu.
haka akai nafara tara kud'i na dan danan a'susu na ya fara nawie, dan babu ranar da zatazo
banyi É—unkuna na manyan mata ba, a'haka har nayi shekara biyu ina tari na, lokacin yayi
dai-dai da cika shekara ta 21 ,Allah ya yiman kyau da zati na ban mamaki, wanda ganin
hakane yasanya baba'na yiman manyan hijjob dan sitirta kaina, a'lokacin na kammala hardata
ina da cikakken Alkur'ani A'kaina, A'makaranta Malam mubarak Kam an'yayeni Dan yanzu ina
daya daga cikin masu koyawa yaran dake tasowa.
Wata rana Baba yace Uwata ya kamata fa ki fito da bankin nan mu kilga kud'in ciki, mugani kinji
ko?

Nace to Baba bari in fiddo!! na tashi cikin natsuwa nafiddo bankin na aje kusa dashi, yata shi
Yarufe shagon ya haskamana fitila, Anan muka juye kudi dasuka bamu tsoro nida Baba na, dan
yan dubu-dubu ne, sai yan É—ari biyar.

"Baba sai cewa yake Alhamdulillah shikenan Uwata ta zama mai kud'in katsina."
"Nai dariya muka ci gaba da kidaya ƙud'in mu har muka gama, muka hadasu suka dawo
naira dubu nari bakwai da sittin da yan kai, bakaramin mamaki mukasha ba nida Baba, nace
Baba kaga a'bunda nasamu kuwa?

Baba yayi murmushi mai had'e da hawaye yace nagani Uwata nagani Wallahi, nakumayi farin
ciki sannan nagode Allah daya kin tsaman wannan shawara ta tarin kuÉ—in nan, a'bunda ya
kamata in maki ne nakasa saike zakiyiwa kanki kiyi Hak'uri Uwata dan Allah yafada yana kuka
sosai.
"Na zubar da kud'in na mike tsaye nafara zaro ido ina nuna shi da hannu" nace Baba badai
kana nufin kaima tafiya zakai kabarni ba?

Baba ya gil-gizaman kai had'e da share hawayenshi yace, Uwata nasaki tarin kud'in nan ne
kawai saboda halin rayuwa, da farin cikin da kike Maki fatan É—ore warshi har a'bada, amma
bazance maki komiba sai gobe Insha Allah kinji ko? kawo kud'in nan a'adana cikin kwalinnan

mushiga gida ki kwanta.

Haka nabashi yamasu wuri mai kyau ya aje, muka bud'e muka fito ya kulle muka shiga gida,
anan muka iske Ammi zaune ta mik'e ka fafuwa tana cin ƙwaɗ'an yakuwa.
Ina shiga na duka na gai'data tare da mikewa zanshiga É—akina, Ammi ta saman kafa banyi
wata wata ba na fado kanta," take ta fasa wani Uban ihu tana fad'in zataiman a'sarar ÆŠan
Albarka, tinda kin ganki gantalalla ai'kwara kiman a'sara Cikin da ko yawu banta ba zidda wa
kanshi ba da sunan ciwo, ta han'kaÉ—ani gefe tare da É—aukar takalma ta fara watsaman
mari, Baba yayo kaina yakwaceni yafarama Ammi fad'a akan ta rika Hak'uri mana, bada
gan-gan zan faÉ—omata ba.

Ammi ta dakamai tsawa tare da fadin to tsaya kaji in baka sani ba, cike ne dani kaganshi wata
bakwai, Amma saboda na É—an Al-barkane ko ciwon a'kaifa banta yiba, dan haka ka jamata
kunne..

Baba yadafe kirjinshi dake mai wani irin fitinan nan ciwo a'yan kwana kin nan yafara magana
yana tari sosai."da sauri natashi na de bo ruwa na bashi yasha, tare da kama mai hannu na kai
shi bakin kofar É—akin Ammi,yakarasa shiga nikuma na ruga É—akina na rufe tare da sanya
kuba na cire katon hijjob d'ina danike rayuwa dashi babu dare ba rana. Natashi nacire kaya na na dauki karamar riga da na É—inka ta roba nasanya nai Addu'a bacci
yakwasheni.

Washe gari Baba yashigo É—akina tinda wuri, bayan mungama Sallah Asuba ya Zauna muka
gaisa! yakeceman Uwata tashi kiyi wanka muje kirakani Unguwa.

Nace to Baba!! haka natashi nai wanka na iskeshi zaune tsakar gidan mu
shape-shape,nashirya na sake sanya wani katon hijjob d'in nakaraso wajen shi muka fito, haka
muka tako har bakin titi yatsare mana a'dai;dai ta muka shiga yace yakaimu Goruba Road. mai
napep ya jamu sai goruba, a'nan ya a'jemu wani fas,keken fili da Baba ya nuna mai, Baba ya
sallameshi yakama gabansa, muka karasa har cikin filin, na kalli Baba cikin mamaki nace Baba
wannan Uban filin fa na miye hakane?

Baba yayi murmushi yace Uwata wannan filin zai iya yin manyan gidaje guda hudu nagani na
faÉ—a, to nawane gonace ta Mahaifina dashi ma ga donta Yayi,kana wajen babu kowa to yana
yin yau da gobe kinga Unguwar tafara cika da manyan mutane, to nima Baba na yabar man shi
yasanya nima nace ke kadai zanbarwa, ko da bayan raina bance a'raba gidan nan da kowa ba
dan nakine ina daÉ—a jadda-damaki Uwata bance ki fadama ko Ammin kiba duk da nason
bazata zauna dake ba balle taji mike tafiya a'lamarinki .

Na kallai na kaÉ—amai kai nace Baba ya zanyi da wannan Uban filin bayan ni macece ba
Namiji ba.?

"Baba yayi dariya yace iyye Uwata wato kin'son gidan wani zaki kenan kina nufin mizakiyi da

gida kina mace ko, hahhah yayi dariya nima n atayashi ina rufe fuska...

Baba yace to shawara da nikeso muyi dake a'nan shine a'barmaki wajen duka ko-ko kinaso
a'sayar da rabi a'barmaki rabi?

Na bu�e baki zanyi magana kenan wani Babban mutum yayi parking d'in motarshi yana
kallona, kallo mai cike da kurullah har yakasa daurewa yafito ya k'araso wajen mu yayima Baba
sallama.
Baba ya am'samashi tare da bashi hannu suka gaisa .
Mutumin ya kalleni na kalleshi tare da É—aure fuskata na juya gefe.
Mutumin yajuyo wajen Baba yace bawan Allah wani abu kuke nema a'wajen nan ne?

"Baba yace aa nazo ganin filin nan ne."

Mutumin yace ok nagane, ko saye zakayi?

Baba yayi dariya yace aa nawa ne na kawo ya'ta ne ta ganshi saboda halin rayuwa, dan ita
kadai Allah yabani.

Mutumin yakalli Baba cike da tausayawa yace Allah sarki! dan Allah malam in na kane kasai
damanshi Wallahi nima zagaye nike �ana zai dawo daga kasar waje, inaso in mai gini danshi
bayason cen gidanmu yace wai ma'aikata ke a'kwai kwara ake'ɓeshi.

Baba yakalleni yace Uwata kinji wata magana, yaki kace dan magana na hannunki?

Nace Baba duk yanda kayi.

"Baba yace ma mutumin gaskiya wannan filin yanzu na bama ya'ta bani da iko dashi," sai Abun
da tace.

Mutumin ya kallan yasakar man murmushi tare da cewa dota zaki sayarma baban ki filinki?

Jin Abun da yace yasani sunkuyar da kai, dan yacikaman fuska banson sadda nace eh Abba na
siyarma ba..
Dagashi har Baba suka zaro ido yace dagaske yata.

Nace tabbas kuwa .
Mutumin yakalli Baba'na yace tokai malam kaji ko ka amince.

Baba yace eh na Amince Alhaji, farin cikin ya'ta shine nawa, amma a'shawarce inaso in fara
dubam ata wani anan dan gaskiya inaso tazauna a Unguwar nan dan wajen baida hayaniya.

Alhaji yayi dariya yace to in hakane faduwa tazo dai-dai da zama, ga wani fili cen opposite da

nan, bai kai wannan ba nawa ne, dashi zan gina mai to amma naga wannan yafi girma, in da ita
macace kuma gidan wani zata in har Abun yamaka ka karɓi wancen din nikuma sai in amshi
wannan d'in sai in maka ciko.

Farin ciki marar musultuwa ya bayyana a'fuskar Baba'na, take ya amince da maganar mutumin.

Haka Alhaji nan ya É—aga wayar shi, ya kira wata number yayi magana ya kashe, dan danan
muna tsaye sai ga wasu mutane sunzo, suka fito mutumin ya kallesu yace kuyi ma filayen nan
kudi bil hakki.

Dillalan suka shiga suka dud'duba suka tsallaka suka duba nashi anan suka dawo suka ce
Alhaji wannan babbar gona ce, Abun da kudinta zai kama munaga million sha biyar ko sha
hudu, shikuma filinka zai iya kama wa million biyar ko hudu da rabi.

"Alhaji yayi dariya yace to masha Allah, yanzu kai malam yana nufin Baba'na kenan, yace
kasayi filina million biyar nikuma zansai naka million sha biyar in'yaso sai in maka cikon million
goma.

Nida Baba duk muka É—imau ce Jin zancen miliyoyi, Baba yace an'barmaka Alhaji nan da nan
akai komi, mutumin yace in ba damuwa mu bishi gidan shi ya bamu kudin. haka muka bishi ba
tare da far'gababa, yabamu kudi cike da manyan jikku na na bacco, anan Baba yakwashi kudi
mai yawa yabama dillalan'nan ya masu sallama suka rabu tare da shedama Alhaji zaikawo
ta'kaddu shima a'bashi nashi, muka yo gida nida Baba'na munata murna, muna zuwa mukayi
shagonshi dan bamu da inda yafi nan, shine wajen sirrinmu.


_Muka shiga nida Baba muka kulle, nan na fara tsalle ina Baba munyi kudi wallahi ."

"Baba yayi dariya yace Uwata kinyi kudi dai, wannan duka na kine wallahi babu a'bunda zanyi
dasu, inaso in- in ganta rayuwarki dan nason mahaifiyarki bata sonki, duk ranar da akace bani
a'doron duniya zata iya am'fani da wanna damar taga ta kassara rayuwarki, shiyasa nima na
zabi wannan damar dan in in'gata rayuwarki..
Nan na fara kuka ina mamakin wani irin Uba Allah yabani, da bai damu da rayuwar shiba kamar
yanda ya damu da rayuwa ta, bata farin cikinshi yakeba ta farin cikina yake..

"Na duk'a k'asa ina ma Baba godiya yace in tashi in zauna muyi magana ta fahimta."

""Haka na zauna ina kallonshi nace Baba ina jinka.
"Yace Uwata mizakiyi da kudinnan?

Nace Baba ina so kabiya makka kaje, kanan ina so infara sana'ar saida kaji dan inason kiwo
Wallahi."

Baba yayi dariya yace kai Uwata badai shirmeba, to tsaya kiji shawara ta a'nan.

Naji zan'je makka ko dan sauke farali tinda Allah yabani iko amma tare zamutai dan bazan tai in
barki ba, abu na biyu zan gina maki wannan fillin, sannan zansai maki wani filli dazai zamana
kamar gidan gona ne, za a'samaki tsun'tsaye ko wane iri,tinda ga kan shanuwa har Abun da
yakawo tan'tabara zansamaki kinji ko Uwata. Nai tsalle na rungume Mahaifina na mai godiya, nace Baba to Ammi fa.?

"Baba yace ai'kinji tace haihuwa zatai ,sai mun dawo muga ni."

Nace to Baba da kudin dinki na a'gyaramana wannan gidan namu mana.

Baba ya amince! tin a'ranar da yamma yakira wasu suka shiga suka ga Abun da ake bukata
sukayima Baba lissafi yabasu kuÉ—i suka fara yo sayayya.
Washe gari Baba yacema Ammi ta shigo shagon'shi za a'É—anyimana gyare- gyare, Ammi
tace Allah ya kiyaye ta zauna kusa da ni, tai tafiyarta tallar ta ko kunya babu, ga tsohon ciki dan
ma tana do guwa ba a'gani sosai.

Sosai akaima gidanmu gyara nagani na faÉ—a har kyaure aka canza, aka fidda É—akin Ammi,
dana Baba da nawa, ga tiles wajen yasha kai kudi sunyi, rana daya a'kayi a'kamana har fenti ,
da daddare muka shiga muka samu muka kwanta, washe gari nida Babba mukaje kasuwa
mukayi sayayya a'kasama Ammi gado da kujeru, nikuma ka tifa babba, Baba ma ka tifa kawai
ya saya sai yasaiman babbar waya yasai karama yasaima Ammi ma karama, atakaice dai
sabuwar rayuwa muka fara dan har kayan kallo yasaiman yar karamar tv ta bango da star time
yama kalaman.

Koda Ammi tadawo taga yanda a'kaima É—aki ta daka wani tsalle tare da bugo ashar tace wai
ina kuka samu kudi haka?, ku kayi wannan gyaran hadda wani gadon munafurci kuna nufin
kudin wakar ne ko-ko.

Baba yayi banza da ita ya kyale, tagama Abun ta ta shige É—aki tayi shuru,.muka kulle
É—akunan mu mukaje shagonshi da yasanya shima akaimai gyara muka ga komi yatafi
dai-dai,nan yaceman muje mukaima wannan mutumin takaddu "haka mukatafi mukaje har
gidanshi muka kai mashi Yayi ta kallona har yakasa hakuri, yace ma Baba wai Amma auta ce
ko? Naga duk inda zaka malam saida ita .

Baba yayi dariya yace aa Alhaji ta fari ce, na zaɓi hakanne kawai dan na tsuwata da kuma
kwanciyar hankalinta .

Alhaji yajinjina ma Baba sosai yana ganin duk yanda ya keson É—anshi ga wanda yadamashi
yashanye.
Baba yace yawwa Alhaji dan Allah kukuka son ta kan gari, inaso zan saya ma Moopy wani fili

tana buk'atar tayi gidan gona


Alhaji yace abu yazo cikin sauki inada wani fili a'nan kwado in kunada buk'ata sai muje kuga ni
tinda bana komi.
""Baba yace muje!!! haka mukata fi mukaga wannan filli ba laifi babbane sosai kuma a'bakin
hanya yake, Baba yace Moopy kina son nan? nace eh Baba wallahi ina so dan wurin yaman
fiye da wancen na goruba.""

""Baba yacema Alhaji yallabai wannan yamata tace.
Alhaji yace" ba matsala Amma wannan million daya nasaye shi satin daya wuce, kana iya
maidaman kudin.
Baba ya duka yanama mutimin godiya, Alhaji ya É—agoshi yace bakomi Wallahi mun zama
É—aya, bani ma number wayaka? Baba yabashi sukai sallama.
A"Takaice sanadin hakan shak'uwa da yawa yashiga tsakain su har sukazama Aboka komi
Baba zayyi saida shawarar Alhaji nan,da har yau banson sunan shiba.

Baya wata biyu anyi nisa da fara ginaman wannan gidan, inda Alhaji yadauki nauyin masu ginin
dan masu yima yaron shi sune sukeman nawa, dan har an'kusa rufe kwano sama, anyi komi
hada bene nace inaso dan ina maseefar son bene.

Muna zaune shago muna �inki nida Baba sai ga wata dalleliyar mota tayi parking akusa
damu, mukai tsaye muna kallon mai motar har ya bude yafito,
Tare muka mike tsaye nida Baba nace yaya Rafel........��
25/03/2022, 22:29 - Khadeejaht Salisu Fari: ��💘��💘��💘��💘
ZAMAN TASHA
💘��💘��💘��💘��
NA UMMY AYSHA
��💘��💘��💘💘��


🔔📚
*JARUMAI WRITER'S ASSOCIATION📚*
_{Marubuta masu aiki da jarumta domin wa'azantawa ilimantarwa, nishad'antarwa tare da
fad'akarwa da jama'a bisa harshen hausa}_
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=337435884671992&id=103920888023494&sfnsn=
mo

*⚜�©J.A.W📚🖌�*

🅿�3�⃣7�⃣&3�⃣8�⃣

"""Rafel daya zama Babban mutum ya kalleni cike da mamakin girman danayi Ya ce "Moopy
kina lafiya ashe haka kika zama!."



"Na sakar mai murmushin da in kaga inayin shi to da Mahaifi na ne, na gaisheshi "ya amsa," na
kalli sa'shin da gudan yake d'ansu biyu ne, in ban manta ba shine mai latsa computer nan, na
gaida shi ya amsa min cikin kulawa..
"Baba Ya ce" sannun ku da zuwa yan samari."

"Rafel ya sosa kanshi dan yama manta da Baba.." Ya ce" yawwa Baba "ina wuni".
Baba ya amsa cikin kulawa tare da basu wani table yace su zauna akai.

Basu musa ba suka zauna" Baba yabude �an fridge din da yasaya saboda masu kawoman
d'inku na, ya d'akko ruwa ya d'ora akan flat yabasu, "sukayi godiya suka fasa suka sha.
Bayan sun gama "Rafel yayi gyaran murya tare da du'kawa kasa yada fa kafafuwan Baba Ya ce
"baba a'karo na karshe nazo neman Alfarma awajan ka... Baba , dama tasamenu zamuyima
wani babban d'an siyasa waka, "Baba duk macen da tazo zamuyi tare sai in raina ma sautin ta,
"Baba dan girman Allah kataima kaman Wallahi Mu Marayu ne nida k'ane na ka ganshi nan
sunashi Fahad, Muka d'ai iyayen
mu suka haifa...In Allah yataima ka mamu bakaramar samayya zamuyi ba...


Baba "Ya ce Allah sarki Allah ya gafartama su da namu baki �aya". A'zahirin gaskiya d'an
samari ni nayi niyyar barin ta duk sadda kazo a'karo na ba a'dadi, zan bar ta tama ka wakar
kamar yanda ka keso, ada d'in ma na fad'ama ba zanso ta hada iliminta da wasu wakoki ba,
amma a'yanzu nason Uwata zata iya 'karawa da kowa ta wannan fannin bani da haufi, sai dai
har gobe a'bunda nikeso in fadamaka bazan iya barin ta ta tafi wajen ka ba Ita kadai...Amma
namaka Alkawari zan dinga kawota dan dama yau zanje in'sawo machine, kaga fad'uwa tazo
dai-dai da zama kenan .

Rafel "Yace Alhamdulillah!!!Wallahi Baba nama rasa da bakin da zan gode ma ni hakan ba
matsala bane a'wajena indai zaka bartan..

Baba Ya ce" na bar ta Allah yasanya ku fara asa'a, Allah kuma ya tsarka'ke halshenku daga
fad'in abunda ba dai-dai ba.

Rafel "Ya ce Ameen ya rabbi!! Baba inba damuwa ina so mud'an fara bitar abun a'yanzu,
saboda a'gobe nike so mu buga wakar, jibi kuma a'fitar da ita Insha ALLAH..

Baba "Ya ce wannan ba matsala bane, bari in'ba ku waje. "yakoma daga bakin kofar yayi

zamanshi yana hango su... Anan wanda aka kira da Fahad ya dakko wata doguwar paper
yabama Moopy, itama tari ke tana jin shaukin abun a'ranta.. Rafel ya fara duba rubutun cikin
sanyin muryar da Allah ya hore mai ya fara sarrafa wakar kamar dan halshan shi akayi, bayan
yagama yacema Moopy koza ta iya yinta akan salon da yayi tashi. "ta d'a tamai kai cike da
zakuwa."

Fahad ya kunna recording d'in wayarshi, "Na d'auka na fara sarrafa halshen na kamar wadda ta
shekara tana waka, cike da kwarewa na ke zubo baiti " har wani juya kaina nake ina lumshe
idona, Fahad baison sadda ya aje wayar akan cinyarshi ba, yabfara yiman tafi, dan na masifar
tafiya da imanin shi ..."Rafel kam har hakorin shi na kurya ina kallo saboda fara'a, ina gamawa
Rafel yasa ki kuka kamar yaro... Ya ce" wallahi moopy nason mu zamuyi na farko."

Fahad ya kunna wakar!!

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login