Showing 27001 words to 30000 words out of 53627 words

Chapter 10 - Tsuntsu Mai Wayo Complete Book by Fadila Lamido.txt

Advertisement

09 Aug 2025

2007

daddy bana son shi ,ni da ku had'a ni da yaya haydar gara asamu ko almajiri ne ahada ni dashi daddy haydar fah mazunaci ne kuma.... alhj yusuf ne ya daka mata tsawa , hunnun ta tasa dukka biyun ta toshe bakin ta tana fadin na shiga
uku.

alhj babba yayi tariya irin nasu na manya ,sannan ya kalli haydar yace haydar kai baka ce komai ba.

kan shi akasa yace ai alhj da dai zaku cenza shawara da yafi danni inason in aure wayayyiyar yariya ne kuma ma ni ai jinin mu be hadu da wannan fatimar ba.

daddy ne yace zai hadu nan gaba dan babu wani uzurin ku da zai lalata mana shiri, mun riga mun gama shiryawa.

haydar babu abin da yake sai share zufah itako fatima kuka take harda majina.

ummi ko tana gefe ta hada rai maganar fatima ce take mata yawo wai fatima ce ke cewa haydar mazunaci wato ita ta manta da tabon da yake jikinta dan ma ta samu za,a rufah mata asiri tunanin ummi kenan acikin zuciyar ta.

alhj babba ya dubi ummi yace hafsat naga kamar bakiyi farin ciki da wannan auren da muke son hadawa bane?

nan danan ummi ta saki fuska tace alhj ba haka bane akwai dai abin da nake tunani ne kaga yaran nan bashiri suke ba ina jin tsoro abarsu agida su biyu dan ni dake zaune dasu ni nasan halin su.

alhj na dariya yace ki daina jin tsora hafsat, babu abin da zai faru dalilin dayasa nace ahada su aure kenan, yusuf ya gayamin halin da suke ci ,dan haka naga idan muka barsu ahaka zasu haifar mana da gadaddiyar gaba, kinga auren da zamu hada su zai dakatar da gabar daman bahaushe yace _*tsuntsu me wayo ta wuya ake kamashi*_

cikin kuka fatima tace alhj indai dan muna gabane za ahadani dashi toh wlh daga yau na bari ,bazan kara gaban dashi ba, dan Allah ajanye maganar auren nan .


duk falon dariya sukayi ban da ummi da haydar.

bayan alhj ya gama darawa yace fatima ni zakima wayo toh naki wayon aure nan babu fashi idan kinga ba ayiba toh dayan ku baya nunfashi, ya waiga gurin ummi yace hafsat na amshi uzurin ki dan haka acikin gidan nan zasu zauna kicigaba da lura da irin zaman da sukeyi kafin wani lokaci.

nan danan ummi ta washe baki tanawa alhj godiya.

sanna ya sake cewa ke kuma fatima tashi ki hada kayanki kibi baban ki ya kai ki gurin mahaifyar ki kafin ranar daurin auren


sumi sumi ta mike ta fita shima haydar mikewa yayi ya fita

gaba daya kayanta dake gidan ta hada ta fara fitowa dasu ta sawa amotar alhj yusuf har ta gama kuka takeyi motar ta shiga ta zauna har sun fara kokarin fita daga gidan alhj babba ya kalli Fatima yace

" kinyiwa ummin taku sallama kuwa?

cikin kuka ta girgiza kai.

cikin fada baba yusuf yace aiko ranki zai baci.

da sauri ta fita daga motar har tana tuntube.

kofar ummi ta tura tare da sallama ganin haydar tayi kwace akan ciyar ummi sai buga bayan shi take kamar me lallashin karamin yaro.

duk d'agowa sukayi suka bita da kallo har haydar.

ahankali tace ummi muntafi.

cikin ya tsuna ummi tace hmmm fatima kenan wai har ke ce kike cewa haydar mazinaci ke kin manta tabon dake jikin ki, ai haydar rufah miki asiri zaiyi kuma kome d'a namiji yayi ado ne .

har ummi ta gama maganar ta haydar be d'ago ya kalli fatima ba.

itako fatima kara rushewa tayi da kuka tana me bakin cikin abun da ya same ta gashi har an fara goran ta mata lallai kowaye yaketa mata mutuncin ta ya cuceta take ta tuna sunan da taji abokin sa na kiran sa da shi wato big boy tana tafiya tana fadin big boy ka cuceni in Allah ya yarda sai Allah ya karbamin hakki na dahaka ta isa motar ko ahanya kuka take sosai dan haka alhj babba yita mata nasiha.

bayan sun sauke alhj suka nufa gida


har suka shiga gida alhj yusuf ko kallon inda fatima take beyi ba, afalo suka samu mama tana kwance akan kujera, tana ganin su ta mike tace alhj lfy na ganka da fatima?

zama yayi yacire hula sannan ya kwashe komai ya fad'a Mata, sannan ya kara da cewa kiyi mata fad'a sosai dan na kula so suke su kawo mana rabuwan kai , ya kalli fatima yace

" fatima kece karama Ina rokon ki da ki kwantar da kai kinga haydar ya fiki wayo tunda yayi mgn su daya yaga ba,a goyi bayan shi ba ,be sake cewa komai ba, dan haka kema kiyi hakuri da hukuncin da aka yake akanku , bana son naji kin sake cewa baki son haydar.

cikin kuka tace toh.

daga nan be sake cewa komai ba ya tashi ya shiga d'aki.

mama tasowa tayi ta dawo kusa da fatima ta dafata sanan tace

" fatima wai me ya had'aki da haydar ne wannan abin naki yayi yawa fah.

cikin shashekar kuka tace mama wlh bansan dalili ba nima haka na tsinci kaina.

shawarwari mama taita bawa fatima har ta dan saki jiki.

ranar da fatima tayi sati 1 dawowa gidan tana kwace afalo hannuwan ta duk suna kan fuskar ta hawaye ne ke tsiyayo mata, tana cikin haka taji sallaman haydar , kara damke idonta tayi kamar me bacci tana jin su suka shigo har takiyan falon shida anas.

zama sukayi anas na fadin maryan tamu ma bacci take, haydar yaja tsaki yace

" bawani bacci zama tashi ne"

daidai lokacin mama ta fito tace a,a su haydar ne?

eh mama ai mushigo ba kowa afalon sai fatima tana bacci sai ma asace ta bata sani ba

dariya sukayi har mama amman mama tasan cewa fatima ba bacci takeyi ba.

komawa d'aki tayi tabarsu afalon .

mama na barin falon haydar ya mike yaje gaban kujeran da fatima take ya sauke ahannuta ya kama hancinta ya matse.

da sauri ta fara cikicikin kwacewa tana bige hannu shi.

sakinta yayi yana fadin munafukkar yariya ai kin kusan shigowa hannu na sai kin gane baki da wayo yar kauye kawai kuma bari kiji na fada miki kin ga wannan hijjaban naki karki sake kizomin dashi gida na ,idan kuma kin ki ji toh kizo dashi ki gani, dashi zan shake ki, ni ba salis bane ni nan da kika ganni mugu ne


πŸ•ŠπŸ•Š
Mmn Yazeed
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
[8:17PM, 4/4/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_

πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š


_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*



56 - 58



Bata ce komai ba in ban da binshi da kallo da take.

komawa yayi ya zauna sannan ya sakke kallon ta yace

meye kika tsare ni da kallo dawani idon ki sai kace na mujiya.

mikewa tayi tana tafiya tana fadin toh me zankalla agurin ka inban da kayan haushi tsaki taja ta shige d'aki.

haydar ya girgiza kai sannan yacewa anas yariyar nan tana wasa dani, amman ba komai bata sanni bane ba dai zata shigo hannuna ba, saita gane shayi ruwa ne.

anas ya tabe baki yace kai matsalata dakai baka daukan shawara, matsalar ka yawa gareta


suna cikin haka sukaga fatima ta dawo ranta bace nesa dasu ta zauna tana zubura baki.

anas ya dube ta yace fatima dama munzo muji ko akwai wani abun da kk bukata sabo da kinga lokaci yana zuwa yama zo.

kasa cewa komai tayi hawaye na tsiyayowa a idon ta tayi matukar bawa anas tausayi.

haydar KO yi yayi kamar besan sunayi ba, sai danna waya yake.

ahankali anas yace fatima kin yi shiru bakice komai ba, kodai na samu taslim ne muyi mgnr?

kuka ta kara rusawa ta kasa furta komai.

anas ya mike yaje har kusa da ita yace haba fatima me yasa kikeyin haka irin wannan ai sai kijawa kan ki wani ciyon.

sai alokacin haydar ya kalleta yace

" kai kake wani lallabata karabu da ita mana tayi kukanta idonta ne zaiyi zafi, kuma bari kiji na fad'a miki kinga irin wan nan kayan dake jikin ki karki zomin dashi gida na dan ni bana ra,ayin su .

" ahankali tace ni dama nace ne kayi ra,yin su, ni Ina ruwana dakai"

mikewa yayi da sauri ya fizgota anas ne ya rike shi yana fadin ya haka ne, kamanta a inda ka ke ne.

da sauri ya saketa yace ai zan rike ki, kuma karkiga kaman wai ina son ki ne ,ni bason ki nake ba, kuma bazan taba sonki ba amman yazaman miki dole kisamin irin kayan da nake so ,ke dole ne ki kumin biyayya ko kin ki ko kinso.

mikewa tayi tana tafiya tana fadin wlh baka isa ba wai kai nan har kana ganin kai namiji ne, katon banza dan daudo kawai.

binta yayi aguje ya ya damke ta ya fara kai mata duka abaki

fatima ihu take tana kiran mama amman taki fitowa.
.
daker anas yaja haydar suka fita agidan .

fatima d'akin mama ta fad'a ta fashe da kuka tace mama kinaji yaya haydar na duka na shine kk barni ya sheni ko?

muryan mama taji cikin kuka tana cewa

Fatima me kk son nace muku sai da baban ki yace miki haydar ba sa,an ki bane kece karama ke ya kamata ki kwantar dakai, ya kamata ace yanzon kin hakura kibin umarnin mu kuma da kk cewa na Bari ya kashe ki, idan na ceceki yau idan kk je gidan shi zan biyu ku ne domin inceceki?


tana kuka take fadi mama toh ai shine yake fadamin bakaken maganganu shi baku ganin lefin shi sai nawa.

toh shikenan karki bari ke zaki sha wuya ni babu ruwana.

haka kwanaki sukaita tafiya mama da ummi a nata shirye shirye fatima ko sai ramewa takeyi kulum cikin tunani.

fatima ce kwace akan sallaya ta kudun dune kanta cikin hijjabi hayaniya muta ne ta faraji afalo ,dumin yau sauran kwana biyu daurin auren.

cen ta ffara jin gud'a, tsaki taja ta kara kudun dunewa har da toshe kunne.

tana nan kwace taslim ta shigo da gudu tace sister , da sauri fatima ta mike tace

taslim sai yau kk ga damar zuwa?

dafah ta taslim tayi sannan tace fatima meya sameki kk rame haka baki da lfy ne?

hawaye ne ya fara zubo mata ahankali ta bude baki tace toh ba dole na rame ba, wai arasa wadda za,a had'ani dashi sai haydar dan dai kawai anga babu yaya salis nasan daya nan bazai bari ayi wannan auren ba sabo dashi yasan waye haydar .

itama taslam kuka ta fara sannan tace

sister kibar wannan mgnr kema kisan da ace yaya salis nanan baza,ace ki aure yaya haydar ba kuma kema ya kamata kiyi hakuri da yaya haydar din kinga fa kamar su daya banbancin kadan ne.

cikin fad'a tace wace miki kyaun fuska ko na jiki nake nema, niba kyaun su ke gabana ba nasan naso yaya salis ne saboda kyawawan d'abi,un sa bawai dan wani abu nasaba kamar yadda kk tunani.

taslim share hawayen fuskarta tayi ta mike sannan tace sister bazaki gane ba, yazon dai ki tashi muje anas najiramu zai kaimu lalle.


itama mikewa tayi tana bin bayan taslim tana fadin ni bazayi lalle ba.

suna fitowa falon fatima taga mutane cike afalon suna kallon akwati sai d'aga rigunan suke suna dariya daidai lokacin da wata mata tace ikon Allah dube wata riga saboda lalacewa wannan ai da ita gara babu kuma duk su sukafi yawa acikin kayan.

hjy amina kawar mama tace ai wannan kayan da kika gani Allah kadai gasan kudin da aka kashe gurin sayan su.

dayar ta sake cewa komai tsadar su ni basu dameni ba dan wlh da ace 'yatace aka kawo wa wannan kayan mayar dasu zanyi haba dubi fah dan Allah sai kace na 'yar arna daga wandona sai wasu yan iskan riguna sake daga wani tayi tace wannan kuma menene?

gaba daya falon akasa dariya ban da mama dumin matar ta fara bata haushi .

itako fatima kitchen ta nufa tanajin maganar da matar ke fad'a dan haka ta fara kuka.

saida mama tasa baki sannan fatima ta yadda tabi taslim, sai dare suka dawo , mama ta kalli fatima tace

kinga har kinyi kyau, dan Allah kirinkka cin abinci kidan ciko kafin jibi..

turo baki tayi tare dasa hannuta ta goge fuskarta.

ana gobe dauri auren ne fatima taita addu,a Allah yasa abin da ya samu salis shima haydar ya faru akansa kafin daurin auren.

washegari da rana aka daura auren haydar da fatima acen gidan kakan su alhj salisu.

tunda fatima ta samu lbri an daura auren hankalinta yayi mummunan tashi.

daddare abokan haydar ne sukazo daukan amarya.

kuka tayi ba kad'an ba da za,akaita gidan haydar.

wani sabon gini kayi kafen nasu ummi nan aka nufa da fatima fuskar ta rufe yake.

abakin gado aka zaunar da ita tana rusa kuka, bayan kowa ya wuce aka barta ita kai tana kuka ta mike ta cire gyalen dake jikin ta dauko wani zunbulelen hijjjabin ta, ta saka ,komawa tayi cen lungun gadon akasa ta kwata ta kudundune acikin hijjabin

zuwacen ta farajin takun ta fiya alamar ana tahowa dakin cen taji an daki kofar garramm.


πŸ•ŠπŸ•Š
Mmn Yazeed
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
[8:15PM, 4/5/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_

πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•ŠπŸ•Š


_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*


*Aslm 'yan uwa da abokan arziki Ina mika gaisuwata agare ku bansan taya zan nuna muku farin ciki naba akan yadda kuke nuna soyayyar ku ga wannan lbrn musam man 'yan group d'ina fadeela lamido novels πŸ‘βœ”βœ”βœ”β€β€*



59 - 60


Kara takurewa tayi guri daya, jikin ta ya hau kerma dan jitayi yau balakin tsoron shi take ji.

shikuwa haydar ganin bata cikin d'aki ya tsaya yana kallon kofar toilet zuwacen yaje ya tura kofar toilet din ganin da yayi babu kowa yasa shi zagayowa lungun gadon , da saurin sa yasa hannu ya jawota saida ya jawota har saitin kafarshi sannan ya cikuikuyeta acikin hijjabin , zama yayi bakin gadon sannan ya dauki kafarshi daya ya daura akan cinyarta, saida ya kureta da ido sannnan yace

" ina wasa dake ne, bana ce karkizo min da wad'an nan hijjaban ba?

jikinta na rawa tace mantawa nayi.

yana murmushin mugunta yace eh ai naji dadi da kk manta daga yau idan nabaki umarni bazaki manta ba, mike tsaye.

da sauri ta mike sannan yace ki cire hijjab d'in' ki mikomin

tana rawar jiki ta cere ta aje agefen shi.

haydar ya lura fatima ta firgita dashi dan haka yayi murmushi ya kara cewa ki bude kunnuwan ki da kyau daga yau karna kara ganin ki da hijjab, wai ke adole kina boye min breast d'in ki, toh indai nine ko abude kika barsu babu abin da ya dameni dasu idan kuma bakiji ba toh kikara sakamin hijjab kiga ni dake da abin da kk boyewa zaku gane baku da wayo.

cikin sauri yabar daki fatima taja Wata ajiyar zuciya ta koma bakin gadon ta kwanta ,kasa bacci tayi sai cen wajen asuba bacci ya kwasheta.

washegari

bayan haydar ya gama shiryawa bebi takan fatima ba dakin ummi sa ya nufah.

yana shiga ta washe baki bayan ya gaidata tace

" haydar sai yanzon da na ganka hankali na ya kwanta dan d'azon taslim taje kai muku breakfast ta dawo wai tata mugawa ba,a bude ba, sosai hankalina ya tashi dan gaskiya fatima tana bani tsoro.

murmushi haydar yayi sannan yace


ummi ki kwatar da hankalin ki bazata yimin komai ba duk cika baki ne kawai.

shiru tayi zuwa cen tace toh ina fatiman ko bazata gaishe mu bane.

dukar dakan shi yayi sannan yace

ummi bacci take har yanzon bata tashi ba .

tiren dake dauke da kayan kari taslim ta aje gaban shi nan da nan yahau ci suna hira da ummi.

be dade da faracin abin cinba fatima ta shigo sanye da riga da siket na atamfah tayi matukar kyau .

ummi ce ta fara ganinta kyau taga fatima ta kara yi mata dan ita kanta rabon da taga fatima babu hijjabi ta manta Kai Allah yayi halitta babu makusa .

sakin fuska tayi sannan tace

a,a fatima har kin tashi.

kanta akasa tace eh ummi ina kwana.

cikin fara,a ummi ta amsa.

shiko haydar tun da ummi ta kira sunan fatima ya d'ago kai ya kalleta kasa dauke idonshi yayi har ummi ta lura da haka.

murmushi ummi keyi sosai tace haydar gyarawa fatima ta zauna kuci abincin tare.

sai alokacin ya sauke idon shi.

ummi ta sake cewa fatima matsa kuci abincin

bata da abin cewa dole ta mike ta isa gurin aksa ta zaune haydar ko yana kan kujera,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login