Showing 24001 words to 27000 words out of 53627 words
Chapter 9 - Tsuntsu Mai Wayo Complete Book by Fadila Lamido.txt
ya bari yayi kalmar shahada, idan na tuna wannan abun hakalina na tashi.
kuka fatima take sosai harda shsheka.
haydar ma haka zuwa ,cen yace fatima kiyi hakuri ki daina kuka
daddy yace ya zaka ce ta daina kuka bayan kai gashi kana yi.
da sauri ya fara share hawaye yana fadin daddy ni ba kuka nakeyi ba.
. yace toh naji haydar Allah yaye muku abinda yake damun Ku.
mikewa fatima tayi zata bar waje idanun ta suka sauka akan kafar haydar kubure take tayi suntun kamar zata fashe dauke idon ta tayi domin har yanzun ganin bakin sa take.
koda suka koma gida ummi batawa fatima mgn ko gaishe ta tayi ayatsune take amsawa.
haka sukaci gaba da tafiya gidan babu dadi ko kadan har salis yayi arba,in.
fatima ko ta kara lalacewa.
daddy ya lura fatima dakin salis take shiga shi yasa hakalinta yaki kwanciyai dan haka yasa aka kwashe komai dake d'akin aka fitar dashi aka rufe dakin
ranar taci kuka kamar ranta zai fita.
shi ko haydar sai da yayi wata uku cur asibiti amman duk da haka kafar bata takuwa dan haka aka bashi sanda anas ko tuni aka sallame shi.
taslim da fatima ne zaune afalo kowa yayi shiru dan yanzon gidan haka ya koma gani sukayi anfara shigo da kaya ana shiga dashi dakin dake kallon na ummi fatima tacewa taslim wannan kayan fah?
atakaice tace yaya haydar ne zaidawo dakin yau za,a salamamoshi .
mikewa fatima tayi zata bar wajen taslim tace sister dan Allah ki rage nuna ma yaya haydar kiyayya abin da kk yi sister yayi yawa gashi har kinsa ummi ta farajin haushi ni ban san me yamiki ba har kk tsane shi haka.
cikin kuka fatima tace bakisan abin da yamin bafah kk ce ?, duk wannan abun da ya faru waya jawo shi inba shi ba, ai yasan yaya salis bazai so ace baya gurin ba amman ya wuce gantalin shi inda beje neman shi ba da yanzun muna cikin farin ciki, dan haka ni gaskiya bazan taba ganin farin haydar ba, ya cuce ni ya rabani da farin ciki na, ke badan ina tsoron Allah ba dasai na kashe haydar in yaso nima akasheni, dan rayuwana bata da wani amfani
muryan ummi sukaji tana fadin aiko zaki bar gidan nan tun da kin fara fado kalmar kisa bari alhj ya dawo.
batace komai ba ta koma daki taci gaba da kukan ta zuwa cen taji shigowan su daddy harda babanta azuciyarta tace ankawo Dan iskan nan kenan.
baya su alhj yusuf sun rako hayadar gida sun koma, ummi da daddy suna zaune abakin gadon da haydar yake ummi tace alhj Ina da magana.
toh inajinki me ya faru?
alhj ni gaskiya nagaji da zama da fatima ta koma gurin mahaifiyarta.
damamaki akan fuskarshi yace me kuma ya faru?
komai ta kwashe ta gayawa alhj haydar najin su .
nufasawa alhj yayi sannan yace
" wlh hafsat kin ban mamaki yazun sabo da Allah fatima zaki biyewa wa , menene ke damun fatima yan zun ban da kuruciya da zafin mutuwan salis dan Allah karki kuma saka wannan mgnr a lissafi idan kinji tana irin wanna mgnr nasiha zakiyi mata ina tabbatar miki da ace nasiha kike mata da tuni ta bari, kuma daga yau inason ki dauki fatima kamar taslim.
ummi tace shikenan alhj dama ni tsanar da naga tana nunamai ce tayi yawa.
wannan babu ruwan ki ni nasan maganin abun zama ta bari ne.
suna cikin haka haydar yace daddy inason na dan watsa ruwa.
da sauri daddy ya mike ya kama haydar ya mikar dashi tsaye ummi ta mikamai sandar sa daddy na rike da daya hannu shi har suka isa toilet din dake dakin , ummi fitowa tayi ta barshi da daddy zuwa cen shima daddy ya fito.
washegari da daddare daddy yace wa ummi ki shirya maza kizo muje cen babban gida.
kallon shi tayi tace
" alhj kana nufin haka zamu tafi mubar haydar shi kadai idan wani uzunrin ya tasan masa fah gashi taslim tana cen gidan.
gaba daddy yayi yana fadin nifa banason mita kizo muje yan zon zamu dawo.
haka ummi tabi bayan shi badan ranta yaso ba.
fatima ko tana ganin fitan su ta sake wani murmushi wanda rabon da tayi irinshi tun kafin rasuwan yaya salis tashi tayi da sauri ta nufi dakin haydar ahankali ta tura kofar ta shiga
ππ
Mmn Yazeed
πππ
[9:33PM, 4/1/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
46-48
Ganin shi tayi kwance yana bacci a hankali ta isa gaban shi kare mashi kallo tayi sannan taje saitin kafar dake da ciwon ahankali tasa hannu ta rike kafan.
ganin da tayi be motsaba yasa ta dage iya karfinta ta murde kafan, kara ya saki me firgitarwa.
uhun da yake besa ta saki kafar ba ci gaba tayi da murdewa.
haydar ya hada zufa yana kurma ihu zuwa cen ta saki kafar ta matsa nesa da gadon ta kwashe da dariya.
haydar ko ihu yake yana salati yana kiran ummi da dadddy .
bayan fatima ta gama dariyarta ta tsaya ta hada fuska sannan tace haydar kadan ka gani indai ni ce kuma da izinin Allah sai an yanke kafar nan, fita tayi adakin ta koma nasu dakin ta kwanta daga dakin tanaji uhun da yake, amman ko ajikin tana cikin bargo ta shige ta rufe idanuwa.
zuwacen taji shigowan ummi aguje tana fadi ihun me kk yi haydar.
ganin shi tayi kwance inda ta barshi sai dai ya mirgina yana kokarin kai hannun shi kafar yana fadin zan mutu daddy Ku taimake ni.
adaran ranar dai basu runtsa ba suna kan haydar kwana yayi yana kuka da kafa dan haka washe gari aka fara cukucukun barin kasar dashi.
fatima ko ranar tayi kwanan farin ciki
da safe alhj yusuf yazo suka dauki haydar aka maidashi asibiti.
bayan tafiyan sune ummi ta shigo dakin su fatima ganin ta tayi zaune tana duba takardun makarantar ta saida ta kare mata kallo sannan tace.
yanzon sabo da Allah fatima abin kikayi ya dace kenan?
jitayi gaban ta ya bada dam dan ta zata haydar ya fada abin da tamai ne dan haka ta kasa cewa komai.
ummi ce ta sake cewa yanzon fatima zakice bakiji ihun da haydar ya kwana nayi ba.
mikewa tayi mama ni gaskiya banji ba bari naje na duba shi.
mama tace ai an mayar dashi asibiti inagama kasar za,a bari dan abin yayi tsanani
washegari aka wuce da haydar London domin asake duba lfyr kafan shi.
*******
bayan tafiyan haydar hankalin fatima ya kwanta dan yazon har tana sakin jiki da kowa na gidan ayi hira ayi dariya amman fah duk ranan da salis ya fado mata haka zata zauna taita kuka har ummi ta saba dan dataga fatima na kuka sai tace abin ya motsa.
kwanci tashi ba wuya gashi har haydar ya cika wata hudu da tafiya kuma da alamun ansamu na sara dan ayau daddy da baba yusuf zasu dawo dan haka yau ummi taketa garke girke taslim da fatima ke tayata.
4:13pm su daddy suka iso gida anas ne ya dauko su.
bayan sunci abinci sun huta ummi ta kalli alhj yusuf tace baku bani lbrn haydar ba.
yace keda kuke waya kullum kuma kike tambaya na jikin shi, ai nace abin naki ko kara babu ke ki kira salamatu ta kira.
dariya ummi tayi sannan tace wlh alhj ciwon ne ya bani tsoro dashi nake kwanciya dashi nake tashi dan gani nake kamar za,a yan ke.
dariya su alhj sukayi sannan daddy yace ai shima har roko yake wai dan Allah ayan ke mai .
ummi tace Allah sarki babana ai yaji jiki.
taslim tace baba yanzon yaya haydar yana tafiya kamar da?
yace ras yake tafiya taslim ai sati me zuwa zai dawo
fatima ko daure fuska tayi domin kuwa bata ji dadin lbrn ba dan ta tabbatar haydar ba zai bar ta ba dan haka hankalin ta yafi na barawo tashi, sai faman zare ido take.
ummi tana lura da halin da fatima take ciki zuwa cen tace alhj na gaya muku abin da kuke kokarin shiryawa bazai yiyuba yanzon ka dubi halin da fatima ta shiga.
hakalin kowa komawa gurin fatima yayi daddy yace fatima me ya faru ?
dukar dakai tayi sannan tace babu komai.
alhj yusuf yace dan Allah ku rabu da ita nasan maganin ta ya nunata da hannu sannan yace wlh karki yadda ki kaini bango dan wlh zanci mutuncin ki fiye da inda bakya zata.
daddy ne yaja alhj yusuf suka fita waje
bayan sati daya
ummi da taslim ne keta girkin tarban haydar ummi ta kalli taslim tace taslim fatima tana bani mamaki kiri kiri take nuna tsanar haydar yanzon ki duba fah hatta me gadin gidan nan murna yake haydar zai dawo amman ban da fatima... wayar ummi ce tayi kara cikin rawan jiki ta dauka tana Fara,a tace haydar yaya ka sauka ne?
daga cen cikin wayar aka bata amsa eh ummi gamu nan ma anas ya dauko ni.
murna ce ta rufe ummi ta mike ta nufa daki.
2:58pm suka iso gidan fira suke suna dariya shida anas amman abin da yaba anas mamaki suna shiga gidan haydar ya daure fuska zuwa cen ya fara kwafa anas ya kalleshi yace haydar lfy kuwa ?
Hmmm anas ina tunanin abin da zanma yariyar nan ne kasan Allah sai tayi nadamar zuwanta duniya
ππ
Mmn Yazeed
ππππ
[7:55PM, 4/2/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
49-51
Anas yace wacce yariya kenan?
" saida yayi kasa da murya sannan yace fatima"
da mamaki anas yace meta maka, ai kamata yayi yanzon ka rinka tausayawa yariyar nan tun bayan rusuwan salis saboda ta shaku da salis.
Hmmm dan ta shaku da salis kuma saita nemi kashini ita fah ta tayar min da ciwan kafar nan saboda taga bana iya tashi tabini har daki ina kwance akan gadona dan tsabar mugunta tazo ta bankaremin kafah.
,dariya anas ya fara sai da yayi me isarsa haydar na kallon sa zuwa cen yace toh ya isheka wlh ka kiyayeni ina nan yadda kasanni ba cenzawa nayi ba
anas ya gintse dariyar shi sannan yace abin ne yabani dariya kaiko kana kwance kabari karamar yariya kamar fatima ta gana maka azaba, kodai mafarki kayi?
dariya haydar yayi sannan yace wlh ba mafarki bane toh yazanyi bacci fah nakeyi kawai naji anrikemin kafah ni kasan ma abin da yafi bani haushi idan na tuna uhun da na kurma amman sai naga ta koma gefe tana kyalketa dariya wato zatace tunda salis ya mutu gara nima na bishi.
anas yace ni kuma atunani na kodai fatima ta gane cewa kaine wadda ka lalata mata rayiwa?
zaro ido haydar yayi sannan yace bana tunanin haka kaima ka daina wannan tunanin idan ba haka ba zaka sa na fasa abinda nayi niyya.
da haka suka shiga falon ummi , ummi ko kunya babu ta mike ta rungume haydar shima kwaciya yayi ajikin ta tana buga bayan shi kamar me lallashin yaro yayi bacci tana fadin mu godewa Allah babana Allah ya karbi addu,a mu.
yana murmushi yace ummi ina godiya da nuna soyayyar ki agareni bansan kuna sona ba ummi sai da ciwon nan ya kama ni.
daga kanshi ummi tayi sannan tace haydar akwai wadda zai haifi dansa yace baya so daman cen munason ka halinka ne bama so dan Allah ka gyara halayen ka ka koma kaman salis
" kasa yayi dakai cikin sanyin jiki yace ummi nima ba ason raina nakeyi ba amman ku tayani da addu,a.
aidama cen muna maka addu,a amman tunda kace haka zamu daura akan na da, kuta shi kuje kuci abinci, anas ga abinci cen.
*******
da daddare daddy da ummi suna zaune afalon daddy fatima tayi sallam ta shigo sanye da hijjab gaban kujeran da daddy yake zaune taje ta zauna ummi ta bita da kallo.
bayan ta gaida su daddy ya kare mata kallo sannan yace fatima me ya faru akwai wani matsala ne?
kanta akasa tace daddy Dama inason nakoma gidan yadidko ne.
murmushi daddy yayi sannan yace kina nufin ki koma cen da zama?
da sauri ta daga kai.
gyara fuskar shi yayi sannan yace saboda me?
ummi ce tayi karaf tace alhj ka mata ne makiyin ta ya dawo
da sauri yace kash haba hafsat wai me yasa kk haka wani irin makiyi kuma ita da d'an uwanta ai babu wata kiyayya tsakanin su , fatima haydar d'an uwanki ne baki da wani d'an uwan da ya wuce shi sai kuma taslim dan Allah ku rungumi juna kinga bayawa gareku ba Ku hudu Allah ya bamu kuma ya karbi daya yanzo sauran ku 3 dan haka muke fatan kuhaifa mana yara masu yawa tunda mu Allah be bamu masu yawa ba
batacewa daddy komai ba tamike tana share hawaye duk suka bita da kallo.
tana kaiwa kofar haydar na sayo kai ko kallon gurin dasu ummi suke beyi ba ya d'aga hannu ya sharara mata Marika har guda 3
wani wawan tsale ta daka takoma gefe ta fasa wani uban ihu domin kuwa Marin sun shigeta.
daddy da ummi kuwa mikewa sukayi kowa bakin shi bude suna kallon haydar
sai alokacin haydar ya kalli su daddy nan da nan ya fara sosa keya , meta maka, tambayan da daddy yayi wa haydar kenan
ahankali yace bigeni tayi.
" shine kamata wannan dukan toh Bari kaji daga yau karka kuma kai hannun ka jikinta , in ban da mugunta ma ko kusa dakai bataje ba , mutumin baza kawai.
ummi ce ta kamo fatima tana ,duba gurin da haydar ya dake ta fatima ko sai kuka takeyi.
itama ummi fada ta shigawa haydar yana tsaye kanshi akasa itako fatima tana kwance jikin ummi.
bayan haydar ya fita ummi takai fatima har daki sannan ta fito ta nufi dakin haydar.
tana turo kofar idonta yayi mata mugun gani haydar ne zaune yana kalon film din batsa ga sigari ahannun shi yana zuka
har takai tsakiyan dakin besan ta shigo ba saboda shagala da yayi da kallon salatin da ummi ta rafka ne ya dawo dashi cikin hayyacin shi da sauri ya kashe tv cikin tashin hankali ummi tace haydar daman abinda kk yi kenan?
kasa cewa komai yayi jiyake kamar ya nutse cikin kasa.
ta sake cewa kai dai bazakaji tsoron Allah ba KO?
nan ma bece komai ba dan haka ummi ta juya ta fita ranta bace.
washegari da yamma alhj yusuf da alhj babbba suka iso gidan su haydar, daman tun kafin sukaraso daddy yasanar musu da zuwan mahaifin shi gidan dan haka ummi ta tanazan musu komai dazasu bukata duk da cewa bata da lfy dan tun sandda tashiga dakin haydar tarasa abun da ke mata dadi.
fatima da taslim KO sunajin tsayowar mota suka rutumo aguje ganin haydar agaban su yasa taslim ta tsaya itako fatima gefen shi tabi aguje taje ta d'ane alhj babba taslim da haydar tare suka iso haydar sai hararar fatima yake.
alhj babba ko farin ciki ne ya lulubeshi ganin inda jikokin sa suke murnan ganin shi, gaba daya suka rankaya sukai cikin gidan afalon daddy su ka zauna.
bayan sun natsune alhj babba yace ni banga salamatu ba.
alhj yusuf yace baba bata jin dadi ne shiya sa bata zoba.
shiru yayi sannan yace toh Allah ya bata lfy ,juyawa yayi ya kali muta nen dake dakin yace toh duk kubani hankalin ku, wani abun alheri muke shirin kullawa tsakanin haydar da fatima .
da sauri cikin fatima ya bada kululuuuuluuu yayin da zufa ya fara karyowa haydar.
ππ
Mmn Yazeed
ππππ
[7:55PM, 4/3/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
52-55
Alhj babba yace in Allah ya yarda nan da sati 2 za,a daura musu aure.
tuni fatima ta fara kuka, xuwa cen ta koma kusa da daddy ta kama kafar shi tace
" daddy dan Allah karka bari ayi haka wlh