Showing 6001 words to 9000 words out of 53627 words
Chapter 3 - Tsuntsu Mai Wayo Complete Book by Fadila Lamido.txt
daya zamu zauna.
cikin sauri salis yace dawa dakai Allah ya kiyaye wlh ba zan zauna dakai ba.
sakin baki haydar yayi yana kallon salis sannan yace salis nine fah.
fuskar salis adaure yace kaidin fah ina hauka ne zan zauna dakai.
daga daddy har ummi basuji dadin maganar salis ba,
ummi ta juyo da kallon ta gurin salis tace
" ni bansan ka da fushi haka ba banji dadin mgnr ka ba idan baka zauna da dan uwan kaba dawa zaka zauna banajin dadin ganin ku cikin wannan halin dan Allah ku zauna lfy.
juyawa tayi gurin haydar ta harareshi sannan tace kai kuma kabashi hakuri dan nasan kaine mara gaskiya.
ahankali yace kayi hakuri in Allah ya yarda bazan kara ba.
har yanzon fuskar salis adaure take dan haka daddy ya kira su gaban shi kama hannun su yayi ya hada yace ya wuce kutashi ku tafi.
suna rike da hannun juna suka fita.
ummi ta dawo da kallonta gurin daddy sannan tace
" salis akwai hakuri amman idan ransa ya baci be iya fushi ba shiko haydar idan be nemi fitana ba bayajin dadi.
ajiyar zuciya daddy yayi sannan yace Allah ya shirye su.
haka rayuwa taci gaba da kasancewa agidan alhj kasim tsakanin salis da haydar yau ayi fada gobe ashirya zuwa anjjima kaga kamar basune suka yi ba.
kwanci tashi ba wuya wajan Allah dan yanzon kusan shekara fatima uku aku agidan, zuwa wannan lokacin shakuwa ce me karfe tsakanin fatima da salis.
yayin da haydar ya hura wutar kiyayar fatima azuciyar shi dan ko mgn bata hadasu da ita
duk da cewa ayanzon idan ka kalli fatima baza taba cewa tayi zaman kauye ba
acin wad'an nan shekarun so daya babanta ya kaita gurin mahaifiyar ta yanzon fatima tana ajin karshi na secondary sakamakon kwanya da Allah ya bata.
ta bangaren ummi kuwa wato mahaifiyar su haydar bata nunawa fatima wani banbanci tsakanin ta dasu haydar dan haka tana cikin kwanciyar hankali matsalar ta daya haydar.
ayanzun dai fatima ta zama cikekiyar budurwa komai na jikin ta ya fito sosai
fatima ce kwace jikin kakarta yadidko tana danna waya yayin da taslim tana gefe tana cin abinci suna fira da taslim.
sallaman alhj yusuf ya katsa musu hira, bayan yazaunaya kalli fatima dake jikin mahaifiyar shi yace ke ashe baki da hankali katuwarki dake zaki kwanta mata ajiki, yajuya ya kalli taslim sannan yace ke kuma bakiyi mata fada.
murmushi taslim tayi sannan tace baba tausa fah take mata.
hararanta yayi sannan yace wai ma me kukeyi agidan nan yau kusan 3 days kenan inaganin ku anan ku koma gidan ku mana.
taslim ce ta amasa munzo tayata zama ne ai yauma zamu wuce.
yace gara dai kutafi hira sukaci gaba dayi shi da yadidko.
zuwa cen su fatima suka fito cikin shirin ta fiya alhj yusuf ne ya kawosu har gida bayan sun gaisa da ummi ya wuce.
washegari fatima nata zuba ido taga shigowar salis har wan 12 na rana bata ganshi ba dan haka ta shiga neman layin shi saida ta kira su uku ba adauka ba dan haka tashiga damuwa.
lokacin da taslim ta kawo musu abincin rana kasa ci tayi tana juya cukalin.
taslim tace sister wai meke damun ki tun jiya naga duk kinyi wani iri.
meko ni bawani abunda yake damu na.
taslim shiru tayi taci gaba da cin abincin ta.
bayan sungama dakin ummi suka nufa suna shiga fatima tace
ummi wai yaya salis baya nanne?
eh bayanan bakuyi waya bane halan?
tace nakirashi yaki dagawa.
ummi tayi murmushi tace kila baya kusa da wayar ne, munyi waya danzon yace min suna hanya.
dariya taslim tayi tace dama shi yasa kika ki cin abinci wai ku soyayya kuke ne?
fatima ce ta harari taslim sannan tace wani irin soyayya.
ummi tace ke rabu da ita neman mgn ne da ita.
dariya taslim ta sakeyi sannan tace wlh ummi soyayya sukeyi.
daure fuska ummi tayi sannan tace wai taslim ina wasa dake ne nace kibar mgnr ina ruwanki da su.
hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace na bari ummi.
daidai lokacin salis da haydar suka shigo bayan sun gaisa da ummi fatima gaida su haydar kadai ne ya amsa shima dan yaga ummi ne hakalin fatima ya kara tashi idonta ya cika da hawaye
ummi ta lura da halin da fatima take ciki bata dai ce komai ba dan bata faye son shiga tsakanin su ba
basu dade ba suka fita zuwa dakin su, fatima ko na gefe tayi tagumi.
ummi ta juya ta kalleta tace
fatima cire tagumin nan tashi maza ki kai musu abinci.
har ta dauki abincin ta tuna salis beson ya ganta babu hijjab dan haka ta koma dakin ummi ta dauki hijjab ta fita.
samun su tayi zaune haydar na nunawa salis wani abu acikin wayar shi sunata dariya aje abincin tayi tajuya har takai kofa haydar yace ke dauki ledar cen ki kaiwa ummi.
dawowa tayi ta dauka ta fita, kafin takai dakin ummi hayawaye ya fara zubo mata saida ta share hawayen ta shiga dakin ummi ta aje ledar ta koma kusa da taslim ta zauna ummi ta bita da kallo batace komai ba ta mike ta fita.
dakin su haydar ta shiga cikin mamaki
suke kallonta.
kallon salis tayi sannan tace waikai yaushe aka daura maka aure da fatima ne bansani ba
da mamaki yace ummi bangane me kk nufiba.
aidama bazaka gane ba kawai dan fatima ta tafi gidan hajiya bata fada makaba kk wannan fushin, matarka ce?
da sauri ya girgiza Kai.
ummi ta sake cewa toh karage wadan nan dokokin takasa mata suyi yawa kuma kazo ka rarasheta
adakin su ya sameta tana kwance tayi rufda ciki ahankali ya kira sunan ta amsawa tayi batare data waigo ba ya sake cewa toh tashin mana.
kintashi tayi dan batason yaga idon ta
gaban gadon yaje ya zauna yace zahara tashi mana kosai nakira ummi ne?
tanajin ya kira sunan ummi ta miki ta fara sakkowa daga gadon binta yayi da kallo dan rabon da ya ganta babu hijjabi ya manta sai yaga ta kara kyau bayan ta zauna ya kalleta yace wato abin harda su kuka?
cikin muryan kuka tace toh bakai bane kake fushi dani.
cikin sauri yace nabari indai nine banason nasake ganin hawayen ki
daidai lokacin haydar ya shigo dakin abakin kofa ya tsa dan haka salis ne kawai yaga shigowan shi
juyawa yayi barayin fatima yace tashi muje gurin ummi.
tana mikewa yace toh kisa hijjab mana.
buga kafa ta fara kamar karamar yarinya cikkin shagwaba tace ni gaskiya a,a nan da dakin ummi saina saka hiijjbi.
binta yayi da kallo zuwacen yayi murmushi yace ji abinda kikeyi saikace wata karamar yarinya
kara shagwabewa tayi
haydar ko dake bakin kofa tuni ya Fara rikicewa dan babu abinda yafi tayar mai da hankali kamar yaga mace tana wannan shagwaban, idon shi nakan kirjinta
salis kuwa ji yake kamar ya rungumita dan betabajin irin yanayin da yaji yau ba, juyawa yayi ya kalli haydar yace waikai wani gulman ne ya kawoka
sai alokacin fatima tasan da shigowan haydar juyar da kallonta tayi gareshi
yace ke dena kallona munafuka kawai me suffar aljanu
salis yakalleshi ya karasa gaban shi sannan yace muje
*******
da daddare duk yan gidan ne suka hadu a falon daddy suna hira zuwa cen daddy yace mun kusa shan biki agidan nan.
Ummita tace dama kuwa inason nama magana tunda su sunki yi .
cikin sauri salis yamike zaibar wajen. alhj yace inakuma zaka dawo ka zauna
bayan yazauna daddy yace yakamata kuyi aure salis kaida nake ma ganin ka kamar me hankali.
ummi tace alhaji ai haydar zakawa mgn shi yariga ya kama tashi gatanan kusa da kai duk da dai ba fada sukayi ba amman duk me hakali yasan sun amice da juna
murna ce ta kama daddy yace toh shine ni baki sanar min ba
dawai inajira ne su fada da bakin su gatanan ansa mata takunkumi zama da hijjab saikace matar liman
taslima ta kwashe da dariya shikuwa salis tunda ya dukar da kansa ya kasa dagowa fatima ma tana kudun dune cikin hajjabin ta
daddy yajuyar da kallon shi ga haydar yace kaifah
Sosa keya yayi sannan yace daddy ni ba yanzon ba.
sai yaushe?
daddy idan na shirya zanyi mgn
cikin fada daddy yace baka isaba rana daya zakuyi aure KO kaki KO kaso kanajina?
daga kai yayi sannan yace daddy inason zamuyi mgn amman su taslim su fita tukum
ππ
Mmn Yazeed
πππ
[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
*Gaisuwa ta mussaman gareku*
_matar abbatie barno_
_hussaina faji_
_murjanatu_
_yahancy_
_hajju_
&
_zinat_
*all in Fadeela Lamido novels group*
24 - 26
Daddy ne ya umarci su taslim da fatima da su fita
bayan sun fita daddy yace toh inajinka.
saida haydar yayi kasa da murya sannan yace daddy dama shawara zan bada yariyar nan fa be kamata salis ya aure ta ba, dan sai da ta gama yawon ta tukun aka kawo ta gidan nan.
da mamaki daddy da ummi suke kallon haydar
daddy yace a ina kaji wannan lbrn ?
kanshi tsaye yace yadidko ce ta fadamin
sai alokacin salis ya dago kai ya kalli haydar
daddy yace hjyr da kanta ta fada maka haka, toh gaskiya bahaka lbrn yake ba kuma ko ba ayi haka ba dama zangawa salis halin da fatima take ciki sannan yajuya barayin ummi yace ke dama tun zuwan fatima gidan nan nafada miki halin da take ciki.
kai kuma haydar karna sakejin wannan kallamar abakin ka fatima bata yawo fayd'e aka mata shine dalilin da mahaifiyarta ta kawota.
kan salis na kasa har yanzun be dago ba hawaye ne kawai ke zubo masa.
ganin halinda salis ya shiga daddy yace wa haydar tashi ka tafi.
mikewa yayi yana kallon salis yana mai farin cikin yau ya dana tarkon shi adai dai.
yana fita daddy ya mike ya taho kusa da salis hannun shi yasa ya dago kansa ganin fuskar yayi tajike sharkaf da hawaye ahankali ya fara sharemai hawayen sannan yace kayi hakuri babana kar kace wannan abun zaisa ka fasa abinda kayi niya inason ka yadda da kaddara mekyau da mara kyau wannan abinda ya faru da fatima zai iya faruwa DA kanwar ka taslima kuma baza mu so taki aurowa ba saboda wannan dalilin, dan haka ka daure,
bece komiba ya mike ummi tace kuma duk abinda haydar zai fada maka karka saurareshi dan na kula so yake ya lalata mgnr.
daker ya bude baki yace toh
yana fita falo yaga wata yariya ta shigo
riga da wando ne jikin ta sunyi matukar matseta cikin mamaki yace lfy wa kk nema.
cikin hausarta wacce bata fita tace dan Allah Ina Neman haydar ne
bece mata komi ba ya yamutsa baki ya shiga daki, yana shiga yacewa haydar kayi bakuwa kaje ka sallameta tunkafin ummi ta fito.
atsorece haydar ya fito yana fadi axuciyar shi wacci yar iskar ce zata Jamai masifa
yana fita sukai arba da ita, wata budurwar shice wacci suka kwashe kusan shekara biyu basu hadu ba suna hada idon suka sakar wa junan su murmushi cikkin sauri ya kamo hannun tasuka fita
salis na lekensu ta window har suka fita sannan ya koma kankujera ya zauna yayi tagumi yana bakincin wannan abu dazai ga wanda yayiwa zahara wanna abu lallai bazasu rabu lfy ba, daren ranar kasa bacci yayi haydar kuwa tunda ya fita sai 7:33am ya dawo lokacin salis ya fito wanka yana kokarin saka riga.
yana shigowa ya fara fadin angon fatima meye lbr kodai haryanzon kana kan bakar ka .
banza yayi dashi ya dauki key din motar sa yayi waje
haydar ko bayan yayi wanka yau be nufi office ba, gidan su wata budurwar shi yaje ya daukota yakaita dakin anas.
ad'akin ya wuni da mubaraka saidare ya maidata gida har ya kama hanyar gida yaji shifa har yanzun hakalin shi be kwanta ba so yake ya sake kasan cewa da wata nan ya fara tunanin wacce yariya zai d'ako wadda zata kwantar mai da sha,awar shi.
tunani ya fara yi cikin yan matan shi wad'an da yake harka dasu wan da besan yawan suba dan sufi dozin, kasa tuna ko guda daya yayi sai dai abinda ya bashi mamaki daya fara tunanin girjin fatima yake gani lokacin da takewa salis shagwaba, lashe baki yayi sannan yace inama nine salis na samu damar da yariyar nan takema wannan girgiza kasa daina tunanin fatima yayi dan haka daganan ya wuce mashayar su yasha yayi tatil besabo komawa gida aranar ba sai washe gari.
damuwa ya taro yayiwa salis yawa abin duni ya isheshi yau haydar kwana biyu kenan be kwana gida ba yana cikin tunanin nan wayar shi tayi kara yana dubawa yaga anas ne abokin haydar da sauri ya dauka cikin faduwan gaba yace anas ina haydar.
daga cen cikin wayar aka bashi amsa gayin nan dama nakiraka ne kazo ka shiga dashi cikin gida bayajin dadi ne, cikin sauri yadar ya mike ya fita.
ganin haydar yayi rike ahannun anas idon shi rufe, yana isa gurin warin giya ya daki hancin shi.
ja yayi da baya daidai lokacin hancin motar daddy ta sawo kai cikin sauri salis ya kama haydar yana kokarin barin wajen dashi, amman ina tuni daddy ya karaso guri yana fadin lfy meya sameshi, salis kasa mgn yayi anas ne yace beda lfy ne
daddy na isa gaban haydar yace innalillahi wa inna ilaihir raju,un haydar dama abinda kake kenan .
juyar da kallon shi yayi gurin anas yace kamayar dashi inda ka dauko shi nabar makushi kar ya Kara dakowa inda nake na yafeshi acikin 'ya'yana.
salis yace dan Allah daddy kayi mai hakuri.
kai salis babu abinda ya dameka dan haka maza ka shiga gida, Ku kuma Ku fitar min agida
juyawa yayi yana waiwayen dan uwan shi har ya shiga gida.
shiko haydar sai dare hakalin shi ya dawo jikin shi anas ya shiga fadamai abinda ya faru.
tashin hankali ya shiga sosai nan da nan ya mike ko sallama bema anas ba.
gidan alhj yusuf ya nufa ya sameshi zaune yana duba wasu takarddu
alhj yusuf yaji mamakin ganin haydar acikin daren nan dan basu cika zuwa gidan shiba sabo da ba mata gareshi ba binshi yayi da kallo sanan yace kai kuma daga Ina?
cikin rawar murya yace baba dan Allah ka taimakeni muje kaba Abba hakuri cewa yayi wai Karna kara shigo mishi gida.
atakaice alhj yusuf yace me ka masa?
kasa magana yayi sai hawayene keta zuba afuskar shi.
alhj yusuf ya sake cewa haydar me yasa bakajin maga ne ,alhj ya dade yana fadamin bakajin mgn kana mutukar bata mishi rai, jiya ya gama cemin wata ranama baka kwana agida, haka ne?
dukar dakan sa yayi kasa bece komai ba.
shima shiru yayi yana kallon haydar zuwacen yace tashi muje
bayan sun isa gidan atare suka fito daga cikin motar alhj yusuf ya dafa haydar yace haydar ko dai aure kk so?
dasauri ya girgiza kai.
murmushi alhj yayi sannan suka shiga har falon daddy
daddy na ganin su ya mike cikin fada yace
meyasa ka shigon min da wannan mashayin cikin gidana.
alhj yusuf yajuya ya kalli haydar yace mashayi kuma.
eh katon mashayi ne ka tambaye shi giya yake sha.
tsayawa alhj yayi shiru daga bisani ya dawo da kallon shi gasu taslim, yace kai ku tashi ku fita, ya juya ya kalli haydar yace kaima jeka dakin Ku.
suna fita alhj yace yaya ni inaganin koran haydar bashi bane mafita ai sai abin ya kara lalacewa addu,a zamuyi tayi Allah ya shiryeshi, kuma ni Ina ganin yakamata amai aure kila ta sanadin haka saikaga ya shiryu, haka yayita wa daddy nasiha cikin dabara har ya saki jiki suna hira.
bayan kwana biyu salis ne zaune shi da fatima ababban falon gidan suna hira kallon shi fatima tayi ta d'a hannunta tanuna mai yaya wai bakaga nayi lalle bane,
nagani Zahara yayi kyau sosai amman ni banason kinayi ki bari sai munyi aure, kinga kayan nan ma na jikin ki da zakiji mgn ta danace ki daina sawa idan kuma zaki saka toh ki daura hijjab akai.
turo baki tayi sannan tace waikai badama nayi ma kwalliya saika gwale ni.
murmushi yayi sannan yace bahaka bane zahara nagani kuma ya burgeni.
cikin muryan kuka