Showing 9001 words to 12000 words out of 53627 words
Chapter 4 - Tsuntsu Mai Wayo Complete Book by Fadila Lamido.txt
tace toh ai baka kallaba.
ahakali ya mika hannun shi ya rike nata duk 2 yana kallon su ,zuwa cen yayi ajiyar zuciya cikin muryar rada yace zahara. dagowa tayi da sauri ta kalleshi cikin ido. yace hannunki laushi.
da sauri ta kwace hannunta tana rufe ido.
ahankali ya sake cewa zahara zaki iya gane mutumin da ya keta miki mutuncinki?
gabanta ne ya fadi dan bata taba zatan salis yasan wannan mgn ba .
muryar haydar sukkaji daga bayan su yana fadin toh iidan kasan shi me zaka mai?
cikin sauri sukka kalli gurin haydar ne tsaye hannun shi cikin aljjihun shi.
salis ya bude baki zayi mgn aka turo kofar falon ,wata budurwa ce agaba bayanta kuma wata matace dagani mahaifiyar yariyar ce
suna hada ido da haydar ya zaro ido yace me kika zo yi agidan mu?
babu ko alamar tsoro atattare da ita tace niba gurinka nazo ba, nazo ne ingayawa iyayen ka ina dauke da cikin ka
ππ
Mmn Yazeed
πππ
[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
27 -29
Da sauri ya farajan yariyar yana kokarin barin gidan da ita ummi ce taji hayaniya yayi yawa da sauri ta fito, ganin haydar najan yariyar ta fara dakamai tsawa cikin sauri ya saki yariyar yana mazurai, ummi takalli dadtijuwar matar da suke tare da yariyar tace sannu da zuwa hajiya shigo ki zauna.
ba musu tahau kujjera ta zauna fatima da salis ko kallo sukabi yariyar dashi.
haydar ko yana jingine jikin bango sai aikawa yariyar harara take
ummi ce taji shirun yayi yawa tace baiyawar Allah ban fah ganeki ba.
kamar jira matar take tace dama ai bazaki gane ni ba amman ai d'aki haydar bazai ce be gane mu ba, atakai ce dai hajiya Nazo ne na shaida miki 'yata zinat ta dauke da cikin danku haydar
wani zufa me dumi ya karyo ma ummi take ta Fara fadin innalillahi wa Inna ilaihir raju,un maimaitawa taitayi zuwa cen ta daga jajayen idonta ta kalli haydar kanshi akasa yace ummi nifa karya suke min.
bata ce komaiba ta mayar da kanta kasa wasu hawaye ne masu dumi suka zubu mata zuwa cen ta miki ta nufi falon alhj salis ne yabi bayan ta yana fadin ummi karki gayamai Dan Allah .
waigowa tayi tace salis wannan ba abun da za,abuye bane , dole ne yasan halin da haydar yake ciki dan ni yanzon ban san yadda zanyi da wad'an nan mutane ba, tana fadin haka ta shige dakin.
bata dade ba saiga su sunfito tare da daddy yana huce.
fatima naganin fitowan daddy tamike ta nufi dakin su cike da tsananin tsanar haydar azuciyar ta.
daddy ko kallon haydar yayi cike da bacin rai sannan ya juya ya kalli bakin nasu sannan yace kai haydar fita kabar min gida, ku kuma kutashi ku bishi karku kara gigin nufumin gida da nufin Ku kawo min shege bazan taba karba ba.
haydar ne ya bude baki yace daddy nifa karya suke min.
idan kasakemin Wata mgn zan illataka ka fita kabar min gida wai gawa yayi barayin matar cikin tsawa yace kutashi ku bishi, cikin rawar jiki suka mike suka fita dan tuni haydar ya fita salis ma mikewa yayi zaibi bayan su
daddy yace karka fita tsayawa yayi ya jingina kanshi ajikin bango.
ummi ko kuka take yi tana fadin alhj wannan hukunci beyi ba, matar tabani tausayi be kamata amata hakaba ,yanzon yaya zatayi kenan?
Oho nidai bazan karbi shegeba d'an karamin shi dashi ya lalata rayuwuwar shi, yace na mashi aure ne ban mashi ba? wacce irin jaraba ce wannan yariyar nan ma ai inbanda jaraba ta girmeshi haka daddy yayita fada wata mgnr ma besanin sanda ta fito bakin shi.
ummi ko kuka take sosai yayin DA salis ke tsaye jikin bango
haydar ko yana fita ko waiwaye babu ya nufi motar shi shiga yayi ya zauna daidai lokacin zinat da mamarta suka fito harara ya wurgawa Zinat itama ta mayar da nata hararan motar shi yaja yabar wajen.
yana fita agidan ya fara kuka hawaye ne yake zubomai kaman karamin yaro yana bakin cikin batawa iyayen shi rai da yakeyi amman ya kasa cen zawa, tsawa yayi bakin hanya yayi kuka sosai sannan ya kama hanyar gidan alhj yusuf.
alhj yusuf naganin haydar gabanshi ya fadi sakamako idanuwan shi dasuka kunbura tahowa yayi ya kamashi ya zaunar dashi ya fara tambayan shi me ya faru amman ina haydar babu baki domin kuwa ya kasa cewa komai illah hawaye dake bin kuncin shi.
alhj yusuf ne ya lura haydar bazaiyi mgn ba, dan haka ya daga waya ya kira daddy.
daddy na daukan waya yace au gurin ka ya taho, toh maza ka ko reshi karka sake kabar shi a gidan ka mazinaci ne dan iska .
takaicine ya kama alhj yusuf yace yanzo yaya dan daka haifa kake kira da wad'an nan mugayan kalamen.
ba d'ana bane ayan zun tunda yace shi d'an iskane na barma duniya kuma kaima karka kuskura ka tareni da mgnr haydar yana fadan haka ya katse wayar.
alhj yusuf ya sauke wayar ya kalli haydar yaga har yanzon hawaye ne a idon sa kamar anbude fanfu
ya mayar da kanshi kasa zuwa cen ya d'ago ya kalli haydar sannan yace haydar aure za,amaka kuma ba ina neman amincewan ka bane za ayi auren ne ko kana so ko baka so.
*Kuyi hakuri yau banyi typing da yawa ba insha Allahu gobe zanyi me yawa*
ππ
Mmn Yazeed
πππ
[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
30 - 32
Bece komai ba har yanzon kuka yake yana mamakin zinat anya kuwa ba karya suka shirya mai ba domin shi rabon daya ganta ya dade kuma ai bakai tsaye yake shigarta ba.
kwanan haydar 2 agidan alhj yusuf zuwa yanzon ya dan saki jikin shi saidai ya dan rame gashi zama agidan ya isheshi dan alhj yusuf ba mata gareshi ba, dan haka gidan babu dadin zama.
shima alhj yusuf zaman ya isheshi Dan haka ya fara tunanin dawo da salame saidai be saniba ko haryanzo iyayen nashi nanan akan bakan su.
washegari yanufi gidan dada sallama yayi ya shiga dada ta tareshi da Fara,a itako salamatu tana ganin shi ta shige daki bayan sun gaisa da dada shiru sukayi nadan wani lokaci sannan alhj yusuf ya fara fadawa dada kudurin sa.
farin cikine ya rufeta har ta kasa boye murnanta daki ta shiga cikin farin ciki amman saita tarar da salamatu tana kuka.
tana ganin dada tace dada nifa bazan koma gidan sa ba, shekarana uku da dawowa garin nan betaba lekomuba tunda ya karbi yarshi sau 1 ya barta tazo gidan nan be mason tayi alaka dani sabo da ayanzo bana gaban shi dan haka ni bazan saurareshi ba.
fada dada ta fara tana fadin wani irin tunani ne wannan da baki gabanshi aida bezo gidan nan da niyar zai maidaki dakin kiba kikasan dalilin shi nayin haka ki tunafah tunda ya rabu dake haryau beyi aure ba dayake ke butulu ce har kk wannan mgnr toh tashi maza kije ki saurareshi .
koda alhj yusuf yayiwa salamatu bayani batace a,aba aman fuskar ta adaure take tam kamar bata dariya dan haka hankalin alhj yusuf ya tashi yace salamatu kodai yanzon baki ra,ayi nane?
cikin fushi ta fara zaiyanane mishi kamar yadda ta fadawa dada.
farin ciki ne ya kamashi ashe har yanzon yana nan makale azuciyar ta yana murmushi yace Allah ya huce zuciyar ki nayi kuskure kuma ina neman afuwarki ki yafemin kuma idai fatima ce harsai kin haji da ganin ta haka alhj yusuf yayita rarrashi salamtu harta yadda ta amince sannan ya fada Mata shifa baya son abun ya dau lokaci dan haka suka tsaida akan ranar juma,a me zuwa.
yana barin gidan gidan mahaifin sa ya nufa ya fada masa kudurin sa.
murnace ta kamasu gaba daya har yadidko godiya sukayiwa Allah tare dayiwa dansu fatan alheri.
*Ranar juma,a*
taslima da fatima zaune adakin su suna hira taslim tace wlh fatima na kosa atsaida ranar bikin ku.
tsaki fatima tayi sannan tace
nidai gaskiya ban kosa ba keni idan ma naji anyi maganar bikin gabana fadowa yake shima yaya kullu maganar shikenan wai ya kosa ranan nan fah har cewa yayi zai gayawa daddy, waishi hakurin shi ya fara karewa
tintserewa tayi da dariya sannan tace ai yadai fad'amiki ne amman ba iyawa zayiba , da dai yaya haydar ne, sake kallonta tayi sannan tace yauwa sister naga wani abu acikin akwatin ki acikin wani d'an karamin akwati.
"murmushi fatima tayi sannan tace eh yaya ne ya bani"
" taslim ta sake cewa menene aciki?
dafata fatima tayi sannan tace kai taslim kin cika gulma toh nima bansan menene aciki ba kuma yace karna bude sai ranar da akadaura mana aure.
cafdi ai inda nice wlh saina bude yasan..........
gud'an da ummi ke rangad'awa ne ya dakatar dasu daga hiran mikewa sukayi atare suka fito suna rige rigen tambayan ummi .
cikin farin ciki ta dafa fatima tace
fatima ki godewa Allah yanzon haka mahaifiyar ki tana gidan babanki an mayar da auren su, yazon salis yayi waya yace gashima agidan.
wani farinci ne ya kama fatima ta saki murmushi zuwacen kuma ta fashe da kuka.
ummi ce ta kamota ta rugume tana fadin haba fatima keda zaki godewa Allah kuma, meye na kuka .
saidare salis ya dawo hannun shi rike da ledoji bayan yayi wa ummi sannu da gida ya kalli taslim yace ke Ina zahara?
kallon shi tayi sannan tace tana daki, yaya wai meye acikin ledar?
"yana tafiya yake fadin inaruwan ki"
washegari
salis ne ya dauki taslim da fatima zai kaisu gidan alhj yusuf murna ce ba kadan ba azuciyar fatima.
suna shiga gidan suka samu haydar kwace akan kujera yana danna wayar shi salis ne ya nufi gurin shi ya kama kafafuwan shi ya d'aga sannan ya zauna agurin tsaki haydar yaja sannan ya tashi ya zauna salis ne yace wa haydar ina mama?
atakaice yace tana ciki.
daidai lokacin salamatu ta fito daga daki fatima ta tashi da sauri ta nufe ta, tureta tayi ta jawo taslim dake bayanta ta rungume sannan tacewa fatima aike babu ruwana dake.
komawa tayi kusa da salis ta zauna tana turo baki.
kallonta kawai salis yayi ya sunkuwar dakai.
mama ko tana rungume da taslim tana tambayan ta karatun ta.
alhj yusuf ne yayi sallama ya shigo zama yayi cikin su bayan sun gaisa ya tashi ya nufi d'aki
itama mama mikewa tayi sanna tacewa taslim tashi ki shiga kitchen ki debo muku abinci, tana fad'an haka tashiga d'aki
haydar ko sai, satan hararar fatima Yake
salis ko kallon fatima yayi yace ke wai baki iya bada hakuri bane?
kara turo baki tayi sannan ta kauda Kai, daidai lokacin taslim ta kawo abinci ta ajewa salis nashi sannan tacewa fatima sister zo muci.
azuciye tace banzanci ba.
" har salis yakai abincin dafda bakinsa yadawo dashi sannan ya kalli fatima yace sabo dame bazakici ba?
saida ta kara turo baki sannan tace toh aini batace dani ba kuma saina kamaci sai kace mayya.
dariyace taso kubucewa haydar amman sai ya dake yaci gaba da danna wayar shi.
salis ma dakewa yayi sannan yace toh ke wai baki iya bada hakuri bane, kitashi maza tun kafin raina ya baci kije ki bata hakuri.
mikewa tayi ta fara kuka tana buga kafarta akasa kamar karamar yariya tana fadin nifah ba abinda na mata ni yaushe ma naganta bare na mata wani abu.
tun salis na kallon fatima har ya gaji ya rufe idonshi dan ya lura yau fatima so take ta rud'ashi.
shiko haydar baki ya saki yana kallon fatima tuni yanayin shi ya fara cenzawa ji yake kamar ya tashi ya rungume ta
fatima ce ta lura haydar ita yake kallo dan haka ta tsaya cak tana mamakin shi kuma wannan me yake kallo.
salis ko yanajin fatima ta daina kuka ya bude ido cikin bacin rai yace meyasa kike min haka ne zahara dan Allah idai baso kk kijamin fushin Allah ba toh ki dakata da irin wannan abun, kije kiyiwa mama sallama kizo mutafi.
sumi sumi ta wuce ta tura dakin mama tana shiga haydar ya kalli salis yace wlh kai wawane d'an kauye.
murmushi salis yayi tare da mikewa yana fadin Allah ya shirye ka.
zuwacen mama da alhj yusuf suka fito fatima na rike hannun babanta .
alhj yusuf yaga salis da taslim tseye yace kardai har zaku wuce?
salis ne yabashi amsa eh baba zamu tafi.
yace toh daman Ina son ganinku kaida haydar tsakanin ku wanene akace sun daidaita da fatima?
da sauri haydar ya d'akai ya kalli salis shima salis d'in kallon shi yayi
ππ
Mmn Yazeed
πππ
[10:02PM, 3/29/2017] Fadila Lamido: _Β©Exquisite Online Writers_
πππ
πππ
πππ
πππ
*_Tsuntsu Me Wayo_*
πππππ
_Storry & written_
By
*_Fadeela Lamido_*
33-37
Alama salis yakewa haydar ya fad'a aman haydar sai make kafad'a yakeyi.
alhj yusuf yace daku nake mgn fa .
" taslim ce ta lura salis kunya yakeji dan haka tayi sauri tace baba yaya salis ne.
haidar ne ya d'ago kai ya harari taslim yace ke dan ubanki dake ake mgn
alhj yusuf yace haydar me yasa bakin ka ya iya furta zagi ne, ai taslim batayi laifi ba abin da tayi kai ya kamata ace kayi amman sai kayi shiru, juyawa yayi ya kalli salis yaga ya dukar dakai yace salis ni dama nasani baban ku ya fad'amin dama naso ne naji daga gareku amman tunda kun kasa magana taslim ta fanshe ku.
ya juya ya kalli haydar yace toh kai kuma fah.
baba ni bayanzon zanyi aure ba .
bata rai baba yayi yace toh sai yaushe?
idan salis yayi ni daga baya zanyi.
baka isaba kafison kai ta d'ako mana mgn ai ni inda sosamu ne nan da one week kayi aure dan haka duk abinda akeci nan da Wata 1 kawo yariyar da kk so,Dan mun riga mun yake rana nan da wata biyu dan haka kuje kufara shiri.
haka suka koma gida cike da farin cike sai dai azuciyar salis ranar da akasa yayi mai yawa
dan haka da suka kebe da fatima yace zahara gaskiya ranar nan da akasa yayi yawa.
haba yaya wata 2 ne yayi yawa toh ni wlh kusa ma naga yayi min dan nifah wlh tsoron ma ranar nakeji.
da sauri ya kalleta tsoro kuma toh tsoron me kikeji, kardai ki kecemin tsoron miji kike, toh idai haka ne gara ma tun yanzon ki cire shi dan gaskiya bazaki takurani ba , zahara kinsan fan nayi hakuri
haharara shi tayi sannan tace hakuri me kayi?
murmushi yayi sannan yace Zahara Kenan kisan fah kina da kyau kuma na kusa najiki jiki na
kawai daurewa nakeyi karne abin kunya, kasa ya yayi da murya ya Kira sunanta sannan yace kifah shirya dan idan mukayi aure akan kirjin ki Zan rinqa kwana.
hannuta tasa ta rufe ido dan be saba mata irin wannan maganganun ba.
murmushi yayi sannan yace zahara idan akace yau andaura mana aure bakaramin farin ciki zanyi ba, bare kuma na ganki ad'akina, Hmmm ranar zan nuna miki irin son da nake miki zan tarairayeki kaman kwai zan nunamiki soyayyar daba kowane namiji bane zai iya nunawa matar sa irin saba.
kwashewa fatima tayi da dariya sannan tace amman dai yaya sambatu kk KO, wannan irin cin buri ne haka.
shima dariya yayi sannan yace aidama nasan bazaki gane ba amman ahankali zan ganar dake, mikewa yayi tare da fadin bari naje gurin haydar.
dasauri tace bayan zon ,muka dawo ba shine har zaka koma, ni wlh natsani haydar d'in nan banason ganin shi.
shima cikin mama ya kalleta yace zahara kinada hankali kuwa d'an uwan nawa, meya miki ?
toh yaya ai shima ya tsane ni dan haka nima bana sonshi wlh ko sunan shi aka kira gaba na faduwa yakeyi.
kallon ta yayi cikin ido yace xahara haydar ba tsanar ki yayi ba haka halinsa yake nima bakiga yana min ba, kuma dan Allah ki yafe masa karki kara kullatan shi aranki kinga d'an uwanki ne , koya miki wani abu kijin haushi toh ki gayamin ni kuma xan faranta miki rai kinji KO ?.
da sauri ta d'aga kai .
yace kin yafe masa?