Showing 30001 words to 33000 words out of 84763 words

Chapter 11 - AIMANA Book Complete by MAMI YUSUF DABO.txt

jikinsa duk a sanyaye danba karamin tsorata yayi
"Allah yasakamin dan wallahi ka bani tsoro"
"Kai wai bazaka rage wannan tsoron naka ba, a haka kuma kakeson Surayya cab duk taron matsorata in abin tsoro yazo gidan naku ba wani jarumi kaida ita duk tughether"
"Dallah ajjemin wandona"
"Naki na ajje ɗin, zoka ranaki ɗakin Aimanah nifa wallahi tsoron rikicinta nake"
"OK gobema idam ankai maka ita tsoron nata zakaci gaba da ji kenan?"
"Gobe kuma haba sai friday goben fa zan koma legos, inna koma zan samo hutun sati ɗaya nazo na more amarci na"
"Angonci dai, ba kwaran kawai"
"E naji nine ma kai, yanzu dai rakani dan Allah aboki"
"Kasan Allah bazani ba tana ma sashin daddy"
"Jar uba wai kana nufin can zan shiga a haka da kananun kaya amma ka cuceni da baka gayamin tun farko ba"
"Ni na hanaka ka nutsu kenan ka tuna gidan surukai zaka zo"
"Nidai rakani please"
"Lalle naka wasa ne bari ma kaga na kwanta"
"Dan Allah kataimaka ka rakani fitsarin nan zai zubo tsoro nakeji" gaba ɗaya suka tun tsure da dariya harda rungume juna
"Kasan Allah aboki inna tuna rayuwarmu ta booding sainayita dariya ni kaɗai, yanzu dai muje na raka ka aramawa kura aniyarta"
"Allah ya nunamin auranka da Surayya nazauna na bata labarinka da sanda ka shiga firgici sanda kaga aljana" dariya suka kuma yi Musty harda rike cikinsa dan dariya kamar yafaɗi
"Allaj sarki Fahad ubangiji yai masa rahama oh rayuwa"
"Ameen" Mas'ud yafaɗa dai dai sun shiga falon Daddy,Musty idanunsa akan kujera inda yake zaton Aimanah ce kwance ganin ana rawar sanyi cikin hijab kai tsaye wajan ya nufa bako kunya ko gaida su Daddy baiyi ba ya kalli Mus'af
"Baka kallon rawar da jikinta keyi ka barta haka ba wani taimakon gaggawa"
"Ba ɓangare na bane" Mus'af ya mike yabar falon, Musty buɗe hijab ɗin yayi ya ɗagota ta buɗe idanunta da sukayi ja taga shine komawa tayi ta maida kanta ta kwantar sannan tasa hannunta ta ture hannun Musty dake taɓa jikinta dayaji yai masifar zafi
"Ka shika ni karka sake taɓani" tafaɗa lokacin daya sanya hannu yana kokarin tashinta zaune ɗan matsawa yayi kusada ita sosai bakinsa saman kunnanta ahankali kamar bayason magana ya ce
"Ki tashi na kaiki hospital ko kuma na ɗauke ki da kaina ba ruwana da su Daddy suna kallona" da sauri ta mike zaune ta zira plate shoe ɗinta dake zube saman carfet ta mike tana kokarin faɗuwa yai saurin rukota jikinsa suka fita daga falon
"Mah waisu kaɗai zasu tafi?"
"Ko zaka bisu?" dariya Ma'aruf yayi ya fice daga ɗakin yana masu saida safe, Musty da kansa ya buɗe mata murfin motar ta shiga saida ya gyara mata zaman ta yamaida kofar ya rufe, ya zagaya driver seat, ahankali yake tukun mota yanayi yana kallonta hannunsa na cikin nata, yana kallonta cikeda kulawa, har suka kara wani babban pravite hospital dake zoo raod, lokacin jikinta yayi zafi sosai, yana rikeda ita a jikinsa, cikeda kulawa nurse suka karɓesu kai tsaye gado aka basu sanda Dr ya dubata yacewa Musty damuwa ce kawai sai fever jininta kuma ya hau dole sai an bata gado
Musty ya siyo komai da suke bukata aka saka mata drip tuni barci yayi gaba da ita, Mustapha ya zauna gaban gadon saman farar kujera ya zuba mata idanu yana kallonta, Mas'ud ya kira ya sanar masa an basu gado yafaɗawa Mah, Mah ta kira Musty sukayi magana ko Anty Hasana tazo shi yatafi gida yabar Sumayya ita kaɗai, yace basai kowa ya zoba zai zauna zuwa safiya sai Antyn tazo, ajjiyar zuciya ya saki sanda ya ajje wayar shi gaba ɗaya ma ya manta da wata Sumayya a gida, yagama duba wayansa yaga ba lambar Sumayyan wayar Shaheed ya kira, Shaheed da baiyi barci ba yana falon Ammi yana kallon wasan kwallo yaga kiran Yayansu
"Hello Yayanmu barka da dar"
"Barka dai Autan Ammi, kaje ka gayawa Sumayya ta rufe ko ina ta kwanta bazan dawo ba ina Hospital Aimah ba lafiya"
"Yayanmu maiya sami Aimah?"
"Fever ne"
"Ok Amma Abba ya rufe gida kasan doka ne, bari na duba in Murjana batayi barci ba saita kira ta a waya ta gaya mata"
"Ok" Musty yafaɗa yai saurin katse kiran ganin Aimanah tana motsi
[2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹


Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰

☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation

*Shafi na goma sha bakwai*

Saurin kallonta yayi zuciyarsa yaji tazo masa har wuya a fusace ya ce
"Ki sani aurena dake ba saki inkinga na rabu dake to mutuwa nayi, kuma karki sake min irin wannan maganar idan na fusata komai zai iya faruwa inada kishi ki kiyaye yimin maganar wancan sojan" turo baki Aimanah tayi ta juya can taci gaba da barcinta, Mustapha kusan kwanan zaune yayi duk motsinta yana kula da shi har zuwa safiya, Anty Hasana ta fara zuwa tanata mita dan bataji ba tun dare da ita zata zo ta kwana da Aimanah,
"wannan ai rashin kunya ne zaka zo asibiti ka kwana da yarinya kamar batada gata wama yasan iya abinda ka mata Allah yasa ma baka lalube mana ƴa ba," Musty baice komai ba yana gefe ya danna wayarsa haɗeda murmushi Anty tanata mita har Ammi tazo ita tasa Anty Hasana tayi shiru ta tisa keyar Musty yatafi gida yai shirin komawa legos, yana tafe a mota yana murmushi shi kaɗai musamman inya tina mitar Anty Hasana wai ya lalube masu ƴa, ina shi ina wannan aikin babba, yana shiga gida Sumayya ta taresa tareda tambayarsa ya jikin Aimanan
"Da sauki" kawai yace ya wuce ɗakinsa yasa key, wanka yayi ya kwanta ramuwar barci, bai tashi ba har bayan azahar, sallah yayi yai wanka yasa Shaheed yasai masa tiket yai sa'a akwai jirgin dazai tashi zuwa legos karfe bakwai na daren ranar, gidan Anty Halima kai tsaye ya wuce jiya basu haɗu ba yanaso su karasa magana ga zancan haɗa lefe, yana shiga gidan yaran Anty Halima suka rinka murna ga Uncle Musty, Mustapha na son yara shiyasa ya rungume su yana tambayarsu school, harya zauna saman kujera yana tareda yaran saida Anty tamasu magana sannan suka fita daga ɗakin, ya cire hular kansa ya ajje gefe yana kallon Anty ya ce
"Kin korar min yara"
"Inba subar ɗakin nan ba bazasu barmu muyi abinda yakawo ka ba gashi kace yau zaka koma legos" Hmm yaja ajjiyar zuciya kana ya ce
"Yau zan koma ya maganarmu ta jiya"
"Narigada nayi masa magana yace anjima zaije ya gano wajan sai asan abinda za'ayi"
"Ok yanzu dai ga ATM card ɗina nan ayi duk abinda yakamata bana son lissafi anyi kaza na kaza kawai ayi komai sannan kuyi magana da Anty Hasana gobe kuje ku haɗa lefe, Akaiwa Aimanah, Anty kusai kaya mai kyau da tsada kuɗin ciki zai isa komai insha Allah,"
"Bakada damuwa Ɗan uwa kawai dai kasan Anty Hasana akwai faɗa da mita"
"Wai kema tana maki?"
"To Anty wata kyale kowa ma yi masa take" Musty yai dariya kana yace
"Kibita a hankali zaku gama komai lafiya"
"Insha Allah" Anty ta faɗa, mikewa yayi sukayi sallama yatafi, asibiti ya wuce yatarar tuni an sallamesu sun koma gida, Anty yakira yana korafin mai yasa ba'a gaya masa ba
"Sannu Mahd ubanmu"
"Nifa Anty ba nan na dosa ba" kashe wayarta tayi bata jira jin mai zai ce ba, Musty yaso yaje gidansu Aimanah amma ya kyale saboda sunyi waya da Ammi take gaya masa gidan akwai mutane dole ya hakura haka yasa kai ya wuce legos batareda yasake ganin Aimanah ba.

Abas wata irin rayuwa yake mai cikeda kunci da damuwa, gaba ɗaya bashida kuzari haka yakejinsa kamar wani mara lafiya ga ayyuka da suka saka sa a gaba, yau yana kwance a ɗakinsu dake barreck, Sulaiman ya kallesa ganin yanda ya kurawa waje ɗaya idanu yayi shuru yana dafe da kansa, Sulaiman dake zukar sigari ya matso kusada Abas ya mika masa sigarin
"Ka karɓi wannan kaɗan zuka aboki, zata rage maka damuwar nan" kai kurum Abas ya girgiza masa alamar bazai sha ba
"Aboki bana son ganinka cikin damuwar nan wai ga manyan babys nan a gari ka tsaya kan wannan yar tatsitsiyar kana ɓatawa kanka lokaci ka shirya a daran yau mu futa club tare, za ka sami wacce zata ɗebe maka kewa ko rumans ku ɗanyi ka rage zafi" Afusace Abas yata shi tsaye yana huci ya nuna Sulaiman
"Ki fita sabgata Suleman dole sai nayi rayuwa irin ta ka ne?"danna shiga damuwa saina jefa kaina a bala'i da fishin ubangiji lokacin inada kuruciya ban nemi mata ba, ban sha sigari ba bare yanzu da shekaru na suka haura arba'in, a yanzu fatana da buri na mutuwa a ko yaushe, nifa musulmi ne na yarda da kaddara mai kyau ko mara kyau, domuwar nan da nake ciki jiki da zuciya ne suka kasa sabawa da rashin Aimanah amma na yarda da kaddara daman banada rabon aurenta, inada kur'ani shine yake mantar dani duk wata damuwa, taba sigari ko wata mace tayi kaɗan ta ɗeban kewar Aimanah" fuuu ya fuce daga ɗakin a fusace, Sulaiman taɓe baki yayi ya koma inda Abas yata shi ya kwanta.

Murjana tana tsaye gaban closet tana zuba kayanta cikin babbar trolly, da sallama Sumayya ta shigo ɗakin ta zauna gefan bed tana kallon Murjana data zama wata katuwa tayi fari ɗau da alama mai tafara shafawa sabida da ba haka take ba baka ce ba can ba bakinta mai kyau ne
"Wai lafiya yaya kika zuba min idanu haka?"
"Gani nayi kin zama wata hajiya ga uban fari da kikayi nidai Allah yasa ba blecing kika fara ba" Murjana tayi far da idanu tai juyi ta ce
"Ai ina gaya maki kuɗi duniya ne, kinga kuɗin danake kamawa kuwa ai Salim ya kyauta min da ya nunamin wannan harkar yanzuma wani Alhaji zanyiwa rakiya Dubai"
"Murjana wai bakiji maganar dana gaya maki ba ran nan, Murja wannan rayuwa bata da tabbas dan Allah kibar wannan harkar ta ɗaukar zunubi"
"Nifa inada mijina a hannu kuma shiya nunamin har kar nan ke karshe shiya haɗani da wannan alhajin yace namasa rakiya Dubai" Sumayya tagumi taja tana kallon Murja, Amarya ta shigo ɗakin ba ko sallama tasami gefen Sumayya ta zauna tana aika mata da harara,
"Murja ga wannan boka tsito yace a zubawa Alhaji a abinci zai manta dake indai yaci abincin bazai sake tunawa da ke ba sai randa ya ganki" tsalle Murja tayi ta ɗane Amarya tana murna
"Sai dake Mama ina alfahari dake uwata maganin kuka na"
"Mama yanzu dan Allah kema biyewa Murjana kike keda yakamata ki gaya mata gaskiyya haba dan Allah karuwanci fa kenan kika ɗaurewa Murja kugu tayi a cikin gidanmu"
"Gidansu dai, ke kunada gida ne, indai namiji ne gaki nan ga shi nan, badai kince ke kin daina asiri ba karya ne gashi nan ai kin fara gani kina zaune a gidan zaki zama bora, maza Murjana ta shi kije ga Alhajin can ya aiko a ɗauke ki naga irin motar jiya ta paka a kofar gida" Murja ta saɓa jaka a kafaɗarta tasa kai zata fita Amarya ta ce
"Yawwa murja nace dan Allah karki manta da abayar nan dana nuna maki irinta babar Salim"
"Bakida damuwa Mama zan siyo maki wacce tafi tatan tsada" Sumayya ta kalli Amarya ranta ɓace
"Mama maice kuma abaya dan Allah Abba fa yana matukar bakin kokarinsa mai kika nema kika rasa na sittura zaki wane ce a siyo maki Abaya ayau kika gayawa Abba kinason Abaya saiya baki kuɗi kin siya"
"Ke! zoki fita daga nan kibar min gida na"
"Mama nifa gaskiyya nake faɗa maki"
"Sumayya koki fita daga ɗakin nan kona saɓa maki" Sumayya ta fita zuwa ɗakin Ammi suka gaisa sun jima suna hira tana bawa Sumayya hakuri kan auran da Mustapha yayi batareda sanin ta ba ta gaya mata yanda abin yafaru, ta bata shawarar yanda zata zauna da mijinta da kuma abokiyar zamanta Aimanah.

Anty Halima sun haɗo kayan lefe na kece raini itada Anty Hasana koda suka kawosa gidan ɗakin Momy suka ajje Anty Hasana bata zauna a gidan ba ta wuce gidan Ana sabida ta gaji sosai, Alhaji Kamal yaga kaya yasa albarka yace akai Momy da Ahmad da Shaheed sukai kayan har zasu tafi Ammi tace
"Alhaji Amarya bataga kayan nan ba amata magana" Momy ta leka ta gaya mata tazo taga kaya, ta leko daga bakin kofar sashinta ta tsaya tana karewa akwatinan da takasa kirga yawansu ta taɓe baki ta koma cikin ɗakinta batare da ta ce komai ba, su Momy suka wuce da kayan, Alhaji Kamal yabi Ammi ɗakinta, jiyowa tayi ta kallesa taja ta tsaya tana kallonsa
"Madam wai maiya canza minke ne?"
"Maizai canza ni kuwa kaine dai naga ka nufi wani waje daban" ajje hular kansa yayi ya zauna saman kujera yana murmushi,
"Alhaji daka futa na sameka a ɗakinka bana son rigima kasan dai yau Amarya ce ke dakai"
"Sabida itace dani kuma sai akace bazan shiga inda raina yakeso ba, ko wacce acikinku ta sani nakan shiga ɗakin da naso koda ba acan nake ba indai inada magana da ita kema dan rigima kike ji shiyasa kika kasa fahimta"
"Au rigima, ni karamar yarinya ce kenan?"
" E mana ni a wajena kinfi Raudah yarinta" dariya Ammi tayi ta zauna kusada Alhajin
"Bani ruwa na sha" Alhaji Kamal yafaɗa yana kallonta
"Nifa Alhaji bazan baka ruwa ba, nama tina banma da shi a ɗakin nan ɗazu nake gayawa Ahmad inya fita ya tawomin da shi"
"Babu a story ne?"
"E haka Shaheed yace dana ce ya ɗakko yasamin a firij"
"Kinga yanda abu yakasance ba zato ba tsammani na tausayawa Aimanah na kuma taya Mustapha murna Allah ya taya sa ruko yabasu zaman lafiya da zuri'a ɗayyiba"
"Ameen" Ammi tafaɗa tana kwantar da kai jikin kujerar datake kai
"Da sonayi nabasa gidana dake Kabuga ya zauna acan sai kuma Halima take gayamin sun gama magana saman gidan dayake ciki zai gyara ta zauna acan"
"Haka nima ɗazu take gayamin hakan yafi amma ya za'ayi ace Aimanah na sama Sumayya na kasa hakan kamar ba tsari"
"Haka Allah ya tsara, yace Sai Juma'a zata tare mai kuke shiryawa koba zakuyi taro ba"
"Naji Mas'ud ɗazu yana cemin zasuyi Party ranar asabar abar tarewan sai asabar saboda Mustaphan bazai shigo kano da wuriba ranar juma'an jirgin dare zai biyo"
"Shikenan na tura masa gudun mawata ta bikin ban samu na masa komai ba"
"To yana godiya Allah yakara arziki mai albarka"
"Amin" Alhaji Kamal yace bayan ya mike, da sauri Amarya dake laɓe jikin window ta salallaɓa ta koma sashinta tana hucin takaici,
Anty Halima ta turawa Musty hotuna da vidion kayan da suka haɗo, Anty Halima ta tsaya kan komai ganin yatafi dai dai itada Ahmad suke komai, tsab aka gyara saman benan inda Aimanah zata zauna Anty Hasana da Anty Ummi sukaje suka gano wajan yayi kyau sosai, Prop yabawa Mah card ɗinsa yace suje da Aimanah ta zaɓi kalar kayan ɗakin datake so, duk yanda sukaso Aimanah taje ta zaɓa ki tayi sai Anty Hasana ce ta zaɓi komai, sukayi komai suka gyara saman inda Aimanah zata zauna yayi kyau sosai, gaba ɗaya Aimanah batada walwala tunda Musty yatafi legos ta kashe wayarta ko yaya Mas'ud yakawo mata wayarsa yace zasuyi magana da Mustapha bata musu kai tsaye zata karɓa daga ya fita zata saka wayar a airplane mode ta ajjeta gefe taci gaba da sha'aninta, daga farko kullum tana cikin kuka da damuwa saida Mah da Daddy suka zauna suka mata nasiha sosai sannan ta hakura ta rungumi kaddararta Mustapha, sau tari takan ɓuya tayi kuka sosai musamman inta tina Abas tanaso tasan halin dayake ciki amma tasan haramcin hakan bata taɓa kwada kiransa a wayaba kamar yanda bai taɓa kiran nataba tun bayan abinda yafaru lambarsa ma bloking ɗinta tayi a wayarta.
Sumayya gaba ɗaya ta shiga damuwa musamman sanda taga an kawo kayan Aimanah an jera ta shiga ɗaki tayi kuka sosai har saida idanunta suka kumbura
[2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹


Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰

☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation

*Shafi na goma sha Takwas*


Shaheed ne yaje airport ya ɗakko Musty, suna tafe a hanya sun kusa gadon kaya Musty ya ce
"Shaheed bazaka biya dani ta gidan Mah naga Aimanah ba kuwa?" Shaheed da dariya ta kama sa ya rike baki yanaso yayi dariya yana tsoron faɗan Yayan nasu ya ce
"Yayanmu ka basar kawai gobe i yanzu fa kuna tare, kuma ma gidan a cike yake da mata ɗazu da Ammi ta aikeni da kyar na samu na shiga banma ga Aimanan ba sai Ruma nabawa sakon ta kai mata"
"Au Aimanah ma, bama sakayawa kace Anty"
"Yayanmu ai kasan daman Yaya nake ce mata kawai yanzun ma suɓul da baka ne" Musty wayarsa ya zaro yana dannawa Mas'ud yakeson magana da shi tun safe yau yake kiran wayarsa bata shiga, yai sa'a yanzu ta shiga saidai harta gama ring ba'ayi picking call ɗin ba, a kofar gidansa Shaheed ya ajjesa ya shiga, shaheed kuma ya shige gidansu da ma da motar Ammi ya ɗakkosa, Sumayya data sha ado tanajin an buɗe kofa tai sauri ta tashi daga inda take zaune da gudu ta nufisa, Musty buɗe mata hannuwansa yayi ta shiga jikinsa yamaida hannun ya haɗe da jikinta yana zugar kamshin turaranta
"Barka da zuwa" Sumayya tafaɗa ahankali tana sake kwantar da kanta a kirjin Mustapha, wani tausayinta ne ya ziyarci zuciyar Mustapha ya tina irin son dayakewa Aimanah indai har haka takeji itama a kansa tabbas ya tausaya mata, ya ɗago kanta yana kallon fuskarta
"Kinyi kyau ya kike ya gida fatan na sameki lafiya?"
"Lafiya kalau sai kewarka data addabi zuciyata gidan shiru ba motsin kowa"
"Gobe iyanzu ai kun zama ku biyu, kinga kin sami abokiyar hira" batace komai ba taja hannunsa zuwa ɗakinsa gefan bed ta masa mazauni tana cire masa takalmin kafarsa
"Na haɗa maka ruwa kayi wanka?" kai kurum yaɗaga mata alamar e ta mike zuwa bathroom na ɗakin yabita da kallon tausayawa, ita ta taimaka masa yayi wanka, yai sallah, yayita zuba idanu yaji ance ga abinci yaji batace komai ba shi kuma harga

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login