Showing 36001 words to 39000 words out of 84763 words

Chapter 13 - AIMANA Book Complete by MAMI YUSUF DABO.txt

kallon p o p silin na ɗaki lokaci ɗaya hawaye suka wanke masa fuskarsa
"Reina da gaske kin daina sona bakya farin ciki da auranmu ko?"nayi nadamar kin zuwa wajan ɗaurin auran nan da banyi ba, inama zan iya dawo da baya da ban bari Yaya Mansur ya ɗaura mana aure ba, nasan da tini najima a kabarina" da sauri Aimanah ta yaye mayafinta tana kallonsa
"Ni nace maka na daina sonka, mu manta da wata soyayya anriga da an ɗaura min aure da kai ba yanda zanyi" wani sanyi yaji a zuciyarsa hakan yabasa karfin gwiwar umartarta kan ta tashi suyi sallah suyi godiya ga ubangijinmu batayi masa musu ba ta mike ya jasu sallah raka'a biyu sukayi ya jima yana addu'a kafin daga karshe suka shafa tare, da kansa ya fita zuwa kicin ya samo plate ya juyo naman daya shigo da shi a hankali yake bata tana ci bata wani ci dayawa ba ta kurɓi lemun exotic ta tashi ta jima zaune gefan gado tana kallonsa ya gyara ko ina ya fita da sauran naman ya ɗebe komai yakai kicin tana jin motsin shigowarsa ta kwanta tana barcin karya , ya cire jallabiyan jikinsa ya rage daga shi sai gajeran wando da singlate ya zauna wayarsa tayi kara alamar kira ya shigo
"Anty Hasana" ya furta a fili sanda yaga sunanta na yawo saman madubin wayar
"Assalamu alaikum" Musty yafaɗa a hankali
"Yawwa nace Musty dan Allah kabi yarinyar nan a hankali, kaga dai ita ba..." da sauri Ammi ta kwace wayar daga hannun Anty Hasana
"Nashiga uku ni Saudatu, Hasana maine kukeyi haka, kefa bakida girma saina jikinki, so kike yaron nan ya rainaki ko" Anty Hasana cikeda damuwa ta kalli Ammi
"Wallahi Yaya Saudat gaba ɗaya na kasa samun nutsuwa tausayin Aimanah nakeji kinga kuwa irin kallon da Musty yakewa Aimanah ɗazu ni kawai nasan mai na gani cikin idanunsa" Mami dake kwance saman bed ɗin Ammi dariya takewa Anty Hasana
"Ke mai ƴa ko to wallahi ki kama girmanki" Mami tafaɗi haka tana dariya, acanma Mustapha dariya yayi
"Hmm Anty Hasana ikon Allah" yafaɗa sanda ya zauna a gefan gadon ya kalli Aimanah da idanunta ke rufe amma suna motsawa ita nan bata yarda ba barci take,
"Alhamdulillah" yaketa jerawa
"Aimaah tashi ki rage kayan jikinki" sake takurewa tayi waje ɗaya, tayi shuru batace komaiba
"Nariga da nasan ba barci keke ba ki tashi kafin na cire maki da kaina" da sauri ta tashi zaune yanda ta tashinne yabasa dariya hakan yasa ya murmusa
"To sakko ki canza kaya, kona canza maki da kaina"
"Nifa banda wasu kayan anan duk suna gidan Mahh"
"Wanda su Anty Hasana suka kawo jiya fa" mikewa yayi ya buɗe wardrove ya ɗakko mata ɗaya daga cikin jerin ringunan barcin dake ciki
"Karɓi wannan kisa"
"Sanyi fa ake Man kace nasa wannan" tafaɗa tana juya rigar a hannunta
"Ok tayi kauri da yawa ko, to bari na canzo maki wata"
"Kifita na canza rigan to" gyara zama tayi saman bed ɗin yana kallonta
"Ni ba inda zan fita ki canza kawai inace mum riga mun zama ɗaya kunyar me kuma zakiyi" turo baki tayi gaba alamar shagwaɓa
"To gyara na sauka na shiga bathroom na canza" gyara kafarsa tayi ya mata hanyar da zata sauka daga gadon, tana matsowa kusada shi yai saurin janyota ta faɗo jikinsa, hannun yasa saman gwon ɗin tata yaja zif kasa
"A'a dan Allah ka bari Kalbie"
"Kalbie" Musty ya maimaita sunan a hankali
"No Aimah Hayatie Kalbie duk bana son jinsu a gidan nan kibar abinki a gidan Mah bana son jin word ɗin nan" Musty yafaɗa a fusace, karasa zuge zif ɗin yayi kana ya ɗora hannunsa saman riganta ta ciki yana kokarin ɓallata, gaba ɗaya Aimanah ruɗewa tayi ta rike hannunsa kam kamar zatayi kuka
"Yayanmu Please dan Allah"
"Ina yayan naku anan" ya raɗa mata a kunne yana cigaba da ɓalle rigan, gaba ɗaya ta makalkalesa sanda taji ya gama ɓalle maɓallin rigan tata,
"Ya Musty banaso dan Allah ka bari" ɗago da fuskarta yayi yana kallon cikin idanunta, ita kuma tayi kasa da kanta
"Nabar me?"nabari karna canza maki kayan ki kwanta da wannan, nasan fa bakya kwanciya da kaya masu nauyi kinsan na san wannan ba tun yau ba,ki saki jikinki dani gobe da safe so nake kimin wanka da kanki ki wanke ni tas" sake bawa Aimanah kunya yayi hakan yasa tai kasa da kanta sake ɗagowa da kan nata yayi ya haɗe bakinsu waje guda🙈
Abubuwa masu nauyi da girma sun faru a wannan dare mai ɗimbin tarihi a wajan Aimanah da Mustapha, Musty ya maida Aimanah cikakkiyar mace bayan yasha kuka cizo da yakushi🤣daga karshe dai ya ɓige da lallashi da ban bakin kalamai masu ɗimi, da kansa ya wanke ta tas bayan yasa ta gasa jikinta cikin ruwan zafi, yabata riga da wando masu kauri na barci tasa a jikinsa tai barci, godiya yake tayiwa Allah a zuciyarsa da wannan kyauta da yamasa ba zato ba tsammani, yazama dole ya godewa Ya Mansur bandama dare yayi da yanzu zai kira sa shi saima yanzu ya tina bai gansa a wajan party ba, agogo ya kalla yaga karfe goma da kwata na dare, kwanciya ya gyarawa Aimanah a jikinsa ya sake rungumeta a jikinsa yana jin wani sabon sonta da kaunarta na daɗa shigarsa

Sumayya kusan kwanan zaune tayi tunda asirin da sukayiwa Al'mustapha ya karye ban sake bin ta kanta ba a shimfiɗa sai jiya, hakan yasa yau take jinta duk ba daɗi bazata taɓa manta jiya ba a rayuwarta sabida rana ce da ta kasance da Mustapha ta kwana a jikinsa tayi barci mai daɗi, hawayan idanunta ta goge ta ɗauki wayarta ta shiga youtube tana kallo ko zai mantar da ita damuwarta,
Aimanah tun barcin farko da tayi ta farka barci bai sake ganin idanunta ba, juyi kawai take wani bin har tashi zaune take taga yanda Musty ke barci hankalinsa kwance ya wani dungule waje ɗaya yana fitar da numfashi a hankali kai daga gani kasan yanajin daɗin barcin nasa sosai, sake shiga bathroom tayi ta haɗa ruwa mai zafi ta shiga ciki wani tsananin zugin azaba takeji a kasanta, ta jima sosai cikin ruwa sannan ta fito tana tafiya a hankali kamar mai koyon tafiya tsayawa taji jikin kofar bathroom ɗin tana ɗan hutawa, dai dai sannan Musty ya farka da sauri yata shi zaune ganin Aimanah tsaye
"Yadai reina maiya faru" idanunta suka kawo kwalla dai dai sanda ya karaso inda take tsayan ya kama hannunta ya zaunar da ita gefan bed
"Kai ba barcinka kake ba ka barni da azaba" kama baki yayi yana yar dariya kaɗan kaɗan
"Au wai wajan bai dana zafin ba, ko sakewa zanyi kila ya daina" da sauri ta karasa hayewa gadon tayi ta juya masa baya, balanket taja ta lulleɓe duka jikinta har kanta, Murmusawa Musty yayi kana ya hau gadon shima ya kwanta nesa kaɗan da ita,da asuba bayan yadawo daga masallaci a kan dadduma ya tarar da ita, gaidasa tayi ta koma ta kwanta bayan ta gama azkhair na safiya, Musty zanin gadon daya cire jiya daga kan gadon wanda yaɓaci da jini ya ɗauka ya sakko kasa da shi ya zagaya can bayan gidan ya wanke ya shanya kana yadawo, ɗakin Sumayya ya shiga ya tarar tana gyangyaɗi saman dadduma
"Barka da safiya Yayanmu"
"Barka dai Sumy fatan kin tashi lafiya?"
"Lafiya kalau" shuru ya biyo baya kana ya mike ya fita yana faɗa mata ta kwanta ta huta, sanda ya koma saman tini Aimanah tayi barci, shima kwanciyar yayi, harya mike zai fita gidan Ammi sai kuma ya koma ya kwanta bayan ya kalli agogo yaga har sannan bakwai na safe batayi ba,barci yakoma shima Aimanah ta riga sa tashi wanka tayi ta gasa jikinta ta dawo ta shirya cikin Atamfa ɗinkin riga da siket ta kafa ɗaurin ɗan kali kalar na yammatan wannan zamanin ta ɗauki wayarta tana chat, sai wajan tara da rabi Musty yatashi a barci idanunsa kan Aimanah suka sauka ya bi kyakkyawar fiskarta da kallo tasha kwalliya fuskar nan tayi kyau sosai, batasan yatashi ba hakan yasa lokacin daya saka bakinsa saman kunnanta yana mata raɗa ta firgita tai wurgi da wayarta saman tiles haɗe da sakin kara
"Matsoraciya nine fa"
"Kai Yayanmu Allah ka tsorata ni"
"Nifa karki sake kirana da wani Yayanku malama kisamin suna mai daɗi irin na masoya" cuno baki tayi gaba tana harararsa ta sunkuya ta ɗauki wayarta, rau rau tayi da idanunta tana kallon wayar ta fashe da kuka, Musty ya leko ya kalli wayar yaga yanda ta fashe, taɓe baki yayi yana kallon yanda Aimanan take kuka
"Abas ya fashe ko?" yafaɗa yana haɗe rai, kallonsa tayi batace komai ba zuciyarta taji tana mata zafi shi kenan ta rasa wayar nan ita kaɗai ta rage mata wacce inta kalli wayar takan tina da Abas, ta tina lokacin daya bata wayar ta sake rushewa da kuka, mikewa Musty yayi ya shiga wanka, yana fitowa ya fice daga ɗakin bai kalli ko inda take ba....✍🏻

*Alhamdulillah daga wannan page ɗin bazan sake posting a ko wanne group ba sai group ɗin Aimanah real fans group 2 dan haka wanda yakeson cigaba da karantawa zai iya min magan ta wannan lambar 07039793439 zanyi adding nashi a group ɗin karku manta free book ne naku kawai comment*
[2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹


Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰

☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation

*Shafi na Ashirin*

Aimanah ta sake rushewa da kuka ta kwanta saman gado ganin ya fita bai kulata ba, tasha kukanta ta gode Allah har sanda taji cikinta yafara kiran ciroma futowa tayi falonta ta tsaya tana karewa ko ina kallo, kofar datake kallonta ta shiga inda take zaton nan ne kicin, ta kuwa gano dai dai, tsaye tayi tana karewa kicin ɗin kallo, komai yaji alhamdulillah babu ce kawai babu a kicin ɗin share hawaye tayi tana godewa Allah, tareda yiwa Daddy da yayunta addu'a, dubawa ta hau yi ko zata sami wani abin da zata sarrafa tasawa cikinta, gaba ɗaya ta gama dubawa ba komai na nau'in abinci a kicin ɗin hakan yasa ta fito falon ta zauna.
Mustapha dake tsaye a ɗakinsa yagama shiryawa cikin koriyar shadda sai sheki take da walkiyya mai ɗaukar idanu, yana saka hula yajiyo sallama daga falo kamar ma muryar Aimanah yaji kamar bazai fito ba sai kuma ya leko ya tsaya daga bakin kofa, Rumana ce tsaye itada Surayya dake rikeda basket cikeda kuloli kala kala, Rumana na rikeda manyan flask tea guda biyu karasa fitowa yayi daga ɗakin nasa yana kallon yaran da suka risina suna gaida sa, ya kalli Rumana
"Ke ce kika zo sai wani kwaɗa mana sallama kike da wata muryarki irinta Aimah"
"Lah Yayanmu kaima kaji?" kowa wai haka yake cewa muryarmu iri ɗaya"
"Hakane ni nazaci ma itace" Musty ya karɓi kayan hannun su yace
"Kuje to mungode ayiwa Ammi godiya, anjima kwa dawo yanzun Aimah barci take"
"Yayanmu ba Ammi bace tabayar Mami ce ta haɗa da kanta"
"To amata godiya zan shigo anjima" suka juya suka fita Rumana na dariya ta kalli Sumayya
"Mai kika fahimta da Yayanmu ya hanamu hawa sama wai Aimanan tana barci" dariya Surayya tayi ta rike baki tana waigen kofar da suka fito,
"Yagama kashe arna shiyasa bayaso muje mu ganta"
"Wayaga idon yaya Aimanah yau anji maza" dariya sukayi gaba ɗaya, Al'Mustapha sama ya haye, Aimanah tai saurin mikewa ta taresa ta karɓi kayan hannunsa ta ajje saman center teble ɗin dake cikin falon, juyawa yayi zai fita da sauri ta rukosa tareda rungumesa ta baya tasa hannunta ta zagayesa
"Hubbi kayi hakuri ni fa ba shine ya saimin wayar nan ba yah Mus'ab ne" juyowa yayi yana mata murmushi ya sumbaci leɓɓanta tareda haɗeta da jikinsa yana sakin numfashi a hankali
"Naji inma shiya sai maki oho" yafaɗa yana lakace mata hanci, tare sukayi break cikeda so da
kauna, bayan sun gama tare suka shiga kicin suka wanke abubuwan da suka ɓata, yana wankewa tana ɗaurayewa, tsokanarta yake tana dariya cikeda shaukin so da kauna, hannunta ya rike har zuwa ɗaki bayan sun gama gyara ko ina gefan gado ya zaunar da ita,
"Kiyi barci ki huta Reina zan fita, bama da komai na kayan abinci a saman nan zan aiko Shaheed ya kawo komai, sannan zanje gidan Mah, dafe kansa yayi
"Wayyo ni yau ko da wanne ido zan kalli Mah" gaban madubi ya karasa ya ɗauki fashashahiyar wayar Aimanah yasa a aljihu yadawo kusa da Aimanah ya sumbace ta yayi gaba yana mata bye bye, Aimanah ta saka kanta kan filo ta kwanta tana share hawaye, shikenan ya rabata da wayar

Hajiya Hafsatu ta ajjewa Alhaji Abubakar wada lemu da ruwa a gabansa ta jiyo zata bar wajan, hannunta ya ruke ta juyo ranta ɓace tana kallon mijin nata
"Hajiya tunda abin nan yafaru kinbi kinsawa zuciyarki damuwa kin fita sabgata kamar wanda yai wani gundumememan zunubi" Hajiyar Abas ta goge hawayen da suka kwaranyo a fuskarta ta zauna kusada Alhaji tana cigaba da goge hawayan fuskarta
"Alhaji wacce irin zuciya ce da kai? baka tausayin ɗanka, yarannan Abas shekarunsa arba'in da ɗaya kenan adauniya idan ban manta ba, a wannan shekarun nasa bai taɓa kallon wata ƴa mace ba kallo irin naso sai Aimanah, sanda yazo mana da zancan nan munyu farin ciki nida kai muka sanya albarka amma saboda can wani dalili naka ka rusayawa yaron nan duka farin cikinsa, rabon dana ga Abas yayi kuka shekaru sha bakwai kenan, sai rana irin ta yau yayi kukan dabai taɓa yin irin saba a rayuwarsa, amma ko ajikinka yau satin Abas ɗaya rabonsa da gidan nan amma abin bai dameka ba, cikin kwanakin nan bance ka kira wayarsa ba bare kaji a wanne hali yake ciki, kasani haifar Abas dakayi bashi zai hana Allah yakama da laifi ba idan ka ɓata masa, shima mutum ne kamar kowa, kai waye ya hanaka auran wacce kaso mahaiyarka ita ta tsaya maka kai da fata alokacin da gidanmu suka so hana auranmu"
Hmmm Alhaji Abubakar Wada Iliyas ya sauke ajjiyar zuciya tareda share hawayen da suka zubo masa
"Nayi kuskure tabbas Hafsat nayi nadama, ba yanda Faruok baiyi daniba akan mu tsaya mu sasanta mu fahimci juna amma naki na kafe, kaicona kaicona tabbas ban kyautawa Abas ba, hajiya kiramin Abas yadawo ayau ɗin nan nakoma na nema masa auran Aimanah"
"Anriga da an ɗaurawa Aimanah aure da wani ɗan uwanta tsohon saurayinta kamar yanda labari yazo mana nida Abas, sai dai ka nemi yafiyar mahaifin Aimanah ku sasanta, kamanta da duk wata gaba, sannan kasan yanda zakayi da Abbas" Alhaji Wada ɗora kansa yayi saman kujera ya runtse idanunsa da hawayan tausayin Abas suka cika masa idanu
"Hajiya kiri min Abbas a wayarki" sau biyu hajiya na kiran wayar Abas tana shiga amma ba'ayi picking ba, ana uku data kirane Sulaiman ya ɗaga shiya shaida mata Abas yana hospital ba lafiya jininsa ya hau, hankalin hajiya yatashi sosai nan ta tubure mota zatabi zuwa garin dayake da kyar Alhaji ya lallasheta kan tabari sai gobe subi jirgin safe.

Amarya tashiga ɗakinta bako sallama turus taja ta tsaya tana kallon Murjana dake kwance saman gado kamar mara lafiya cikeda firgici ta karasa gaban gadon tana taɓa jikin Murjana
"Murja mai zan gani duka kwananki nawa da tafiya dubai ɗin nan kikace sati biyu zakuyi da Alhajin" Murjana ta fashe da kuka tana bawa Amarya labarin abinda tagani yatashi hankalinta ya hanata barci, tsaki Amarya taja ta zauna gefan gado tana hararar Murjana
"Yanzu sabida ɗan wannan abun kika baro Dubai ɗin, kai Murja kinyi asara wallahi, tur maye a cikin wannan ɗan abu na lokaci ai koni na samu yi zanyi badai za'a bani kuɗi ba, kai Allah wadaranki Murja"
"Mama tayaya zan iya aikata wannan babban zunubin, nayi nadamar biyewa Salim danayi ma harya sani aikata zina yake kuma so ya sake jefani a wata masifar Mama na tuba na daina harka da maza aure zanyi"
"Murja aure kuma yanzu? maiye a cikin auran banda tarin damuwa kina dai kallon halin da yar uwarki ke ciki ai garama ki ci duniyarki da tsinke kiga duniya ki wataya, nima yau na haɗu da wata hajiya a wajan boka tamin tallan harkarsu ina ganin ciki zan faɗa kawai nima nasami kuɗi na daina dogaro da abinda Alhaji zai ban daman ai duk gidan nan nice banda abin yi, Ammi na koyarwa a sa'adatu rimi Momy principal ɗin makarantar sakandire ce, ni ce ba cas ba ass to nima na sami abin yi in auran zakiyi sai kije kiyi kyaji da abinda kika tarar a gidan mijin"
"Mama karki min baki mana, ke kullum bakinki baya faɗar alkhairi ne, bantaɓa ji haka kurum kin samin albarka ba sai dai in kuɗi na kawo maki ke kawai abaki ki kawai boka kika sani, kina kallo tareda Surayya da Shaheed muka kammala scoundry school a year ɗin Ammi gashi nan tanata fafutukar samawa ɗanta gurbin karatu a malesia Surayya tuni ta fara poly amma ni karatuna baya gabanki kiwai inje inbawa karti kaina su bani kuɗi na kawo maki, ko sau ɗaya baki taɓa yiwa Abba maganar cigaban karatuna ba, haba Mama ke wacce irin uwa ce?" Mama batace mata komai ba ta shige ban ɗakin dake cikin ɗakinta, Murja tabi Maman nata da kallo tanajin inama ba itace ta haigeta ba, nadama ta daɗa shigarta sosai na abinda ta aikata nasoma istigifari tana neman yafiyar ubangiji.

Musty bai wani jima a waje ba yakoma gidansa yatarar Aimanah na barci ya koma falo ya zauna yana kallo duk minti goma saiya leƙa ɗakin da Aimanah ke barci yaga kota tashi, yanzuma lega wan yayi yatarar tashinta kenan tana kokarin sakkowa daga kan gadon, taimka mata yayi ta mike ya haɗata da jikinsa
"Kinsha barci fatan kin tashi lafiya" batace masa komai ba tasake shigewa jikinsa sosai, kwalin waya ya ɗakko daga kan madubi ya ɗora mata kan hannunta, rufe ido tayi ta buɗe su tarwai kan kwalin wayar da murmushi saman fuskarta
"Iphone wow, masha Allah ina godiya sosai Yah Musty Allah yakara arziki mai albarka"
"Amin" yafaɗa yana shafa kwancancan gashin kanta daya sha gyara sai tashin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login