Showing 57001 words to 60000 words out of 84763 words

Chapter 20 - AIMANA Book Complete by MAMI YUSUF DABO.txt

tunda kikayi jikoki ai tafiya ba taki bace na rantse maki bazan zauna ba kinga ma tafiya ta" Mah ta fice daga ɗakin
"Ammi ni na zauna mana sai kije ke ki huta"
"Tunda mahaukata ne mu ba, ga Aimanah batada gata ai sai mu barka da ita, tashi ma kabar asibitin nan mara kunya"
"Ammi ki barsa mana basai ku zauna tare ba"
"Na shuga uku ni saude, yau ga ranar Anty Hasana data nan data fige ku tas, to bazan barsa ya zauna ɗin ba tashi kaban waje" ba yanda Musty yaso haka yasa kai yabar ɗakin yana waiwayan Aimanh, itama idanunta na kansa🤣

Washe gari sassafe saiga Anty Hasana kamar daman a kasar ta kwana, agaba tasa jariran tanata kallo da yabawa, har inda ɗayar babyn take sai da taje ta ganta, tana zuwa hospital ɗin Ammi ta koma gidanta, kulawa ta musamman Ake bawa Aimanah ɗakin Shaheed daya tafi malesia karatu nan aka gyarawa Aimanah ita da babys ɗinta nan zasuyi zaman jego, kwanan Aimanah biyu a hospital aka sallame su har babyn data ji sauki ta murmure sai dai bata kai mazan girma ba, kulawa ta musamman Aimanah ke bawa babyn da aka sanyawa Saudat sunan Ammi kenan, haka kurum duk cikin yaran tafi jin yarinyar a ranta ganin itace mai lalura ga karamin jiki, mazan akwai cikakkiyar lafiya da kuzari karma Faruok yaji labari, kwanan Aimanah huɗu da haihuwa saiga Abbas da Rumana sunzo hannu biyu Mustaphaa ya karɓi Abbas sun jima suna hira nan falon Ammi sai da Abbas yata shi tafiya ya ce
"Aimanah ga yar zaman wanka nan na kawo maki" yafaɗi haka yana kallon Rumana
"Kai Hayatie nice yar zaman wankan fisabililahi"
"Indai ba zaman wanka zakiyi ba sati nawa kika ce zakiyi ko inaga tare zakuyi jegon da Yaya Aimanah" dariya akayi gaba ɗaya Abbas da Musty suka fita, siyaya sosai Rumana tayiwa babys ɗin nan kaya masu kyau da tsada harda atamfofi guda uku wai inji Abbas, Sosai Anty Hasana ta tsaya a kai da fata ganin Aimanah tayi jego mai kyau abinci mai kyau da inganci take ci ko kusa bata wasa da cikinta dan sosai yaran ke yawan shan nono har saida Mustapha yai magana ko za'a haɗa masu da madara wai karsu ramar masa da mata, Anty Hasana ta ce la baza'ai haka ba, Sosai Mustapha ke kulawa da Aimanah ba ruwansa da yawan matan dake cika gidan kullum ko yaushe yana tareda Aimanah abokan wasa nata tsokanarsa, kwana biyar da haihuwa saiga manyan raguna guda uku daga Alhaji Farouk mai nera, kamar haɗin baki jimawa kaɗan saiga wasu ukun daga Abbah Alhaji Kamal, a ranar Sumayya tadawo daga legos tazo taga yara tanata yabawa da addu'ar Allah ya raya, Murjana ma tuni sunzo itada mijinta sun kawowa babys riguna guda goma sha biyu ta tafi tana faɗin sai ranar suna zata dawo, Surayya kullum sai anyi vidio call da ita taga babys wani bin har kuka take tana rokon Mas'ud daya barta tazo amma ya kafe ba inda zata tafi ta barsa a wata kasa, kayan fitar suna set sha biyu Mustapha yayiwa Aimanah, Sumayya kuma guda shida, tun saura kwana biyu suna aka fara soye soyan kayan snack su Anty Ruma da Rumana da Anty Ummi data zo daga london sune kan gaba wajan komai, Ranar suna mun sha shagali nan compound na gidan Ammi mukayi komai Anty Huda taso ɗakko mai dj Musty yamata jan ido kan baza'a masa kiɗa ranar sunan yaran saba, ranar suna kuwa sai ga masu kiɗan kwarya na gidan saraikai Anty Hasana ta ɗakko su ba yanda Musty ya iya dole yanaji yana gani aka cashe da kiɗan kwarya na gargajiya, sosai aka raba abubuwa babbar jaka ce mai ɗauke da hotunan yaran jota biro sai kayan snack da lemu da ruwa har da naman suna sune acikin ko wanne jaka, sai bayan insha aka tashi daga kiɗan yayinda su Rumana da Anty Huda suka sha rawa kamar ba gobe, tsab su Anty Ummi suka gyara gidan a washe garin suna, da ɗaya da ɗaya kowa yabar gidan daga Aimanah sai Ammi sai ko Anty Hasana da tace bata barin gidan sai nayi arba'in, Musty ma tuni shida Sumayya sun koma legos sai faman uban kiran waya da muke sha da vidio call ko yace na masa vidion yaran ya gansu haka zanyi na tura masa, Rumana tasawa Yaran Aslam Tasnim da islam
Umar farouk shi u
Ake kira da Aslam, Muhammad Kamal kuma Tasnim, Saudat ake kiranta da Islam, Aimanah jego suke na gata ga sabaya da Anty Hasana ta haɗa mata take dama mata kunun kullum tasa mata zuma da madara ta sha, kafin wani lokaci sunyi kuɓul ɓull ita da yaran har Islam ma ta murmure duk da bata kai su Aslam girma ba, Musty satinsa huɗu rabonsa da kano, yau suna waya Aimanah ke masa korafin rashin zuwan sa
"Reina bafa wani abu ya hanani zuwa ba ayyuka suka tusoni a gaba ga transfer danake so nadawo kano cikin yan uwa na na haɗe ku waje ɗaya ku zauna keda Sumayya nan gidan yamana kaɗan innace zan haɗe ku"
"Ni bazan yadda da wani uzurin ka ba kawai dai dan bani da abin baka ne shiyasa".
"Bakiji haka a baki na Aimah"
"Hakane mana rashin zuwanka ganin mu ya bayyana gaskiyya" bata jira mai zaice ba ta katse kiran ta saka number sa a black list a whatsapp ma tayi bloking ɗinsa, Murmushi yayi sanda yaga aikin datayi a fili ya furta
"Aimah rigima" ba shiri washe gari asabar yatawo kano da yamma, Aimanah sai ganinsa kawai tayi, sosai yayi farin ciki da ganinta musamman ganin yanda tayi kiba ta kara haske kai baza kace jego take ba, duk yanda yaso ya keɓe da Aimanh Anty Hasana bata basa dama ba, sarai ta lura da zulamarsa akan Aimanah, yau da sassafe aka kira su Ammi Ana ba lafiya tana Anty Hasana da Ammi suka tafi hankali tashe, suna tafiya kamar Musty yasani ya shigo gidan yaji shuru baiga kuma gilmawar Anty Hasana ba yasan daman Ammi ba mazauniyar gida bace tunda tana fita aiki musamman daya kasance yau ɗin monday, Aimanah na rike da Islam tana bata mama Musty ya ɗan lego ɗakin ganin Aimanah ita kaɗai yabasa kwarin gwiwar shigowa ɗakin zama yayi kusa da ita ta kauda kai gefe
"Aimah wai mai yasa kike da rigima ne kince naki zuwa na ganku kuma nazo ɗin ma baza a sakar min fuska ba" batace komai ba hannu yasa ya gyarawa Islam nonon da take tsotsa
"Ni ka daina taɓa ni" Murmushi yayi yana kallonta kallon dayasan bata iya jure masa, ai kuwa tayi kasa da kai tana murmushi,
"Ko kefa reina har kinsa raina yayi fari" saka Islam tayi a kafaɗa tayi gyatsa kana ta kwantar da ita cikin net ɗinta ta dawo nesa da shi kaɗan ta zauna
"Bazan koma legos ba zan zauna nan kano na koma aiki na, Anty Sumy ta zauna acan" wani kallo yamata kallon baki isa ba kafin ya ce
"Daman ke zaki zaɓa ma kanki inda zaki zauna"
"Daman ai kasan abinda ya kaini legos kuma gasu nan sun fito Allah ya yaye min" baice komai ba sai matsowa da yayi kusada ita da sauri ta mike zata bar wajan ya roko hannunta suka faɗa saman gado, shi yana kasa yayinda ita kuma ta kwanta saman kirjinsa, hannu biyu yasa ya zagayeta ya haɗa ta sosai a jikinsa yana kallon fuskarta, kautar da kanta tayi gefe tana haɗe rai
"Beb kalle ni, kisa idonki a idona nace" yafaɗa da muryar bata umarni
"ke mao yasa kika fiye rigima ne, yanzu fa ba da bane kalli bebys ɗinki kin girma"
"Ni ban girma ba Allah karka sake maidani tsohuwa"
"Ai nima ba cewa nayi kin tsufa ba girma nace, girma daban tsufa daban" ta buɗe baki zatai magana ya haɗe bakinsa da nata ahankali yana tsotsar harshanta duk yanda taso ta kwace kanta ta kasa, gaba ɗaya yagama birkita mata lissafi, a wannan yanayin Anty Hasana tazo ta riske su, da sauri tayi baya ta koma ta maida kofa ta rufe su basu ma san ta shigo ba, jikin kofar ta tsaya tana maida numfashi haɗe da dafe kirji
"Na shiga uku ni hasana ashe abinda zan gani kenan shi yasa Ana ta ce natawo gida na kula da mai jego" kofar ta soma bugawa da karfi, jiki sanyaye Musty ya janye Aimanah daga jikinsa yana gyara rigar Shaddar sa data tattare waje ɗaya
"Wa ye?" yatambayya muyarsa a shake
"Uwarka ce Mustapha nace uwarka ce, uban me kake a ɗakin mai jego?" zaro idanu Musty yayi jin muryar Anty Hasana yai saurin mikewa ya fito daga ɗakin kafin ta tara masa mutane kowa yaji abinda yayi, simi simi ya fito ta gabanta yabar falon bai ko kalli inda take ba, sai da ya shiga gidansa sannan yafarawa kansa dariya
Sanda Aimanah taji shigowar Antyn gyara kwanciyarta tayi tai lamo kamar mai barci
"Kyayi likimo mana Aimanah yar daɗi miji maza biye masa ya kuma ɗirka maki wani cikin kiyi kazamin jego ga ciki ga goyo" Anty nata mita ita kaɗai Aimanah batace kanzil ba tun tana barcin karya harna gasken yayi gaba da ita...✍🏻
[2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹


Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰

☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation

*Shafi na Ashirin da tara*

"Wai Mustapha ya koma ne? tunda nadawo daga gidan Ana ban gansa ba" Ammi ta tambayi Anty Hasana, taɓe baki Anty Hasana tayi tana kyauda kai gefe
"Ni nasan masa ne, Allah ne fa yai mana taimako da tuni kila Aimanah ta kuma ɗaukar wani cikin, nan fa nazo na tarar da shi ya tisa yar mutane a ɗaki yana latsata" Ammi dariya tayi kawai batace komai ba
"Allah yaya saudai kisa yarinyat nan ta yi planing kafin ta koma dan da alama mahaifarta mai saurin ɗaukar ciki ce indai kina lisaafe da watan auran su watan Aimanah tara da kwana goma sha biyu ta haihu"
"Yau nake ganin rayuwa au har kwanaki kika arga masu bayan watanni"
"To yaya abinne ai daga aure sai haihuwa"
"Allah ya kyauta amma Aimanah bazatai planing ba, dama can family ɗinmu bamasu yawan haihuwa bane azo kuma ayi wani planing daga baya azo ana nadama inaga fa duk cikinmu Yaya Aiahatu ce kaɗai ta haifi shida daga mai biyu sai mai ɗaya saini da yaya Mukhtar da muke da uku,"
"Kuma hakane yaya, Amma dai inzata tafi karta tafi ita kaɗai nida cewa nayi ko Gwaggo fulani za'ayiwa magana tazo su tafi tare kinga ta tayata kula da su Taanim"
"Kuma fa hakan za'ayi bari Ana ta warware sai asa driver ya ɗakko ta daga ɗanbattan"

Mustapha bai samu an maida sa kano da aiki ba, Abuja aka tura sa haɗe da garmin girma da lambar girmamawa, anan legus yabar Sumayya ya sauka Abuja nan ma dai gida aka basa karamin gidan da bazai ɗauki mata biyu ba inma an zauna zai zama a takure, hakan yasa ya fitar da kuɗi yasai dankareran gida babba plate hause ne ginin tsakiya Babban falo mai ɗauke da manyan ɗakuna kowanne da banɗakinsa a ciki ga kicin nan cikin falon da kuma wani babba a compount na gidan, shiya saka komai na gidan daya kamada da kayan gado manyan kujeru labilaye kayan kicin komai ya zuba iya yanda zai iya kicin komai yaji babu ce kawai babu duk wata na'ura akwai ta a kicin ɗin nan nan cikin falon da babban dake farfajiyar gidan, gidane da ya kawatu da bishiyoyi na yan gayu da furanni ta ko'ina, mai gadi yasa sai mai kula da fulawoyin gidan, sai da yagama komai sannan ya sanarwa dasu Ammi sukazo itada Mah da Anty Hasana da momy harda yayun Mustapha guda biyu mata da Ahmad da Murjana wacce keta yaba gidan tana hotuna tana turawa Sumayya dake legos, ga Daddy da Abba

Sun yaba gida sosai sun kuma sanya albarka, Abinci mai kyau Mustapha yasa aka kawo masu da lemu da ruwa nan suka yini sai dare suka bi jirgin karfe tara na dare suka koma kano kowa na santi da yaba gidan

Daddy har yayi shirin kwanciya yana kokarin kashe wayarsa kiran Mustapha ya shigo, ban gajiya ya masa har zai katse kiran Daddy ya kira sunan sa
"Mustapha"
"Na'am Daddy"
"Gida yayi kyau sosai Allah yasa rai akayiwa, sannan Sumayya itace babba ita yakamata ta fara zaɓar ɗakin da yayi mata kafin Aimanah"
"Insha Allah Daddy za'ayi yanda kace"
"Masha Allah ubangiji yakara arziki mai albarka akuma ci gaba da rike amana harkar banki wuya gareta misamman kana ganin gilamawar kuɗi, ka tsarkake zuciyarka kagadai yanda gaskiyya ke kai ka gaba, rike gaskiyya da amana shike kai mutum ga matakin nasara, aci gaba da riko da gaskiyya a kuma kau da kai daga haram komai kankantar ta"
"Insha Allah Daddy"
"Yawwa Allah yamaku albarka ya kara haɗa mana kanku aci gaba da zumunchi koda bama raye"
"Amin Daddy Allah yakara lafiya da nisan kwana mai albarka"
"Amin Muhammad Mustapha" sallama sukayi Musty yaja gwauran numfashi yana tina yanda zasu kwaso ta da Aimanah idan yafara bari Sumayya ta rigata zaɓi, saboda rigimarta ya hana Sumayya ta biyo sa nan Abuja yace tabari yazo tukunna, yanzu kuma ga abinda Daddy yace

Aimanah sun zubar da wanka, tuni Anty Hasana ta koma Qatar bayan ta gama tsuma Aimanah da ingantattun maganin mata wanda Antyn ta haɗa mata da kanta, sai wanda kawarta yar sokoto ta aiko abawa Aimanan, ziyara sukayi sosai itada yara da Gwaggo fulani mace mai kirki wacce batada son jiki ga tsabta da fara'a, kwanan su hamsin da biyu Musty yazo kano kwanan sa ɗaya sai ga Sumayya washe gari kuma ya haɗa su suka koma Abuja gaba ɗaya,

Aimanah bin babban falon daya kawatu da manyan kujeru tayi da kallo tana kallon yanda aka kawata falon da kujeru, tsaye tayi tana bin ko ina da kallo tsaɓanin Sumayya data yiwa kanta mazauni a ɗaya daga cikin kujerun da ke falon,
"Aimah kinyi tsaye baki zauna ba, Gwaggo ga waje zauna"
"Kanuna min ɗakina zan shiga" kallon Sumayya yayi kana ya ce
"Ku biyo ni" bayansa suka bi suka zagaya ko wanne ɗaki suka gani Aimanah ta fara magantuwa
"Gida yayi kyau sosai Baby" Musty Sumayya ya zubawa idanu yana kallon yanda tayi kasa da kanta
"Sumy wanne bedroom kika zaɓa?" da sauri Aimanah ta ɗago ta kallesa cikeda mamakin maganar sa
"Duk wanda kace na shiga" murmushin gefan baki yayi yana kallon Aimanah,
"Ga ɗakin ki can" yanuna mata wanda ke bangon yamma, bata ce komai ba ta yi baya ta shiga,
"Nifa" Aimanah ta faɗa tana turo baki gaba
"Ga wanda nai maki sha'awa can na kusa da na yara," batace masa komai ba ta shige ɗakin, ɗakun nan gaba ɗaya iri ɗaya ne ba wani abu daya banbanta sai ko kala na labulaye, rayuwa ta ba ruwan kowa da kowa ake tsakanin Aimanah da Sumayya, sumayya daman ma'abociyar son zaman ɗaki ce, girki kowa nasa yake sai ranar girkin ka kabawa mijinka, Aimanah tuni ta koma makaranta zatai Masters dgreee, Sumayya ma gurbin karatu Ya sama mata ta fara karatu sosai ta maida hankali ga karatunta batai sake ba kamar yanda tayi a baya, Mustapha yasami nutsuwa da kwanciyar hankali, yai kiba sosai kuɗi sun zauna ga aikinsa da yakeyi da albashi mai tsoka ga kasuwanci dayake yi shiyasa tako ina kuɗi ke shigo masa, Salman ɗan gwaggo fulani ya ɗakko daga ɗan batta yasama masa makarantar gaba da scoundry yafara zuwa yana karantar business, Mustapha mutum mai taimakon na kasa da shi, ya rungumi yan uwan Anan na Danbatta wanda basuda hali yana taimaka masu sosai,

Yaran Aimanah kyawawa masu matukar kama da mahaifinsu karma mazan suji labari, sun girma sosai dan yanzu shekarunsu uku sun taso cikin gata da kulawar iyaye da gwaggo fulani dake ɗawainiya dasu, soyayya sai abinda yayi gaba tsakanin Mustapha da Aimanah, sosai yake kamanta adalci a tsakanin matansa Aimanah taci gaba da karatunta gefe kuma tana aiki da ɗaya daga cikin gidajan redion dake garin Abuja, itama tana taɓa kasiwanci na online tana ordar perfume da abays da takalma daga waje har atamfofi kusan ba abinda bata kawowa sai dai in bakace kana soba, Mah itada Daddy tuni suna kasar saudiyya shugaban kasa ya yiwa prof ambasada a kasar saudiyya Mah da Ma'aruf da Dadyy na can, gaba ɗaya yayun Aimanah ba wanda yake kasar kowa ya kama gabansa wasu na karatu yayinda wasu ke aiki a kasar da suke

Sumayya yau baki tayi kawanta ne wanda suke karatu tare suka kawo mata ziyara suna zaune nan falo suna hira, Aimanah tadawo daga wajan aikinta yau bataje makaranta ba, gwaggo fulani da suke ɗakinsu itada yara suka fito tun sanda sukaji tsayawar motar ta, Salman ɗan gwaggo fulani ya shigo falon da sallama ya mikawa Aimanah car key ɗinta yana faɗin
"Hajiya ga keys ɗin nan"
"Yanzu dai bazaka daina kirana da Hajiya ba, nace in bazaka faɗi suna na ba kace min Anty mana"
"Da dai yafi sauki kam" gwaggo fulani ta faɗa tana dariya
"Yawwa salman bari na ɗakko maka kuɗi kasiyo mana hanta yau miyar alaiyahu nakeson yi a gidan nan naga kuma bama da hanta" Aimah tafaɗi haka tana tafiya zuwa ɗakin Al'Mustapha dake can karshan falo cikin wani lungu, gaba ɗaya kawayan Sumayya suka bi Aimanah da kallo wacce ita sam bata lura da suba, mintina kaɗan da dawo hannunta rike da kuɗi ta mikawa Salman, ya juya ya fita
"Amma" Islam ta faɗa tana shigewa jikin Aimanah, ɗaga ta tayi sama tana mata wasa
"Maman Hanif ta shigo ɗazu bakya nan"
"Allah sarki bari na gama aiki zan dai shiga mu gaisa" Aimanah sai sannan taga bakin Sumayya ta karasa wajansu fuska a sake tana gaida su, suma faram faram suka amsawa Aimanah gaisuwarta taja yaran suka shiga bedroom ɗinta, Gwaggo Fulani ta koma ɗakinsu, Feenah ta kalli Sumayya ta buɗi baki zatai magana sai Leena ta ce
"A'A kar ce komai mu shiga daga ciki" Feena hannun Sumayya taja suka shiga Bedroom ɗinta suka kullo harda saka key, zama sukayi gefan gado fina ta rike baki tana kallon

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login