Showing 24001 words to 27000 words out of 84763 words
Chapter 9 - AIMANA Book Complete by MAMI YUSUF DABO.txt
tayi tana gyara zaman mayafinta ta ce
"Yau kam insha Allah zaka shiga can ciki ba shamaki duk da dai inajin tsoro bantaɓa yi ba"
"Haba karkiji wani tsoro aiba da zafi zan maki ba, jiya na tabbata baki san harkar ba ganin yanda jikinki ke rawa, gaba ɗaya kin hanamin nutsuwa barcin danayi gaba ɗaya mafarkinki ne, yanzu ma fa saida nayi wanka da zan fito, bakiji yanda na kwaɗetu da naji zumarki ba, kinsan ku yan duma duma ɗin nan kunada wani sirri daba kowanne namiji ne yasan shi ba, shiyasa a kallo ɗaya dana maki randa mom ɗina ta aikani wajan Mom ɗinki na faɗa" Murjana dariya tayi tana kashewa Salim idanu
"Yanzu to ina muka nufa?"
"Gidanmu mana"
"Wai kana nufin yau ma acan za muyi nifa kunyar Mom ɗinka nakeji"
"Mom ai vatada damuwa, Dad ɗina ne masifaffe shi kuma baya ma kasar yana thailand kuma ta kofar baya zamu shiga gidan ba wanda zai san ina gidan ma bare a hanani morewa" Murja tayi shiru tareda kwantar da kanta saman kujerar motar, har suka karasa gidan bata sake magana ba, Salim da kansa ya buɗe get ɗin bayan ya shiga ya faka motar a ciki ya maida get ɗin ya kulle, buɗewa Murja kofa yayi ta fito suka jera kai tsaye zuwa ɗakinsa, babban ɗakine daya sha kayan alatun more rayuwa kamar wani ɗakin Amarya basu tsaya a falon ba kai tsaye bedroom ya wuce da ita ya zaunarta gefan gado yafara rage kayan jikinsa, yarage daga shi sai gajeran wando Murja gaba ɗaya kunya ta kamata ta rufe fuska ya zauna kusa da ita ya hata da jikinsa ya kama hannunta ya ɗora saman j ɗinsa, jikin murjana ya kama karkarwa saboda hannunta daya taɓa abinda bata taɓa gani ba,
"Kinga nutsu muyi magana nawa ne farashin wannan ranar" Murjana jin anzo wajan da take bukata ta saki jikinta tana kallonsa
"Nawa zaki biya?"
"Zan biya farashi mai tsada indai kinmin abinda nakeso" Salim ya biya bukatarsa wacce yadaɗe yana fata da buri akanta, shi daman harga Allah ba auranta zaiyi ba, bukatarsa kenan, tun daga ranar yamaida Murjana tamkar matarsa sanda duk yaji bukatar kasancewa da ita waya kawai zai mata yaje ya ɗakkota in bukatarsa ta biya yadawo da ita gida da makudan kuɗaɗe da siyayya kala kala Amarya tayita rawa tana murna ƴarta mai farin jini.
*Al'Mustapha*
Ba wani ɓata lokaci likitoci suka karɓesa emargency sukayi da shi, Ammi kuka take sosai momy na rarrashinta, har sanda likitocin suka fito, Ammi bata tsaya jin abinda suke cewa Abba ba tabi gadon da aka turo Al'Mustapha zuwa word, zama tayi gaban gadon ta ruko hannunta cikin nasa, yayi firit fuskar nan tayi fayau kai daga ganin barcin dayake kasan bana daɗi bane,
Aimanah tasa kafa ta zunguri Rumaisa dake barci
"Allah Rumaisa in baki tashi ba zan gayawa Mah har yanzu bakiyi sallah ba takwas saura fa"
"Anty ki barni nai barcin nan Allah na gaji sosai"
"Ok saboda kin gaji bazakiyi sallah ba akan lokaci ba ni ma ai da gajiyar amma haka nayi sallan da asuba, ki tashi kona saɓa maki" Aimanah jin anbuɗe get na gidan za'a fita da mota tai saurin ɗaga labulan window ɗin ɗakinta, Mah ta gani da Daddy a mota zasu fita, da sauri tasaki labulan ta fita compound na gidan kafin ta karasa har sun fita sai Yah Mas'af da Ma'aruf tsaye fuskarsu fal damuwa
"Yah inasu Daddy suka tafi da safiyar nan?" Aimanah ta faɗa tana kallon Yaya Mas'af, baice komai ba yaja hannunta zuwa cikin gidan
"Yah kamin magana fuskarku fal damuwa nagani"
"Kinga kwantar da hankalinki ba wata damuwa bace bafa, Musty ne ba lafiya yana hospital tun jiya da dare sai aman jini yake" Aimanah ta dafe kirji tareda fito da idanuwa
"Musty fa" tafaɗa cikeda damuwa, hannunta ta cire daga na Mus'af ta shige ɗakinta, Rumaisa ta tarar a tsaye tana zagaye ɗakin tana ganin shigowar Aimanah ta rokota ta fashe da kuka
"Anty wai Musty ne a hospital an rasa gane kansa sai aman jini yake yanzu Anty ta kirani tana kuka take faɗa min, kizo muje hospital ɗin" Aimanah hararar Rumaisa tayi ta koma gefan gado ta zauna tana danna wayarta Rumaisa na tsaya tana kallonta ganin ko a jikinta wayama take da Abas hankalinta kwance, Rumaisa ficewa tayi daga ɗakin a fusace tayi sa'ar ganin Ma'aruf zai tafi asibitin suka tafi tare, Mus'af duk ya damu jin Aimanah shuru a ɗakinta kusan awa bata fito ya laƙa ɗakin barci yasamu tana yi hankalinta kwance, shima hankalinsa ya kwanta duk a tunaninsa zata damu da halin da Misty yake ciki, shima shiryawa yayi ya tafi hospital ɗin, asibitin ya cika sosai da ƴan uwa kowa hankali tashe har saida likitoci sukayi magana aɗan ragu kana wasu suka dawo gida akabar Ammi momy da Mah sai Anty Hasana daketa shuga da fita wajan likitoci dan jin abinda ke damun Musty yanzuma tana zaune gaban babban likitan dake kula da Mustapha
"Hajiya gaskiya ɗanki na tsakanin rayuwa da mutuwa zuciyarsa ta kumbura sosai da alama akwai wani abu da yake damunsa a zuciya mun dai yi kokari mun tsaida aman jinin dayake, sauran kuma saidai mu ɗorasa a magani sannan inya farka ayi kokari a rinka kwantar masa da hankali sannan duk wani abu da kukasan zai sanyaya zuciyarsa ayi masa kana a guji ganin wani abu da zai tada hankalinsa"
"Ok Dr mun gode" ta fita daga office ɗin wayar Aimanah ta kira lokacin Aimah tashinta daga barci kenan taga kiran Antyn saida gabanta yafaɗi haka kurum takejin tsoron Anty Hasana sabida tasan masifar ta,
"Hello Anty" Aimanah ta faɗa cikeda ladabi
"Sannu Aimanah yanzu a faɗa maki Musty ba lafiya amma ki kasa zuwa kusan kowa yana wajan nan banda ke, to inkinga dama kiyimin fatan dankali ki kawomin nan bance dole ba sai kinga dama" bata jira tace komai ba ta katse kiran Aimanah sakkowa tayi daga saman gadon tana turo baki gaba ta shiga kicin, Haule ta taimaka mata suka haɗa fatan dankalin daya sha alayyahu ta shirya cikin doguwar rigan atamfa da babban hijab ta ɗauki basket ɗin data gama haɗa komai a ciki ta fita, bata hau motanta ba titi ta fita ta hau adaidaita zuwa hospital ɗin, bata sha wuyan samun su ba tasami Ammi da Anty Hasana a recepsion, Ammi ce kawai ta amsa gaisuwarta Anty harara kawai take aika mata tana tsugunne a gabansu ta kasa cewa komai tayi kasa da kanta daga ta ɗago suka haɗa idanu da Anty Hasana harara kawai take aika mata
"Zaki tashi ki shiga kikai masa abincin ko bazaki iya ba?"
"Anty kiyi hakuri"
"Naki na hakura, nace bazan hakura ba gashi nan sai kije ki karasa shi banda ma ke Aimanah gida bata koshi ba a...."
"Kai Hasana dan Allah ki rage masifar nan taki kina girma kina daɗa cin kasa, ke Aimanah shiga ciki ki bawa Mah abincin tana ciki" Ammi tafaɗi haka tana kallon Aimanah, jiki sanyaye Aimanah ta shiga ɗakin akai sa'a Musty na kallon kofa, da sauri ya mike zaune harya na neman faɗowa kasa saida Mah tai saurin rikesa ta gyara masa zaman jikin filo har sannan idanunsa na kan Aimaah da take gaida Momy, Mah ce ta soma fita daga ɗakin kafin Momy ba tabi bayanta, Aimanah na tsaye jikin gadon takasa cewa komai idanunta na kasa tana hawaya ganin yanda Mustapha ya rame sosai ya kara wani fari tas kamar wanda ba jini a jikinsa,
"Aimahh zuba min abinci naci yunwa nakeji" hannunta na rawa ta mika masa plate ɗin data zuba fatan dankalin, jikinsa duk ba kwari hakan yasa ya kasa rike plate ɗin, kujera taja gaban gadon ta zauna ta rike masa plate ɗin yana cin abincin a hankali, harya gama ta basa goran ruwa ya sha batace masa komai ba, tana kallonsa ya gyara zaman sa idanunsa a kanta
"Ya Musty na sani duk saboda nine ne hakan ta faru, kayi hakuri ka ɗauki kaddara daman can kasa a ranka ni ba matarka bace, tabbas har yanzu zuciyata na sonka amma son dana kewa Abas yadame naka ya shanye koda ace nafi sonka a kansa lokaci ya rigada ya kure mana bazan maida iyayena kananun mutane ba, kayi hakuri ka zauna da matarka ko ka auri Rumaisa" kallon Aimanah kawai yake yama kasa cewa komai saboda tsabar takaici wai Aimah ce yau take kallon idanunsa take gaya masa tana son wani sama da son datake masa har tana basa shawarar ya auri wata,
"Shikenan Aimah naji na gode kuma da kika gayamin gaskiyyar dani na kasa fahimta na hakura dake har abada😭sannan bazan iya auran Rumaisa ba, dan Allah Aimah ki daina guduna mu koma Aminai tunda kin daina sona, guduna da wulakanta ni da kike yafi komai ɗaga min hankali"
"Insha Allah na daina gudunka daga yau banida aboki amini sama da kai" Aimanah tafaɗi haka tana saka hannunta cikin nasa, saurin cire hannunsa yayi daga cikin nata yaɗan ɓata rai
"Abas ya ɓata min ke ko?"haramun ne rike hannun wani wanda ba muharramin ka ba kin rigada kinsan haka"
"Yah Musty nifa kaida yaya Mas'ud ba ku da bambanci a wajena"
"Da bambanci Aimah ni da aure a tsakaninmu shi kuma ba aure a tsakaninku"
"Hum mubar maganar nan aboki"
"An bari gimbiyata"
"Gimbiya kuma ba ruwana in Anty Sumy ta jika" dariya sukayi tare, Mas'ud da Anty Hasana da suka shigo tare saroro sukayi suna kallon Musty dake kyalkyala dariya
"Da kyau douther aikinki yayi kyau kinsa gawa ta tashi"
"My Anty nine gawar" Musty yafaɗa yana kallon Anty Hasana" Mustapha zare allurar dake jikin canuler ɗin hannunsa yana kallon Mas'ud
"Kaga Aboki kira Dr yazo ya sallame ni gida zan koma"
"Sannu majanun Ka koma gida mana tunda lailar ka tazo"
"Hmm" kawai Mustapha yace yana mikewa tsaye ya fita recapsion, Anty Hasana ta kalli Aimanah ta taɓe baki ta fice daga ɗakin.
Murjana ta kalli Salim daya fito daga wanka yana tsaye gaban madubi yana gyara kansa,
"Nifa Salim inajin tsoron shan wannan kwayoyin da kake bani kar sumin illa nan gaba,"
"Haba ba abinda zasu maki nafa hana ɗaukar cikine am Dector bazan baki abinda zai zamo mana matsala anan gaba ba, auranki fa zanyi" Murja ta mike ta wuce ta gabansa zata shiga bathroom
"kai yarin nan kifa daina juya min mazauna nan naki zan iya komawa fa"
"Haba kai kama isa gida zan koma Abba da Yah Ahmad sun fara matsamin fa naga kwanan nan idanunsu a kaina yake musaman Yah Ahmad kasan gayan nan ɗan bala'i ne, yanzuma basai ka kaini gida ba a daidaita zan hau" harasa sawa yayi kusa da ita ya rungumeta a jikinsa yana mata raɗa a kunne dai dai sannan Mom ɗin Salim ta shigo ɗakin kallo ɗaya tayi masa ta ɗauke kai ta zauna gefan gadon nasa tace
"Saketa to ta shiga wankan zo magana zamuyi kasan yau Dad zai dawo kasar nan inajin kuma anan kano zai sauka" Murja ta faɗa bathroom cikeda kunya shi kuwa Salim ya zauna kusa da Mom ɗinsa yana kwantar da kansa saman kafaɗarta.
Abas ya kalli Hajiya datake buɗe kayan da Hajiya Maimuna ta kawo
"Malam Abas kayan nan basuyi yawa ba kuwa"Abas yashafi kansa yana murmishi ya ce "Hajiya basuyi yawa ba duba da gidan daza'a kai kayan"
"Shikenan Allah yasa albarka" hajiya tafaɗa, Allahji Abubakar Mahaifin Abas yashigo kallon tarin akwatinan da manyan manyan jakukunan dake zube a falon kallon kayan yayi ya zauna saman kujera
"Hajiya wannan kayan fa kamar za'a buɗe babban store"
"Kayan ɗanka ne yanzu Hajiya maimuna ta kawo su" buɗewa Hajiya tasomayi tana nuna masa
"Masha Allah kaya sunyi Abas Allah ya sanya alkhairi"
"Amin Baba"
"Au kace Amin" dariya akayi gaba ɗaya, Abas yamike yana shirin fita daga ɗakin
"Abas ina zaka barmin kayan nan anan, maza gayawa su Alhaji Habu da yamman nan suzo sukai kano"
"Abba wai kai lefanma bazakaje ba?"
"To inje inyi me Abas ga wakilai na nan su Alhaji Habu ma sun isa komai" Abas yafita batare daya ce komai ba, a ranar aka kai lefan Abas gidansu Aimanah tareda invitesion na ɗaurin aure a baban kwali lodi guda, sati biyu ya rage hakan yasa ta ko'ina shirye shirye kawai ake daga ɓangaran Abas harna Aimanah tuni Anty Hasana ta ɗauke Aimanah zuwa gidan ta dake Kabuga gyara sosai take mata tareda magani sanyi bata zuwa ko 'ina, ko aikinta ma ta daina zuwa ta ɗauki hutu, ta kara kiba da haske alamun hutu sun bayyana karara a jikinta Abas tunda yazo washe garin da aka kawo lefe bai sake zuwa yana Abuja yace sai ranar ɗaurin aure zai zo waya kawai suke ba kama hannun yaro soyayya sai abinda yayi gaba,
Bawan Allah Mustapha ya kasa mantawa da Aimanah yanzu suna waya sosai ana gaisawa ba batun soyayya sai zumunci, a gidansa kuwa gaba ɗaya Sumayya ta kasa gane kansa yafitar sabgarta wataran saita kwana ta wuni ma bata saka sa a idanunta ba, ga komai ya tsaya boka cin kuɗinsu kawai yake aiki baya ci, dan sosai Musty ya rike addu'a musaman azkhar ɗin safiya da maraice baya wasa dasu kusan ko yaushe yana makale da wayarsa yana karatun kur'ani cikin haka ne yasami karin girma da canjin wajan aiki aka maidasa CBN bank reshansu dake legos, shi kaɗai ya tattara ya tafi bayan yayi sallama da Ammi tasa masa albarka, wata kalar rayuwa yake a legos mai ɗauke da kunci da damuwa baya zuwa ko ima sai office ɗinsa kusan duk abinda zai siya ma oder yake akawo masa har gida,ko yaushe ka gansa fuska ba walwala, cikin haka har yau yarage saura kwanaki uku bikin Aimanah shi baima sai ba, saida yakira Ammi suka gaisa take ce masa
"Mai babban suna baza kazo bikin Aimanah bane?" kirjinsa ne yai wata irin bugawa da har saida ya rikesa
"Zanzo Ammi yaushe ne?"
"Ranar Asabar ne mai zuwan nan" baice komai ba ya katse kiran ya jingina kansa da jikin kujera hawaye suka fara zubowa daga idanunsa kifa kansa yayi saman teble ɗin dayake kai yafara kuka a hankali, kuka yayi sosai kafin yafara ambaton Allah a zuciyarsa tareda fatan Allah yasa hakan shi yafi masa alkhairi,
Anan kano kuwa sosai aka fara shirye shirye ba wasu event zasuyi ba dinner ce kawai ranar juma'a washe gari a ɗaura aure a wuce da amarya jigawa ranar lahdi Hajiya zatayi nata yinin litinin su wuce Abuja, inda amarya zata tare sosai abas ya gyara gidansa ya zuba komai na bukata bai bari su Aimanah sunyi komai ba duk da nacin da yaya mansur yayi amma yace subar komai shi zaiyi, gida yayi kyau sosai Anty Ummi data je ta gano ranar da zasu tawo kano sai yaba gidan take a jirgi ma ta cika Mansur da surutu duk akan gidan, yau Juma'a tun yamma kowa keta shirye shiryan tafiya tafiya wajan dinner da za'a fara karfe bakwai, waje yayi kyau sosai musamman ango da amarya kowa ka gani yana cikin farin ciki dangin ango basuda yawa sosai kusan dangin Aimanah su suka fi yawa a wajan anci ansha an gyagije amarya da ango sun rausaya wajan goma na dare aka tashi saboda gargaɗin da Daddy yayi kan kar ayi dare, Aimanah gaba ɗaya batajin daɗi misamman dataga ba Al'Mustapha a wajan dinner dan har Sumayya tagani a wajan, hakan yasa suna dawowa ta shige ɗakinta ta kullo ta zauna gefan gado tana danna wayarta Musty ta kira, Mustapha dake kwance ɗakinsa ya kasa barci ganin kiran Aimanah yai picking call ɗin da sauri
"Yah Musty" kawai saita fashe da kuka
"Aimah kuka kuma kukan me kike a wannan daran daya dace ki kasance cikin farin ciki daran da nine yaka mata nayi kuka"
"Yah shine bakazo wajan dinner ba"
"Bazan iya zuwa ba Aimah na ganki da wani nayi nadamar zuwa garin nan ma inaga jirgin safe zanbi na koma inda na fito"
"Yaya kazo na ganka" da sauri yamike daga kwancan daya ke ya zari car key ɗinsa dake ajje saman firij ya fito, dai dai zai fito daga gidan a mota ita kuma Sumayya ta shigo bai tsaya ba kamar yanda take tsayar dashi yayi gaba, Kiran wayar Aimanah yayi ta fito compound na gidan inda yake zaune kan daya daga cikin fararan kujerun daya gani a wajan da alama wasu ne suka tashi a wajan, gidan yayi shiru kusan kowa yayi barci musamman daya kasance lokacin sanyi ne ko ba barci zakayi ba saika dangana da ɗaki,
Aimanah tana hango Mustapha ta karasa wajan da gudu ta tsugunna ta fashe da kuka, shima kukan yake a haka Anty Hasana ta karaso wajan ta tarar dasu
"kukan me kike, kukan munafurci kona yaudara?"wuce ciki kafin naci ubanki anan wajan salon ki saka ciwonsa yatashi muzo muna karasa biki a hospital, kai kuma ka wani zo gabanta kana wani kuka kamar karamin yaro Allah ya kaimu gobe zanyi magana da Alhaji kamal ɗin aure za'a sake maka" tana gama faɗar haka taja haunnun Aimanah suka wuce ciki,
Wai akace rana bata karya sai dai uwar ɗiya taji kunya hakance ta faru yau waje waje yayi manyan mutane ta ko ina an taru ana kokarin ɗaura auran Abas da Aimanah liman ke kira ina waliyan amarya dana ango a matso kusa za'a ɗaura aure, Alhaji Abubakar ya matso kusa sukayi ido huɗu da Alhaji Farouk mai naira, hannu yasa yana nuna Prop Faruk mai nera fuskar Alhaji Habu ba walwala ya ce
"Faruku maiya kawo ka wajan bikin ɗana"
"Habu kai dai zance mai kazo yi wajan ɗaurin auran ƴata"
"Kana nufin Abas ƴarka zai aura?"inko har hakane adakata adakata nace liman kar a ɗauran wannan auran na rantse da Allah ɗana bazai taɓa haɗa jini da naku ba Faruku...✍🏻👩🦯
[2/13, 4:44 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹
Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰
☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation
*Shafi na goma sha biyar*
Prop cikeda damuwa ganin yanda idanun mutane yadawo kansu ya ce
"Habu abinda yafaru ya rigada ya wuce iyayanmu ne sukayi mu bazamu biya bashin gabar dasukayi ba"
Alhaji Abubakar daya ɗauka da zafi huci kawai yake