Showing 42001 words to 45000 words out of 84763 words

Chapter 15 - AIMANA Book Complete by MAMI YUSUF DABO.txt

Hanne ita ce ke sakkowa daga saman bene tana sanye da riga da wando jajaye kanta bako hula saima uban gashin doki data cika kanta, kai tsaye tana zuwa kusada Amarya hannu tasa a jikinta tana shafata tana wani lumshe idanu, getman juyawa yayi ya fita yana girgiza kai
"Sannu da zuwa tun ɗazu nake jiranki ashe da gasken zaki zo"
"Zanzo mana ai na gaya maki indai zan sami kuɗi zan iya aikata komai" kai Hanne ta jinjina tareda zaunar da Amarya kan kujera ta miko mata lemu a cup tace
"Yawwa sha wannan bari na shiga daga ciki ga kayan abinci nan kici duk abinda kike so zan komasama inada baki ne yanzu zan sakko inna sallamesu" Amarya kai kurum ta ɗaga ta kai cup bakinta bako bisimillah ta kwankwaɗe lemun daya sha magunguna tas a bakinta, mintina kaɗan da shanye lumun nata tafara jin wani yanayi a jikinta na daban, tun tana jure yanayin har ta mike ta hau saman tasoma laluban inda zataga Hanne, Hanne dariya tayi sosai ganin Amarya na laluban inda zata ganta kenan maganin ta yayi aiki dariya tayi sosai , fitowa tayi daga ɗakin ta ja hannun Amarya suka faɗa ɗakin, Amarya ba tinanin komai ko abinda zaije yadawo ta biyewa Hanne suka aikata ma sha'a son ransu😰

Al'Mustapha takwas saura minti biyar ya isa gidansa, wanka yayi yasha tea yai shirin kwanciya gobe fitar safiya zaiyi so yake bakwai tamasa a office yasan kwanakin nan daya shafe baya nan ayyuka zai tarar jibge a office ɗinsa, yana kwanciya kewar Aimanah ta lulluɓesa wayarsa ya jawo ya danna call wa Aimanah sai dai wayar bata shiga ya kira yafi a kirga bata shiga ba hakan yasa ya kira Ammi saida suka gaisa kana ya ce
"Ammi waye yaje wajan reina na kira wayanta bata shiga kodai har yanzu kukan take?"
"To yanzu wacce amsa zan baka" dafe baki yayi kana yana yar dariya ya ce
"Allah yakara lafiya Ammi wacce duk kika bani zan amsa" itama dariyan tayi kana ta ce
"Muhammad Mustapha anya kuwa kana kamanta adalci a tsakanin Aimanah da Sumayya" Musty shafa kansa yayi yana murmushi ya ce
"Ammi zan kamanta insha Allah, nabaro Aimah tana kuka ne shiyasa gaba ɗaya na damu na kira wayarta kuma a kashe"
"Tana lafiya kila ko ta kwanta barci ne ta kashe wayar, ɗazu bayan sallar insha na tura mata Surayya da Rumana su kwana tare" sallama ya mata da sauri ya katse kiran, Ammi tabi wayar da kallo tayi murmushi tareda girgiza kai ta ce
"Hmmm Musty kenan, Allah yabaku zaman lafiya da zuriya ɗayyiba" Musty gaba ɗaya damuwa ta mamaye sa musamman daya kira wayar Rumana yaji a kashe wayar Surayya kuma duk sanda zai kira number basy
"Mas'ud" Mustapha yafaɗa yana murmushi, layin Mas'ud ɗin ya kira shima dai Number basy, dafe kansa yayi ya mike yana rike da waya a hannu yana zagaye a ɗakin, minti biyar tsakani kana ya sake kiran wayar Surayya wannan karan ta shiga, lokacin da kiran ya shiga Surayya tana kusada frige tana shan ruwa wayar na kusa da Rumana, Rumana dake dariya ta ɗauki wayar tana kallon fuskar wayar
"Surry yayanmu ne" kwarewa Surayya tayi da ruwan datake sha ta fito da idanu haɗe da dafe kirji
"Na shiga uku ni Surayya mai nayi kuma da daran nan?" Aimanah na dariya tamike ta shige bathroom na cikin falon, Surry na ɗaga wayar bai tsaya amsa sallamar datake masa ba ya ce
"Ina reina bata wayan"
"Ta shiga bathroom"
"Kice ta kunna wayarta" katse kiran yayi yana kallon wayar tasa ransa ɓace, tsawon mintuna yana jera kiran wayar Aimanah amma bata shiga ransa ya kara ɓaci yasake kiran wayar Surayya lokacin suna dayan ɗakin sunyi shirin kwanciya barci,
"Kai dan Allah yayarmu ki kunna wayarki nifa harga Allah innaga kiran Yayanmu gabana har faɗuwa yake saboda nasan hakanan bai kiran wayata" Surayya ta faɗi haka tana kallon Aimanah, Aimanah gyara kwanciyarta tayi ta juyawa masu baya tana murmushi, Surayya ɗaga kiran tayi
"Yayanmu wallahi taki kunna wayarta fa nama rasa inda tasa wayar tata"
"Sa wayar a hansfree" tayi abinda yace ɗin da sauri Aimanah tasa hannu ta toshe kunnuwanta, Rumana ta fisgo wayar daga hannun Surayya ta ɗorawa Aimanah a kunnanta suka ruke hannuwanta
"Aimanaaa" yanda yaja sunan yasa taji wani yanayi na daban a jikinta, gaba ɗaya jikinta yayi wani irin sanyi
"Aimanaaah"
"Uhmmm" tafaɗa a kasalance
"kinaso na biyo mota a daran nan na dawo kano ko? kinsan yanda nakeji kuwa Aimana kinsan yanda sonki yake azabtar da ruhi da gangar jikina, kinsan yanda kewarki ta addabi zuciyata kuwa Aimaaah, na rokeki duk laifin da zanyi kar a hukunta ni da rashin jin sassanyar muryar nan taki please Aimahh, gobe ki biyo jirgi kizo kona samu nutsuwar yin aiki"
"To kadawo kano da aikin mana" Aimanah tafaɗi haka tana turo baki gaba
"Zanso hakan ta kasance zan kuma gwada Allah yasa su min transfer"
"Nifa barci nakeji"
"Haka zamuyi dake bama ko tambayya ya hanya ya nake" katse kiran tayi tareda kashe wayar Suraiyan tasa ta kasan filo
"Yaya Aimana nayi magana"
"Kice me?"
"Ni sai nake gani kamar baki kyauta ba, bafa ke kaɗai bace a wajan mijin nan naki yana bin kanki kinata masa yawo da hankali karfa ya karkata ga Anty Sumayya kizo kuma kina mana koke koke" dariya Aimanah tayi tana sake gyara kwanciyya ta ce
"Surayya kenan nasan abinda nake ko zuba idanu kawai"
"Yaya maganar Surayya fa abar dunawa ce"
"Abbas ya kiraki?" tafaɗi haka tana kallon Rumana,
"Ba wannan maganar muke ba," Rumana tafaɗa itama tana gyara kwanciyarta, Surayya ma filo taja ta kwanta tana binsu da kallo.
[2/13, 4:45 PM] +234 904 746 4048: 🌹 *AIMANA*🌹


Story and writting by
Mamie Yusuf Daboo🥰

☀️ *First Class Writer Asso*☀️
Home Of Qualities And Trusted Writer's Of The Nation

*Shafi na Ashirin da uku*

Alhaji farouk ya kalli Alhaji Abubakar idris wada dayake ta faman basa hakuri, murmushi Alhaji farouk yayi kana ya ce
"Alhaji ni daman ban rike ka ba kaine ka ɗauka da zafi ko lokacin ɗaurin auran Aimanah ma sai da nace mu tsaya mu fuskanci juna amma kaki yadda, yanzu dai kaga yanda abubuwa suka kasance Allah yasa haka shiyafi alkhairi garemu gaba ɗaya, yaya Abbas yake"
"Yana lafiya yanzuma shiya taso ni daman kuma ina son zanzo nabaka hakuri"
"To Allah dai yasa lafiya" Alhaji farouk yafaɗa yana gyara zamansa saman kujera
"Lafiya kalau ya tasoni ne kan maganar dai auransa yacemin akwai yarinya kanwar Aimanah Rumana in wani bai rigasa ba amasa izini" Prop yafaɗaɗa murmushinsa yana faɗin
"Alhamdulillah masha Allah nayi matukar farin ciki da haka sai dai ban sani ba ko akwai maganar wani akanta, amma bari na kira mahaifinta muji" Alhaji ya ɗanna wayarsa ya lalubo lambar Dr Makthar mahaifin Rumana kiran farko Dr dake zaune cikin ɗakin sa shida Anty Hasana ya nunawa Anty Hasana fuskar wayar
"Abin mamaki kinga kira daga prop da yammacin nan" ɗaga kiran yayi tareda ruko hannun Anty Hasana ya jawota jikinsa
"Barka da yamma prop"
"Yawwa barka dai Dr ya gida ya Qatar?"
"Alhamdulillah sai godiya"
"Masha Allah, daman kan maganar Rumana ne...gaba ɗaya yanda sukayi da Alhaji wada idris yafaɗa masa jimm yayi kafin can kuma ya ce
"Prop banida abin cewa kan maganar nan indai har Abas yayiwa Rumana to nabasa ita Allah ya basu zaman lafiya, nabar ragamar komai a hannunka har ɗaurin aure ka ɗaurawa Ruma aure Allah yasa albarka" Anty hasana mikewa tayi daga jikinsa ta zauna tana lega fuskar mijin nata dan sarai taji yanda sukayi
"Dr da wirwuri haka Ruma fa karamar yarinya ce duka duka yaushe na haifeta ko Mujahid fa shekarunsa ashirin fa yanzu" dariya Dr yayi
"Rigima dai rigima ke ko yaushe zaki girma sanda na aure ki shekarunki nawa?" dariya tayi ta ɓoye kanta a kirjinsa tana dariya sosai, shigowar babban yaronta Mujahid yasa ta cire kanta daga kirjin Dr
"Alhaji kaji yanda mukayi da mahaifin Rumana na yarda da tarbiyar Abbas tun a farko na basa ƴata Aimanah a yau na sake basa Ƴata Rumana na tsaida biki nan da makonni biyu masu zuwa lefanku daman yana nan, yanzu sun zama na Rumana sadaki kawai muke bukata daga gareku"
"Prop nagode sosai da wannan karamci dakayi min nagode Allah yasaka da alkhairi"
"Amin" prop yafaɗa sukayi sallama, kafin wani lokaci labarin tsaida ranar bikin Rumana ya karaɗe dangi gaba ɗaya kowa murna yake sosai musamman Aimanah, Abbas ne kawai gashi nan gashi nan shi bazaice yana farin ciki ba haka bazaice yana murna ba.

Mustapha gaba ɗaya yakasa gane kansa baijin nutsuwa sam atare dashi ko yaushe Aimanah aimana burinsa kawai ya gansa gashi ga ita, ita kuma taki basa haɗin kai gaba ɗaya ko kiransa bata ɗagawa hakan yasa yau laraba yabi jirgin yamma zuwa kano, Aimana tagama gyara ko ina na gidanta sai tashin kamshi yake, wanka tayi ta shirya cikin doguwar rigar yar maroco ta yane kanta da mayafi ta feshe jikinta da kalolin turaruka masu saukin kamshi falo ta dawo ta zauna tana danna wayarta, haka kawai yau takeji kewa dason jin muryar Musty ko ganinsa, tunda ta zauna a wajan kiran layinsa take amma bata shiga, karar buɗe kofa alamun mutum ya shigo baisa ta ɗago ba bare taga wace tasa a ranta ma Rumana ce dan bata daɗe da fita ba, Surayya bata nan tana makaranta,
"Amaryar Abbas bani wayarki na kwada kiran Baby gaba ɗaya wayarsa bata shiga kuma Allah so nake naji miryarsa ke ni ganinsa ma nake son yi" ɗagowar dazatayi sukai ido huɗu da Mustapha, zaro idanuwa tayi tareda buɗe baki zatai ihu yai saurin saka hannunsa saman bakinta alamar tayi shuru, idamunsa cikin nata harya zauna saman kujera
"Kin wahalar dani reina kin kin azabtar da zuciyata Alhamdulillah nagodewa Allah kema yanzu kinji yanda naji"
"Yi hakuri to" hannu yasa ya lakace mata kumatu yana harararta
"Bakiji kewata ba"
"Naji sosai ma"
"Ban yarda ba" yafaɗa yareda ɗaukarta gaba ɗaya suka shiga ɗaki.

Sumayya tunda taje Katsina tana gidan babanta wanda tun tuni yasake aure ya auri matarsa Ramatu mace mai kirki da son mutane, kusan ko yaushe tana ɗaki a kwance cin abinci ke fitowa da ita daga ɗakin, yau tun safe take shirin tahowa kano ta haɗa komai nata jira take ayi a azahar taje tasha ta hau mota, gaba ɗaya batada kuɗi tana son tambayar Mustapha kuɗi tana tsoro batason ya zargi wani abu daban daga danginta, App ɗinta na opay ta shiga ta duba taga sauran nawa take da shi in bazasu isheta zuwa gida ba ta kira Murja ta roketa ta tura mata kuɗin mota, murza idanunta tayi ta rufe su ta buɗe tasake rufewa ta buɗe kuɗindai suna nan kamar yanda ta gani kasa ta duba taga waya mata transfer mai kauri irin haka,
"Mustapha Kamal Sarina" tafaɗa a fili, rungume wayar tayi hawaye na zubowa daga idanunta, tarufe idanun tana cigaba da kuka kasa kasa, kiran daya shigo wayarta yasa ta goge hawayen fuskarta tai picking call ɗin
"Ina kwana"
"Lafiya kalau Sumy ya kike ya katsinan, ga kuɗi nan na turo maki ki dawo gida da wuri yau zan dawo kinsan wajanki zan sauka bana son na rigaki shiga gida"
"Insha Allah" tafaɗa murya a raunane, bai jira abinda zatace ba ya katse kiran, ɗakin babanta taje ta masa sallama yabata dubu goma aciki tayi kuɗin mota zuwa gida, falonta ba wani kura sosai ba kamar ɗakunan ta ba da sukai kura da alama Aimanah na kula da falon, jakarta kawai ta ajje ko wanka batayi ba ta shiga kicin, komai akwai a kicin ɗin sosai, turus tayi taja ta tsaya bayan ta gama duba komai, hawaye suka zubo mata na takaicin duk waɗan nan abubuwan bata iya komai ba banda dahuwar farar shinkafa da mai da yaji bata iya komai ba, batajin ma ita nan rayuwarta ta taɓa haɗa miya da kanta, komawa tayi ɗakinta ta kira wayar Murjana, Murja dake tsaye a ɗaki tana kallon Amarya dake waya tana kashe murya taga kiran yayarta ta ɗaga da murmishi
"Anty kin dawo?"
"Nadawo ƴar uwa zo dan Allah"
"Ok gani nan shigowa" Sumayya ta koma ta zauna saman kujera tana jin kamar ta haura saman Aimanah su gaisa kamar kuma kartaje, haka ta zauna har sanda Murja tazo, Sumayya hannunta taja zuwa kichin suka tsaya Murja na karewa kicin ɗin kallo,
"Sumayya kalli kicin ɗin nan dan Allah gaba ɗaya a hargitse kamar ba mace ke amfani da shi ba, ke komai naki ba tsabta shiyasa kuke faɗa da Mama"
"Murja ba wannan bama yau Musty zai dawo so nake na masa girki na rasa maizan dafa nifa inba shinkafa fara ba sai indomie su kawai na iya dafawa" dariya Murja tayi kana ta ce
"Cab ina zan tsaya ban iya girki ba, kema Allah Sumayya sake kikayi kika biyewa son jiki irin naki bakya komai, dai dai da sharan ɗaki sai mama tayita fama dake kana zakiyi"
"Duk zan daina son jikin nan yanzu dai kwadamin yanda zan yi jar miya saina dafa faran shinkafa"
"Shinkafa kuma mijin naki zai dawo zaki masa wani shinkafa kamar a kauye"
"To Murja mai zanyi ni ban iya komai ba" Sumayya tafaɗi haka tana ɗora tukunya saman gas, Murja ta buɗe firij ta ɗakko naman sa ta wanke kana ta soma yankawa, Sumayya na kallonta harta gama yankawa ta sake wankewa ta ɗora a tukunya ta zuba albasa da kayan kamshi komawa tayi ta sake ɗebo kayan miya a frezar ta wanke su ta markaɗa a blanda, ita ta haɗa miyan, lasar miyan tayi a bakinta da sauri ra fito daga kicin ɗin ta faɗa toilet ɗin dake falon tafara kwarara amai, gaba ɗaya hankalin Sumayya yatashi ganin yanda Murja ke amai tana kallo ta gama ta wanke fuskarta suka fito
"Sumayya jiya da yau olsa ke wahalar dani wallahi da zaran naci wani abu mai maiko sai amai" Sumayya ta zubawa Murja idanu can kuma ta ɗauke ganinta daga kanta ta mata sannu suka koma kicin ɗin, kayan da suka ɓata Murja ta tattara zata wanke Sumayya ta ɓata rai
"Da kinbarsu sai anjima mu huta"
"Zaki gayyato kudaje kenan kicin ɗinki, ai da zaran kin gama aiki yi wanke wanke ki gyara ko ina shine dai dai" Murja ta kalli agogo taga bakwai saura na yamma maza Sumayya jekiyi wanka ki gyara jikinki Yayanmu jirgin shida na yamma yake biyowa kar yazo ya ganki haka ba wanka"
"Kai Murja kefa daɗina dake kamar wata kwaɗuwa haka kike da wanka ɗazu fa na yi wankan da zan tawo kano" Murja rike baki tayi
"Cab zauna nan to kar kiyi wankan ki fesa turare kyaji wasu sunayi ai"
"Zan canza kaya fa innayi alwala" Murja barin wanke wanken da take tayi taja hannun Sumayya zuwa ɗakinta ta turata bathroom
"Kinsan Allah Sumayya sai kinyi wankan nan"
"To sani nayi dole uwata" Murja bata kulata ba ta fice daga ɗakin.

Aimanah tun safiyar juma'a data tashi tayi sallar asuba bata koma barci ba, aiki tayi sosai a gidan itada Rumana zaman kujerun falon ma saida suka gyara haka labulaye suka saka wasu kana suka shiga kicin samosa sukayi da metpie da lemun abarba suka saka a firij wanka sukayi da la'asar suka fita, karan farko kenan da Aimanah ta fito daga gidan tun randa aka kaita, wajan saloon sukaje aka gyarawa Aimana gashinta aka mata jan lalle tayi kyau sosai sai gafda mangariba suka koma gida Aimanah wanka ta sake ta shiga kicin tana kokarin ɗora tukuya Rumana ta katseta da
"Yaya naga kamar fa Sumy tadawo"
"Data dawo sai akayi yaya sai akace karna farantawa mijina"
"Ni bance ba amma nayi tunanin wajanta zai sauka"
"Koya sauka wajanta koya sauka nan banda damuw akai abinda kawai na sani shine sai yaci abinci anan wallahi" tafaɗa tana haci
"Lafafa min yayarmu"
"Kece da abin haushi Rumana har kinsamin damuwa ma, nama fasa yin fride rice ɗin" ta kashe gas ɗin ta dawo falo ta zauna, wayar Shaheed ta kira yana ɗagawa ta ce
"Shaheed zo" bata jira amsar saba ta katse kiran, mintina kaɗan ya shiga gaba ɗaya abinda suka soya ta ɗakko ta mike masa
"Shaheed ungo rabawa almajirai" ya kalleta ya kalli abinda take mika masa ya ce
"Na rabawa almajirai kuma"
"E! haka nace ko bazakayi ba" tafaɗa a tsawace Shaheed ya mike zai fita Rumana dake kallonsu ta ce
"Yah Shaheed na Yayanmu ne fa kawai daga nace mata yaya wajan Anty Sumy zai sauka shikenan tahau masifa da fushi" zama ya koma yayi yana kallon Aimanah sai kuma ya ɗauki babban flask ɗin ya koma da shi kicin harya juya zai fito sai kuma ya ɗauki meatpie ɗaya yafito yana ci Aimana hararansa tayi
"Wayace kaci abin mijina" dariya Rumana da Shaheed sukayi a lokaci ɗaya
"Kefa Yaya Aimana rigima ce dake sai kace karamar yarinya kodan gado ba karambani ba na tini ke ɗin ƴar Anty Hasana ce" dariya sukayi gaba ɗaya sai kuma aka ware aka fara hira har zuwa sanda aka fara kiraye kirayan sallar insha Shaheed da Rumana tare suka fita zuwa gidan Ammi ita kuma Aimanah ta shiga ɗaki zatayi sallah, Shaheed da Rumana na tafe a hanya Shaheed yace
"Gaskiyya meatpie ɗin nan yayi daɗi waima maiyasa na ɗauki daya kawai"
"Yai daɗi sosai danma bakaci samosa ba" Shaheed tsayawa yayi
"Rumana kodai mu koma to" dariya Rumana tayi harda sunkuyawa
"Kaje man ka haɗu da Yaya ai yau kam zanso ace ina gidan nan Yayanmu zai dawo nasan akwai dirama"
"Yaya Aimana da yayanmu na matukar burgeni har jinake inama akwai sauran wata macan kara dana kama"
"Kajira na haifa maka"
"Cab Allah ya kyauta badani za'ayi wannan abin kunyar ba tayita tacemin uncle kamar a school" dariya sosai Rumana tayi, suna gafda shiga cikin gida ta kofar baya suka hangi shugowar motar yaya Ahmad ta get na gidan Musty
"Boss yadawo" Shaheed yafaɗa yana dariya ko mu juya ne, juyawan kuwa sukayi wajan motar Shaheed ya buɗewa Musty murfin motar yafito, ɗan risinawa Shaheed yayi alamar girmamawa ya ce
"Barka da zuwa yayanmu"
"Autan Ammi barka dai" Musty ya faɗa yana sha kan Shaheed
"Yayanmu barka da hanya"
"Yawwa barka dai Amaryar Abbas" rufe fuska Rumana tayi tareda kwasa da gudu tabar wajan, Shaheed ne ya ɗebi ledojin dake zube a bayan motan mai ɗauke da tambarin wani babban kanti dake nan kano ya shiga da su cikin falon Sumayya, yana fitowa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login