Showing 51001 words to 54000 words out of 72176 words
Chapter 18 - KAREN BANA complete by ammey laylerh .txt
 yawa bace kawai tsabar rakine irin nata.
Cikin tamke fuska dan karma taga damarsa ya qaraso gareta, cirota yayi daga kwancen da take kan nata ya ɗora saman cinyarsa, sai kuma yashiga share mata hawayen dake fita daga cikin idaniyarta, "me ya sa!' me yasa samm samm baki duba irin condition ɗin da kike ciki AYUSHHH" me yasa kikes0n wasa da hankali na aduk loƙacin da kike cikin daru da rigimarki Ni kuma kike jefani cikin tashin hankali? Uyummmm kodan kawai kinga na damu dake sosae har haka?" Dan Allah ki daina ki daina hakan pls na roqeqi AYSHA".
Ya haɗe hannayensa biyu alamun roqo.
"Baxan sakeba baxan kuma tada ma da hankalin naka ba ya MALEEKkkk kayi haƙuri na daina, amma sai inhar kace min bazaka na kulata ba" ta faɗi hakan cikin sakalci da shogoɓar daya qara zame mata jiki.
Tunda shine yake qara daure mata gindin hakan, tunda kuma tasami wannan cikin rigimar taci uban tada.
"Nayi! Nayi alqawarin AYUSH, bana qarawa kuma bana qara kulatan dama cen, ba kulatan nake ba ai! Kene baki da wayo shi yasa take amfani da rashin wayon naki take s0n kawo mana nakasu cikin rayuwan aurenmu!" Na gane na fashimta hakan YAA YAA NAA"
CIKIN tsantsar zallar soyayyar da yake mata ya miƙe da ita tsaye tare da soma tafiya da ita, xuwa bedroom nashi Cikin toilet ɗin sa ya wuce da ita****
Wanka yayo mata mai rai da lafiya, kana ya shiryata cikin riga da wando pallazo inda ɗan tudun cikin nata ya bayyana kaɗan, daga nan kuma kitchen suka nufa. haɗaɗɗan  sandwich suka haɗa, da lafiyayyan kunun gyaɗar daya zamewa maleek tamkar rai da mutuwa, dan so goma duk shigowa saiyasha abunsa.
"Kai yasin kunun markaɗaɗɗiyar gyaɗa duniya ne, wanda baisan shiba ko baisha hhhhhhhh daɗi ya barshi ya kuma barrrr🫰🏻🫰🏻uyummmm ba magana dai kammm kawai"
Haka suka fito ɗauke da kayan kwalaminsu a tsakar parlourn suka bajeee haja dan basa da buƙatar hawa dining table, haka dai suka shashanta wannan yinin nasu cikin sakalcin da shi kuma yake biye mata.
Daga qarshe ma zuwa yamma cannn ya ɗauke ta sukayi wajensu ammeynsa, ko acikin motarma hakance ta faru tace ya tsaya yasai mata wancan yasai mata wannan, ahaka dai suka samu suka qarasa, ammey tana  cikin kitchen tana abincin dare  suka ranbaɗa mata sallama, cikin tarin farin ciki take amsasu l0qacin da suka qarasa shigowa  cikin parlourn fitowa tayi daga cikin kitchen ɗin.
Atare shi da ita suka shiga gaidata****
Cikin annashuwar ganinsu cikin farin ciki da kwanciyar hankali take tambayar yaya jikin nata, maleek ne yayi charab ya amshe zancen daba nashi ba, "Ai wllh Ammey samm bata s0n shan magani kinganta Nan, ɗaxuma saida muka gama rigima sanan tasha, kuma bataji sosae don Allah kimata faɗa ammey!"
Tunda ya fara zuba uban wannan jawaban ammeyn da jaddah suka bishi da idanu, kafin daga bisani ita ta sadda kanta qasa tana wasa da yatsun qafarta, 
"To sannu sarkin sara! Faɗi ba'a tambayeka ba kuma, yawasa dakai ko kaine mai jikin?"
Bakinsa ya turo mata gaba tare da ɓallama jaddan harara ganin tana masa gwalo, gwalon ta kuma yi masa hakan yasa shi ɗauki wa fil0n kujerar ammeyn ya jefa mata, tare da mata waning da idanunta, hakan yasa ta ɗan harareshi kaɗan.
Ammey da komai ke faruwa akan id0n tane kuma batare da sunsan tana ankare da su bane yasata, miqewa tsaye tare da bar musu parlourn, ta komawarta kitchen tare da ci gaba da aikinta, qiran sallar magrib ne yasa shi miqewa ita kuma tace da ammeyn tana zuwa bara taje su gaisa da mutan gidan.
Da to ammey ta amsa mata tana daga cikin kitchen, kai tsaye ɓangaren hajiya talatu nera ta fara yi, a zaune ta tadda ita ƙafar Nan ɗaya kan ɗaya sallamar ma da qar aka amsa mata, "Barka da dare momie"
"Wani sabon kilibibin kuma aka qara kwasowa? Wai momie, toni ba momienki bace kin gani kalli cann Ni momien waɗancan ne" ta nuna yaranta dake zaune.
Wani irin murmushin da ita kaɗai tasan ma'anar abinta tayi kana tace mata "kina bani mamaki  dan hakan da tun farkon zuwa na ganewa idanuna abubuwa da yawa!, Tabbas idan har ahaka kika shimfiɗa rayuwar auren acikin wannan gida to tabbas, hasashena da tunani na basu bani qarya ba, tabbas anci da rabonki HAJIYA, an kuma kutsa cikin rashin wayon ki! Da rashin iya adana wayonki agunda yadace, tabbas anyi miki tura yaro rami anyi amfani da damarki an dama abubuwan da Allah ne kaɗai yasan iyakar abunda aka dama ɗin MOMIE;"
"Na barki lafiya 🙏amma tabbas  daga yau kika iya tauna halshenki da sanin kalaman dake fita daga cikin bakin ki,
Da kuma sanin abinda zaki ka furtawa jama'a bye nayi wajen uwarr" sai kuma ta kanne mata id0 ɗaya tana barin parlourn baki ɗaya.
Baki sake ta fita bar Hajiya talatu nera, dan zata iya rantse wa tunda uwarta ta sunkuya ta haifeta, ba'a taɓa jifanta da kalamai munana irin waɗannan ba, kai koda kwatankwacin hakan ba'a taɓa ba, amma sai gashi yau ƴar cikinta ta faɗa mata maganar data gadama.
Kai tsaye ɓangaren hajiya LUBNA tayi, tana zaune tana latsa wayar dake hannunta qirar iPhone 7, cikin zallar bariki da iya taku ta faɗaɗa fara'ar dake kwance saman fuskarta,  "A ahhhh yau kuma amaryarmu ce agidan barka da xuwa ƴata! Ƙaraso ki zauna tana nuna mata kusa da inda take zaune, cikin tafita sanin mai duniyar take a ciki itama tazo ta zauna ta hakimce akan kujerar data mata nunin.
Tashi tayi tana faɗin " bara na kawo miki abin kwalam danku wani sa'in masu cikin Nan kwaɗayi gareku"
Ta ƙasan ido ta shiga binta da kallon baki da hankali LUBNA " Atafin hannuna kike tarrr nake ganinki"
Ahaka ayadda take ta dawo ta tadda ita****"yauwa gashi lemun kwakwane da sanyinsa ɗaxun nan nahaɗama abbanku dake yana gari yau"
Amsa tayi tana faɗin yawwa mommah Naaaaa shiyasa nake ƙaunarki bani amsa tayi ta ajje a gefe, Nan suka shiga fira, kafin tace mata ita salla zatayi.
Dadduma ta shimfiɗa mata ita kuma tayi bayin dake cikin parlourn dan ɗauro alwula, fitowa tayi tahau kan daddumar tare da tada fara sallar, tana idarwa maleek na shigowa parlourn, cikin murmushin Nan nata kamar koda yaushe ta shiga faɗin "id0n ka kenan my S0N yanxun ganinka sai an ciki form" 
Murmushi kawai yayi tare da shafa sumar kansa yana faɗin "wallahi Mommah abubuwan ne sai ahankali**
"Ga ayyukan da suka tiso miki Ni agaba!"
 
"Ayya sannu my S0N komai zai wuce wata rana sai labari" 
"Mai labarin ma wata Rana babu shi" cewar jaddah take zaune saman dadduma duka su biyun da kallo suka bita kowa da abinda yake saƙawa aransa daban, 
"Oya tashi muje zamu tahi gida" ayya sorry yaya bara na amshi lemuna awurin Mommah" da kallon baki da hankali ya  bita dashi, itama kallon da hankali na tsabb ajikina tayi masa tana amsan jug ɗin sanyin da Mommah tayi saurin ɗauko mata.
Lemunta ta juye domin acikin cup ɗin, dan harga Allah ranta ya biya lemun***
Afusace yaja hannun ta suka bar parlourn, suna barin harabar ɓangaren nata yasaki hannunta yace " ke baki da hankali ga dukkan alamu, to wallahi jikina yasama matsala saikin biyamin abuna;" ya faɗi hakan yana huci "mene yayi zafi saina zo ka kuma yimin wani meye aciki"  ke nine nake faɗa miki Magana kike maida min" 
Hannuntan mai lemun ya kama ya murɗe hakan yasa kofin subcewa ya faɗi lemun ya zube, ganin lemunta malale bisa tyless ɗin tsakar gidan ne yasata fashewa da kuka, ganin shiru babu ita da mai qiranne kuma yasa ammeyn biyo bayansu,turus taja ta tsaya ganin jaddah da maleek tsaye ga kuma jaddahn tana kuka, hakan yasa ta qarasa sowa gaban su cikin qiɗima ta shiga faɗin "meya faru?  Menene? Meye yasameki AYSHA"
"Babu abinda ya sameta sai tsabar bakin ciki, wai matar Nan ce ta bata lemun kwakwa shine ta amshe zata sha!" To meye aciki dan tasha ɗin BABANAAA banason fitina faaaa"
"Ke kuma muje dama nima haɗa miki wani dake nasan yanxun kina s0nshi, shima dana shi na gyaɗar dana masa" 
Kai kawai ta iya ɗagawa ammeyn tana bin bayanta, ko inda maleek yake bata kalla ba haka tabi ammeyn sukayi gaba suka barshi, yana kallon ikon Allah suna zuwa ko zama ammey bata barta tayiba tace mata "ga naki shima yazo ya ɗauki nashi bazan iya muku da wannan shegiyar rigima takuba"
Yana xuwa dama yana daga bakin qofar parlourn hakan yasa ya suri nashi fuuuuuuu ya fice, itama fuuuuuuu tabi bayan nashi "kwadaiji dashi" ammeyn ta faɗa tana shigewarta bedroom nata.
Acen harabar gidan ta tsinceshi hakan yasa tayi sauri ta cimmasa hannunsa ta kamo cikin nata, fusge hannunsa yayi yana ɓalla mata wata uwar harara hakan ne ita kuma yasata saurin ɗauke wa qasa tana riqe cikinta yafara murɗaɗɗawa,cikin hamzari ya duqo xuwa gare ta yana faɗin****
"NOORIE mene yasami cikin mu wuce asbitin, ganin yacce duk ya bi ya tada hankalinsa ne yasata fashewa da wata iriyar dariya, ganin hakanne shima yasa shi sakin murmushi sai kuma kawai ya sureta sai cikin motarsunnn.
Kuyi haƙuri dajina shiru pls Ina mai qara baku haƙuri.
Ayyukane sukamin yawa inawa kowa fatan alkhairi🙏🏻🙏🏻🙏🏻 Na GODE da qaunarku gareni♥️♥️♥️♥️♥️♥️♥️
*🔥♥️ KAREN BANA♥️🔥*
NA MARYAM NASEER MIRRAH ✨
*AMMEY LAYLERH SHALELEN DAZZLING STAR'S*
Page 36&37
08104493215
✯D͟A͟Z͟Z͟L͟I͟N͟G͟ S͟✯T͟✯R͟'✯W͟R͟I͟T͟E͟R͟S͟✯
===≠===≠======≠=====≠====≠==
_____________________
Ganin hakanne shima yasa shi sakin murmushi sai kuma kawai ya sureta sai cikin motarsunnn.
Shima zagayawa yayi shima ya shiga yawa motar key, kafin ya cilla motarsa  kan shimfiɗeɗen titi, haka jaddah taci gaba dawa maleek dariya har bacci yazo yayi awon gaba da ita.
ganin tayi barcine kuma yasa shi sakin wani shegen murmushi irin na gefen bakin Nan, har suka qarasa gida bata farka ba ganin hakan ne kuma yasa maleek ɗaukar ta, akafaɗarsa tare da nufar  parlourn su kai tsaye da ita, bedroom nashi ya wuce da ita ya kwantar da ita akan bed, kayan jikinta ya samu ya  rage mata.
Shi kuma ya faɗa  toilet ruwa masu ɗumi da ƙamshi ya haɗama kansa, acikin ƙaton  bathtube wani irin lumshe idanunsa yayi tare da budewa yana shaƙar daddaɗan ƙamshim turaren wankan  kuma ɗumin ruwan loqacin daya shige cikin bathtube ɗin.
Akalla ya kusan mintina goma akwance acikin ruwan, kafin ya samu yayi wankan nashi***
Ɗaure da towel ya fito akan west ɗin sa ɗaya hannuwansa kuma wani mini towel ɗin ne, yana tsane gashin kansa da inban daddaɗan ƙamshim na gyaran data Kesha babu abinda take fiddawa,dan kuwa ba qananun kuɗi maleek yake kashema sumar tashi ba:
Haka ya qarasa gaban tanqamemen mirrorn ɗakin  lotions masu daɗin qamshi ya shiga shafe jikinsa dasu, kai tsaye kuma cikin clothes na kayansa ya shige tare da shiryo kansa cikin wasu haɗaɗɗan kayan barci riga armles da dogon wando masu santsi kana ya fito sai zabga uban qamshi yake.
Sai kuma yanufi kan bed tare da kwanciya, bayan ya gama tofesu da adda'oina barci****
Kwanciya yayi agefen jaddah tare da rumgumota jikinsa tare da jan duvet yaja ya rufesu.
*********
 Suna fita Hajiya LUBNA ta saki wani irin shegen munafikin murmushi tare da komawa cikin sofa ta kule, wayan ta ta ɗauka tare da ci gaba da abinda take yi, "MALEEK! MALEEK!! Zans0 ganin ranan dazan ga zubar ruwan hawaye daga cikin idanunka MALEEKkkk"
Sai kuma taci gaba da latsa wayarta. Inda kaikayi da karan bani na suka sa na lekoma masu karatu wani abu daya kusan tashin kaina baki ɗaya!.
         *6 Bosses*
*The leaders of the country and you know* 
Naga tana chart dasui!
"Yanxun haka sune suka shigo kuma suka fita, tabbas matarsa tana ɗauke da cikinsa!"
Hhhhhhhh
Shine abinda Kashim baba ya turo tare da emoji na dariya against,
        *K baba*
 "idan kuwa har haka ne to tabbas zamu ajje duk wani shiri da harin da muke shirin farmakar MALEEK dasu, mun samo hanya ɗaya mafi sauƙi mafi muni kuma ta hanyar tarwatsa RAYUWAR MALEEK ɗin!."yanxun duk wani hari namu yana kan abinda MALEEK zai haifa dole ɗin dole!!"
*Tanbuwal*
    Akwai babban shagali kenan dole mu shirya ma wannan babban shagali tsaraba ta musamman!
              *Atiku*
Har naji kamar mu janwo nesa kusa, dole yayi kukan jini wannan karon, kafin yayi mutuwar na mutu ban mutu ba, mutuwar wulaƙanci tare da tsinuwar al'umma, dan kuwa inajin kabb DUNIYAR Nan nafi kowa tsanar MALEEK, domin shine maqasuɗin abinda ya rabani da kujerata, ya sani tseren tsiran da ban shirya waba! Shege la'antacce"
*Isa hasarara*
              Hhhhhhhhhh lalle tafiya da gwani akwai daɗi hausawa sunyi gaskiya, basuy qarya ba dole wannan karon ya amshi SAKAMAKO mafi munin gani, MAZA bisa kanka ba MATA ba yaro!
  
*Ibrahim NERA* 
 *The worst*
*more dangerous*
*The president*
Hahahaha hahahahaha
Hahhahahaha MALEEK harka bani tausayi yaro! 
"K baba bayan sheƙesu na baka kwangilar auren matarsa!
Idan har Ni na aureta me duniya zata ji za kuma ta gani, dan haka qungiyar mu ta baka AUREN AYSHA MATAR MALEEK,
Zan ga zan ga zan ga wannan ranan Ni na saniiiii, ZANYIIIII party zanyi rawa zanyi yadda nakesooooo0 kuma da ƙasa ta"
"Dama wancen munafikin chief of army ɗin ne yasa ban tsige banza daga kan matsayin saba,  yanxu kuma hhhhhhhhhhhhhh"
***************
                Naji tsoro na kuma firgita da ganin wannan abu, innalillahi wa'innah ilaihir'raji'un, innalillahi wa'innah ilaihir'raji'un, shugabannin mu maka sanmu!.
To miye hakan yake nufi*****
_______________
         ADAMAWA
_________________________
Gaba ɗaya Al'amura sun sako Hajiya LAURA gaba ta kasa gane kan al'amarin, gashi gaba ɗaya mai martaba sarki abdulphata Omar yasa andakatarta da xuwa sashen sa gaba ɗaya, amma dake makirar macece sai take nuna hakan tamkar bai damemeta ba****
Nan kuwa idan da abinda yafi ɗaga mata hankali to wannan abu ne da mai martaba yasa aka mata, MARYAM ABDULJALAAL tayi tayi tayi magiyar taba da haƙurin wajen ganin mai martaba ya janye wannan babban al'amarin atsakankanin uwar gidansa, amma ya nuna mata ɓacin ransa qarara akan Wagga batu.
Hakan yasa take kaima Allah kukanta haɗi da naimawa abokiyar zamanta yafiyarsa da kuma ta mijinta, tsawon watanni huɗun Nan a haka take fama amma kullum maganar ɗaya ce ta janye tun kafin ya hmmmm, ba'a dai magana kawai.
        Su Malam Abdullahi kuwa suna Nan cikin garin Adamawa, inda mai martaba ya bashi wani qaton gidansa, tare da aiki yin dake dama malam Abdullahi yayi karatu, sammm baisamu mastala da hakan ba, haka suke zaune kusan kullum sukan ziyarci wadannan bayin Allah, domin dangin su ma ba'a barsu haka ba kowa da irin tarin alkhairukan da aka masa.
Hakan yasanya wasunsu kuka, da LADAMAR Rayuwa.
Lallai Malam ba haushe yayi gaskiya dayace  da yace****
Lokutta da dama akan yiwa wasu kall0n wulaƙantattu daga baya suzam abin misali a rayuwa* tabbas haka yake, dan sun ɗauki kyakkywan darasin rayuwa akan kansu ma ba sai anje ko ina ba.
Rayuwa tama su ummey da malam Abdullahi daɗi dan kuwa harta ɗalibansa almajiransa ya dawo dasu Nan Adamawa, inda babu wani ɗalibin dayake Bara kamar da sun tashi daga matsayin Disciples  sun koma  free people kamar kowa.
Adda'oi kuwa wannan bayin Allah suna shanta,  tuni Malam Abdullahi Rano da almajiransa suka bazu sunansu yayi popular, Inda aka maida malam Abdullahi limamin babban masallacin Adamawa, dama limamin ya rasu babu jimawa.
***********
Haka rayuwar su MALEEK taci gaba da waka na cikin aminci da kuma kwanciyar hankali,inda suke baiwa junansu wata iriyar kulawa da  SOYAYYAR da take wahalar samu a yanxun, sai wurin ɗaidaiku, S0 da ƙauna suke nunawa junansu zalla, inda ɓangare guda suka cigaba da bama cikinsu kulawa ta musamman, yanxun haka jaddah tayi nauyi ɗan cikin ta yana wata na tara haihuwa Yau ko gobe***
Hakan yasa Ammey ta dawo da ita gabanta tunda haihuwar farice, aykuwa maleek na yace baisan zance ba haka shima ya dawo gidansun da zama, suka tarema ammey agida,badan ma albarkacin aiki ba dasu ammey sun ga boni, abu kaɗan yace kodai haihuwar ne mutafi asbiti, sannu kuwa bata yanke wa motsi kaɗan sannu da sannu tana yawa to data fara akan jaddah****
JUMA'AT
Babbar rana tunda jaddah ta tashi takejin maranta na mata wani irin ciwo, amma ta daure gudun kada ta tadawa su ammeyn hankali kuma taje ba haihuwar bane, tunda ta jima tana jin irin hakan a tattare da ita shi yasa take daurewa.
*******
           Misalin ƙarfe huɗu da rabi na yammacin ranan tana zaune, tana tsincewa ammey Ayar da zata mata kunun Ayar da tacema Ammeyn shi kawai takes0****
Duba da yana yin nata bayan ta gama tsince Ayar tass ta miƙa zata kaima ammey ayarne kuma, taji zuuuuuuu wani abu mai kama da ruwa nabin ƙafarta, hakan yasa tayi saurin komawa birnin ta zaune, tare da kwalla ƙiran ammeyn.
Kasancewar tasan  halin yanayin ta yau ɗin ta tashi, acine yasa ta rugowa a guje, ashe duk ɓoye ɓoyen da take ammeyn tana sane da ita, ganin bata nuna mata bane yasa itama ta tafi ahakan, tasan dai dole idan me gaba ɗayar tazo tofa dole ta nemeta.
Tana zuwa gurinta tace "AYUSHA  ko haihuwar ce" cikin qarfin hali da girgiza mata kai haɗi da faɗin "a ahhhhh ammey kawai dai marana ce naji tana sukana, ina miƙewa kuma naji wani abu nabin ƙafafuna".
"Haihuwar ce mu tafi asibiti kawaiiiiii" mu bari ajima koda zuwa dare ne Ammey"
Ganin kuma ba wani abu bane yasa ammeyn dakatawa kaɗan, ganin kuma ta ware harma tayi sallar magrib lafiya ne yasa ammeyn sakin ranta, wajajen isha'i tace ma da ammeyn tana s0n balangu amma na siyasar wa, haka ammey ta bada aka siyo mata balangun aka kawo mata shi a baƙar leda.
Soma cin balangun nata kenan, wani irin azababben ciwon mara ya turnineƙa a furgice ta soma ambaton sunayen Allah, nan danan kuwa ammey ta ida rikicewa. Ana haka sai ga maleek ya dawo a wurin aiki, tamkar kuma wacce dama shigowar nasa ake jira Nan take ta soma  wani irin murɗaɗawa tare da kukan azaba,tun tana ambaton sunayen









