Showing 1 words to 3000 words out of 55707 words

Chapter 1 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt

31 May 2024

8039

🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨




Gargaɗi❌❌❌
Ban yarda a sauyamin littafi ta wani fanni ba tare da izinina ba ko kuma a copy wani ɓangare na littafina ba.


1️⃣----2️⃣


KADUNA


Zaune suke ɗaliban shiru a aji kasancewar malamin Maths ne kuma gashi mugu, hakan yasa ɗaliban maida hankulansu gaba ɗaya gun allon,calculations yake yana bayani amma babu mai ganewa, yana kai karshe yace "Do you all understand" ɗaliban sukace "yes" saboda tsoransa da sukeyi.
Uncle Musa yace"Good, now let me give class work ".
Nanfa ɗaliban suka ruɗe,Uncle Musa ya rubuta calculations guda biyu a board, sannan yace su fara.
Kwasam saiga wata yarinya wacca bata wuce shekara 15 a duniya tashigo da gudu tana haki, saboda gudun da tasha, kawai ɗaliban sukeyi Uncle Musa yace," Stop there!!!", cike da tsawa, haka yarinya ta tsaya jikinta na ɓari, kafafunta suna rawa.


Uncle Musa yace" why are you late in my class". Cikin rawar murya yarinyar tace"I'm sorry Sir". Kawai sai tafashe da kuka, suko ɗalibai daɗi suke taji, harda dariya ƙasa ƙasa kar malamin yaji su,Uncle Musa yace "kneel down and give me your hand, next time you won't there come late to my class".


Haka yarinyar ta miƙa hannunta tana kuka, yako zaneta babu sassauci, tashi tayi daga kneel down ɗin ta wuce seat ɗinta wanda yake gaba ta zauna, kuma yace saita yi class work ɗin.
Baiwar ALLAH haka ta ciro littafinta tafara rubutu,cikin wasu mintuna sai gata tagama class work ɗin taje yin submitting, cike da mamaki Uncle Musa ya bita da kallo, ɗaliban ma sai haushinta sukeyi saboda tafisu nacin karatu da hazaƙa, haka ɗaliban suka kasance har lokacin tashi break yayi suka fita.


Bayan sun fita suna wasa naji ance Sa'eeda, ashe yarinyar nan ce wacca Uncle Musa ya duka a aji ce, waiwayowa tayi tana kalonta tare da cewa "Maryam ya akayi ne" wacca aka Kira da Maryam ta ce "Sa'eeda meyasa kikayi latti, bayan kinsa yau Uncle Musa muke dashi" cike da damuwa Sa'eeda tace"Hmmmm Umma kande ce ta aikeni kuma wurin da nisa, shiyasa nayi latti" Maryam tana kallonta da mamaki ta ce"Amma tasan zaki makaranta ai, shi ne ta aikeki alhalin tanada mayyan Yara 'yan mata ", murmushi mai ciwo Sa'eeda tayi sannan tace" Bakomai ai lokacine, watarana sai labari ".


Haka suka cigaba da hiransu har aka koma aji, darussa aka cigaba dayi har 2:00pm tayi aka tashi gida.

@@@@@@@@@


Anatse suke tafiya ita da Maryam suna hiransu, har kowa yabi hanyar gidansu. Tana shanyo kwanar gidansu gabanta yafara dukan uku uku saboda tasan aikin gida na jiranta,hakan ta isa har zauran gidansu tana ɗauke da sallama, amma babu amsa duk da akwai mutane agidan, shiga tayi ɗakin mahaifiyarta tare da sallama, cike da so da ƙaunar ƴarta ta tilo ta amsa tana fara'a, gaisheta tayi sannan ta ajiye jakarta.


Zama tayi tana" Washhhhhh ALLAH na", Ummanta dake linke wankin kayan mutanen da tayi ta ce"ALLAH yasa dai ba'a miki dukan latti ba" marairaice fuska tayi kamar zatayi kuka sannan ta ce"ALLAH Umma saida Uncle Musa ya dukeni hada sani kneel down"cike da tausayin ƴarta ta ta ce"Karki damu ƴar albarkha watarana sai labari kinji, ki cigaba da haƙuri, in shaa ALLAH baza mu dawwama ahaka ba, Ubangiji zai taimake mu".


Sa'eeda tace "Umma bara nayi sallah sai inje inyi aikina" da kallo tabi ƴarta dashi tana tausayin halinda suke ciki.


Tuno kyara da tsangwamar da suke fuskanta ita da ƴarta wurin kishiyarta da mijinta yasa ta zubar da hawaye. Fitowar Sa'eeda daga ɗaki keda wuya taji Umma Kande na kwalla mata kira har da ɗura mata ashariya da ce wa "Ubanwa kika ajiye da zai miki aikin gidan! " a daburce Sa'eeda tace"Uhm... Uhmm sallah dama nakeso nayi sai nafito aikin ".


Tsaki mai karfi taja tana ce wa" Aikin banza, Ke ga ustaziya koh, maza kiyi sallar nabaki minti 10 kizo kiyi aikin ". A tsorace tace" To".


Haka taje tayi sallah Ummanta na kallonta cike da tausayi ko abinci bataci ba, taje ta gama aikin kafin ta dawo ɗakinsu tashi abinci.


@@@@@@@@@@


Wurin karfe 4:00pm na yamma tashirya zuwa islamiya wacca take bayan layinsu, tana tafiya tana karatunta cikin murya mai zaqi ga ƙira'ah mai daɗin gaske,har ta isa makarantar.


Faslul Imam Shafi'i naga ta shiga wato ajin ƴan sauka,zama tayi a bencin farko, duk da akwai ɗalibai amma basuda yawa, saboda yanxu ake shigowa, jakarta ta bude tafito da Hadisi tana dubawa,ahaka aka cika ajin har malaminsu yashigo tare da sallama, duka ɗaliban suka amsa , sannan ya zauna yana fuskantar ƴan aji.


Malam Yusuf yace "Alhamdulillah tunda kun sauke har sau biyar, kuma wasunku ma sun kammala haddar alqur'ani mai girma, toh don haka time table na jarabawan sauka zai fito gobe, kushirya sosai, sannan zamu fara Karatuttukan sauka cikin satin nan".
Farin ciki ne ya mamaye ƴan ajin banda Sa'eeda wacca tasan basuda halin biyan kuɗin saukar duk da tafi kowa hazaƙa a ajin gaba daya.
Malam Yusuf ya katse musu surutu da cewa"Sannan kufada wa iyayenka maganar kuɗin sauka akan anyanke naira dubu ashirin ga kowani ɗalibi (#25,000) ".
Haka ya bar ajin, su kuma sai murna sukeyi banda Sa'eeda wacca ko ƙawa bata da ita a ajin sede a boko, haka suka fara maraji'ah har lokacin tashi yayi aka tashe su, suna fitowa Sa'eeda tanufi office ɗin shugaban makarantarsu, don ita gaskiya ta fasa saukar don Ummanta batada halin biyan kudin saukar, gashi mahaifinta yana dashi babu laifi yana noma amma bazai biya mata ba, koda ma yayi niyyar biya, kishiyar Ummanta zata hana saboda taga yaranta basa karatu sai talla,da wannan zancen zucin tashiga office ɗin shugaban makarantar da sallama.
Malam Harun ya amsa cikeda fara'ah yace"Sa'eeda kace haka ". Tana murmushi ta ce" Eh malam, daman nazo ne wurinka".
Sai ya ce "To to inajinki Sa'eeda". Sai data lunfasa kafin ta ce "Malam dama game da maganar saukan mune, shi ne nazo incema ko za'a iya cireni daga cikin ƴan saukan saboda a gaskiya iyayena basu da halin biyamin kuɗin sauka, shi ne nace ko za'a cireni sai wani lokacin".
Shiru yayi yana kallonta tare da yin nazari, don gaskiya yasan basuda halin biya hasalima a scholarship Sa'eeda ta ke tun daga aji daya har zuwa aji shida saboda hazaƙar ta,haƙiƙa bai dace ya dakatar da Sa'eeda ba kodan ƙoƙarinta da natsuwarta.
Kawai ya ce "Sa'eeda ", cikin taushin murya ya ƙara da cewa" Naji bayananki, kuma na fahimta, in shaa ALLAH hukumar makaranta zata duba don baza muji daɗi ace mai hazaƙar aji batayi sauka ba saboda rashin kuɗin sauka ba, ki kwanatar da hankalinki in shaa ALLAH, ALLAH zai rufa asiri".
Haka sukayi sallama cike da farin ciki tawuce gida.


@@@@@@@@@


Isarta gida keda wuya aka fara Kiran sallah, jakarta ta ajiye taje alwala sannan tayi sallah, sai taci abincin dare kana ta dauko assignment ɗinta na makaranta tayi, sai tayi karatun littattafanta na boko da islamiya, sannan ta sanar ma Ummanta yanda sukayi batun sauka da shuganban makarantar su, cike da farin ciki ta ke jin ƴarta na mata bayanin yanda sukayi da shuganban makarantarsu.
Sa'eeda na kammala bayininta sai mahaifiyarta ta ce"ALLAH kaine abin Godiya, ka ƙara rufa mana asiri duniya da lahira". Ameen Sa'eeda ta bita dashi.
Washa gari ta tashi da wuri kasancewar tasan aiyukanta na gida, ta somayi don tsoron yin latti a zaneta, haka ta kammala tayi shirinta tsaf, sannan ta karya kumallo,ɗaukar jakarta tayi tafito tsakar gida tana shirin wucewa taji an ƙwalla mata kira, a tsorace ta waiwayo sannan ta amsa saboda jin wacca tai mata Kiran, "Ke dan uwarki zo nan".
Kanta aƙasa ta nufo inda take, kafin ta ƙaraso wurin taji an hankaɗeta, ji kayi timmmmm aƙasa gashi gidan nasu ko siminti babu, haka uniform ɗinta yayi buju buju da shi,a raunane ta ɗago idanunta cike da ƙwalla tana kallon budurwar wacce ta riƙe ƙugu tana girgiza kai alamun masifa.
Sa'eeda da ƙyar ta iya miƙewa tana dubanta ta ce "Haba Nusaiba, mai na miki kika tureni alhalin akwai filin da zaki iya wucewa ba tare da kin tabani ba" tana magana hawaye na zuba a idanunta, itako wacca aka kira da Nusaiba mai zatayi inba shekewa da wata bazawarar dariya ba tana tafiya left and righg tana girgiza jiki kamar wata karuwa.
Buɗan bakin Nusaiba ta ce "Hmmmm Sa'eeda kenan, to ke a tunaninki zan bi wata hanyar don ina jin tsoranki, to wallahi kinyi kaɗan, ke bama keba hatta wannan Uwartaki bata isa ba, eheh! Irin wai ita Allazi bokon nan, ana dai yawan tazubar ne kawai aka ɓige da boko!!!".
Duk wannan abinda yake faruwa a idanun ƴan gida banda mahaifiyar Sa'eeda da take ɗaki tana jinsu, saidai tayi murmushi da girgiza kai alamar ALLAH ya kyauta.
Sa'eeda ba mai hayaniya bace, haƙuri ta bata ta wuce wurin Umma kande,a ƙasƙance ta ke duban Sa'eeda, ta ce "Jeki wurin Maman Dije Kice nace tabani saƙon", da, "To" tabita dashi ta wuce don tasan idan tayi musumma ɓata lokacinta zatayi gashi gidan Maman Dije akwai ɗan nisa kaɗan.
Haka ta wuce tana sassarfa taje ta amso saƙon ta kawo mata ba tare da ta shiga ɗakinsu ba ta wuce school.


@@@@@@@@@@


A class kuwa, principal na gani ya shigo Jss3, ashe ajinsu Sa'eeda ne, a tare ƴan aji suka miƙe suna gaisheshi, ya amsa musu cike da kulawa kana ya ce cikin harshen turanci "Dan gane da Junior waec ɗinku, kowanne a cikinku zai biya #2500 sannan za'a zana exams ɗin 3rd na watan da zai shigo, don haka kowa ya maida hankalinsa sosai a karatu banda wasa". Principal ya ɗau tsawan lokaci yana jawabi kana ya fita daga ajin.
Ɗalibai sai murna sukeyi sun kusa zama seniors, haka darussa sukaita wakana har lokacin tashi yayi suka wuce gida .
BRIGHT STARS INTERNATIONAL SCHOOL shi ne sunan makarantar su Sa'eeda, makaranta ce mai kyau da tsari, ga koyarwa sosai,babbace sosai don tana da field ɗin football da handball duk aciki, tana ɗaya daga cikin makarantun da ake ji dasu a garin.
Kasancewa Sa'eeda ƴar talakawa ce kuma a cikin wannan makaranta yasamo asali ne a dalilin wani malamin primary dinsu wato Uncle Saleem wanda yake koyarwa a matsayin corper a government school ɗinsu, ganin Sa'eeda da ƙoƙari yayi cuku cuku har ALLAH ya ƙaddara tasamu scholarship a makarantar,wannan kenan.


@@@@@@@@@@@@


Bayan dawowarta makaranta ta sanar ma Ummanta batun Junior waec.
"lallai akwai karatu gabanki Sa'eeda, ga shima islamiya kun kusa fara exams" cewar Umma.
Murmushi Sa'eeda tayi tana fadin"Ai Umma yanxu zan fara karatu in shaa ALLAH ".
Umma ta murmusa da faɗin" ALLAH ya miki Albarkha, ya cigaba da tsare gabanki da bayani, yasa ku fara a sa'a ku gama a sa'a"
"Allah humma Aameen Ummina".
Haka dai Sa'eeda ta cigaba da zuwa islamiya da boko, ga kuma karatun da tasa gaba tanayi, ba kama hannun yaro, a wannan week ɗin time table ɗin exams ɗinsu na boko da islamiya ya fito, aka fara shirye shiryen exams.
Alhamdulillah sun gama exams ɗin islamiya sannan sukayi na boko wanda ya ɗaukesu har tsawan wata daya.

@@@@@@@@@@@@@@


KEBBI


"Mum, don ALLAH ki roƙamin Abba ya janye tafiyana UK karatu,duka abokaina Federal University, Birnin KEBBI sukayi applying , amma ace ni sai ƙasar waje"
A shagwabe yake magana kamar zaiyi kuka.
Mum tace " Haba Sadam, sai kace yaro, bayan kasan ƙa'idar gidannan, duka ƴan uwanka acan Oxford University sukayi, sai akanka kake so a canja tsari, haƙuri kawai zakayi katafi, kar Dad ɗinka ya ɓatama rai ba ruwana"
Kamar zaiyi kuka yace, "shikenan Mum", murmishi mum tayi sannan tace, "Yawwa Autana, kaga tafiyarka jibi ne sai ka fara shirye shirye ko", " Toh Allah ya kaimu" kawai Sadam ya iya cewa.................................


Comment and share🙏Fisabilillah
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044: https://whatsapp.com/channel/0029VaRTjCw8vd1HiLjaNK2y 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️



Narrnarhh Bukar✍️


🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨




Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:Narrnarhh002


3️⃣----4️⃣


Tashi yayi ya wuce ɗakinsa, "Maa shaa ALLAH ", kawai na iya furtawa ganin haɗadɗan ɗaki, dan ko amarya sai haka, in fact ko amaryan ma sai wacca ta cika amarya,ɗaki ne mai kyau da tsari, gashi babu wani tarkace dayawa,paint ɗin ɗakin fari ne tas, bed ɗin ma fari ne haɗe da ratsin gold,acan ta gefe kuma akwai sofa da centre table mai kyau, gaskiya ɗakin ya kai ƙarshan haɗuwa.
Wanka yayi kana ya fito, a gurguje ya shirye saboda jin an kusa tada sallah, ash color jallabiya yasa mai taushi haɗe da sheƙi, sannan ya daddala kalolin turaruka masu ƙamshi da tsada sannan ya fito,wayarsa da take a aljihu ya ciro jin tana vibrating, ya kalla naɗan wasu seconds sannan yayi picking.
A can naji murya wani yana faɗin"Hello Sadam, yane kana gida ne", Sadam ɗan jimmm kaɗan yayi kafin ya ce"Eh, yanxu zan shiga masallaci",acan naji ance "OK, gani nan zuwa, in shaa ALLAH ", da OK da bishi dashi kana ya katse wayan.


@@@@@@@@@@@


Massallaci ya nufa don sallar Asr, bayan an kammala ya dawo cikin gida da yake a cikin gidan massallacin yake,kafin ya shiga ciki naga ya tsaya, ganin mai gadi ya buɗe tanƙameman gate, wata rantsatstsan motar ta danno cikin gidan, kana ta nufa inda ake parking tayi parking, wani guy ne nagani wanda bai wuce sa'ar Sadam ba ya fito d'an kimanin shekara 20 da haihuwa, Kamal kenan na hannun daman Sadam, abotarsu ba ta yanxu bane, sunyi makaranta tare tun daga primary har secondary saidai abinda kowa yakeson zama a rayuwarsa ya banbanta, Sadam nason ya gaji mahaifinsa kasancewar shi kadai ne ɗa namiji a gidansu wato cikakkyan ɗan kasu shiyasa yake son karantar Business Administration a Oxford University, UK.
Sa'annan Kamal nason zamowa ɗan Jarida, shiyasa yake da sha'awan karantar Mass communication.


@@@@@@@@@@@@@@


Rungume juna sukayi sannan suka nufa ciki a tare, hannunsu na sarƙafe dana juna, da sallama suka shiga, Mum dake a falon ta amsa musu tare da faɗin "Kamal kazo yin sallama da ɗan uwan naka ne? Kamal wanda yake a russune ya amsa mata da" Eh Mum ya faɗamin jibi ne tafiyar kuma jirgin safe zai bi ", Mum tashe" Toh maa shaa ALLAH ,Auta ya faɗamin kaima kasami admission", Kamal yace"Eh Mum"
"Toh ALLAH yasa Albarkha, yasa Kugama lafiya", da Ameen suka amsa sannan suka nufi sama ɗakin Sadam .
Nan suka fara hira kamar karsu rabu kasancewar Kamal akwai zuba kamar famfo, sai ƙarfe 8:00pm Kamal ya wuce gida.
Haka dai Sadam yayi shirye shiryen sa, sannan ya ziyarci sister ɗinsa ɗaya wacca ta ke aure a nan KEBBI, tana auran wani ƙusan gwamnati, ita ɗayar sister ɗinshi tana aure a Pakistan da ƴarta mace, sannan washa gari jirginsu ya cilla sararin samaniya sai UK.


@@@@@@@@@@@@@@


KADUNA


Wasa wasa lokacin sauka ya ƙarato, Alhamdulillah Umman Sa'eeda tayi bakin ƙoƙarinta wurin ganin tama Sa'eeda kayan sawa na fitan sauka dai dai gwargwado wanda da adashen kuɗin kayan wankin mutane da ta ke yi ne ALLAH yasa tasamu kwasan farko.
"Abban Sa'eeda don ALLAH ka taimaka koda na pure water ne mu samu tunda kaga ranar asabar ne saukan, gashi yau ne kasuwa ta ke ci",
Duk wannan zancan da Umman Sa'eeda ta ke yi yana jinta a kishingiɗe a ɗan gadonta yaƙi kulata, ta ƙara da faɗin" kayi shiru Abban Sa'eeda "
Buɗar bakinsa ya ce" Toh mekike so nace, nina sata makarantar dazan bada wata gudun mawa na ehhh! , tun farkon karatunta ai nace miki banda halin biyata mata kuɗin makaranta amma ke gaki ƴar iyayi ke don ace ɗiyar tana makaranta kikayi cuku cuku har tafara, kina wahalar da kanki da wankin dauɗar mutane!!!
saida ya lunfasa duk tana jinsa bata ce komai sannan ya ɗora da faɗin"Don haka karki sakemin maganar karatun Sa'eeda kuma wannan kashedi ne na miki, ban hanaki ba ko dako zakiyi don ƴar gold ɗinki tayi karatu bai shafeni ba, ki ƙarata can da gulmarki"
Zunbur ya miƙe ya kakkaɓa babbar rigarsa zai ƙara gaba, Umman Sa'eeda ta tashi da sauri tana dubansa sannan ta ce"Duk naji bayananka, kamar yanda kace karatun Sa'eeda bai shafeka ba,toh in shaa ALLAH daga yau bazaka sake jina na maka batun karatun Sa'eeda ba, wannan alƙawari ne, kuma sai Sa'eeda tazamo fila mai haske wannan gidan wanda yake cike da duhu, in shaa ALLAH "
Taɓe baki yayi kana yace" Wannan ke ta shafa, ni kinga tafiya ta"
da sauri ya ƙara gaba, Sa'eeda da ta ke bakin ƙofa tayi saurin matsawa, ALLAH yasa bai ganta ba,da tasha ranƙwashi, ita wallahi ta rasa mai tayiwa mahaifinta yake kyararta baya sonta, sai dai ƴan ɗakin Umma Kande wanda basuda aiki sai tsagwaran talla titi titi da garage garage din motoci, duk sun sha bleaching, har da sa'arta Iklima tafara bleaching da taɗi a zauransu.
Duk fa wannan zancan acikin zuci Sa'eeda ta ke yi,zumbur kamar wacca aka tsikara ta dawo hayyacinta ta shige d'akin.


@@@@@@@@@@@@@@


"Ummina mai ya sameki kike kuka, kinaso in fara kukane, Abbana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login