Showing 3001 words to 6000 words out of 55707 words
Chapter 2 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
ne koh, toh kiyi haƙuri wataran sai labari,banason zubar hawayanki Ummina"
tana maganar muryarta na rawa saboda zuciyarta na mata suya akan maganganun da mahaifinta ya faɗama Ummanta kamar bashi ya haife ta ba.
Hawaye suka fara sulalowa bisa kuncinta, ganin haka Ummanta tsagaita kukanta tana dubanta, don a rayuwarta ta tsana jin kukan ƴarta ta,haka ta tallafo kuncinta tana dubanta da murmushi ta ce " Haba sayyin idaniya na, bansanki da saurin karaya ba, da juriya da jarumta nasanki, don haka bar kukan nan, sha re tsadaddun hawayanki kinji, abar kaunata"
da wannan kalaman Sa'eeda ta tsagaita da kukanta ta ɗago sannan ta kalli Ummanta tace "Toh kema ki daina kukan kinji Ummina"
Cike da shagwaba ta ke maganar har taso ba Ummanta dariya, tace "Toh nabari tawan", a tare suka murmusa,sannan suka cigaba da sabgar su.
@@@@@@@@@@@@@@
Umma Kande ce da ƴaƴanta mata uku da namiji ɗaya wanda ya kasance babba a gidan ɗan kimanin shekara 25,suna zaune a ɗaki suna ƴar hirarsu cike da annashuwa har da shewa.
Nusaiba wacca ta ke bima Musa tace" Wai ni ya waccan Allazi bokon da mamanta suka ƙare da babane, ya basu gudun muwan ne, naji biki bamu chapter munsha ba"
Umma Kande ta sheƙe da wata bazawarar dariya har da buga cinya,"Yo kema kinsan maganar gizo bata wuce na koɗi,zan bari babanku ya bama wannan mai kama da mayun tallafi ne, haba ina bade ni jikan sarkin ruwa ba sai dai wata"
Sai suka ƙara sheƙewa da dariya sannan da ɗora ta faɗin"Ai kusha kurumunku, in har kunga kuɗi sun fita daga aljihun Babanku saidai ku za'a ma hidimar, don wlh ko zanyi yawo tsirara sai naga ƙarshen wa'incan mayun"
Alamar jinjina naga ƴaƴan suna mata tare da wasata kamar ƙaura. Haka suka cigaba da hirarsu har aka kira sallah amma babu wanda a cikinsu ya iya miƙewa don yin sallar(Wa iyazubillah🤔🤔🤔) .
@@@@@@@@@@@@@@
Yaune ranar sauka, fili ne nagani babba wanda yake cike da kanopils, ƙananun kujeru da na alfarma, filin ya cika maƙil da mutane har babu masaka tsinke, a bangare guda ƴan sauka nagani ajere suna shigowa filin don fara karatu, haka suka kammala karatun cikin tsari da burgewa.
Manyan baƙi tun daga kan wakilin sarki da na hakimi,ƴan siyasa da masu hannu da shuni duk sun hallarta . Alhamdulillah haka karatuttuka sukaita wakana da wa'azuzzuka da dai sauransu har aka fara shirin bada kyaututtuka ga wa'inda suka cancanta.
Mc mai magana ya fara da faɗin "Toh yanxu yanxu bada jimawa ba zamu fara bada kyaututtuka ga ɗaliban da suka cancanta sannan sukayi zarra"
Kowa a filin ya natsu don sauraron zakarun shekaran, Umman Sa'eeda na hango can a zaune tasa wata atampa roba taji jiki sosai, sai murmushi ta ke ganin yau ƴarta tilo ta kammala haddan Al Qur'ani mai girma cikin nasara da aminci duk da tasamu ƙalubale a baya sannan yanxu ma dai bata gama fuskan ƙalubalan ba hasalima wasan yanxu aka soma(wasa farin girki).
Mc ne ya fara da ce wa " Wacca tafi kowa hak'uri da natsuwa itace Sa'eeda Sulaiman", haka ta taso tana murmushi tazo filin inda za'a bata kyautar wanda wakilin mai girma sarki zai bada, haka akai ta bada kyatuttuka wanda kusan Sa'eeda tai ta tasamu.
Daga ƙarshe Mc ya fara wasa gwarzon/gwarzuwan shekaran, nan da nan fili da rincaɓe da hayaniya don jin zakara/zakariyan shekaran, Mc yace"Gwarzo ko gwarzuwan shekaran nan shi ne ko ita ce", sannan ya tsagaita, mutune sai tsuma suke da ƙosawa don jin overall best student, Mc ya ƙara da faɗin "ita ce Sa'eeda Sulaiman", filin ya ɗauka da kabbara"Allahu Akhbar!!!
haka taje ta amsa kyautarta had'e zunzurutun kuɗi har #100,000,wanda kyauta ne daga wakilin sarki abama wanda yayi Zarra.
@@@@@@@@@@@@@@@
Haka suka dawo gida ita da Sa'eeda da maƙotan da suke mutunci dasu, wa'inda kwata kwata ba sufi mata uku ba, don Umma kande woman leader ɗin unguwan ne . Daidai gwargwado Sa'eeda da gudanar da walimar saukanta wanda ƴan walimar basuda yawa daga Maryam aminiyarta ta boko sai wasu sa'oninta ƴan layi.
Bayan sallar Isha'i, Sa'eeda ta dubi Ummanta tace"Ummina ya za'ayi da wannan kuɗin da nasamu ", Umma Sa'eeda tace" Zan buɗe account asa kuɗin gobe in shaa ALLAH don tun yanzu zan fara tarin kuɗin karatunki na jami'ah, tunda nasan bazan samu daga Abbanki ba kuma Koda na fara sana'a ba karɓuwa zatayi ba, saboda Kande, ko ya kike gani ke"
Sa'eeda saida ta lunfasa sannan tace"Toh ummina duk yanda kika tsara banda jayayya, ALLAH yayi mana jagora ", da" Aameen ", umminta tabita dashi, sai sukeyi shirin bacci don garin ya soma yin shiru.
@@@@@@@@@@@@@@@
Haka dai rayuwa ta cigaba da tafiya yau da daɗi gobe babu daɗi, a bangaren Sa'eeda sai a hankali, hutun boko ya ƙare sun koma makaranta ka'in da na'in babu kama hannun yaro.
Ta shiga SS1 Art class saboda tun tana ƙarama ta ke da sha'awan kasuwanci kuma Ummanta tanason haka, shiyasa ta ke son karantar Business Administration,saboda fannin kasuwancine, haka ta fara SS1 cikin nasara da aminci.
Sa'eeda karatu ta ke ba dare ba rana tunda yanzu ba islamiya ta ke zuwa ba sai dai tilawan Al Qur'ani mai girma da litattafai,karatu yayi nisa sun fara shirin exams na kammala SS1 zuwa SS2.........................
Comments and share 🙏🙏🙏fisabilillah.
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044: 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:Narrnarhh002
5️⃣----6️⃣
Karatu yayi nisa sun fara shirin exams na kammala SS1 zuwa SS2. Sa'eeda ta shiryawa exams ɗin tsaf kuma takan koyawa Maryam inda bata fahimta ba kasancewar Maryam slow learner ce, duk da mahaifin Maryam ya kawo ma Maryam lesson teacher wanda zai dinga koyar da ita, hakan baisa ta cimma Sa'eeda Koda da taku ɗaya a karatu ba, a gaskiya hakan nama Maryam ciwo a zuci, gata ƴar masu kuɗi,ƴar gata gurin iyayenta amma ace ƴar talakawa tafita komai, ga kyau, ga ilimi, ga natsuwa, ga, ga, haba abin yayi yawa.
Duk wannan zancen a zuci ta ke yinsa,bayan Sa'eeda ta kammala koya mata wasu calculations a Economics kasancewar su ƴan Art students ne,itama tanada burin zamowa ƴar kasuwa daga jin Sa'eeda sanda suka kammala exams din ƙarshe tana faɗin ita Art class zata shiga saboda tanason harkar kasuwanci carab ta ce itama shi zata karanta saboda yanda taji Sa'eeda na kururuta course ɗin Business Administration, don haka tana zuwa gida ta sanar ma Mom ɗinta, da farko taso yin jayayya don ita tafi son ƴarta ta karanci bangaran likitanci(saikace tanada kwakwalwar ne😂😂😂),don ace ƴarta ta tanada ilimi amma jin ta ce ita Business Administration zata karanta kuma Dad ɗinta ya goya mata baya yasa ta haƙura.
Mafi ƙololuwan ɓacin ranta shi ne ashe saboda Sa'eeda zata karanci Business Administration yasa itama tace zatayi, amma babu yadda ta iya tunda mijinta ya bada go ahead. Cikin ikon Ubangiji su Sa'eeda sun kammala exams ɗinsu,makaranta ta basu hutun wata ɗaya da kwana huɗu saboda gab da azumi suka kammala exams kuma a ƙa'idan makarantar basa karatu cikin azumi shiyasa su ka yi hutu.
@@@@@@@@@@@@@
"Ummina anga wata, anga wata, yiriri!!! ", Sa'eeda da murnarta ta ke sanar ma Ummanta, dayake kusa dasu akwai masallaci wanda ladanin masallacin ne yayi shelar ganin watan, Umma dake zaune kusa da ƙofar ɗakinta tana shan iska tace " ALLAH ya sadar damu albarkarsa, ya kuma amsa mana addu'oin mun gaba daya," da "Ameen ", Sa'eeda ta faɗa wacca ke cike da zumuɗin ganin wata, don tun tana ƴar shekara 12 ta dena shan azumi, complete ta ke yi wanda har mamaki Ummanta ta ke yi ganin ko Nusaiba da ta ke budurwa da ƙyar ta ke yin azumi 15 Duk da tana shan na haila wanda wajibine ga duk wacca ta balaga saidai mai ciki, ko mai jinin biƙi, ko mara lafiya,wacca ta ke bi mata ma Zaliha itama duk kwanwar ja ce, balle Ilkima wacca ta ke sa'ar ƴarta sa'eeda.
"Yawwa Idi shigo da kayan ciki" Nusaiba ce ke bama wani almajiri wanda yake karatu a wata makarantar Allo dake kusa da gidansu, kwalin indomie ne da kret ɗin Kwai, carton ɗin madarar peak, Bournvita, da dai sauransu. Sai wani ɗadɗaga kai ta ke ita ga saurayi mai kud'i ya kawo mata Ramadan basket.
Umma Kande da futowarta kenan daga bayi ta cillara uban guda haɗe da faɗin"Arziki kashi, yau gashi ƴata ta tako mana ", harda wani rungume da murna.
Nusaiba dai sai murmushi ta ke kawai, don ita kadai tasan yadda ta samu ramadan basket ɗin, abinda Umma Kande bata sani ba shi ne, Nusaiba ta daɗe da zubar da mutincinta awaje, hasalima tun tana ƴar kimanin shekara 17 ta fara zubar da mutincinta,a lokacin Umma Kande na saida gyaɗa da aya soyayya, haka zata ɗora mata tallar tare da mata gargaɗin ta tabbatar ta saida sannan ta dawo gida, Umma Kande irin matan nan ne masu son abin duniya, da wannan gardaɗi da Umma Kande ta ke ma Nusaiba a kullum yasa ta fara bin maza, har daga ƙarshe ta zama gwana bata wannan hotel ɗin bata wancan, tanayi ne duk don faranta ran mahaifiyarta.
Yanxu ma wani sugar daddy ne ALLAH ya haɗata dashi, yana kashe mata kuɗi sosai kuma a lokaci guda yana amfanuwa da albarkatun jikinta.
**Ƴan Uwana iyaye mata, a rage son abin duniya da dogon buri, bakida gashin wance ba lallai sai kinyi kitson wanca ba, haƙiƙa iyaye mata wani lokacin mukan tafka kuskuran da a ƙarshe zamuyi dana sani mara amfani,ba dole saikin tsawatarwa ƴarki akan lallai saita saida ta kawo miki kuɗi ba, duk abinda ALLAH ya ƙaddara takawo miki sai ki godewa masa,ki roƙeshi yasa Albarkha,amma tirsasa yara musamman ƴaƴa mata akan sai an saida talla na ɗaya daga cikin abinda ke fara sasu bin maza wanda a ƙarshe siyo abin kunya,Allah ya tsare mana imani**
Sa'eeda dai da Ummanta kallon ikon ALLAH su ke yi kawai, don duk habaicin da Umma Kande takeyi da Umma Sa'eeda ne, amma ko ihhmmm batace mata ba hasalima da taga abun nasu ba gaɓa, ta ce ma Sa'eeda su wuce ɗaki, haka suka tattara tabarmarsu suka shige ciki abinsu.
Haka suka fara azumi abinsu, kuma ba laifi suna yinsa ciki kwanciyar hankali.
@@@@@@@@@@@@@
Azumi dai wasa wasa yasoma yin bankwana, don yanxu in sunkai sunkai na 25,har an soma shirye shiryen sallah, masu ƴaƴa tuni an siyawa yara kayan sallah, wasu ma har kala shida shida, kamar yanda hakan ta faru a gidansu Sa'eeda.
Abban Sa'eeda yama Nusaiba,Zaliha da Iklima ɗinkin sallah har kala biyu biyu,sannan kowacce da takalmi bancin wanda suka samu daga samarinsu , haka Umma Kande tafito da kaya niƙi niƙi waje daman saida ta fakaici Umman Sa'eeda na waje sannan tafito da kayan, da gayya take fito da kayan ɗaya bayan ɗaya tana faɗin "Kai! Kai!! kai!!!, daɗi kasheni, wannan gata haka, ƴaƴa masu ƙashin arziki bancin wanda babanku yayi kala biyu biyu har da wanda mazajenku sukayi(wai fa mazajenku😂😂😂su Umma Kande badai ilimi da sanin ya kamata ba).
Tana wannan surutan ne duk don ta ƙunsa ma Umman Sa'eeda baƙin ciki saboda tasan ba'ama Sa'eeda kayan sallah ba hasalima ita ta hanashi yayi mata, dan tsoranta yake sosai dalilin mugun asirin da take mishi akai akai tare da rufe bakin danginsa akan ƴar dukiyarsa wanda daga ita sai yaranta sukeci. Ko ƙala Umman Sa'eeda batace mata ba, saidai murmushi kawai tayi da girgiza kai,ita ba baƙuwar zafi bace hakan da Abbansu Sa'eeda yayi bai dameta don tasan watarana sai labari.Haka dai Umma Kande tagama iyayinta da kayan ta koma ɗaki.
@@@@@@@@@@@@@
KEBBI
"Oyoyo oyoyo mutan India, ashe dai da gaske kuke zakuzo sallah", Mum ce mai faɗin haka tana rungumar wata ƴar kyakkyawar yarinya mai kimanin shekara 3 a duniya da murmushi ita kuma yarinyar sai ciccijewa ta ke ita ala dole mai ƙyuya duk da sukanyi video call da ita hakan bai hanata nuna halin nata ba (ƙyuya) .
Wata kyakkyawar mata nagani ƴar wanka, fara tas kamar balarabiya ta ƙarasowa cikin falon tana samun guri kusa da Mum da faɗin "Washhhhh wallahi duk nagaji", cire veil ɗinta tayi wanda yayi daidai da kalan jallabiyarta marun,mai adon stones haɗe da veil ɗin, sannan ta russuna ta gaida Mum.
"Mum mun sameku lafiya? ", Mum da ta ke fama da Fanan ta amsa mata cike da kulawa tana faɗin "lafiya lau , ya mijin naki, ya aiki ", da "Duk lafiya lau" ta amsa mata
kai da Mum taga Fanan taƙi zama wurinta ta saketa da faɗin "Ja'irar yarinya zakizo hannu na ne" da gudu da haye saman cinyar mamata tana dariya sai duk suka fashe da dariya.
Mum tace " Sameera zoki ɗauki kayan Sadiya da tazo dasu kiwuce mata dashi ɗakinta", haka wata mai kimanin shekara 46 ta fito zuwa wurin Sadiya ta gaishe ta,Mum ce ta bada umarnin a dafa ma Fanan noodles taci.
@@@@@@@@@@@@@
Bayan sunyi wanka itada ƴarta a lokacin ankusa kiran sallar magrib dayake saukan yamma su ka yi, masallacin gidansu sukaji an kira sallah, sai suka fara haraman shan ruwa, sannan suka gabatar da sallah.
Bayan isha'i Sadiya ta wuce ɗakin Mum don yin hirar yaushe gamo,da sallama ta shiga, ganin Mum na lazimi yasata zaunawa a sofa tare da ɗaukar Fanan bisa cinya.
Sanda Mum ta kammala lazuminta har sarauniyar ƴan ƙyuya tayi bacci,Mum ce ta dawo itama kan sofar bayan ta cire mayafin sallarta,ƙara gaisawa sukayi sannan aka shiga hirar ƴa da uwa anan ne take sannar ma Sadiya dramar da tasha kafin Sadam ya yarda zuwa UK karatu.
Dariya Sadiya ta saki tana cewa "Mum ai duk ke kika sangartashi, in yana tare dake ji kike kamar ki komar dashi ciki, ba dole yaƙi yarda ba duk da most friends ɗinshi a nan KEBBI University suka samu admissions hakan bazai mai daɗi ba"
"Amma yasan qa'idar gidan ai, ke da Sakinah acan UK kukayi Karatunku", dariya Sadiya ta sukeyi tana fad'in "Auta ne fa", tsaki da ja Mum sannan tace " wallahi ranar Auta ya ɓatamin rai, da ƙyar na shawo kansa ya yarda da tafiyan" hamma Sadiya tayi tana faɗin "yanxu dai su Auta ana can ana boko, duk da nasan Auta da ƙoƙari Saidai sangarta in yana gabanki", Mum tace " Naji ina ruwanki imma yayi sangartar", wannan karon dariya Sadiya takeyi har da riƙe ciki "Ni!!! na'isa shiga tsakaninku", Mum tace "kyadai ji dashi", sallama sukayi don har 10:25pm yayi ta ɗauki Fanan suka nufi ɗakinta wanda tun tana budurwa ta ke ciki, ta shimfiɗar da Fanan sannan tabi lafiyar gado.
Washi gari kuwa har gidan ƴar uwarta Sakinah saida taje, nanma sukayi hira sannan ta dawo gida.
@@@@@@@@@@@@@
Yaudai ake sa ran ganin wata, Alhamdulillah da ƙarfe 11:45pm na dare Sarkin musulmi ya sanar da ganin wata,kowa sai murna yake, da addu'ar ALLAH ya karɓa ibadun da a kayi a watan.
Bayan an fito Idi Aunty Sakinarh da familinta suka iso gidan Mum, kasancewar mijinta tafiyar gaggawa ta samesa zuwa Germany. Maa shaa Allah🥰 Tabarakallah kawai na iya furtawa ganin wata hamshaƙiyar mata wacca baza tawuce shekara 28 a duniya ba, tasha peach colour lace da ratsin gold wanda ko makaho ya taba yasan lace ɗin na ɗaruruwan kuɗine, ga gwala gwalai ya cika mata wuya kasancewar ta ƴar duma duma, bayan awarwaraye da zobba a hannunta, ta yafa yalwataccan gyale mai adon stones da takalmi tu match, ga twins ɗinta Maa shaa Allah🥰 Tabarakallah, suma sun sha kyau.
Haka dai wannan family suka sha shagulgulan sallah, sai bayan sallah da sati ɗaya Sadiya ta koma India cike da kewar ƴar uwarta da mum ɗinta.
Bayan tafiyarta da kwana biyu Daddyn Sadam ya dawo Nigeria da yake yayi tafiya zuwa China akan wani harkar kasuwancinsa bayan ya gama ne ya wuce Saudia aikin Umra.
@@@@@@@@@@@@@
KADUNA
Bagaren su Sa'eeda sunyi shagalin sallah dai dai malisa, kaza ɗaya Umma Sa'eeda ta siyo musu suka yanka, suka soya suka ci, ita kuma Hajiya Umma Kande kaji ɗai ɗai har goma suka yanka haɗe da ginsamin naman shanu da Abbansu Sa'eeda yakawo taƙi rabawa taba Umman Sa'eeda, haka su Zaliha da iklima sukai ta suya tsabaragyan rashin mutinci a ƙofar ɗakin su Sa'eeda suka sa kaskon tuyar(Kai jama'a in kana duniyar nan kasha kallo😂😇), so suke Umman Sa'eeda ta tanka amma taƙi hasalima jawo ƙofarta tayi kasancewar akwai wutar nepa sai suka kunna fanka abinsu, duk wannan soye soyan da ake Nusaiba bata gida, tadai cema mamanta zataje tasha amsar saƙo wanda bata sanar da ita wani kala ne saƙon ba tun safe ta fita.
Ashe ashe Nusaiba tama sugar daddynta Alhaji Sagir alƙawarin goron sallah ne, yace su haɗu a hotel, saida tafito daga layinsu ta tari ɗan keke napep a lokacin tasa niƙaf da yake duk sanda zata hotel yin harka da niƙaf ta ke zuwa, tana isa hotel ɗin ta kira number sa, sai ya sanar da ita number ɗakin, sai da ta cire niƙaf ɗin sannan ta wuce direct ɗakin, isarta keda wuya ta ƙwanƙwasa, kamar jira Alhaji Sagir yake ya buɗe mata ta shige,ce mata yayi ta zauna yana son suyi wata muhimmiyar magana, ba musu ta zauna tana wani lanƙwasa da lashen lebe irin na tsoffin karuwan nan, (sai Kace mayya😀, Fans ai ita ta cancanta da zamowa mayyar ba Sa'eeda