Showing 24001 words to 27000 words out of 55707 words
Chapter 9 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
sanda yaran nasu suke gida ba,don yanzu basa samun ko sisi a hannun yaran nasu wa'inda suka aurar hasalima tunda a kayi auran nasu babu wacca ta leƙo gidan da sunnan gaishesu,kuma idan suka tuntuɓi mai yasa sai dai suce mazajensu sun hanasu zuwa,abu fa kamar haɗin baki.
Kamar kullum Sa'eeda da Ummanta sun fito daga ɗaki zasu wuce sai ga Abbansu Sa'eeda ya shigo gidan da sallama, amsawa su ka yi,sai ya dubi Sa'eeda fuskarsa ɗauke da murmushi ya ce
"Sai ina Kuma Sa'eeda "
Banbaraƙwai Sa'eeda taji maganar tazo mata sai ta ce
"Abba makaranta zani"
"To ina unifoam ɗinki,a haka zaki makarantar ne,ko kinaso a miki duka ne"
"A'a Abba,yanxu ba nasa unifoam ai"
"Bangane ba,makarantar kuma yanzu bakya mata unifoam idan zaki,kodai unifoam ɗinki ya lalace ne,sai ki siya wani? "
" A'a Abba,ai yanzu ba'a secondary school nake ba"
"To kina ina ne yanzu"
"Abba ai na shiga university ina karantar Business Administration a Kasu"
"Au haba!,yaushe kika fara zuwa makarantar,ai bansani ba"
"200 level nake ma yanzu ai saura shekara biyu na gama"
"To to,maa shaa Allah,ki maida hankali sosai a karatunki kinji Sa'eeda"
"To Abba in shaa Allah"
"Yawwa ƴar albarka"
Hannu yakai aljihunsa ya ciro kuɗi ƴan dubu dubu da yawa wanda ni kaina mai ɗaukar rahoton bansan nawa bane ya miƙa mata sannan ya ce
"Ki ƙara kuɗin mota,tunda makarantar da nisa"
Har ƙasa ta ɗurƙusa hannu bibbiyu ta amsa kuɗi haɗe da yi masa godiya da adduar buɗi agaresa,Sosai ya amsa mata cike da kulawa.
Haka suka fito ita da Ummanta cike da ɗunbin mamakin sauyawansa lokaci guda.
Tun daga fara maganar Abbansu Sa'eeda da Sa'eeda Umma Kande dake da niyyar fitowa don tayi alwalar sallar subh duk taji kuma a gaban idonta Abbansu Sa'eeda ya fito da maƙudan kuɗi ya miƙa ma Sa'eeda.
Tashin hankali wanda ba'a sa mai rana ai a rikice ta shiga ɗakin Maman Jummalo ko sallama babu ta banko ƙofar ɗakin ta shiga,Maman Jummalo dake bacci cikin kwanciyar hankali tayi saurin buɗe ido jin an banko mata ɗaki babu sallama balle izinin shiga.
"Lafiya Ƙawas? "
"Ina fa lafiya Maman Jummalo, shi ke nan,tawa ta ƙare! "
"Bangane ba ƙawas,fahimtar dani,kin barni a duhu"
"Aikin gama ya gama ƙawas,yau da idona naga Babansu Nusaiba na miƙa ma Sa'eeda kuɗi masu uban yawa harda sa mata albarka wai ta maida hankalinta akan karatunta"
"Kuɗi!!! Kuɗi!!! Kuɗi fa kika ce,anya kin gani da kyau kuwa? "
" Wallahi tallahi,billahillazi Kinga har da salati nayi ko, to nagansu da idona Maman Jummalo! Nace miki nagansu! Ke kwarankwatsa tannatsa! Na gansu da idona kuma ni ganau ce ba jiyau ba,har da tambayarta makarantarta haɗe da samata albarka,yihuhuuuuu ni Serere jikar sarkin ruwa na mutu! Na mutu ho ho hooooo! "
"Kwantar da hankalinki duk wannan kururuwan da kike bashi bane bafita Ƙawas"
"To ne kike so inyi bayan hankalin Babandu Nusaiba ys fara karka garesu,ai wallahi kashina ya bushe"
"Haba don Allah nace ki kwantar da hankalinki,zamu samu mafita akan wannan lamarin,ke bari kiji akwai mafita amma mafita ɗaya ce garemu yanzu "
"Akwai mafita kika ce MamanMaryam
lo,to mecece mafitar? "
"Ba wata mafita bace illa...................
Sai mun haɗu a pages na gaba in shaa Allah🙃🙃🙃
****ya kuke ganin soyayyar Sauban da Sa'eeda, shin zai kaisu har aure ko ko wata ƙaddara zata gitta???
****Shin wace mafita ce Maman Jummalo ta ce akwai??
***Mai yasa ƴaransu Umma Kande da Maman Jummalo kamar haɗin baki babu wacca tazo ganin gida???,Mai hakan yake nufe??? Mai yasa mazajansu suka hanasu zuwa ganin gida?? sannan yaya zamansu da mazajansu yake???
Duk ku biyoni zuwa next pages domin samun amsoshinku✍️✍️✍️🙃🙃🙃🙃🙃🙃💝💝💝💝💝🌹🌹🌹🌹
Ku cigaba da zubo ruwan coments da reactions My Esteem Fans ni kuma zan cigaba da suburbuɗo muku updates wanda zaku nishaɗantu tare da ilmantuwa🌹🌹🌹💝💝💝🏵️🏵️🏵️🏵️😁😁😁🙃🙃🙃
Ina matuƙar alfahari daku my Esteem Fans🤗🤗🤗🏵️🏵️🏵️🏵️🙃🙃🙃
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044:
🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Masu telegram zaku iya following ɗina acan🤗🌹👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
🌹🌹🌹I'm not born to be a writer but born to be a great professional writer✍️✍️✍️🙃🙃🙃🌹🌹🌹
🤗🤗🤗Special greetings to y'll my Esteem fans,i love y'll💝💝💝💝🤗🤗🤗
2⃣1⃣----2⃣2⃣
"Kwantar da hankalinki duk wannan kururuwan da kike bashi bane bafita Ƙawas"
"To mai kike so inyi bayan hankalin Babansu Nusaiba ya fara karka garesu, wallahi nasan kashina ya bushe idan na bari hankalinsa ya koma kansu"
"Haba don Allah nace ki kwantar da hankalinki ko,zamu samu mafita akan wannan lamarin,ke bari ma kiji akwai mafita amma mafitar ɗaya ce garemu yanzu "
"Akwai mafita kika ce Maman Jummalo,to mecece mafitar? "
"Ba wata mafita bace illa mu shiya ranar lahadi muje wurin boka Sankeru,ita kadai ce mafitar tamu kinga sai ya duba yaga ko asirin ne ya warware"
"Haka ne kuma,kin kawo shawara mai kyau amma anya zan iya bari har lahadi Ƙawas,lahadi tayimin nisa ji nake kamar yanzu na ganni gaban boka Sankeru,ko hankalina zai kwanta"
"Haba Saratu,kin cika gaggawa a al'amuranki wallahi ina nan ina ranar lahadi,kin manta yau alhamis baifi saura kwana biyu ba amma duk kin bi kin tada hankalinki a banza,haba don Allah"
"Allah ya kaimu ɗin"
A haka Maman Jummalo ta cigaba da kwantar ma Umma Kande hankali har ta natsu,sai daga baya ta wuce ɗakinta ,sallar subh ma da ta ce zatayi tafasa sai bayan ta dawo daga wurin boka Sankeru zata cigaba da sallah.(Ohhhh niii!!! Duniya ina zaki damu🤔🤔🤔,wannan wani irin jahilci ne haka,kai! Kai!! Kai!!!,to Allah ya kyauta🤔🤔🤔).
Haka duk wunin ranar jikinta a sanyaye yake,abinci ma sai da Maman Jummalo ta lallabata sannan ta samu taci shima kaɗan,duk tayi sukuku da ita kamar mai ciwo ko kuma ance wani shaƙiƙinta ya rasu haka take ji a jikinta.
@@@@@@
Bayan su Sa'eeda sun fito waje sai ta dubi Ummanta tace
"Ummina kinga ikon Allah ko"
"Haka ne sanyin idaniyata,tabbas wannan ikon Allah ne ba na mutum ba,amma a gaskiya nayi mamakin sauyawan Abbanki lokaci guda haka"
"Nima haka Ummina,Allah shi ne abin godiya"
"Haka ne kuwa Allah shi ne abin godiya, don ba yin mu bane,nufin Allah ne"
"Hakane Ummina,kinga kuɗin nan da ya bani saina ƙara kuɗin mota sannan zanyi sadakar naira dubu ɗaya wa almajirai ko ya kika ce Ummina"
"Wannan haka yake,Allah dai ya cigaba da maido da hankalinsa gare mu"
"Aameen Aameen Ummina"
Haka suka cigaba da hira har kowa ya nufi hanyarsa.
@@@@@@@@
Cigarta aji keda wuya saiga Maryam itama ta shigo,murmushi Sa'eeda ta sakarma Maryam sai itama ta maido mata da ɗan murmushi wanda bai kai zuciya ba, babu yabo babu fallasa a fuskar Maryam ta gaida Sa'eeda don yanzu Maryam ta fara jan baya baya da Sa'eeda dalilin samun ƙawaye ƴan gayu masu ji da kuɗi tare da class da tayi.
Yanzu ko karatun da Sa'eeda ta ke koyama Maryam ta daina saboda yanxu Maryam bata ce mata ta koya mata karatu,kusan yanzu Maryam hankalinta yafi karkata ga ƙawaye da gayu,sun haɗe kai su biyar wanda har suka sama group ɗinsu suna da (high classic babes squad).Duk yaran masu kuɗi ne sosai,asha wanka iya wanka sannan a ratayo fashion bags ana yanga amma brain ɗin empty😁😁😁.
Akwai lokacin da Sa'eeda ta taɓa samun Maryam da magana akan ko ta mata laifi ne yanzu take jan baya baya da ita,sannan yanzu kuma bata son suna tafiya gida tare,babu komai Maryam ta iya ce ma Sa'eeda kawai yanzu bata da ra'ayin tafiya gida tare da ita ne,shi kenan Sa'eeda ta ce da Maryam ta wuce abinta,tun daga ranar bata sake yiwa Maryam magana ko kuma ta ce su tafi gida tare ba, saidai idan ta ganta tayi mata murmushi sai ita ma Maryam ɗin ta maida mata.
Karatunsu ya fara zafi yanzu kuma suna gab da fara first semester exams ɗin na 200L,gashi Vice Chancellor ya ce continous semeter zasuyi babu hutu,shi yasa lecturers suke zafafa musu da karatu babu ji babu gani saboda lecterers ɗin suna so su kammala lectures ɗinsu complete kafin a fara exams.Wannan kenan.
A haka a haka har lokacin exams ɗinsu yayi suka rubuta exams dinsu cikin nasara da aminci musamman Sa'eeda da take karatu babu kama hannu yaro.
Suna kammala exams ranar Friday suka fara karatun second semester 200 level ranar Monday duk da ba duka ɗaliban suka zo ba kasancewar basu daɗe da kammala exams ba amma lecterers suka ɗaura sabon babi a karatun nasu.
@@@@@@@@@@@@
Ɓangaren Sa'eeda da Sauban baza muce komai ba don suna soyayya sosai,Sa'eeda har ji take anya zata iya auran wani inba Sauban ba,zata iya zama ta rayu da wani wanda ba Sauban, a kullun wutar soyayyar Sauban a cikin zuciyar Sa'eeda ƙare ruruwa take.Sauban yana nuna mata tafi kowacce mace daraja a idonsa kuma ita kaɗai ce a cikin zuciyarsa.
Sauban yanzu ya gama gane Sa'eeda ta mutu a so da ƙaunarsa sosai,don wani lokaci idan bai kirata a waya ba ita take kiransa taji lafiya kuwa,hakan na mugun yima Sauban daɗi a rai don yanzu haƙarshi ta cimma ruwa.
Wanene Sauban?
****Sauban Muhammad Ja'afar Ƙaraye shi ne asalin cikakkyan sunansa,wanda shi ne ɗa na uku a familinsu,su biyar ne mahaifiyarsu ta haiha,yana da ƙanne biyu mata tare da yayyi biyu duk maza,mahaifinsu asalin ɗan ƙauyen ƙaraye ne a jihar Kano,ita kuma mahaifiyarsu ƴar Zaria ce a jihar Kaduna.
Muhammad Ja'afar Ƙaraye cikakkyan ɗan kasuwa ne amma baiyi karatun boko ba kasancewar a ƙauye ya taso,a lokacin da yake ɗan 20 ya fara zuwa ci rani a kaduna,yana saro kaya a Kano ya kawosu Kaduna ya saida har Allah ya mai jagora a kasuwancin nasa ya zamo mai kuɗi sosai,a Kaduna ne yaga mahaifiyarsu Sauban lokacin tazo ita da yayarta mace kasuwar bacci siyayya wanda a lokacin sunzo biki tufun wada ne, a nan ya ganta har Allah ya ƙaddara ya aureta.
Allah ya azurtasu da ƴaƴa har biyar,da yake mahaifinsu Sauban yanada sha'awar karatun boko kasancewar shi baiyi karatun boko ba sai dai karatun Allo yasa ya bada himma da ƙwazon ganin yaransa sun tashi cikin karatun boko da na islamiya.
Babu laifa daga mazan har matan sun samu karatu daidai gwargwado duk da matan su biyu da yayyinsa maza ma duk sunyi aure shi kaɗai ne ya rage baiyi ba.Mahaifiyar Sauban ita kaɗai ce a wurin mahaifinsu Sauban.Allah yama mahaifinsu Sauban rasuwa a shekarar da ta gabata wato shekara ɗaya ke nan.Wannan shi ne taƙaitaccan tarihin Sauban Muhammad Ja'afar Ƙaraye.****
@ @@@@@@
Ɓangarensu Umma Kande kamar yadda Maman Jummalo ta bada shawarar suje ranar lahadi haka ko akayi,da sassafe suka buga sammako zuwa wurin boka Sankeru.
Isarsu keda wuya suka ga mata dayawa na layi a wurin bukkar boka Sankeru,mamaki da al'ajab ya cikasu har da riƙe baki,lallai boka Sankeru ya fara shahar sduba da yadda suka bugo sammako har sun tarar da layi ba kamar da ba da zaku shige direct.
Haka suka jira har layi yazo kansu,Umma Kande ce ta shiga kasancewar ita Mamam Jummalo rakiya tayo,tana shiga kamar yadda suka saba ta mishi kirayi tare da ƙasƙantar da kanta garesa(Wa'iyazubillah,Allah kasa mufi ƙarfin zukatanmu baki ɗaya😞😞😞).
Bayyanarsa keda wuya ya tintsire da wata mahaukaciyar dariya yana bubbuga ƙafa tare da nunata da yatsa yana ƙara tintsirar dariyarsa.Ita dai Umma Kande kanta a ƙasa.(ummm su Umma Kande masu ladabin ɗan tsako😂😂😂🙃).
Saida yayi mai isarsa kana ya tsagaita yana dubanta tare da cewa
"Yanzu tafi ƙarfinki Umma Kande!!! Tafi ƙarfinki!!! Saidai kiyi haƙuri"
A razane Umma Kande ta ɗago kanta tare datakai dubanta ga boka Sankeru sai kuma ta fashewa da kuka tana roƙo da magiya akan ya taimaketa kar asirinta ya tonu saboda tasan mijinta yafi son Umman Sa'eeda akanta bayan haka danginsa da batason su raɓesa yanzu zasu dinga zuminci sosai daga ƙarshe zasu maidata saniyar ware ita da ƴaƴanta,haka taita roƙonsa tana kuka sao kace wata yarinya.
"Naji! Naji!! Najiiiii !!! "
Sai kuma yayi shiru na tsawan wasu mintuna,Umma Kande har ta zaci bazai sake magana ba,sai kuma taji ya fara magana cikin amon muryar nan nasa mai sauti tare da firgitarwa.
"Akwai sharaɗi mai girma Umma Kande!!! Sharaɗi babba Umma Kande!!! Sharaɗin shi ne,zamu baki kwalba wanda ruhinsa ke aciki,sannan karki sake!!! Karki kibari!!! Karki yarda !!! A hir ɗinki !!! Kibari kwalbar nan ta fashe!!! Idan kuma ba haka ba....................
Pages ɗin yau babu yawa kasancewar banda caji a wayana,in shaa Allah pages na gaba zai kasance🔥🔥🔥
Ku cigaba da kasance da alkalamin Narrnarhh Bukar✍️✍️✍️ zaku nishaɗantu tare da ilmantuwa harda ma wa'azantuwa In shaa Allah🤗🤗🤗🙃🙃🙃💝💝💝💝
***Anya babu wani dalilin da yasa Maryam ta sauya Sa'eeda kuwa bancin ƙawaye???
****Shin bakwa tunanin soyayyar da Sa'eeda takewa Sauban baiyi yawa ba,karfa a samu matsala fa???
****Mai kuke tunani akan kwalbar da boka Sankeru yake da niyyar bawa Umma Kande??? Sannan mai yasa yace karta bari kwalbar ta fashe??? Shin wai idan ta fashe mai kuke tunani????
Ku cigaba da kasance dani taku har kullum Narrnarhh Bukar🤗🙃🌹💝 domin tafiyar tamu ta dabance🙃🙃🙃 na tabbata zaku ilmantu sosai tare da nishaɗantuwa in shaa Allah🤗🤗🤗 kudai ku cigaba da zubomin ruwan comments🤗🤗🙃🙃🙃 ni kuma bazan gaji da suburbuɗo muku da sababbin updates a kullum ba wanda zaku wa'azantu sosai da sosai🤗🤗🤗🤗💝💝💝💝💝💖💖💖💖🏵️🏵️🏵️🏵️🏵️🌹🌹🌹🌹🌹
Ina Kaunarku da yawa da yawa my Esteem Fans Allah ya barmu tare har a jannatul firdausi💖💖💖💖🏵️🏵️🏵️🏵️🌹🌹🌹🤗🤗🤗🤗🙃🙃🙃
Ina yinku over my Esteem Fans🤗🤗🤗🤗🌹🌹🌹🌹🏵️🏵️🏵️🏵️💗💗💗🌼🌼🌼
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044: 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
🌹Special greetings to y'll my Esteem Fans, ina kaunarku over,ina alfahari daku domin da bazarku nake taka rawata🙃🙃🙃💖💖💖💖💝
2⃣3⃣----2⃣4⃣
Sai kuma yayi shiru na tsawan wasu mintuna,Umma Kande har ta zaci bazai sake magana ba,sai kuma taji ya fara magana cikin amon murya mai sauti tare da firgitarwa.
"Akwai sharaɗi mai girma Umma Kande!!! Sharaɗi babba Umma Kande!!! Sharaɗin shi ne,zamu baki kwalba wanda ruhinsa ke aciki,sannan karki sake!!! Karki kibari!!! Karki yarda !!! A hir ɗinki !!! Kibari kwalbar nan ta fashe!!! Idan kuma ba haka ba asirin zai karye kuma zaki kuka da kanki Umma Kande!!! Tabbas zaki kuka da kanki!!! Sannan muma zai shafe mu, don haka dole ki kula !!! Dole ne ki kula !!! Ki kula da kwalbar kamar ruhinki Umma Kande!!! Idan ba haka ba komai naki zai rushe!!! Komai zai taɓarɓare miki Umma Kande!!! "
Bayan ya gama faɗin sharaɗinsa sai kuma ya ɗaga hannunsa na hagu sama yana a tsayan tare da yin wasu surkulle,yana cikin yin surkullen ne sai wata guguwa mai ƙarfin gaske da taso,duka bishiyoyin nan da suke zagaye da bukkar sai karkaɗawa suke,gayyayakin suna kakkaɓa,kamar za'ayi ruwan sama,tabbas wannan asirin mai girma ne ba irin kowani asiri da boka Sankeru yake basu bane,Maman Jummalo da take a zaune a wajen wata bishiya saida da tsorata matuƙa ainun,ganin yadda lokaci guda guguwa ta taso gashi yanzu ba lokacin damuna bane balle ace ruwan sama ne zai sauka,haƙiƙa da tsorata harda ma sauran matan da suke kan layi saida suka tsorata wasunsu ma harda ƙankame juna saboda firgici da ya shigesu lokaci guda.
A cikin bukkar kuma bayan ya gama surkullensa sai kuma guguwar ta tsaya cak kamar daukewar ruwan sama,bishiyun suma suka daina rangaji,haba kamar walƙiya sai ga wata kwalba matsakaiciya ta bayyana a hannunsa sannan ya miƙa ma Umma Kande tare da cilla mata hararar gargaɗi,a natse kamar ƙwai ya fashe ma Umma Kande ta miƙa hannayanta bibbiyu tare da russunawa cike da girmamawa ta amsa kwalbar jin gargaɗi haɗe da kashe din da aka mata akan kwalbar,a zuciyarta take ayyana dole ta kiyaye wannan kwalbar kamar ranta.
Bayan ta amsa kwalbar sai ta cire ɗankwalinta tare da nannaɗe kwalbar sosai kasancewar ɗankwalin nata mai girma ne sosai sannan ta lallaɓa a hankalin kamar ƙwai tasa kwalbar a cikin jakarta cike da kulawa kana ta kulle jakarta ta.
Boka Sankeru ne ya ƙara da cewa bayan ta saka kwalbar a jakarta.
"Wannan sihirin na daban ne Umma Kande!!! Ba kowa muke bamawa ba sai wanda yayi tsawan lokaci yana mana biyayya tare da bin dokokin mu haɗe da sharudɗanmu,haƙiƙa kinyi tsawan lokaci kina bin dokokinmu tare da sharudɗan mu,shiyasa muka baki,don haka ki kula!!! Ki kula Umma Kande!!! Sihirin nan ba irin wanda kika saba sani bane,dole ki kula kar asamu matsala!!! Don muma zai shafemu idan aka samu matsala Umma Kande!!! "
Cikin rawar murya Umma Kande ta fara magana saboda tsoro da firgicin da ya shigeta tun lokacin da guguwan nan ta taso har zuwa yanzu da ta ƙara jin kashedi tare da gargaɗi akan kwalbar.
"Zzzan kula shugabanmu,mai sha re kukanmu,ba.. ba.. bbaza a masu matsala da yardarka "(wa'iyazubillah,shirka!!! Shirka,ke duniya ina zaki damu🤔🤔🤔,Allah shi kyauta)
"Da yafi miki!!! Ko kuma kiyi da nasani mara adadi Umma Kande!!! "
Kamar yanda boka Sankeru ya saba kasancewa da Umma Kande yau ma hakan ta kasance,sai daga baya Umma Kande ta fito waje tana tafiya a hankali kamar ƙwai ya fashe mata a ciki sannan ta nufa inda Maman Jummalo take.Zaune ta sameta wurin wata bishiya tana shan iska,miƙewa tayi da sauri tare da tambayarta ya ta ƙare da boka Sankeru sannan mai ya haddasa guguwa.
Shiru tayi tana dubanta idanunta duk sun shige ciki kamar wata mars lafiya, har wata ƴar rama tayi,cikin murya mai sanyi ta fara magana.
"Dole na kula ƙawas,dole na kula da kwalbar nan ko kuma in shiga uku"
"Wace kwalba kuma"
"Kwalba boka Sankeru ya bani tare da min gargaɗi mai tsauri akan karna kuskura na bari kwalbar ta fashe saboda ruhin baban Nusaiba na a cikin wannan kwalbar,idan kuma nabari ta fashe shikenan komai nawa zai taɓarɓare"
Tare da nuna mata jakar a hankali sannan ta cigaba da cewa
"Yanzu ƙawas wani irin mugun ɓoyo kike tunanin zanyi ma kwalbar nan don wallahi na shiga ruɗu haɗe da