Showing 21001 words to 24000 words out of 55707 words

Chapter 8 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt

31 May 2024

8070

da yayarsa ɗaya sai kuma ƙaninsa namiji sukazo bikin.


Dayake suna shiri sosai da Umman Sa'eeda haka sukai ta janta da Sa'eeda a jiki.Hakan yama Sa'eeda daɗi a rai,ganin yanda suke janta a jikinsu da hira har da Ummanta.


Daman auran Umman Sa'eeda su ne suka ƙarfafa gwiwar sai ya ƙara aure saboda halin Umma Kande,bata girmama iyayansu tun suna raye,gashi da tsani wani daga daginsu ya raɓa Abbansu Sa'eeda saidai ita da yaranta kaɗai,wannan dalilin ne yasa aka aura masa Umman Sa'eeda saboda tanada hankali da girmama na gaba da ita ba kamar Umma Kande ba.


@@@@@@@@@@@@


Umma Kande dai ta dangana,tayi haƙuri sai bayan biki kamar yanda Maman Jummalo ta ce da ita saboda bikin,ta haƙura ta cigaba da shirya shiryan biki sosai,tun ana saura kwana uku amare suka fara shagalin biki har yau da ya kasance gobe ɗaurin aure suna shagali kala-kala.


Day 1 sunyi ƙauye day, sai day 2 sunyi fulani day sai yau kuma ana kamun amare,anyi kashe kashen kuɗi,ba laifi angwaye sunyi ɓarnar kuda don Naira tayi kuka😁.Nusaiba tayi ɓarin Naira sosai dan yanxu ta zama wata himmm da ita sai kace wata babbar mace ,tayi ƙiba sosai ga bleaching ɗin da take yanxu na allura ne, tayi haske sosai sosai.


Duk wannan bidirin da ake yi a gidan bai hana Sa'eeda zuwa makaranta ba,sannan Ummanta ma haka kullun sai ta fita shara abinta,a tare suke fita da safe abinsu.


@ @@@@@@@@@@@@


Ranar ɗaurin aure


Yau take asabar kuma ranar ɗaurin auran yara uku a gidan Malam Sulaiman Sani,a Masallaci aka ɗaura auran na ƴaƴan uku akan sadaki Naira dubu #100,000 lakadan ba ajalan ba ga kowaccansu,sannan aka shafa fatiha aure ya ɗauru(Su Umma Kande sai a zuba ruwa a ƙasa a sha😁😁😁😁).


Angwaye babu wanda yazo gaisuwan iyayen amare kamar yanda ake a al'adan ce,nan ma akaita surutai musamman ƴan layi( Ƴan layi akwai gulma,kunsama su Umma kande da Maman Jummalo ido,kun hanasu rawar gaban hantsi haba😁😁😁🙃🤔) ,wurin ƙarfe 8:00pm aka zo ɗaukan Jummalo, sai kuma Zaliha,ita kuma Iklima sai 11:00pm aka ɗauke ta,wannan abu ya janyo surutun mutane da dama, su Umma Kande hakan bai dame su ba tunda an ɗaura mai ya rage can tamatse musu da gulmar,duk lokacin da suka zo ɗaukar amare suna mara ba dasu tunda dai an ɗaura auran ƙarshen tika-tiki-tik.


Haka aka kai kowacce ɗakinta,babu laifi angwaye sunyi bajinta sosai,sai dai bamusan ya yanayin zaman auran nasu zai kasance ba.


@ @@@@@@@@@@@


Bayan kwana biyu da biki,dangi na kusa da na nesa kowa ya koma gidansa da abin arziƙi daga wurin su Umma Kande da Maman Jummalo banda dangin Abbansu Sa'eeda taƙi basu abin biki wai tunda dama ba sonta suke ba kuma wannan zuwa biki wurin su Umman Sa'eeda suka tare to wallahi babu abin biki da zata basu,har Abbansu Sa'eeda saida ya roƙa amma taƙi,haka suka wuce garinsu daman su can basu sa rai a abin bikin ba balle hakan ya damesu.


A ranar bayan tafiyar ƴan uwan Abbansu Sa'eeda daman su kaɗai suka rage, Musa ya shigo gidan,tun sanda yazo gidan ta fara kuka bai sake zuwa ba kuma koda yaje ɗaurin auran bai zo nan gida ba.


Lokacin ƙarfe 12:00pm na rana,shiga ɗakin Umma Kande ya yi da sallama kamar mutumin arziƙi amma muryar nan a lanƙwashe take kamar mace,ya samu wuri akan kujera ya zauna.


Maman Jummalo ce ta amsa masa sallamar amma Umma Kande ko kallan inda yake batayi ba.


Ɗakin shiru ya ɗauka na ɗan wani lokaci kowa na zancen zuci kafin Musa ya ƙatse shirun da gaishe dasu.


"Mommy na barka da rana,na same ku lafiya,ya gajiyan biki"


Yana maganar yana yanga sai kace mace,su Umma Kande dai ido suka zuba mai babu ɗaya a cikin wanda ya iya amsa mai,tsabaragyen mamaki da ya cika su musamman Umma Kande wanda har yanzu ta kasa yarda ɗanta ne Musa,shi Musa ɗanta ya zama ɗan daudu.


"Yanxu Musa wannan wani irin ɗabi'a ne ka ɗauko,kaga kuwa yanda ka koma yanzu sai kace mace wallahi abinda kakeyi ko wata macan baza tayi ba,haba Musa ya kamata ka dawo cikin hayyacinka don Allah" cewar Maman Jummalo


"Nahiiiiii Maman Jummalo inji ƴan india kinsa nayi yaransu , wannan ra'ayina ne,babu ruwanki koma mai zanyi,haka nake da ra'ayin zama,kuma ina alfahari da zama na haka,chass wallahi"


Miƙewa yayi duk suna binsa da kallo yayi wani juyi a ɗakin tare da girgiza ɗan ƙaramin kafaɗunsa sannan ya ce


"Yanzu ki kallo dubeni kyakkyawa dani san kowa ƙin wanda ya rasa,ke a Calabar ma har bukin ɗina akai manya manya Mata suna ji dani,zaki wani ce in dawo hayyacina,to da ba a hayyacina nake ba"


"Shikenan ni Saratu, ta faru ta ƙare Musa,yanzu a gabana ni mahaifiyarka kake girgiza kafaɗunsa haɗe da rangwaɗa,wayyo ni Sarere jikar sarkin ruwa!!!,na shiga uku!!! "


Kuka take yi mararan,da sauri Musa yazo wurinta haɗe da dafa kafaɗunta tare da cewa" Sorry mommy mi,kibar kukan nan don Allah babyn ki da kika sani a da bana yanzu bane,don nayi kuɗi sosai sosai "


Tsagaita kukan Umma Kande tayi tana dubansa tare da cewa"Da gaske kake Musa na ɗan albarka"


Ɗaga mata kai ya yi alamun eh,haba sai Umma Kande ta haɗe ido da Maman Jummalo nan suka kwace da dariya.


"Haba sai yanzu naji sanyi a raina,mai yasa tunda kazo baka faɗamin ba,kabarni ina kuka akan yanayin da ka koma,ai babu laifi tunda akwai samu"


"Wallahi mommy naso faɗa miki amma sai naga duk kin rikice kawai sai na bar gidan na tafi hotel abuna,daman na bari sai bayan biki nazo muyi maganar dake"


"Toh yanzu dai fadamin maganar ina jinka kace kayi kuɗi,ni kuma banga komai ba"


Dariya Musa yayi yana wani lanƙwasa ƙafa ɗaya kan ɗaya sannan ya ce"Suna account Mommy,daman nazo ne da niyyar siyan gida,tare da shaguna koda biyar ne a kasuwa,sai nasa haya,kinga zaki dinga samun kuɗi akai-akai ko Mommy na? "


"Da kyau ɗan albarka,naji daɗin wannan batu wallahi, Allah yama albarka,amma gaskiya idan zakazo garin nan,inaso ka koma yanda kake a da,bayan ka tafi sai ka juya saboda ƴan gulmar layi kaji ɗana"


"Bakida case Mommy mi, yanzu sai ku fara cigitamin gidan haɗe da shagunan ko"


Da "Eh" dukkaninsu suka ce suna murmushi ,sai ya ciro bandri ɗin dubu kuda uku ya miƙa ma Umma Kande da Maman Jummalo, haba wannan karon harda kuɗa tare da rungumeshi su duka(Allah ya kabamu wadatar zuci da ƙarin imani).Wannan kenan.


@@@@@@@@@@@@@


A bangaren karatun Sa'eeda sai dai muce maa shaa Allah,tana maida hankali sosai da sosai dan yanzu har sun kammala first semester suna a second semester a lokacin first semester result ɗinsu har ya fito.Sa'eeda ce ta samu highest score a class ɗin nasu wanda baima da yawa daga cikin ƴan ajin daɗi ba.


Yanzu ma haka su Sa'eeda sun tashi a school kasancewar yau Friday da wuri suke tashi.Bayan sun fito daga department ɗinsu ita da Maryam zasu nufo wajen gate ɗin makarantarsu don su samu mai keke napep ya kaisu gida,sukaji horn ɗin mota a bayansu,dukkansu babu wacca ta zuyo suka cigaba da taifiyarsu,mai mota da yaga alamun ba tsayawa zasuyi ba,yayi saurin parking a gefen titi sannan ya fito daga motar.............






****waye wannan mai yima su Sa'eeda horn kuma mai yazo dashi wurinsu?.......




****Gashi dai burinsu Umma kande ya cika an aurar da ƴaƴa,koya zaman nasu zai kasance da mazajensu?.........




🌹🌹🌹Shin ya kuke ganin mugun son kuɗin Umma Kande wanda ko kallon yanda ɗanta ya koma batayi ba,mai zakuce akai........




Sai mun haɗu da pages na gaba in
shaa Allah🙃🙃🙃




Ina matuƙar alfahari daku My Esteem Fans💝💝💝🌹🌹🌹🌹




I love y'll lodi lodi domin da bazarku nake taka rawata💝💝💝💝🙃🙃🙃🙃🤗🤗🤗🤗






Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️


Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044: 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️



Narrnarhh Bukar✍️


🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨




Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002








My Esteem Fans ina matuƙar alfahari daku, i love y'll all Lodi Lodi🤗🤗🤗🏵️🏵️🏵️🌼🌼🌼🌹🌹🌹🙃












1⃣9⃣---2⃣0⃣




Yanzu ma haka su Sa'eeda sun tashi daga school kasancewar yau Friday da wuri suke tashi.Bayan sun fito daga department ɗinsu ita da Maryam zasu nufo gida,sukaji horn ɗin mota a bayansu,dukkansu babu wacca ta juyo suka cigaba da taifiyansu,mai mota da yaga alamun ba tsayawa zasuyi ba, sai yayi saurin parking a gefen titi kana ya fito daga motar.


Wani handsome and classy guy ne ya fito daga motar,yana sanye da shadda mai kalar sararin samaniya,sanye yake da hula mai ƙube wacca ta saje da kalar kayan.Yana da tsayi sosai,baƙi ne amma ba cancan ba,sannan fuskarsa zagaye take da gemu wanda kana gani kasan yana shan gyara,his face look very innocent,babu laifi guy ɗin ya haɗu sosai,da murmushi a fuskarsa ya nufo wurinsu da ɗan sauri kasancewar tafiya suke.


"Assalamu Alaikum Malamai"


Maryam ce ta amsa mishi da fa'arta,ita ko Sa'eeda ko kallansa batayi ba,idonsa na kan Sa'eeda yana murmushi,don mace mai aji tana burgeshi sosai.


"Naga akwai rana sosai yau,gashi kuna tafiya babu mai keke napep suka balle ku hau,mai zai hana na rage muku hanya koda ban kaiku gida ba,kar kusha wahala"


A lokacin ne Sa'eeda ta bashi amsa da cewa"Kaga munyi ma kana da musu son a rage musu hanya ne,to karka damu,mun gode da kulawarka amma......."


Bata ƙarasa zancen da tayi niyya ba Maryam tayi saurin cewa"Babu komai muje Sa'eeda, kinsan uzirin da ya bari ya ce zai rage mana hanya ne? "


Sunan ya sake maimaitawa a zuciyarsa ' Sa'eeda suna mai daɗi'


Babu yadda Sa'eeda ta iya tunda abokiyar tafiyarta tana son a rage musu hanya amma a ranta baso take ba tuno da nasihar Ummanta akan kula samari,haka dai ta shiga motar.


Maryam ce ta zauna a front seat,ita kuma Sa'eeda ta shiga baya,tada motar yayi suka fara tafiya.


Motar shiru babu mai magana sai can ya katse shirun da cewa"Wani department kuke? "


"Department of Business Administration muke,100level" cewar Maryam


" Woow,ashe fresh students ne ku"


"Eh wallahi amma yanzu muna a second semester ne"


"Allah ya taimaka,ya bada sa'a"


"Ameen ya Rabbi" cewar Maryam


"Wai ƙawarki kurma ce,bata magana ne? "


Dariya Maryam tayi sannan ta ce"Magana kuwa sosai,saidai da alama ƴan surutun basa nan yau"


"Oh really ai naga alama kuwa"


Maryam ce take nuna mishi hanya,har ya kai daidai inda take so a sauke su wato hanyar da zata sadasu da layinsu,sannan yayi parking gefen titi,ya juyo yana duban Maryam yace.


"Sunana Sauban Muhammad ƙaraye,ina aiki a wani kamfinin sarafa shinkafa a matsayin Manager nice meeting you friend"


"Nice meeting you too"cewar Maryam


Dukkansu fitowa sukayi,a tare har shima don yana son magana da Sa'eeda amma ta mishi kwarjini a fuska.Har zasu wuce yayi saurin cewa


"Friend ko zaki aramun wannan ƙawarta taki mara son magana,zsmuyi magana ne just for 2 minutes"


Yana maganar da zolaya duk don Sa'eeda da tanka amma shiru,hasalima ƙara murtuke fuska tayi.


Ɗan jimmm Maryam tayi sannan ta ce "Haba bara na matsa,sai ku tattauna da ita"


Matsawa tayi ɗan gaba dasu,shi kuma ya matso kusa da Sa'eeda da murmushi a fuskarsa,sai da yayi gyaran murya sannan ya fara magana da cewa.


"Nasan ba a jinki bane magana a hanya amma taimako nake nema wurinki,don Allah ba dan ni ba ki taimaka min da number wayanki,Don girman Allah"


Hannu biyu ya haɗa alamar roƙo,fuskar nan ta shi tayi kalar tausayi,Sa'eeda a da bata da niyyar ba shi numbarta amma haɗata da Allah da yayi yasata aminta saboda ta tuno nasihar Ummanta da ta ce ' Sa'eeda duk wanda ya nemi abu wurinki kuma ya roƙeki da Allah koda cutarki zaiyi ki basa,sannan ki barshi da Allah' tuno da wannan nasihar yasata amsar wayarsa tasa numbarta sannan ta miƙa mai wayar tare da wuce wurin Maryam suka nufo gida.


@ @@@@@@@@@@


Ƙarfe 11:53am ta iso gida,lokacin Ummanta ta dawo daga aikin sharanta tana ɗaki.


Da sallama ta shiga gidan kasancewar yanxu babu ƴan mata a gidan daga ita sai Nusaiba,ita kuma Nusaiba ba zaman gidan take ba, yanxu ma kamar kodayaushe shiru gidan saika ce babu mutane ko a da can da akwai mutane a gidan ba amsa sallamarta da Ummanta suke ba.


Direct ta wuce ɗakinsu,haɗe da sake Sallama, Umman Sa'eeda dake a tabarmarta ta amsa mata tare da cewa.


"Da wuri haka"


"Eh Ummina,kinsa ranar jumma'a bamu cika lectures da yawa ba,yau kuma lecturer ɗaya ne ya cigo ajin namu"


"Ai gwara,zaku ɗan dinga hutawa,ba ace kullun sai wurin biyar zaku dinga ta shi ba,wahalar yawa zata muku"


"Nima Ummina nafi son duk ranar Friday mu dinga tashi kamar haka wallahi"


Buta Sa'eeda ta ɗauka ta zagaya bayan gida,bayan ta dawo ne taji wayarta na ringing,sai ta nufa jakarta ta ɗauko wayar.Sabuwar numbar ta gani,ɗan jimmmm kaɗan tayi har saida Ummanta ta ce


"Kina ji ana kiranki amma kin wani tsaya kamar hoto kina kallon wayar"


Picking call ɗin tayi haɗe da karawa a kunnanta sai tayi shiru,acan bangaren aka fara magana.


"Tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gareki Sa'eeda"


"Wa'alaikumussalam"


A gajar ce ta amsa haɗe da tsuke fuska kamar mai shirin kuka Ummanta dai na binta kawai da kallon mamaki ganin yadda take amsa wayar,a can a ka cigaba da Magana.


"Nasan kin gane mai maganar don koda jin kamar kina ɗaure fuska nasan yes kinsan mai maganar"


A zuciyarta ta ce 'Sai ka ce maye,to taya yasan na tsuke fuska na,ohon masa' katsa mata tunani yayi da cewa


"Sa'eeda ganinki na farko da nayi a ɗazo,lokaci guda kika shiga raina,kuma a gaskiya bazan ɓoye miki ba ina sonki da aure ne ba da yaudara ba,zuciya ta gama yarda da ke ce wacca take adduarka samu a kullum haɗe da burin kasancewa tare da ita a matsayin miji da mata,please Sa'eeda ba nazo dan na yaudareki bane ko ko wata manufa tawa don in cimma,a'a ko kaɗan nazo ne a gareki saboda ƙaunarki da nake yi wanda lokaci kuda ya shigeni,don Allah ki aminta dani please,in ma kina tunanin karatunki ne ni a shirye nake tare da goyon bayan karatunki ɗari bida ɗari,inaso kiyi tunani akai don girman Allah Sa'eeda bada wasa nazo gareki ba"


Duk wannan surutan da yake wayar na a kunnanta kuma tana ji amma ta kasayi mishi magana,hasalima shiga kogin tunani tayi 'Wai yana sonta da aure huhh',ita da a tsarin rayuwarta bata kawo aure nan kusa ba,amma shi yanzu yana mata maganar aure.


"Hello,baki jina ne Sa'eeda"


Firgigit ta dawo hayyacinta tare da fara magana cikin murya mai sanyi da dadi ta fara magans"Ina jinka,but can you please give me some days to think about it?


"Quite sure dear"


"Alright Nagode da kulawa"


Bata jira mai zai ce ba ta katse kiran,sai da dubi Ummanta da tun ɗazu da zuba mata na mujiya.


"Naga sai wani taɓe baki kike haɗe da ya mutsa fuska tunda kika ɗau wayan lafiya? ”


" Wallahi Ummina wani ne mai suna Sauban ɗazu ya takuramin haɗe da haɗa ni da Allah in taimaka mishi da number na,lokacin mun taso daga school ni da Maryam kuma yanzu da ya kirani sai sai..."


"Uhmmm ina jikin sai kuma me"


Kwashe duk abinda ya ce mata tayi ta sanar da Ummanta har aikin da ya ce yakeyi duk ta sanar mata, shiru Ummanta tayi tana kallonta sannan ta ce


"To ke kuma me kika ce masa"


"Nace ne ya bani lokaci zanyi tunani a kai"


"To ai shikenan,amma dai ki kula da kanki Sa'eeda,don mazan yanzu wasunsu ba abin yarda bane,sun iya kalamai masu daɗi ga ƴan mata duk don suja hankulansu,ina ƙara fadamiki ki kula da kanki sosai,ban hanaki kula samari ba amma ki duba wanda yasan ya kamata sannan kuma mai addini da halaye masu kyau a cikinsu sai ki kulashi,amma ba kowani kala ba,ko kuma kita tara samari,kin jini ko"


"Toh Ummina,zan kula sosai in shaa Allah"


"Allah yasa"


"Aameen"


Sai kuma suka cigaba da wata hirar .


@@@@@@@@@@@@@


Bayan ƴan wasu kwanaki


Sa'eeda dai ta aminta da soyayyar Sauban,dan yanzu yakan zo har ƙofar gidansu,duk da a wata baifi sau ɗaya yake zuwa ba kasancewar Sa'eeda bata cika son hira ba hasalima shi yake matsa mata akan yanason yazo koda sau ɗaya ne a wata.


Sunyi exams ɗin second semester wanda azumi baifi saura kwana shida a ɗauka ba suka gama,duk wannan lokacin suna tare da Sauban wanda yanzu soyayyarsa ta riga da ta gama mamaye ilahirin jikinta da gaɓoɓinta gaba ɗaya.


Sauban ya iya kashe mace da salon soyayyarsa,don zance professor ne a ta wannan fannin,ya kama zuciyar mace taji duk duniya babu wanda take so sai shi,haƙika ya rikita Sa'eeda da kalaman soyayya masu saka mutum shauƙi,sannan yana kula da lamarinta sosai duk da idan ya bata kuɗi bata amsa sai in ya mata jan ido kana take amsa haɗe da yi masa godiya.


Haka sanda aka fara azumi ya kawo mata ramadan basket da ƙyar ta amsa saboda Ummanta ta hanata yawan amsar kaya wurin samari,haka zalika lokacin sallah kaya kala biyar ya mata haɗe da jaka da takalmi masu tsada,shima da ƙyar ta amsa sannan ta masa godiya sosai.


Duk wannan abubuwan da Sauban yake ma Sa'eeda sai ta faɗama Maryam tun daga kalaman soyayya da yake mata,kyaututtuka da dai sauransu,duk da wani lokacin ba Sa'eeda take fara bata labari ba,ita Maryam da kanta take tambayar ta ya friend ɗinta,to a nan ne sai ita kuma Sa'eeda tai ta zubo mata zancansa.


Haƙiƙa wannan sallar su Sa'eeda sunyi shi cikin farin ciki da annashuwa ba kamar saura shekarun da suka gabata ba kasancewar yanzu babu laifi Umman Sa'eeda na ƙoƙarin ganin sunyi cima mai kyau.


Bayan sallah da sati ɗaya suka koma 200 level,soyayyar Sauban bai hana Sa'eeda karatu ba hasalima yanzu karatun nata ya ƙara bada wuta saboda tana so taga a kowanni result ta fito da flat A,shi yasa kullun zaka ganta da littafi a hannu tana karatu.


Akwai specific time da taba ma Sauban zai dinga kiranta ba koda yaushe ba,kuma hakan ta faru sai lokacin yake kiranta don baya son matsa mata da yawa.


@ @@@@@@@@


Waje guda kuma,rayuwarsu Umma Kande da Maman Jummalo ta cigaba da tafiya cikin daɗin rai da annashuwa duk da ba kamar

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login