Showing 30001 words to 33000 words out of 55707 words
Chapter 11 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
jiran ranar mutuwarta,Wannan kenan .
@@@@@@@@@@@@@@
Ɓangaren Iklima ita ma dai gidan auran nata sai a hankali,duk da mijinta ba mai shan giya bane, kuma sannan ba ɗan mafiya bane mai aiki da dodo amma fa mijin nata duk kanwar ja ce da na sauran ƴan uwan nata,saboda mijin nata cikakkyan ɗan luwaɗi ne wanda har ƙungiya suke dashi kuma yana ɗaya daga cikin ƴan ƙungiyar wa'inda suke faɗa aji.
Itama dai Iklima daren farkonta baizo mata da sauƙi ba,kasancewar angon nata ba ta hanyar daya dace ya nemi biyan buƙatarsa da ita ba,wanda hakan ya kawo musu saɓani sosai,kasancewar iklima akwai tsiwa yasata turo baki da cewa
"Mai kake nufi,a ta bayana zaka biya buƙatarka,babu kyau biyan buƙata a ta baya fa "
"To ni ina ruwana da rashin kyayunsa,kinga malama in kin gama wa'azin naki kizo don ni a matse nake"
" Tab,wallahi haramun ne,bazanyi ba"
"Haramun ɗin ubanki! Nace haramun ɗin uwarki! Shegiya mai suffar masu ciwon ƙanjamau,ke kike ganinsa haramun amma a wurina halas ne,don haka karki ɓatamin rai idan kuma ba haka ba kici na jaki don naga alama bakida kunya,to ni sanda ake rabon kunyar bana kusa,shegen kaina ne wallahi,kina ɓatamin lokaci" ranshi a ɓace yake maganar haɗe da zaƙuwa kasancewar yasha maganin ƙarin ƙarfi sosai.
"Yanzu mai iyayena suka maka da zaka sasu ciki ehh..."
Bata ƙarasa da maganar ba ta fara kuka har da shassheƙa,duk da iyayenta su suka ja mata wannan fitinar da bala'i,amma a ce saboda kafirci haɗe da yahudanci ya rasa inda zai nemeta sai a ta duburarta kuma a daren farkonta wannan wani irin musiba ne haka,bata ƙarasa zancen zucin da take yi ba taji an fijgota da ƙarfi.
"Wayyo Allah na,yau na mutu shikenan mamana zai kashe miki ni!!!"
"Duk wannan kururuwan da iface ifacen da kikeyi na banza ne domin babu mai cetonki a gidan nan,dama kin natsu na biki a hankali da yafi miki,amma tunda irin wannan salon kika zaɓa muje zuwa ɗan halak ka fasa "
Dambe suka fara yi,tana fizge fizge haɗe da tsugunli da cizonsa amma ƙyam kamar ba da mutum take ba,tayi iya ƙoƙarinta don ta ƙwaci kanta amma jikin mace da na namiji ba ɗaya bane haka yaci galaba akanta,kuma ya biya buƙatarsa da ita a ta duburarta,wanda tana kuka tana magiyar yayi haƙuri ya ƙyaleta babu kyau Allah ya haramta amma ina gogan naku yayi nisan kiwo.(Subhanallah,Allah ka tsare mana imaninmu baki ɗaya🤔🤔🤔)
Biji-biji yayima Iklima wanda ko motsin kirki ya gagareta saidai hawaye,shi kuma tunda ya biya buƙatarsa ya tashi daga kanta ya ma fita daga ɗakin ko kallon inda take baiyi balle tunanin taimaka mata, ya ƙara gaba abinsa.
Wuya tayi wuya,kuka kam Iklima tashashi kamar ba gobe, ( Fans karku manta fa Iklima auta ce ga Umma Kande kunga ko dole tayi taɓara,gashi anji maza😂😂😂).
Iklima da taga kuka ba shi ne mafita a gareta ba yanzu,miƙewa tayi da ƙyar tana dafe da bango har ta isa toilet ɗin sai ta haɗa ruwan zafi don gasa jikinta,a toilet ɗin ma kuka ta dinga yi tana masa Allah ya isa bazata yafewa ba har kabarinsa naci da wuta(Wayyo Allah na😂😂😂,gaskiya an taɓo autoci,wannan sangarta haka,kai kai kai😂😂😂🙃🙃🙃).
Kuka ta cigaba dayi har ta kammala gasa jikin nata sannan ta ƙara dafe bango ta fito zuwa stool ɗin da yake a gaban mirror,haka ta shirya cikin kaya marasa nauyi kasancewar kamar zata faɗi haka take ji,tayi wani fayau da ita.Saida akayi kwana uku batasa mijinta a ido ba,Allah yasa ma akwai kayan abinci a store ɗin shi ne sauƙin ta.
A washa garin ranar sai gashi ya shigo gidan har ɗakinta kamar abun arziƙi ya kirata tazo ga abokansa sunzo su gaisa har da sakar mata murmushi wanda baikai zuci ba,ita a tunaninta ƙila bazai ƙara yi mata abinda ya mata a kwanaki hudun da suka wuce ba.Hijab ta ɗauko zatasa yayi saurin riƙewa tare da cewa.
"Don Allah wani irin ƙauyanci ne haka zaki fita da ƙaton hijab sai ka ce matar liman"
Galala Iklima ta tsaya tana kallonshi,ko ya manta ne abokansa fa zataje gaisarwa kuma sai tafita daga ita sai ƴar yaloluwan riga wacca batakai gwiwaba,maido da ita yayi cikin hankalinta da cewa
"Look banason wannan halin naki,duk sanda abokaina zasu to banaso ki dinga saka hijab,kawai kizo a wadda kike,ok"
"To"
Shi ne amsar da ta iya bashi ta ta mike zata fita kitchen ɗauko musu ruwa shima wannan karon da sauri ya hanata abinda tayi niyyar ɗaukowa ya ce su tafi suna jiransu,haka suka isa falon a tare.
"Assalamu Alaikum"
Cikin murya mai sanyi tayi maganar tare da russunawa saidai kafin ta ƙarasa da maganarta taji wani yace
"Wow,gaskiya babe ɗinka ta haɗu wallahi"
Cikin abokansa wani ya faɗa,kuma babu wanda ya amsa mata sallama a cikinsu,idanunsu kyar akanta har ta soma jin wani iri da kallon da suke mata,data gaji da tsayuwa kuma babu mai magana a cikinsu saidai kallonta da sukeyi kamar sun samu television yasata shirin komawa bedroom sai kuma taji mijinta ya ce.
"Ina zaki kuma"
"Bedroom mana"
"Aka ce miki angama dake ne"
"Naga mun gaisa to me yayi saura "
"Wurinki suka zo ai"
Kallonshi tayi da mamaki,wai wurinta suka zo kuma shi ne suke mata irin wannan kallo haka kamar mayu,can kuma ta ce.
"To ai mun gaisa ko,shikenan ai,ko kuma in musu girki ne yanzu ba yanzu zasu tafi ba? "
"No karki takura kanki akan wani girki can,abinda ke a gareki ma ya wadatar dasu ". Shafa gemunsa yayi yana kallonta haɗe da yin wani munafikin murmushi, suma abokan nasu murmushi suke tayi suna kallonta.
Waro idanu tayi waje jin abinda ya furta wai abinda ke agareta ya wadatar dasu,me ke nan kuma,ƙara tambayarsa tayi
" Ni kuwa wani abu nake dashi da zai iya wadatar dasu banda abinci? "
"Sosai ma kuwa babe"
Wani daga cikin abokansa ne yayi maganar yana shafo sumar kansa haɗe da kashe mata ido ɗaya,ita fa a gaskiya bata gane wannan abun da yake agareta wanda zai wadatar dasu ba sannan kuma kallon da suke mata shima bata gane masa ba,ƙara tambayarsa tayi wanda amsar da ya bata yasata saurin dafe ƙirji haɗe da waro ido waje tana dubansa
"Ka ce me? "
"Na ce abinda yake a wurinki wanda zai wadatar dasu ba komai bane illa....................
Mu haɗu a pages na gaba my Esteem fans✍️✍️✍️
*** Tofa ƙaƙa ƙara ƙaƙa,wannan wani abu ne haka wurin Iklima da zai wadatar da abokan mijinta???🤔🤔🤔
****hmmm da alama dai su Umma kande da Maman Jummalo garin nemo ma yaransu mazaje masu kuɗi sun ɗeboma ƴaƴansu bala'i haɗe da wahala wanda ƙilama har ta shafesu baki ɗaya,kaiconsu da bin ruɗin duniya,Allah ka kare mu daga faɗawa halaka.
Ina sonku,ina ƙaunarku,ina ji daku my Esteem Fans,Allah yabar ƙauna🙃🙃🙃🤗🤗🤗🤗💖💖💖💖💝💝💝🌹🌹🌹🏵️🏵️🏵️
Ina jin daɗin sharhin da kukeyi akan littafina Allah yabar ƙauna yasa mu amfana da abinda ya ƙunsa a ciki🙃🙃🙃💝💝💝💖💖💖🏵️🏵️🏵️🌹🌹
Ku cigaba da zubo ruwan comments🌹🌹🌹🤗🤗🤗🙃🙃🙃 ni kuma bazan gaji ba wurin sambaɗo muku new updates wanda zaku nishaɗantu tare da ilmantuwa gami da wa'azantuwa🌹🌹🌹🤗🤗🤗🙃🙃🙃
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.[5/23, 8:09 AM] Narnarhh Bukar: 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
🌹🌹🌹Da rarrafe yaro kan tashi,wata rana jiriri ango ne🌹🌹🌹
🌼🌼🏵️🏵️🌹🌹🙃🙃🤗🤗Special greetings to y'll my Esteem Fans,Allah yabar ƙauna,I love y'll Lodi Lodi🤗🤗🙃🙃🌹🌹🏵️🏵️🌼🌼
2⃣7⃣----2⃣8⃣
"Ka ce me? "
"Na ce abinda yake a wurinki wanda zai wadatar dasu ba komai bane illa duburarki"
" Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un,mene! Kasan me kake cewa kuwa,da alama baka cikin hayyacinka"
"Da hankalina kuma ina cikin hayyacina,and so what idan kin basu duburarki ai abokaina ne ba wasu can ba sannan da izinina ai"
Wannan karon maganar tasa a zafafe yayi ta tare da cilla mata wata uwar harara.
"Wannan wani irin jahilci ne,a ce ina matarka ta sunnah kake faɗamin irin wannan maganar tare da umurta ta,lallai duniya tazo ƙarshe kuwa,idan ma mafarki kake to ka farka don wallahi bazan biye maka ba na saɓawa Ubangijina yasa sakani wuta"
"Daman ba biyemin nakeso kiyi ba ,hasalima idan kina ihun yafi kawo light"
Iklima da taga ba jinta zaiyi ba sannan ga abokansa har su uku yake mata zancen yahudancinsa tare da jahilci,ai wannan yahudanci ne mararan wallahi,bin shawarar zuciyarta tayi akan ta gudu toilet tasaka key kota tsira,hakan kuwa tayi amma ta makaro dan batafi taku biyar ba mijinta da abokansa suka bita tare da riƙota ta ihu tana cewa
"Ku sakeni la'anannuuuu!!! Jahilai marasa imani da tsoran Allahhhh!! Wa'inda bazasu gama da duniya lafiya baaaaa!!! Allah sai ya sakamin,ku sakeni wayyo Allah naaaaa!!"
Babu wanda a cikinsu ya kula mai take cewa hasalima mijinta cushion ya samu tare da zama ya ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya haɗi da ɗauko wayarsa don yin videon abinda sukeyi (Wa'iyazybillah,Ya Rahman kasa mufi ƙarfin zuciyoyimu😞😞😞).
Haka tana kuka tana magiyar suyi haƙuri babu kyau haramun ne,amma ina babu wanda ya kulata balle ya tausaya mata,haƙiƙa tasha wuya matuƙa ainun a hannun abonkansa kusan sumanta huɗu,datà sume wahala zata sake farfaɗo da ita,shi kuma mijin nata mara imani yayita videon abinda sukeyi hasalima shi nishaɗi abinda sukeyi yake sakashi sosai.(Subhanallah,kaico da irin rayuwar yahudawa🤔🤔🤔)
Saida kowan ne a cikin yayi yadda yakeso da ita sannan suka ƙyaleta,tana nan a yashe a ƙasa babu kaya jikinta,don rashin imani a haka suka bar gidan batare da waiwanta ba.
Iklima ba ita ta dawo daga suma ba sai cikin tsakiyar dare,kasa tafiya tayi saidai rarrafe,a haka ta rarrafa zuwa toilet,da ƙyar ta iya zama a cikin ruwa zafin saboda both her front and back duk zugi suke mata kasancewar abokan nasa wuri biyu sukayi amfani da ita,tana kuka ta gasa jikinta tare da da nasanin biyewa mamanta akan sai ta auri mai kuɗi gashi yanzu ta saka kanta cikin wahala da damuwa,a haka ta kammala gasa jikinta wanda haƙiƙanin gaskiya tamayi namijin ƙoƙari duba da yadda shi mijin nata ya afkar mata wanda bata daɗe ta warkewa ba hasalima wurin bai dena mata ciwo ba gashi yau har mutane uku sun afka mata.
Da ƙyar ta iya rarrafowa zuwa bed ɗinta ba tare da tasaka kaya ba taja bargo ta lulluɓa kasancewar zazzaɓin ya rufeta jikinta sai kakkarwa yake saboda mugun zazzaɓin daya shigeta lokaci guda,haka ta kwanta sai daga baya bacci ya sureta haɗe da mugayanmafarkai bila adadin mafi yaws duk akan mijinta ne da abokansa.
Haka Iklima ta cigaba da rayuwa a gidan mijinta cikin wahala da tashin hankali gashi kusan every week shi da abokansu sai sun biya buƙatarsu da ita wani lokacin da taji isowarsu zata ruga toilet ta saka key ta kuma ƙi cire key ɗin haka zasu wuce wani lokacin kuma su yagalgalata son ransu,babu halin ta faɗama mamanta saboda kashe din da ya mata haɗe da nuna mata videos ɗin da yayi mata a lokacin da suke biyan buƙata da ita tare da cewa tana faɗama wata ko iyayenta sai ya ɗaura a social media kowa ya gani,da wannan ya toshe bakin Iklima,koda sunyi waya da Umma Kande bata faɗa mata komai hasalima lafiya take cewa idan Umma Kande ta tambayeta suna lafiya babu wata matsala. Wannen kenan
TUNATARWA
*****Ƴan uwana mata mubi duniya a sannu,muyi taka tsantsan da duniya domin idan ba muyi taka tsatsan ba zamu kai kanmu ga halaka,baki da gashin wance ba lalle sai kinyi kitson wance ba,izina ga mata masu zuwa wurin boka ko malamin tsubbu don biyan wata buƙata tasu,kisani yake ƴar uwata mai daraja da a ce cikin salisalin dare kika tashi tare da ɗauro alwala sannan kikayi sallah koda raka'ah biyar ne haɗi dakai kuka gurin Ubangiji maji kukan bawansa to wallahi da kinga canji a rayuwanki basai kin bata aljihunki ba tare da imaninki ba.
Milasi ne mai ƙarfi a nan domin kasancewar Umma Kande da Maman Jummalo sun aurar da ƴaƴansu wahala da damuwa bata ƙare musu ba hasalima yanxu zasu fara girbar abinda suka shuka domin kuwa ba turbar Allah da manzansa suka bi ba wurin aurar da ƴaƴansu hasalima taimako suka nema wurin ɗan Adam kamarsu ba wurin Allah ba wanda su a nan imaninsu ya soma rauni sannan kuma zasu girba abinda suka shuka da hannunsu tare da ƴaƴansu da basu samu tarbiyya mai kyau ba.
Allah kasa mufi ƙarfin zuciyoyinmu,ka ƙarama mana imani tare da tsarkake zukatanmu,ka bamu ikon bin dokokinka,ka kuma hanamu kallon haram koda da ƙwayar zarra ne.********
@@@@@@@@@@@
"Assalamu Alaiki"
Wata ƴar matashiyar budurwa ce tama Sa'eeda sallama haɗe da zama a seat ɗinta tana ɗan murmushi har dimples ɗinta na lotsawa.
"Wa Alaikissalam"
Sa'eeda ita ma ta mayar mata da martanin murmushin data mata.
"Sunana Halima Ɗalhat amma anfi kirani da Iman"
"Ni kuma sunana Sa'eeda Sulaiman"
"Maa shaa Allah, duk da nasan ba wani sanina kikayi a class ɗin nan ba hasalima a 200 level na shigo saboda direct entry nayi"
"Allah sarki,ina ganinki a class ɗin nan amma bamu taɓa magana ba,kinsan wallahi nayi mamakin ganinki a cikin class tare damu alhalin bamu fara karatu dake ba"
"Eh wallahi, nayi ND na a Nuhu Bamalli polytechnic Zaria a business administration sai nayi applying DE (Direct Entry) saboda banason HND,shi ne suka bani admission a 200 level"
"No wonder!!! I'm so surprise seeing you in our class"
Dariya sukayi lokaci guda,zakayi tunanin ƙawaye ne tun tali-tali ba yanzu suka fara magana da juna ba,Iman ce ta katse dariyar tasu da cewa
"Please Sa'eeda will you be my friend? Ba zan ɓoye miki ba,tun da na fara karatu a class ɗin nan ban ga mai natsuwa,hankali tare da ɗumbi karatu kamarki ba,bana yin ƙawaye amma kece ta farkon da naji zan iya ƙawance da ita ba tare da nayi tantama ba ko shakku akai,Sa'eeda ni ba irin ƙawayen banza bane,a lokacin da na fara karatu daku na lura ƴan class ɗin nan basa son tarayya dake,bayan haka suna gulmarki a ɓoye wai ke ƴar talakawa ce kaza da kaza"
Katse mata magana tayi Sa'eeda da cewa
"Koda za'ayi gulmana banda Maryam a ciki saboda aminiyata ce tun muna secondary school,so i know she will never be among them"
Galala Iman tayi da baki tana kallonta,kardai tana nufin Maryam Tukur,sai kuma ta ce
"Kina nufin Maryam Tukur"
"Sosai ma kuwa"
Iman mamaki ya cikata sosai jin Maryam wacca tafi kowa gulmarta tare da fallasa sirrinta ga friends ɗinta yanzu take cewa she trust her and she will never be among those that will hurt her,how is that possible,tab akwai lauje cikin naɗi kenan.Sai kuma can ta ce
"Amma duk da haka be very careful,karki yarda da mutum ɗari bisa ɗari dan wani lokacin mutum kan canja daga yadda kika sansa"
"Hakane Iman amma zuciyata tana faɗamin a kullum Maryam will never betray me"
"Naji hakan kuma ina fatan she will never betray you,amma dai kibi a hankali "
"In shaa Allah dear,nagode da shawararki sosai,sannan maganar friendship dani you are always welcome,Allah yasa ƙawancanmu ta kaimu har zuwa Jannatul Firdausi"
"Ameen ya rabb,nagode sosai da yarda da kikayi akan na kasance ɗaya daga cikin friends ɗinki"
"Babu damuwa Iman nike da godiya"
Rungume juna sukayi suna jin ƙaunar junansu na ratsasu.
Tun daga wannan lokaci Iman ta kasance ta hannun damar Sa'eeda sannan idan ƴan aji suna gulmar Sa'eeda da sunga Iman zasu kama bakinsu saboda sunsan halinta,bata musu da wasa har Maryam ma shakkar Iman take saboda akwai ranar da Iman tazo wucewa ta gefansu taji Maryam na gulmar Sa'eeda tare da fallasa sirrin Sa'eeda ga ƴan group ɗinsu,su kuma sai dariya suke suna tafawa,taso ta wuce ba tare da ta kulasu ba amma jin Maryam tayi wani lafazi akan Sa'eeda yasata tsayawa cak tare da juyowa ta duba Maryam sannan ta ce
"Me kika ce? "
Maryam ta zaci Iman itama ta tsani Sa'eeda ne yasata ƙara maimaitawa tana dariya
"Kina nufin Sa'eeda bata da asali? "
"Sosai ma kuwa Iman"
"To ke waya faɗa miki bata da asali? "
"Da kanta ta fadamin ai"
Iman girgiza kai tayi tuno da yabon da Sa'eeda take yi game da Maryam akan ta yarda da ita,lallai ɗan Adam ba abun yarda bane a wannan rayuwa,can kuma ta ce
"Yanzu ke Maryam da ta faɗamiki sai ta ce kizo cikin friends ɗinki ki fada musu,kina faɗa musu kuna dariya lokaci kuda ko,shin bakisan yarda da amintuwa da tayi dake ne yasa har ta iya faɗa miki wannan sirrin nata wanda ba kowa zata iya fadama mawa ba,amma sai gashi kinci amanar yarda da amintuwar da tayi dake kinzo cikin ƙawayenki kina fallasa sirrinta garesu"
Taɓe baki Maryam tayi sannan ta ce
"To ni ina ruwana,ni na ce ta faɗamin "
"Tabbas bake kika ce ta faɗamiki ba amma she trust you that's why she is revealing her precious secret to you but you betray her,shame on you Maryam,kin ban kunya,na zaci idan kika ji wani yana fallasa sirrinta sai idan ƙarfinki ya ƙare amma sai gashi ke da kanta,wannan kuskure ne Maryam sannan idan baki tuba ba kin daina fallasa sirrin mutane sai Allah ya kamaki"
"To miye a ciki don na fallasa sirrinta,sannan ni ai bance ta faɗamin ba,hasalima in zaune na har seat ɗina tazo ta sanar min,sai kuma inƙi faɗa don ina jin tsoranta Allah ya bani baki,a'a wallahi ke idan ta ƙara fadamin wani sirrin nata bazan fasa zuwa fallasashi ba,ke yanzu ma na fara wallahi"
"Eh lallai Maryam kin cika munafuka amma baki da hankali,ke a tunaninki don kin fallasa sirrinta shi zai hana Allah ya ɗaukakata,wallahi kinyi kuskure,kuskure ma babba,wanda zakiyi nadamar da bata da amfani a ƙarshe,sannan kiji tsoran Allah kisan cewa Allah baya barci yana kallon kowa,yasan abinda ke a cikin zuciyar kowa,ita da kuke ganin she is nothing wata rana sai kuga she becomes something,sai Allah ya ɗaukakata sama daku,sannan rashin asalin da kike cewa bata dashi wataran sai kiga Allah ya haɗata da asalinta,who knows she comes from a rich family ƙaddara ce yasata zamowa haka,ki kula Maryam, ki kula,daga yau idan ina wuri karki sake aibanta Sa'eeda inba haka ba,ubanki zanci lakada a waje wallahi,ni ba kamar Sa'eeda bace shiru-shiru ayita cutarta tana haƙuri,bana ɗaukar iskanci ko raini,idan baki kiyaye ba