Showing 54001 words to 55707 words out of 55707 words
Chapter 19 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
ya mutu.(Da sauri na ɗauko nose mask ɗina na saka saboda kar a samu erro mai Esteem fans😷😷😷)
Zuwa wurin wata ƴan ƙwarya dake rataye a ɓukkar ya ɗauko kwallin tare da cilla musu, sannan kamar yadda ya saba kasancewa dasu a duk sanda sukazo hakan ta faru,amma fa yafi daɗewa da Maman Jummalo wanda har Umma Kande taji tsoro saboda da ita ya fara,kusan awa biyu yayi da Maman Jummalo kana tafito tana gumi tare da ɗingisa ƙafa kamar mai ciwo.Haka suka taho gida wanda basu suka iso gida ba sai wurin Isha'i saboda daɗewan da boka Sankeru yayi da Maman Jummalo.
Bayan sunyi wanka sun huta,sannan Umma Kande ta dubi Maman Jummalo tare da cewa
"Ƙawas yanzu ya zamu shawo kan yaran nan su saka wannan kwallin ba tare da sun bamu matsala ba"
"Wata sabuwa inji ƴan caca,tab akwai drama kuwa,kinsan yanzu sun fara biyewa Sa'eeda har da ce mata tayi musu ƙari a karatunsu,kinga da wuya su yadda su saka wannan kwallin kuwa"
Shiru ɗakin yayi kowa na neman mafita,sai can Umma Kande cikin murna ta ce
"Yawwa!!! Na samo mafita ƙawas!!! Wallahi nasamo mafita!!! Kinsan me Ƙawas"
Girgiza kai Maman Jummalo tayi,sannan Umma Kande ta cigaba da cewa
"Mu musanya musu kwallinsu da wannan ta hanyar cire bayan kwallin nasu saimu saka musu wannan kinga ai bazasu gane ba,muyi shiru abunmu,koya kika ce"
"A yyiriri nanaye!!! A Gaskiya ƙawas kin iya bada shawara,haka kuwa za'ayi wallahi, yooo ina dalili ai gwara su sake wani auran mu huta"
"Wallahi kuwa"
Haka suka cigaba da hirarsu cike da annashuwa,abinda su Umma Kande basu sani ba shi ne,Iklima tazo shiga ɗakinsu taji Mamanta da Maman Jummalo suna shawarar yadda zasu sake aurar dasu harda kwallin da zasu musanya musu duk don su shafa a rashin sani,ai tuni ta wuce ɗakinsu Maman Jummalo kasancewar a ɗakin Umma Kande suke hirar,babu ɓata lokaci Iklima ta sanar ma Jummalo abin iyayensu su shirrin aikatawa akansu,haka suka yanke shawarar kar kowaccansu tasa kwallin,tunda ita Jummalo tanada wani sabon kwallin wanda mamanta batasan dashi ba kawai saisu shafashi amma tare da taku kar susan basu shafa ba.
Da wannan shawarar Iklima da Jummalo suka kwana,haka suma su Umma Kande da shawararsu sukaje suka kwanta,da safe kamar yadda su Iklima suka tsara haka sukayi ba tare da iyayensu sun gane ba kwallin da suka sauya musu bane suka shafa ba.
Bayan wasu satittaka saiga Maman Jummalo da sassafe da fito ɗakinta da gudu tazo wurin inda ake wanke-wanke haɗi da kwara amai babu ƙakƙautawa,da sauri Umma Kande ta ƙasaro inda take domin a lokacin da Maman Jummalo ta fito da gudu,Umma Kande fitowarta kenan zata zagaya bayi.
"Ƙawas lafiya kuwa,meya sameki haka"
Cikin galabaita Maman Jummalo ta fara magana
"Nima na rasa meke damuna ƴan kwanakin nan wallahi, sai inji zuciyata na tashi kamar zanyi amai,ga yawan bacci da kasala,anya ba shawara bane kuwa? "
"Da alama tunda kina yawan bacci,shirya kawai anjima muje asibiti"
"To"
Taimaka mata Umma Kande tayi ta wanke bakinta sannan tayi brush,sai ta ƙara taimaka mata ta shiga ɗaki.Da ƙarfe 10:21am na safe su Umma Kande da Maman Jummalo suka shirya zuwa asibiti,a gwajin farko likita ta tabbatar musu da Maman Jummalo na ɗauke juna biyu na sati uku da kwana ɗaya,ai kan likita ta kammala bayaninta Maman Jummalo ta miƙe tsaye,jiki na rawa ta fashe da kuka tana cewa
"Na shiga Uku na lalace ni Hafsy,wace baƙar rana ce yau a gareni ni Hasfy"
Umma Kande tayi saurin rufe mata baki kar tayi ɓaran-ɓarama a gaban likiti,jawota tayi suka fita zuwa gida,ko a cikin keke napep ɗin kuka take sosai,bayan sun isa gida Maman Jummalo ta nufa ɗakin ita ma Umma Kande ta biyota bayan ta sallami mai keke napep ɗin.Allah yasa ma gidan babu kowa kasancewar Iklima da Jummalo suna Islamiya,ita kuma Umman Sa'eeda da Sa'eedar duka basanan.
Tana shiga ɗakin ta yakice gyalenta tare da ɗan kwalinta tana kuka tana cewa
"Na shiga Uku ni Hafsy !!! Yau na ɗau ciki boka,shikenan zan haifi ɗan boka,wayyo Allah ni Hafsy,shikenan tawa ta ƙare!!! Yiiiiiii yiiiiiiiii yiiiiiii !!!! "
Haƙuri Umma Kande tayita bama Maman Jummalo akan tayi hakuri sai a zubar da ciki kawai kar mutane su sani,tun bata da aure,da maganar zubar da ciki Maman Jummalo hankalinta ya ɗan kwanta.
A ranar sukaje inda ake zubar da ciki na sirri,maƙudan kuɗi suka bada sai aka bata magunguna tasha tunda cikin nata ƙarami ne baikai a saka engine a makare tayin ba(Wa'iyazubillah🤔🤔🤔)
Haka suka dawo gida tayi tashan magani babu ƙakƙauwata,amma ikon Allah sai cikin yaƙi fita,har ya fara ɓullowa ana gani, haka suka zuwa a cire cikin amma likitan ya ce idan aka cire cikin Maman Jummalo zata iya rasa rayuwarta saboda yanayin mahaifarta mai rauni ce.Haka suka ƙi haƙura da yawan inda za'a zubda cikin,amma kamar haɗin baki duk inda sukaje magana ɗaya ce,Maman Jummalo zata iya rasa ranta.Wannan Kenan.
@ @@@@@@@@@@
A ɓangarensu Sa'eeda kuwa,babu abinda ke damunsu,ga karatun Sa'eeda nata tafiya abun sai sam barkha,shaƙuwarsu da Dr.Nabila kullum ƙara yawa take,ga Iman ma suna ƙawancensu mai tsafta babu munafinci a ciki.
Tun Sanda Sauban ya yaudari Sa'eeda taji ta tsani maza a rayuwarta,tunani take duk halinsu ɗaya ne babu bambamci.Kasancewar Exams ɗinsu na first semester 400 level ya kusa,kowani lecturer yana alla-alla ya gama lecturer ɗinsa ga ɗalibai ya huta,hakan ta faru ga Dr. Nabila.
Kasancewar yau Thursday kuma yau Dr. Nabila take shirin yima su Sa'eeda test,gudu take a titi babu ƙakƙautawa saboda tayi latti,wayar ce a gefanta take kukan agaji,tana tuƙin ta dau kiran
"Hello Abban Twins baidai har kun isa airport ɗin ba"
Mijin nata ne a can ya amsa da cewa
"Eh wallahi muna jira a kiramu ne,kinsan sai 11:00am jirgin namu zai tashi"
"Maa shaa Allah ya kaiku lafiyyyyyyyy"
Ƙkkkkkkkkkkkkiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiiii!!!! Motar Dr .Nabila tayi da ƙara kamin ta kusa bige wata mata da niƙaf a fuskarta tana sharan titi,taso kaucewa matar amma ina saida motar ta kwance a hannun Dr .Nabila haba tayi sama da matar nan,Allah yasa Dr. Nabila tayi saurin gyara kan motar da motar ta ƙarabi ta kan matar nan.
Da sauri tayi parking a gefen titin haɗi ta fitowa da sauri jiki na rawa ta nufa inda mutane suka taru a inda matar take,da sauri ta ce a dauki matar a saka a motarta su tafi asibiti, da sauri aka saka matar a motar Dr. Nabila suka nufi asibiti wanda daƙyar aka anshesu wai sai sun kawo police,direct emergency room aka nufi da matar wanda a lokacin niƙaf ɗin na a fuskar matar hankalin kowa baikai wurin a cire mata ba,wani wanda sukazo da Dr.Nabila a asibiti ya ɗau wayar matar don kiran makusantanta,ganin an rubuta *SANYIN IDANIYATA* da manyan haruffa yasaka shi kiran numban bugu ɗaya ana na biyu ta ɗauka tare da sallama
A ɓangaren Sa'eeda tun safe ƙirjinta ke bugu ta rasa dalili,har ta kasa haƙuri ta sanar ma Iman,sai Iman ta ce tayi ta addu'a in shaa Allah alkhairi ne,sai kuma yanzu ga kiran Umanta wacca tasan bata kiranta a wannan lokacin,cikin sanyi murna tare da tsoro ta amsa kiran
"Assalamu Alaikum"
A can mutumin bai amsa mata basaima ya sanar da ita mai wayar mota ta kaɗe ta yanzu tana asibiti
"Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un,Allahuma ajurni fi musibati wa'aklifni khairan minsa"
Cikin kuka ta tambayi wani asibiti ne,sanar mata yayi tare ta katse wayar,fadama Iman tayi Ummanta yanzu mota ta bigeta ashe shiyasa ƙirjinta yake bugu ɗazu,babu ɓata lokaci Sa'eeda da Iman suka nufi asibitin da aka sanar musu Umman Sa'eeda na can.
A ɓangaren Dr.Nabila kuwa,sai a lokacin ta tuna wayar na mota,da sauri ta ɗauka wanda taga missed calls ɗin mijinta yafi goma,kiransa tayi tare da sanar dashi abinda ya faru sannan yace suma baifi mintuna ashirin su tashi ba,sallama sukayi sai a lokacin aka fito da Umman Sa'eeda a gadon marasa lafiya,idanunta a rufe suke har ɗakin da aka kwantar da ita,Dr. Nabila ce ta kefe Umman Sa'eeda da ido babu ƙyaftawa,haka tabisu har ɗakin da aka kwantar da Umman Sa'eeda still idanunta na akan Umman Sa'eeda ƙirjinta da fat! fat,tana a wannan yanayin ne saiga su Sa'eeda sun bako ɗakin babu sallama turus sukayi ganin Dr. Nabila a ɗakin,itama da mamaki take kallonsu,cikin murya mai sanyi Dr. Nabila ta ce
"Umman kice wannan Sa'eeda"
"Eh malama"
Waro idanu tayi waje,idan ta kalli Umman Sa'eeda sai ta kalli Sa'eeda don tabbatar da abinda zuciyarta take rayawa game dasu,ai tuni Dr Nabila jikinta ya fara rawa tana kallon kowannansu lokaci guda ta ɗauko wayar,dailing numban mijinta tayi,shi kuma a lokacin yana gab da shiga jirgi,da mamaki ya kalli wayar,lafiya kuwa take kiransa yanzu duka-duka yaushe suka gama wayan,amsawa yayi da
"Hello darling hope lafiya"
Dr.Nabila da duk ta ruɗe ta ce mishi
"Abban Twins kazo asibitin nan yanzu don Allah"
Cikin mamaki yace
"Ban gane nazo asibiti yanzu bayan kinsan tafiya zanyi kuma mai muhimmanci..."
Katseshi tayi da cewa
"Ba tada muhimmanci yanzu Abban twins,na roƙeta kazo kaga abinda nagani da idona,wallahi ƙwalƙwalwata ta rikice,don Allah ka fasa tafiyan sai gobe ka tafi ................"
Mu haɗu a *BOOK 2* in shaa Allah don cigaba da jin wannan rikita-rikitar wanda zaizo muku bada daɗewa ba🙃🙃🙃🙃📚📚📚✍️✍️✍️
*Waye mijin Dr. Nabila da take cewa dole yazo yaga abinda ta gani??? Wai idan yazo mai kuke tunanin zai faru??? Mai yasa Dr. Nabila take kallon Umman Sa'eeda da Sa'eeda lokaci guda???*........
*Tofa🤔🤔🤔yanzu dai a Maman Jummalo da cikin boka Sankeru,koya zata kaya????*.....
*a tunaninku kwalbar nan bazata fashe ba har abada ko kuwa akwai wa'adinta indan Allaj yayi????*.....
****Ya zata kasance Shugabar ƴar lawuɗi Nusaiba????......
*Anya Maryam zata yarda da auran da Sauban zai ƙara kuwa???....kuma wani mataki kuke tunanin iyayenta zasu ɗauka idan sukaji za'ama ƴarsu kishiya ko kuwa???*......
*Wace ce Haj Zulfa'u sannan wani sirri ne tale ɓoyewa wanda bataso asani????*........
*Shin kuna ganin Sa'eeda zata samu wanda yafi Sauban ko kuwa????*
*Wasu abubuwa ne suka faru shekaru aru-aru da suka gabata???*........
*Alhamdulillah ala kulli Halin,anan na kawo ƙarshen littafina na ɗaya wanda na biyun yana nan tafe,in shaa Allah, in fatan kun ilmantu,kun nishaɗantu tare da wa'azantuwa a littafina na ɗaya,na biyun ma yana nan tafe wanda yake ɗauke da amsoshinku wa'inda na 'issafa da wa'inda ma ban lissafa ba in shaa Allah, ina godiya sosai da goyon bayan da kuke bani ta hanyar like,comments da luma sharing,ina matuƙar alfahari daku my Esteem fans,Allah yabar ƙauna,sai mun haɗu a BOOK 2 in shaa Allah*💖💖💖💘💘💘🌼🌼🌼🌹🌹🌹🌹🙃🙃🙃🙃✍️✍️✍️
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.