Showing 51001 words to 54000 words out of 55707 words
Chapter 18 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
duk Sa'eeda ta tattarasu amma saboda wani dalili wanda baikai ya kawo ba,ka wofantar da damarka Sauban"
Shiru Sauban yayi yana sauraron abokinsa,wanda sai yanzu yake gane kuskuransa,tabbas yayi wasa da damarsa,sauke ajiyar zuciya yayi kafin ya ce
"Duk abinda ka faɗa Fu'ad gaskiya ne,na riga na ɓata rawata da tsalle,sai yanzu na gane illar da kake nunin abaya amma nayi burus da shawararka,yanzu dai nothing we can do tunda is already a past"
"Hakane,yanzu wacece Mom ta baka shawarar da aura "
"Cousin sister ɗina ce wacca take a Malaysia tana karatu,yanzu haka baifi watanni huɗu ya rage ta dawo ba"
*Waiwaye*
****Wata ɗaya da tafiyar Maryam,Mom ɗin Sauban ta kirasa har bedroom ɗinta,bayan ya shiga da sallama ya samu wuri ya zauna,cikin girmamawa ya gaisheta,ita kuma ta amsa masa cike da kulawa tana murmushi,shiru ɗakin yayi na tsawan wasu seconds duk a lokacin idanun Momin Sauban yana kan Sauban ganin ya rame sosai,gashi ba annuri a tattare dashi,gyaran murya tayi sannan ta kira sunansa cikin sassayyan murya
"Sauban"
Gaban shi ne ya faɗi jin irin wannan kiran sunan da ta masa,domin idan Mominsa tanason ta faɗa mishi wata muhimmiyar magana,sunansa take fara kira cikin sanyin murya.Dagowa yayi yana kallonta tare da cewa
"Na'am Mom"
Cikin muryar damuwa ta fara magana
"Yanzu haka Sauban ka koma? Duk ka rame kayi baƙi,ko baka da lafiya ne?"
Girgiza mata kai yayi alamun a'a sannan ta cigaba da cewa
"Sauban wata shawara na kawo maka kuma na tabbata mai ɓullewa ce da yardar Allah"
"To Mom ina sauraranki"
Ci-gaba da maganarta tayi tana cewa
"Aure nake so ka ƙara Sauban,tunda ita waccan batasan mai yake me yake mata ciwo ba"
Daramm! Gabansa ya faɗi jin wani sabon tashin hankali,ba wai bayason ƙara aure bane,a'a da wuri haka ko shekara ɗaya ba suyi ba,cikin girmamawa ya ce
"Momina da wuri haka,nifa ko budurwa banda ita yanzu"
"Da wuri kuwa Sauban tunda ba samun kulawa kake wurin Maryam ba,hasalima ban ga amfanin auran ba tunda ana yinsa ne don samun natsuwa,amma kai sai akasin haka,yanzu dai akwai Khairat ƴar wajan Auntynku Habiba wacca take karatu a malaysia,tana da hankali da natsuwa ga ilimin addini dana boko,ita naso ka aura tun farko amma ka nuna kai Sa'eeda kakeso wanda ni sai yanzu nagane ashe makirci Haj.Labara ta ƙulla don ka auri ƴar ƙwantarta,gashi dai yanzu aure baiyi riba ba hasalima faɗuwa aka samu,zan baka numbanta ku daidaita kafin ta dawo tunda ta kusa kammala karatun nata"
"To Mom ba damuwa,Allah yasa hakan shi ne mafi alkhairi"
Daɗi ya kama Momin Sauban jin ɗanta ya karɓi shawarata,murmusawa tayi sannan tace
"Allah ya maka albarkha,yasa ƴaƴanka sumaka biyayya irin yadda kamin kuma kake faranta mun rai,Allah yasa ta zamo sanyin idaniyarka tare da farin cikinka"
"Aaaameen ya Hayyu ya Qayyum"
Tashi yayi haɗi da mata sallama ,yasan khairat farin sani,tabbas ba ƙarya tanada tarbiyya sosai da natsuwa, haba sai yanzu yaji hankalinsa ya fara dawowa jikinsa.
Tunda ya amshi numban khairat soyayya ta ƙullu a tsakaninsu,babu laifi akwai natsuwa a tattare da ita.*****
*Cikin labari*
Bayan Sauban ya gama faɗawa Captain Fu'ad yadda sukayi da Mominsa harda soyayyarsa yanzu ta ƙullu a tsakaninshi da Khairat, ya wuce gida.
Kwana uku da zuwansa gidan Captain Fu'ad sai ga Maryam ta shigo gidan kamar an jefota,a lokacin yana falo ya baje abincin da yayo takeaway ɗinsa yana ci.Sallama tayi ta shigo tare da akwatinta,babu yabo babu fallasa ya amsa sallamarta ya cigaba da cin abincinsa hankalinsa kwance.Kasa haƙuri Maryam tayi ganin yadda bai nuna yayi maraba da zuwanta ba ta ce
"Haba Sauban ko sannu da zuwa babu"
"Oooh sorry,sannu da zuwa"
Ƙara maida hankalinsa yayi ga abincinsa,sai can ya ce
"Hope kin gyara halin naki da nace ki gyara"
Kallonsa tayi da mamaki wai halinta,to ita wani hali take dashi da zata gyara mtsw! Sai kuma can ta ce
"Na gyara shikenan"
"Better"
"Wai Sauban wani irin wulaƙanci ne haka,jiba yadda kake amsamin magana babu kulawa haba"
Cak ya tsaya daga cin abinsa,sai ya ɗago yana kallonta ƙasa da sama a zuciyarshi yana cewa 'Wai me wannan take dashi da na dage sai na aureta,gashi babu abinda na mora sai wahala,damn it! ' katse mishi tunani tayi da cewa
"Ko zuwa gidanmu bikona bakayi ba,gashi ba kira a waya balle nasan ka damu dani,yanzu kuma na dawo ko maraba ba kayi da zuwana ba,wai miye haka,nima fa shegiyar kaina ce wallahi,bar ganin kana duka na ina ƙyaleka,kaci darajar son da nake maka ne wallahi"
Wannan karon miƙewa yayi yana mata wani shegen kallo irin na in kin isa,sai kuma ya saki ƙyayataccan murmushi yana kallonta kamar bazaiyi magana ba sai kuma ya ce
"Darajar so huhhh!!! Kina sona ne kike zagin Mom ɗina? Kina sosa ne kike ƙin abinda nake so? Kina sona ne kike faɗamin baƙar magana,haka ake so a garinku? To bari kice gwara na sanar miki tun yanzu karki ce na munafin ce ki AURE ZAN ƘARA"
Darammm!!! Dammm!!! Darammmm!!! Tashin hankali wanda ba'asa mai rana,zuciyar Maryam ce ta tsinke lokaci guda,ƙwaƙwalwarta ta tafi hutun wucin gadi na wasu sakanni,kirjinta dukan tara-tara ya fara bama uku-uku ba,dafe ƙirjinta tayi da hannu bibbiyu tare da waro idanunta waje tana cewa
"Kishiya Sauban zakamin!!! "
"Ƙwarai kuwa Maryam"
Ai wani irin daka tsalle Maryam tayi,haɗe da cira gyalanta da ɗan kwalinta lokaci guda tana cewa cikin masifa da bala'i har idanunta sunyi ja
"Kan bura Uban can!!! Wallahi tallahi baka isa ba!!! Yau akwai bala'i a gidan nan!!! Yau akwai yaƙin duniya na uku a gidan nan!!!...............
Mu haɗu a pages na gaba don jin wannan Chakwakiyar chakwalkwalin da yake faruwa a gidan LOVE BIRDS wato🕊️🕊️🕊️ Sauban da Maryam😂😂😂😂✍️✍️✍️
*****shin su Umma Kande da Maman Jummalo sunyi nadama ko ko har yanzu akwai sauran rina a kaba???......
*****Shin mai yasa Dr Nabila take kyautatawa Sa'eeda sannan wasu abubuwa takeso ta tabbatar game da Sa'eeda???......
****shin Maryam zata yarda Sauban ya ƙara aure kuwa,ganin yadda ta haukace lokaci guda???......
Kai! Kai! Kai! Abubuwa da yawa🙃🙃🙃,amsoshinku na nan tafe a pages masu zuwa,kudai ku cigaba da zubo ruwa comments da reactions🌹🌹💖💖🌼🌼💘💘,ni kuma bazan gaji ba wurin suburbuɗo muku new updates zafafa🌹🌹🙃🙃💖💖🌼🌼💘💘😂🔥🔥🔥🔥🔥
Ina ƙaunarku My Esteem Fans Lodi Lodi🌼🌼💖💖🌹🌹🙃🙃💘💘
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[5/23, 8:09 AM] Narnarhh Bukar: 🏵️ NACINA YA JAWO MIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹*PERFECT ESSENTIAL WRITER'S ASSOCIATION*🌹
✨ *P. E. W. A*✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
3⃣9⃣----4⃣0⃣
Darammm!!! Dammm!!! Darammmm!!! Tashin hankali wanda ba'asa mai rana,zuciyar Maryam ce ta tsinke lokaci guda,ƙwaƙwalwarta ta tafi hutun wucin gadi na wasu sakanni,kirjinta dukan tara-tara ya fara bama uku-uku ba,dafe ƙirjinta tayi da hannu bibbiyu tare da waro idanunta waje tana cewa
"Kishiya Sauban zakamin!!! "
"Ƙwarai kuwa Maryam"
Ai wani irin daka tsalle Maryam tayi,haɗe da cira gyalanta da ɗan kwalinta lokaci guda tana cewa cikin masifa da bala'i har idanunta sunyi ja
"Kan bura Uban can!!! Wallahi tallahi baka isa ba!!! Yau akwai bala'i a gidan nan!!! Yau akwai yaƙin duniya na uku a gidan nan!!! Yau akwai tashin bama-bamai a gidan nan!!! Ni Sauban zaka ci amana tare da yimin kishiya,mene ne bana maka a gidan nan,aikin da ko a gidanmu banayi amma a gidan shi nakeyi,nace ka kawo ƴar aiki kace a'a,still na haƙura duk don saboda soyayyar da nake maka Sauban,amma da kishiya Sauban zaka sakamin,da kishiya, kishiya fa Sauban, inaaaa wallahi bazata saɓu ba bindiga a ruwa,banzan yarda ba wallahi,ban taso gidanmu naga Mom ɗina da kishiya ba,haka duka familinmu baki ɗaya babu mai kishiya saini wacca ko shekara ɗaya banyi ba,Wallahi baka isa ba Sauba......."
"Dallah malama kin cikani da hayagagarki wacca babu abinda zatasa balle ta hana,ke kin isa ki hanani aure ne,yooo ke awa awani dalili,you are just nothing for nothing in the absence of nothing in terms of nothing stupid human being,Mahaukaciya kawai"
A hargitse shima ya taso mata don yaga alama hauka take shirin yi masa,hala kuws domin idanunta duk sun kaɗa sunyi ja,ga kannan nata duk ya yamutse saboda matsifar da take cinta,dole ya taka mata birki,shi yama rasa waca ƙaddara ce ta sakashi auran wannna jalilar da batasan komai a zaman aure ba.
Rashin nasani hausawa suka ce yafi dare duhu domin da Sauban yasan abinda zai ɓallowa kansa da baima ko fara fada zai mata kishiya ba saboda hauka tuburan Maryam ta fara,tare da kururuwa tana cewa
"Yi huhu!!! Wallahi baka isa ba Sauban!!! Yau zan nuna maka ni cikakkyiyar mahaukaciya ce wacca take da cerficate a psychiartry mai tambarin shugabar mahauka mata a Nigeria yeeeeee!!! Tabbas ni mahaukaciya ce a sonka da ƙaunarka kuma ban yarda wata ta raɓeka da sunan soyayya ko kuma na illata rayuwarta gaba ɗaya!!! Yi huhu ni Maryam mahaukaciya!!! Mallahi saina nuna maka cikakkyar mahaukaciya ce mai certificate yanzu nan!!!
Ai bata jira mai zaice ma ta fara watsi da abubuwan da yake a falon kama daga flower vest,show glasses,television,centre table da dai sauransu,tabbas Maryam ta kwance kamar yadda ta faɗa,domin mai hankali da tunani bazai fara kwatanta irin wannan haukan ba da sunan kishi.Sauban mutuwar tsaye yayi ganin irin aika-aikar da Maryam take yi,tabbas ta hauka ce saboda yadda take watsi da kayan falon zai tabbatar maka ba'a hayyacinta take ba,anya bata da aljanu kuwa,idan fa ta taka wani uban tsalle kamar wata buriya zata sauka akan abinda tayi niyyar tarwatsawa,sai dai kaji Tatsatsa!!! Tas!!! Ɓas!!! Kas!!! Ya tabbata yaƙin duniya na uku ake a gidan Sauban,ko'ina na ɗakin ya birkice hatta curtains ɗin ɗakin basu tsira a hannun Maryam.
Sauban da yaga alamun tabbas noties ɗin kan Maryam sun kwance yayi saurin cafkota habawa wani gagarumin dambe suka kacame dashi,yana riƙita tana dukansa haɗe ta yaƙushinsa tana cewa
"Kasakeni in cigaba da aikina Sauban!!! Kasakeni!!! Sauban!!! Yau ake yaƙin duniya na uku a gidan nan!!! Saina tarwatsa gidan nan!!! Saina ƙona gidan nan!!! Sauban!!!"
Kamar mai almatsutsai haka Maryam ta koma,da bala'i yayi bala'i zuciyar Sauban takai maƙura haba tuni ya fara jibgarta kamar Allah ne ya aikosa,tun Maryam na iya ramawa har takai ko matsin kirki ta kasa,a fusa ce ya bar gidan baki ɗaya,Allah yasa ma Mom ɗinsa bata nan tayi tafiya lamarin ya afku da ko da ita za'ayi dramar saboda dole idan taji hayaniya ta fito ɓangarensu taji mai ke faruwa.
Sai dare Sauban ya dawo gidan,ko daya shigo falon samunta yayi a idan yabarta a kwance kamar bata motsi,da sauri ya isa inda take,tattaɓata yayi amma ina shiru da sauri jikinsa na rawa ya ɗauketa cak direct sai cikin mota,da sauri ya fizgi motar da gudu wanda har mai gadin saida ya tsorata dashi,gudu yake bisa titi kamar ya samu titin ubansa har ya isa hospital ɗin dake kusa dasu,direct nurses suka ɗauketa zuwa emergency room domin bata taimakon gaggawa.
Safa da Marwa Sauban yake domin ya kasa zama,ga uban gumi dake tsuttsugo masa a duk ilahirin jikinsa,tunani ne ya addabi ransa kala-kala,yama rasa wanne zai ɗauka ya fara,shin da tashin hankalin Maryam zai fara ko kuwa da aikinsa na office wanda tun sanda asalin mai company wato CEO ɗinsu yazo da wasu tsararraki masu tsauri ya daƙile handama da babakeran da Sauban da sauran ma'aikatan sukeyi,kasancewar CEO ɗin companyn nasu wayayye ne,ɗan boko kuma gogagge a harkar kasuwanci,wuta iya wuta,ga kuma auran khairat da immediately tana dawowa daga ƙasar Malaysia Mominsa tace za'a saka ranar auransu,tabbas ko ba'a faɗa ba kan Sauban ya ɗau caji sosai,shi saima yanzu yake ƙara da nasanin mai yasa ya auri Maryam bayan ga Sa'eeda mai hankali ga alkunya,wacca tasan girman naga ba da ita,kacona ni Sauban, nayi wasa da damana.Tunaninsa ne ya ɓace ganin likita ya fito daga emergency room ɗin,da sauri ya isa inda yake,likitan ne ya ce ya sameshi a office,babu musu ya bisa.
Bayan likitan ya zauna sai Sauban shima ya zauna zuciyarsa na dukan uku-uku,yana addu'ar Allah yasa babu wata matsala.Likitan ne ya dubesa tare da cewa
"Kwantar da hankalinka,ba wata matsala sosai,matarka was shock on something sannan kuma jikinta ya nuna alamun an duketa,su ne suka haifar mata da suman har na tsawan lokaci,amma Alhamdulillah she is under treatment zuwa nan da kwana biyu ko uku zamu sallameta saboda sai mun bata gado gaskiya"
"Ok Doctor,ina godiya sosai"
"Karka damu aikinmu ne,yanzu zan rubuta mata wasu allurorai tare da magungunan da zaka siya a pharmacy"
"Ok toh"
Rubuta masa abubuwan da zai siya yayi a paper sannan ya miƙa masa,fita yayi zuwa pharmacy ya siyo maganin tare da allurorin sannan ya tambayi wata nurse da a lokacin daya kawo Maryam tana daga cikin nurses ɗin da suka kai Maryam emergency room,ya tambayi ina ne room ɗin da aka kwantar da ita,direct ta kaishi har ɗakin sannan tayo gaba abinta.Shiga yayi ɗakin da sallama sannan ya duba ta ,sai kuma ya fito saboda yanaso yaje gida ya ɗauko musu kayan da suke buƙata a asibitin.Wannan kenan
@@@ @@@@@@
*ABUJA*
A ɓangaren Haj. Zulfa'u kuwa,hankalinta yanzu ya kwanta sosai saboda tama tifkar hanci sannan ta dage Daddyn Fadila ya bana ɗan aminsa da yake sonta aure saboda ayi-ayi auran kowa ya huta,babu musu yabi shawararta saboda shima kansa yafi amincewa Fadila ta auri yaron abokinsa Ambassador.Ranar biki aka saka wanda ba a ɗau lokaci mai tsayo ba just in 5 month coming,hakan yama Haj. Zulfa'u daɗi a rai domin koba komai asirin da ta daɗe tana ɓoyewa bazai tonu ba saboda idan Fadila tayi aure shikenan wani ɓangare na matsalarta ta kau,saura kuma ɗayan wanda kullum dashi take kwana kuma dashi take tashi wato arangama da tsatson maƙiyiyarta,wannan abu naci mata tuwo a ƙwarya idan ta tuna,gashi batasan wace hanya zatabi wurin ganin hana faruwan wannan matsalar ba irin na Fadila, kullum cikin taraddudi ta tsoro take,ta hana kanta saƙat,fita ma ta daina yinta yanzu duk saboda tsoran kar watara ta fita su haɗu wani bala'in ya hau kanta.
Bikin Fadila baifi saura wata Uku ba yanzu,shirye-shirye ne har an fara yinsa musamman Haj. Zulfa'u saboda ta ƙosa ayi-ayi auran hankalinta ya kwanta,an shirya bikin na gani na faɗa wanda yawanci abubuwan auran ba'a a Nigeria aka siyesu ba,gidan ma complete aka sake gyarashi.Haka sukayi ta shirye-shiryansu.
@@@ @@@@@@@@
*KEBBi*
Ilimi shi ne tubalin komai a rayuwa,sannan idan rayuwa ta kasance bisa tsari haɗi da ilimi to tabbas tasha bambam da wanda baya da ilimi tare da tsari a rayuwarsa.Sadam Dauda Gali Mai Nasara yazama tauraro a cikin matasan Kebbi state masu ji da kuɗi da ilimi, domin cikin ƙanƙanin lokaci tauraronsa ya haska saboda a komai nasa zaka samesa yana aiki da lokaci,baya wasa da lokaci,komai nasa a rubuce yake kama daga cin abincinsa,fitarsa kasuwancinsa da komai nasa a tsari yake shiyasa a lokacin da Daddyn ya ɗanƙa mishi ƙaddarorinsa ya ƙara maida hankalinsa kacokan a harkar kasuwancinsa,wanda yanzu ƙaddarorinsa sun ƙara yawaita kama daga companies,plazas,petroluem companies harda gidajen gona wanda bai daɗe da siyansu har uku manyan-manya ana noma kayan lambu,kiwon kifi,kaji,talo-talo,geese,da dai sauransu ana fitar dasu zuwa ƙasashen waje, duk fa a tsakankanin watanin da Daddynsa ya bashi ƙaddarorinsa ne.
Bangaren soyayya tuni Sadam ya ajiyets,bama ya kallon ƴan mata balle wata ta birgeshi ya ce zai aura,lokacinsa kawai na kasuwancinsa ne,don har P.A garesa da bodygaurds masu kare da lafiyarsa,kuma duk inda yaje suna nan tare dashi.Mominsa tasha mishi magana akan yaushe zaiyi aure,amma amsarsa a kullum ita ce shi baiga yarinyar da ra'ayinsu yazo ɗaya ba,ko a lokacin da yake tare da Fadila saboda darajar Sadiq abokinsa ne yasa ya aminta ya soyayyarta ba dan yana son ba,babu yadda Mom ta iya,haka ya ƙyalesa.
Kamar yadda kuka sani duk babbar Sallah familin Alhaji Kabir Dikko suna family meeting don magance matsalolinsu,wannan karon da Sadam akayi family meeting ɗin,harda ƴan Kaduna wato Dr. Nabila da mijinta wanda auran dangi ne aka musu.A nan ne Dr .Nabila take ma Sadam tsiya akan baya da mutunci a ce yana zuwa Kaduna amma ko sau ɗaya bai taɓa cewa zaizo gidanta ba koda da wasa ne,hakuri yayi ta bata akan in shaa Allah idan ya shigo Kaduna zaizo gidan yamayi kwana biyu,duka familyn sai dariya suke musu ganin yadda suke drama kamar ba ɗa da uwa bane.Haka taro ya tashi bayan anci ansha an gwangwaje.Wannan kenan.
@@ @@@@@@@@@@
*KADUNA*
A ɓangaren su Umma Kande da Maman jummalo sun ƙara komawa gidan jiya,domin haka kurin bazasu bari gulmar layi ta kashesu da ransu ba,dole su samo mafita kuma mafitar ɗaya ce wato ƙara komawa gun boka Sankeru don tuntuɓar ko basuyi yadda ya umurcesu bane,sannan da ƙara nemama yaran nasu wasu mazajen daban.(Oooo! Su Umma Kande da alama wahala bata ƙare musu ba kenan😂😂😂🙃🙃🙃).
Kasancewar jiya asabar sukayi shawarar,yau suka buga uban sammaka direct sai tasha,bayan sun sauka a mota sai suka hau machine su biyu,haka a ɗaukesu har gefan dajin inda zai sadasu da wurin boka Sankeru.Bayan ya saukesu suka nufa dajin a ƙafa har bukkar boka Sankeru,Allah yasa yau babu layi sosai mata uku ne a gaban su.lokacin da layi yazo kansu suka shiga ciki a tare .Kamar yadda suka saba mai kirari haka sukayi.
Kamar walƙiya haka ya ɓullo cikin bukkar daman daya gama aiki yake ɓacewa sai kuma idan wasu sunzo sai ya sake bayyana.
Bayyanarsa keda wuya ya tsintsire da wata mahaukaciyar dariya,tumbinsa sai jijjiga yake,su Umma Kande da Maman Jummalo kansu a ƙasa har ya gama dariyarsa sannan ya dubesu dakyau musamman Maman Jummalo na tsawan lokaci sannan ya fara magana cikin amon muryarsa mai firgitarwa
"Nasan Zaku dawo la'anannu!!! Nasan Zaku dawo dangin shayɗanu !!! Kun yarda da shaydanu irinmu hhhhhhhh!!! Ba kuyi kuskure a aikin da nasaku ba saidai ku kuka zaɓama yaranku mazaje !!! Kun nasar damu kuna son yaranku su auri mazaje kowani iri shiyasa muka basu mazaje kowani iriiiiii!!!! "
Har yanzu su Umma Kande babu wacca a cikinsu ta ɗago kanta balle tayi magana,cigaba da maganarsa yayi
"Karku damu tunda kun yarda damu!!! Zamu baku kwalli su shafa gobe da safe idan zasu fita!!! Na tabbata komai yazo ƙarshe!!! Zasuyi aure ba irin wancan ba !!! Zasuyi aure tabbas! Tabbas! "
Yana gama magana yayi wata jijjiga kamar wani alade tare da sakin wata uba-uban tusa mai ɗoyin gaske,tuni suka toshe hancinsu saboda warin kamar mushe