Showing 39001 words to 42000 words out of 55707 words

Chapter 14 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt

31 May 2024

8058

kai so da ƙaunar da kike ma karatunki,ina yake Sa'eeda,yanzu duk wahala da nasha babu ko sisin mahaifinki akan karatunki zai tashi a banza kenan Sa'eeda,sakayyar da zakimin kenan a matsayina na mahaifiyarki wacca bata da wani buri illa ganin rayuwarki ta ginu,ban damu da ci ko sutura mai kyau ba duk ganin rayuwarki ta ginu amma aaaam.........."




Fashewa tayi da matsanancin kuka harda shessheƙa,da sauri Sa'eeda da dawo hayyacinta daga tunanin da da nasanin faɗawa mahaifiyar wannan magana,cikin rawar murya Sa'eeda ta fara magana cike da dana sani




"Ummina kiyi haƙuri don Allah ki daina kuka,wallahi na haƙura zan cigaba da karatuna Ummina, ki yarda dani Ummina"




Girgiza mana kai Umman Sa'eeda tayi tare da cewa




"A'a Sa'eeda shikenan ai sai ki haƙura da karatun naki,saboda wasu wa'inda basu suke baki ci da sha ba kikeso ki rushe tsarin ginin rayuwarki Sa'eeda, saboda wani can banza wanda baisan kina sonsa ba kikeso ki lalata rayuwarki Sa'eeda, ina juriya da jarumtar dana sanki da ita,ina kika kaisu Sa'eeda!!! "




Tabbas maganganun Umman Sa'eeda ya ratsa ƙashi har zuwa ɓargon Sa'eeda sannan ya shiga kusufa-kusufa na jini dana jijiyar Sa'eeda tabbas yanzu zata dawo da NACINTA a karatu,sannan tana saka ran NACINTA ZAI JAWO MATA NASARA,dole ne ta farka daga nauyayyen bacci da take,dole ne ta iya fuskantar kowani irin ƙalubale a rayuwarta,cikin dakiya tare da tabbatarwa Sa'eeda ta fara magana




"Na ɗau miki alƙawari Ummina, zan dawo da juriya da jarumtar da kika sanni da ita,zan kasance jaruma mai fuskantar kowani irin ƙalubale da zaizo min a rayuwa,zan dawo da NACINA domin zai JAWO MIN NASARA babba a rayuwata,ki yarda dani Ummina,daga ranar irin ta yau na cire so da ƙaunar da nikewa Sauban a zuciyata,bazaki sake jina da maganar Sauban ba koda shi ne autan maza,in shaa Allah zan cigaba da addu'ar Allah ya zaɓamin wanda ya fisa zama alkhairi a rayuwata"




Jinjina kai Umman Sa'eeda tayi saboda ganin gaskiya tare da tabbatuwa a cikin zantuttunkan ƴarta,murmushi ta saki sannan ta ce




"Dakyau sanyin idaniyata,haƙiƙa naji daɗin cire Sauban da kikayi a zuciyata sannan da maida hankalinki da zakiyi a karatunki,Allah ya miki zanbin miji na gari mai sonki da ƙaunar,ya baki nasara a karatunki,ya tsare gabanki da bayanki,ya miki katangar ƙarfe tsakaninki da maƙiyanki,ya albarkaci rayuwarki baki ɗaya"




"Allahu Aaaamen Ummina, in shaa Allah daga yau kin daina kukan baƙin ciki a kaina saidai na farin ciki"




"Allah ya yarda sanyin idaniyata"




Haka suka cigaba da hirarsu cike da annashuwa kamar ba wani ɓacin rai mai samesu ba,tun daga ranar Sa'eeda tayi deleting contact ɗin Sauban,messages ɗinsa,hotunansa,da komai nasa a wayarta sannan ta ƙara bada himma a kan karatunta saboda exams ɗinsu baifi saura kwana biyar ba.Wannan kenan.














TUNATARWA








******Ƙalubali ga mata masu makauniyar soyayya,kusani wasu mazan suna amfani da wannan damar ne don su cimma wata manufa tasu a gareku saboda suna ganin baza ku iya rayuwa babu su ba,tabbas wannan hanya ce dayawa daga cikin maza suke amfani dashi wurin lalata rayuwar mata wanda daga ƙarshe zusa wulaƙantasu,su ɓata tarbiyyar ta iyayensu suka daɗe suna ginawa,mu kula ƴan uwana mata,Allah ka tsaremu da samari shaho,ka haɗamu da masoyanmu na gaskiya.




Ƙalubale ga mata masu bayyana sirrikansu da ƙawayen,kamar caka ma kanka wuƙa kake ba tare da kasani ba domin wasu ƙawayen ba tsakani da Allah suke tare da suke,bayan haka ma ɗan Adam yakan canja daga yadda kasansa,mu kula ƴan uwana mata,Allah mana tsari da ƙawayen banza masu nuna suna son a bayyane amma a ɓoye suna sukarmu******






@@ @@@@@@@






Ɓangaren Sauban sai shirya-shiryan bikinsa yake yama manta da wata Sa'eeda a rayuwarsa hasalima komai nata ya gogeshi a wayarsa,hankalinsa kacokar ya koma kan Maryam saboda a ganinsa tafi Sa'eeda wayewa gashi bata da asili.




Kasancewar yau asabar saura ƴan kwanaki bikinsa,yana zaune shida da amininsa Captain Fu'ad suna tattaunawa game da bikin wanda Captain Fu'ad ya gaza haƙuri saida ya yayi masa magana saboda abin na ci masa tuwo a ƙwarya




"A gaskiya Sauban bazan ɓoye maka ba,kaci amanar Sa'eeda wallahi,mai tayi maka da zaka mata irin wannan muguwar sakkaya,in fact bama kai kaɗai harda wacca zaka aura,guna ganin kun mata adalici ne musamman ma kai"




Taɓe baki yayi irin ko a jikinsa ɗin nan, a da baiso tanka masa ba sai kuma yace




"Naci amanarta huhhhh!!!,mai zanyi da marar asali wacca bata waye ba,kai ko ɗan taɓa hannun Sa'eeda ban taɓa yi ba,common outing Sa'eeda bataso wai sai munyi aure,haba i'm tired of her stupidity "




Girgiza kai Captain Fu'ad yayi tare da cewa




"Marar asali kuma,bata da mahaifi ne?"




"No tanada mahaifi saidai mamanta da kakarta tsintarsu akayi a titi suna gararamba"




"Innalillahi Wa'inna Ilahi Raji'un yanzu saboda wannan ne yasa ka fasa auranta Sauban,ina hankalinka da tunaninka ya shiga ne,who knows asiri akama kakarta ko kuma ƴan gudun hijira ne,haba Sauban wallahi kaban mamaki,tukunna ma waya faɗa maka bata da asali"






"Ƙawar Mum ce sannan kuma Aunty Maryam ta sanar mata hakan kuma kasan ba ƙarya zata faɗa ba"




"Mata! mata! Akwai makirci wallahi, yanzu in mum ta kasa gane makirci ne suka ƙulla don ka auri Maryam kai bazaka iya hankalta ba Sauban"




"Mtssss! Don Allah mubar zancen nan mukoma yadda zamu tsara bikin kaina ma harya fara ciwo"




"Dawa Allah ya sawwaƙe ni Fu'ad na zauna don aci amanar wata,Allah ya kiyaye,ai tunda nasan dalilin rabuwarka da Sa'eeda wallahi kaji na rantse bazaka ga ƙeyata a bikinka ba domin ni ba mayaudari bane"




Sauban kallon Captain Fu'ad yake da mamaki sai kuma yace




"Mai zai hana ka aureta mana sai ka tusa mana baƙin ciki"




Dariya Captain Fu'ad yayi sai ya ce




"Wallahi da badan ansa ranar aure na ba da kuwa babu abinda zai hana na aureta saboda she is complete"




"Can ta matse maka"




"Kasani Allah baya barin hakƙin wani akan wani,kaji tsoran Allah Sauban, kasan yanzu wani hali take ciki dul saboda kai,in shaa Allah sai Allah yabata wanda ya fita komai wallahi kuma muna nan dakai"






Fuuuuuuu ya ɗau makullin motarsa ya ƙara gaba ba tare da yama Sauban Sallama.wannan kenan






@@@@@@@@






Ɓangaren Umma Kande ita da Maman Jummalo komai na tafiya musu normal,kamar kullum yau ma suna zaune a kan tabarma suna hirarsu cike da annashuwa kawai sukaga mutum ya faɗo cikin gidan babu sallama, haba da sauri suka miƙe dukansu,cikin tashin hankali Maman Jummalo tace






"Ni Hasfy wazan gani haka babu ɗan kwali balle hijabi,meya sameki....................






Mu haɗu a pages na gaba domin cigaba da suburbuɗo muku wannan cakwakiyar labari🙃🙃🙃💘💘💘💖💖💖✍️✍️







*****tofa,wacece a cikin yaranya su Umma Kande ta shigo babu ɗan kwali balle hijabi












Ku cigaba da zubo ruwan comments🤗🤗🤗🙃🙃🙃💝💝💝,Ni kuma bazan gaji ba wurin suburbuɗo muku da zafafan updates wa'inda zasu nishaɗantar,ilmantar tare da faɗakar daku🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️








Ina matuƙar alfahari daku my Esteem fans,Allah yabar ƙaunar🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️💖💖💗💗💓💓




















Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️


Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[5/23, 8:09 AM] Narnarhh Bukar: 🏵️ NACINA YA JAWO MIN🏵️















Narrnarhh Bukar✍️












🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨












Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002


















Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
















🌹🌹🌹I'm not born to be a writer but born to be a great professional writer✍️✍️✍️🙃🙃🙃🌹🌹🌹














🌼🌼🌼Special greetings to y'll my Esteem Fans🙃🙃🙃💖💖💖🌼🌼🌼
















3⃣3⃣----3⃣4⃣












Ɓangaren Umma Kande ita da Maman Jummalo komai na tafiya musu normal,kamar kullum yau ma suna zaune a kan tabarma suna hirarsu cike da annashuwa kawai sukaga mutum ya faɗo cikin gidan babu sallama, haba da sauri suka miƙe dukansu,cikin tashin hankali Maman Jummalo tace






"Ni Hasfy wazan gani haka babu ɗan kwali balle hijabi,meya sameki Jummalo? "




Wuri-wuri takeyi da idanunta kamar wata motsattsa,gata tayi baƙi sosai kasancewar bleaching take,yanzu babu kwanciyar hankali balle a shafa cream😀.Maman jummalo ce ta riƙo hannun Jummalo da sauri Jummalo ta fizge hannunta tana ja da baya tare da girgiza kai hawaye na zuba a bisa kuncinta ta ce




"A'a! A'a! Karki taɓani mama,wallahi nayi da nasanin zamowarki uwa a gareni,baki bani tarbiyya mai kyau ba,kin ɗorani akan turbar son abin duniya da dogon buri,gashi tun a daren farkona naaa........."




Bata ƙarasa abinda tayi niyyar faɗa ba Umma Kande tayi saurin rufe mata baki,ita kuma Maman Jummalo ta jata ɗaki har uwar ɗaka tare da rufo ƙofar har da jan labulan windo don kar ajisu,suna shiga ɗakin Jummalo ta ƙara fizge hannunta daga hannun Maman Jummalo don yanzu ta ɗau ma kanta alƙawarin baza da sake biye musu sukaita ga halaka,zama Jummalo tayi akan gado su kuma suka zauna kusa da ita duk hankalinsu a tashe.Lokaci guda ta fashe da matsanancin kuka harda shassheƙa,bata jira mai zasu ce ba tara magana cikin shassheƙan kuka mai ratsa zuciya




"Nayi nadama tafi dubu,nayi da nasani tafi cikin kwando,kaicona da biyewa ruɗin duniya,Mama kin cuce rayuwata,kin cuceni Mama,baki bani tarbiyya mai kyau ba,Allah sarki babaaaa naaaaa!!!........."




Ƙara sakin wani sabon kukan tayi mai ƙarfin gaske,Umma Kande ce tace ta rage sautin muryarta kar ajisu,galla mata harar tayi sannan ta cigaba da maganarta,ita dai Maman Jummalo kallon ƴarta take babu ko ƙiftawa saboda muguwar ramar da tayi,ga wani mugun baƙi da tayi kamar baƙin tukunya.






"Tun ranar da aka kaini gidan aurena,a ranar na fara fuskantar baƙin ciki da tsangwama,ga duka,zagi,tozarci,aikin wahala duk babu wanda bangani ba a zaman aurena,kullum cikin baƙin ciki da da nasani nake akan biye muku,Allah ne yanzu ya kuɓutar dani,kuma daga yau bazan sake biye muku ba sannan su Zaliha da Iklima ku gaggauta zuwa ɗaukosu saboda nasan suna cikin halin dana tsinci kaina a ciki,kuma ku jini dakyau wallahi na daina biye muku ,sannan Islamiya zan koma in shaa Allah"






Miƙewa tayi ba tare da ta kallesu ba ta fito falon ta ɗau buta don zagayawa,su kuma su Umma Kande binta sukayi da kallo,sai can Umma Kande ta fara magana cike da damuwa






"Mun shiga uku ƙawas,anya ba zuwa zamuyi muga halin da su Zaliha suke ciki ba"






"Hmmmmm ni nama kasa magana wallahi don bansan me zance ba Ƙawas,kinsan me kawai gobe da sassafe mu shirya muje gidan nasu,inta kama ɗaukosu zamuyi kawai mu ɗaukosu,ji yadda Jummalo ta kuma don Allah"






"Allah ya kaimu,a gaskiya hankalina yayi ƙololuwan tashi ganin Jummalo a irin wannan hali,amma a gaskiya boka Sankeru bai mana adalci ba,ai ba haka mukayi dashi ba,daga munce munason yaranmu su samu mazaje masu kuɗi kawai zai haɗasu da bala'i,kai kai kai ni Saratu jikar sarkin ruwa munga takanmu"






Haka sukaita jimamin abinda ya samu yaransu,Jummalo kuwa zama tayi ta basu labarin tun daga daren auranta har zuwa yau da wuya tasata barin gidan afujajan babu ɗan kwali balle hijab.Umma Kande ta shiga tashin hankali tare da zullumin su Zaliha da Iklima ko a wani hali su kuma suke ciki da mazajen nasu,idan ita Jummalo mai shan giya ne mijinta su kuma fa gashi daman suna son saka ranar zuwa gidan kowaccansu saboda basu taba zuwa ba,sai gashi kan susa ranar zuwa Jummalo tazo musu da labarin da ya kirkita musu ƙwaƙwalwa tare da lissafi.








@ @@@@ @@@@ @@@@






Ƙarfe 9:45am na safe su Umma Kande da Maman Jummalo suka shirya tsaf don zuwa gidajen su Zaliha, Umma Kande ce ta bada shawarar su fara zuwa gidan autarta Iklima sai daga baya su zarce gidan Zaliha, haka kuwa akayi direct suka ɗau drop ɗin keke napep har gate ɗin gidan Iklima,basu sha wahala ba kasancewar layinsu Iklimar sananne ne.Bayan sun sauka daga keke napep ɗin, sai Maman Jummalo ta biya mai keke napep kuɗinsa sannan suka nufa gate ɗin gidan,babu laifi gidan hadɗaɗe ne ya tsaru iya tsaruwa,ga wasu flowers masu ban sha'awa an shukasu a gefe-gefan gidan masu launin orange colour da milk,kowannansu bakin buɗe yana kallon kyau da tsarin gidan wanda ya tafi da imaninsu,Maman Jummalo ce ta ce






"Kai gidan nan ya tsaru saikace a ƙasar waje?"






"Ke dai bari Ƙawas ni namá kasa cewa komai,don gidan nan ya tafi da sauran imanina"(Tofa Umma Kande ɗan sauran imanin naki gida ya tafi dashi tun kan ki shiga ciki,jahilci baiyi wallahi😂😂😂)






Ƙarasawa sukayi bakin gate ɗin gidan tare da ƙwanƙwasawa,shiru babu amsa,ƙara ƙwanƙwasawa sukayi,sai a sannan mai gadin gidan ya buɗe ƙofar,kallonsu yayi ƙasa da sama kafin ya ce






" lafiya,wa kuke nema"




Gyara tsayuwa Umma Kande tayi irin gamai ɗiya tana auran mai kuɗi ta ce




"Munzo ganin ƴar muce Iklima fatan dai tana nan"




Shiru yayi mai gadin yana kallansu sai can kuma ya ce



"Ina zuwa"




Bai jira mai zasu ce ba,ya juya tare da kulle ƙofar ya nufa ɗankinsa ya ɗauko waya haɗi da kiran mai gidansa,kira yakai sau uku yayi masa,sai ana huɗun ya ɗauka,cikin girmamawa ya fara gaida mai gidan nasa sannan ya ce






"Yallaɓai iyayen madam ne sukazo amma nace su jira sai na kirata"




A can mai gidan nasa ya bashi amsa da cewa




"Good,ka barsu su shigo,amma idan sun shigo tsakiyar gidan bayan ka kulle ƙofar sai ka sakar musu Pistol da Ninja su tayasu exercise"




"An gama yallabai"








Katse wayar yayi tare da sakin wani munafikin murmushi,har ya fara harsashen yadda zasu kaya da Pistol da Ninja.






Kamar yadda mai gidansa ya umurcesa haka yayi,bayan su Umma Kande sunkai tsakiyar gidan,sai ya kulle ƙofar gidan tare da nufar cages ɗin Pistol da Ninja,ya buɗe kowannan su,fitowa sukayi tare da girgiza jikinsu,manyan karnuka ne na turawa baƙaƙe,kumatunsu duk sun zazzago ga miyau da dalala,fuskar nan tasu a kwaɓe take,haba kamar jira suke,tunda sukayi tozali dasu Umma Kande suka nufo inda suke da gudu tare da haushi ganin baƙi a gidan.






Umma Kande da Maman Jummalo da basusan meke faruwa ba,suka ji haushin karnuka a bayansu,juyawar da zasuyi sukayi aran gama da jibga-jibgan kurnaka wanda tunda suke basu taɓa ganin irinsu ba,ganin kansu karnukan sukayo,habawa ƙafa mai naci ban baki ba,kowa sakin jakarsa yayi ya fara gudu,karnukan biyosu sukayi,gudu suke suna ihun a kawo musu ɗauki amma ina gidan shiru alamun babu kowa,Umma kande ce tana gudu tana da cewa






"Mun mutu mun lalace! Mun kawo kanmu ga halaka! Jama'a! Jama'a! A kawo mana ɗauki zasu cinyemu ɗanye! Wayyo ni Sarere jikar sarkin ruwa! Iklima dan Ubanki ki buɗe ƙofar! Iklima! Iklima! Auta! Auta buɗe mana ƙofar! Karnuka zasu cinyemu! Iklima!!! "




Haka tayita nanatawa tana gudu,zaninta ma da yaji wahala saida ya kwance,saukinta ma akwai skirt da abin ya munana kasancewar tana da manyan ɗuwawuka,sai saɓaɓar saɓaɓar suke tana gudun.Ita ko Maman Jummalo babu bakin surutu sai ihu,mai gadi dai na zaune akan benchinsa sai video yake musu yana dariya,saboda yadda suke ihun da gudun dole idan ka gani ya baka dariya,karnuka bisun suke babu ƙakƙautawa,idan sukeyi hagu suma suyi hagu haka idan sukayi dama suma suyi dama,abin gwanin ban dariya.




Iklima dake baccin wahala kamar a mafarki taji muryar mamanta tana kiranta ta kawo mata ɗauki,buɗe idanu tayi tare da sake jin tabbas muryar mamanta ne da Maman Jummalo suna ihu,da sauri ta sauko daga kan gaɗon ta nufo falo tana tafiya a gwale kamar wacca aka mata kaciya haka nufi wurin windonta tare da jaye labulan,zaro idanu tayi waje tana ganin yadda Maman Jummalo da mamanta babu zani a jiki suke shan gudu babu ƙakƙautawa ga karnuka na biye dasu a duk inda suka nufa suna haushi,da sauri ta buɗe ƙofar tare da kiransu Maman Jummalo da mamanta, ai a sittin sukayo ɗakin suma karnuka basu fasa binsu ba,saura ƙiris karnukan su shigo ɗakin,Allah ya taimake su Iklima tayi saurin rufe ƙofar ɗakin.




Su Umma Kande na shiga falon kowaccansu ta baje a ƙasa tana haki,ga uban zufar da take tsuttsugo musu a duk ilahirin jikinsu sai kace sunyi gudun kilometer 3 haka suke ji.




Iklima ce take bin kowaccansu da kallo,kallon ma irin na takaici sai kuma can ta ce




"Yanzu saboda ɗan wannan gudun da kuka sha kuke haki haka,Allah ya bani haƙuri nida kusan kullum sai maza sama da biyu sun afkamin ta gaba da ta baya"




Zaro jajayen idanunsu sukayi suna kallonta cike da mamakin furucinta,Maman Jummalo ta ƙara tambayarta don ta gasgata zancen nata




"Maza sama da biyu suke afka miki Iklima,to shi ina mijin naki? "




Taɓe baki tayi irin na autoci sannan ta ce




"Harda dashi ai,a daren farkona ma a ta duburana ya biya buƙatarsa,sannan bayan kwana hudu yazo da abokansa kusan su uku sukayi lalata dani,ta baya da ta gaba,kuma tun daga wannan ranar kusan duk sati sai sunzo sunyi lalata dani gashi harda videon abinda suke aikatamin yake,yanzu tafiyata ma ta canja,a gwale nake tafiya saboda muƙurƙusar da nake sha gunsu"






Kowacce a cikin zaro idanunta tayi waje tare da dafa ƙirji kamar haɗin baki,Umma Kande ta fara magana da cewa




"Innalillahi Wa'inna Wa'innar Raji'ana,Iklima shi ne tunda muke waya dake baki taɓa sanarmin ga halin da kike ci ba,na shiga uku ni Saratu,mun kawo yaranmu cikin bala'i,innalillahi Wa'inna Wa'innar Raji'ana,Sambuhanillahana!!! " (My Esteem Fans ku koyi Innalillahi wurin Umma Kande tare da Sumbuhani.....kai! kai! kai! bazan iya ƙarasawa ba😂😂😂😷😷😷)






"Yamin kashedi akan kar na sanar ma kowa idan ba haka ba,zai ɗora videos ɗin da yimin a sanda suke lalata dani a social media kowa ya gani"




Maman Jummalo ce ta cire tagumin da tayi sannan ta ce




"Hmmmm ni nama sara mai zance yanzu,kalmomi duk sun ɓacemin,ƙwaƙwalwata ta rikice ta daina bani haɗin kai,ke yanzu Iklima ko guduwa kin kasa yi,ace kina cikin irin wannan mawuyacin hali kin zauna kina kwasar baƙin ciki Iklima ummm"




Zama Iklima ta gyara a hankali kamar wacca akama kaciya sannan ta ce




"Nayi yunƙurin guduwa amma ban samu dama ba,ni tsorana ma yanzu kar yazo shida la'anannun abokannan nasa su afka muku"






Ai da sauri suka kai dubansu ga Iklima jin abinda take faɗa,nan da nan suka rikice suna dube-dube kamar sunyi ajiya duk tsabar ruɗewa ne da sukayi,Umma Kande jikinta na ɓari ta fara magana




"Mun shiga Uku mun lalace,su afka mana kikace Auta,yanzu ya zamu gudu daga gidan nan harda ke"




Maman Jummalo ce ta cafke maganar da cewa






"Iklima musan abunyi kar mutanan suzo gidan nan mu shiga Uku"




Dogon tunani Iklima ta lula,tare da tunanin yadda zasu kuɓuta daga hannu mijin nata da abokansa,dubara ce tazo mata sai ta dubi su Umma Kande tare da cewa




"Mafita ɗaya ce yanzu,akwai ƙofar sirri wacca idan misali gidan yayi gobara mutane suke fita don su samu su tsira da rayukansu,amma yanzu matsalar saina nemi key ɗin ƙofar wacca

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login