Showing 48001 words to 51000 words out of 55707 words
Chapter 17 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
nasa,cewa yayi suje dining suci abinci,babu musu suka miƙe musamman Captain Fu'ad wanda ya ɗebo yunwarsa,yazo yaja girkin amarya.(hmmm Captain Fu'ad a shirya cin girkin Maryam kuku😂😂😂🙃)
Zama sukayi a dining room ɗin sai Sauban yayi serving ɗinsu,kasancewar ya umurci Maryam ta wuce ɗaki,serving ɗinsu yake amma zuciyarsa na dukan tara-tara bama uku-uku ba,ganin yadda colour ɗin abinci yayi so scary babu kyan gani,gashi baya fidda wani aroma mai daɗi sai uban ƙauri,haka dai ya gama serving ɗinsu shima yayi serving kansa sannan ya samu guri ya zauna.
Captain Fu'ad ne farkon fara kai spoon ɗin abinci a bakinsa wanda a lokaci guda amai ya tasa sama jin wani uban ƙarni,ga yajin data zambaɗa a ciki,kai kai kai,amai Captain Fu'ad yake kwarawa babu ƙakƙautawa lokaci guda ya ɗau gorar ruwa ya kwankwaɗe,baiji yajin ya daina masa zafi a baki ba,ya ƙara ɗaukar wata sabuwar goran ruwan ya shanye,su kuma Sauban ganin yadda Captain Fu'ad ya rikice lokaci guda suka kasa cin abinci tare da miƙewa suka nufo inda yake suna masa sannu.Bai amsa musu ba ya miƙe ya dauki key ɗin motarsa ya fita,har waje Sauban ya bisa yana basa haƙuri haka ya ƙyalesu suka tafi,a fusace ya shigo falon har bedroom,lokacin Maryam na kwance abinta,batayi aune ba taji saukan zafafan maruka har guda huɗu lokaci guda,habawa a haukace a miƙe tare da sakin wani razanannan ihu,bai ƙyaleta ba saida ya mata dukan tsiya tare da ce mata ta tafi gidansu gobe,sannan ta tabbata ta goyi girki tare da gyaro munana halayanta kafin ta dawo gidan.Fita yayi baibi takan kukan da take ba ya wuce wani ɗakin ya kulle tare da kwanciyarsa.
Washe gari Maryam ta tattara kayanta ta nufi gidansu,wanda Sauban yasha tsinuwa a hannun iyayenta kasancewar ƙarya da gaskiya ta faɗa musu,su kuma babu bincika ba sukaita zaginsa.Wannan kenan
@ @@@@@@@@@
Ɓangarensu Umma Kande da Maman Jummalo da alama basuyi nadamar abubuwan da suka faru da yaransu ba,domin har yanzu ƙiyayyar Umman Sa'eeda da ita Sa'eedar na nan daram! A zukatansu.
Suna zaune su duka da yaransu wato Iklima da Jummalo,sai Umma Kande ta ce
"Kodai mu ƙara komawa gun Boka Sankeru ne muji a ina aka samu matsalar"
"Tabb wallahi ko kusa Mama karku fara,yanzu duk abinda ya samemu bai zamo muku isharaba,harda rasa ɗiya kikayi amma bakiyi ladama ba Mama"
Cewar Iklima wacca ta harzuƙar sosai saboda halin uwarta ta domin haushinta take ji sosai,Maman Jummalo ce ta ce
"Haba Iklima daɗi da hutu muke nema muku ai,wannan ma matsala aka sam....."
"Matsala! Matsala! Kika ce fa Mama, wallahi bazamu sake biye muku ku kaimu ga wahala ba,da alama kema kamar yadda Iklima ce bakiyi nadama ba,to bara kuji tun a asibiti ni da Iklima muka shirya komawa Islamiya,don ƙara sanin Allah da addinin mu,wanda kuka kasa bamu"
"Tabbas kuwa Jummalo zan tambayi Sa'eeda yadda karatun islamiyarsu take"
Umma kande ce ta hayayyaƙo Iklima da masifa tana cewa
"Ɗiyar maƙiyiyata zaki nema shawara wurinta Iklima"
"Maƙiyiyarki ko ko ce maƙiyiyarta,wani irin asiri ne baku musu ba,amma gashi sai cigaba suke, ku kuma kuna nan jiya iyau"cewa Iklima
"Rufemin baki dan Ubanki,da hassadar Umman Sa'eeda aka haifeni sannan yanzu ma na fara nuna mata ƙiyayya wallahi, koya kika ce ƙawas"
"Ƙkkkwaraiii da gaske yanzu muka fara nuna mata ƙiyayya"
Suna cin hakane akan kira numban Umma Kande wanda tsabar masifa bata duba mai kiranta ba ta amsa kiran
"Hello"
A can ne ake mata magana,wanda lokaci guda ta rikice tana cewa
"Mai wayar!!! "
A can aka ƙara tabbatar mata,habawa sakin wayar tayi a ƙasa haɗi da zaman ƴan bori,tana ihu da kururuwan ta bani ta lalace shikenan ta mutu.Kanta su Maman Jummalo sukayi suna tambayar lafiya mai ya rafu,cikin kuka haɗi da majina take cewa
"Na shiga Uku ni Sarere jikar Sarkin ruwa!!!na mutu na lalace wayyo ni Saratu!!!! Yanzu..................
Mu haɗu a pages na gaba My Esteem Fans🙃🙃🙃🌹🌹🌹
****Wata sabuwa inji ƴan caca,wani bala'in ya kuma saukar ma Umma Kande ne???.....
****Anya Zaman Sauban da Maryam zai cigaba da wanzuwa ganin yadda tun kan aje ko'ina an fara kai duka tare da tafiya gida???.....
****Shin Fadila zata haƙura da Sadam kamar yadda ya haƙura da ita koko yaya???......
*****Shin wasu abubuwa ne suka faru shekaru aru aru a baya wanda Momin Sadam da ahalinta suka kasa mancewa???........
Ku cigaba da zubo ruwan comments🤗🤗🤗🙃🙃🙃💝💝💝,Ni kuma bazan gaji ba wurin suburbuɗo muku da zafafan updates wa'inda zasu nishaɗantar,ilmantar tare da faɗakar daku🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️
Ina matuƙar alfahari daku my Esteem fans,Allah yabar ƙaunar🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️💖💖💗💗💓💓
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[5/23, 8:09 AM] Narnarhh Bukar: 🏵️ NACINA YA JAWO MIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
🌹🌹🌹I'm not born to be a writer but born to be a great professional writer✍️✍️✍️🙃🙃🙃🌹🌹🌹
🌼🌼🌼Special greetings to y'll my Esteem Fans,Ina ƙaunarku Lodi Lodi🙃🙃🙃💖💖💖🌼🌼🌼
3⃣7⃣----3⃣8⃣
Suna cin hakane aka kira wayar Umma Kande wacca tsabar masifa bata duba mai kiranta ba ta amsa kiran
"Hello"
A can ne ake mata magana,wanda lokaci guda ta rikice tana cewa
"Mai wayar!!! "
A can aka ƙara tabbatar mata,habawa sakin wayar tayi a ƙasa haɗi da zaman ƴan bori,tana ihu da kururuwan ta bani ta lalace shikenan ta mutu.Kanta su Maman Jummalo sukayi suna tambayar lafiya mai ya rafu,cikin kuka haɗi da majina take cewa
"Na shiga Uku ni Sarere jikar Sarkin ruwa!!! Na mutu na lalace wayyo ni Saratu!!!! Yanzu mai yayi saura gareni,yiiiiii!!! Yiiiiii!!! "
"Ƙawas wai meya faru ne,kinsamu a duhu,ga kuma kuka kina yi"
"Maman Jummalo gobara ta tashi da Musa!!! Shikenan ɗana a duniyi,yanzu ya tafi ya barni,ina ganin bala'i da masifa ni Saratu!!! Wayyo Musana!!! Shikenan ko gawan ɗana bazan gani baaaaa!!!! Yiiiiiii!!! Yiiiiiii!!!
Jin abinda Umma Kande ta ce gidan ya kaure da kuka haɗi da iface-iface musamman Iklima wacca suka fi shiri da Musa,tayi kuka haɗi da birgima a ƙasa kamar sabuwar kamu.Maman Jummalo itama tayi kuka sosai tare da ba Umma Kande haƙuri,amma ina Umma Kande kamar wata zautatta haka tayi,gashi tayi zaman ƴan bori haɗi da cire ɗan kwalin kanta tana ihu da kururuwa
" Musa! Musa! Musa! Ka dawo karka tafi ka karbi,kaine rayuwata,ka dawo,ka dawo Musana na roƙekaaaaaa!!! "
Waiwaye
******Abinda su Umma Kande basu sani ba game da rasuwar Musa shi ne,kasancewar Musa ɗan daudu ne kuma mai harka da manya-manyan mata a Calabar,manyan matan suna zuwa ɗaukarshi har gidajensu domin suyi sharholiyarsu sannan su biyashi maƙudan kuɗi saboda yasan sirrin mata sosai.
Hausawa suka ce tsautsayi baya wuce ranarsa,ranar data kasance ranar da Allah ya ɗauki ran Musa shi ne,wata customersa ce tazo har gidan karuwai ta ɗaukeshi suka tafi gidanta,zama yayi a falonta sai tace bara ta girka musu abinci sai suji daɗin harkar dakyau,bayan matar da ɗaura girki a gas cooker mai mazaunai hudu sai ta fito falon,tana zuwa sai Musa yayita janta da kissarsa ta riƙakƙun ƴan daudu,habawa tuni mata ta manta da abinda ta ɗaura kan gas cooker suka fara masha'arsu,wanda har girkin ya ƙone,tukunyar tayi baƙi amma hankalinsu baya a jikinsu balle suji ƙauri,nan da nan wuta ta tashi a kitchen kan kace me ta gauraye ko'ina,su Musa kafin suyi wani aune,wuta ta shigo falon,haka su biyu suka ƙone ƙurmus sai ƙashi,wannan ne asalin sanadin mutuwar Musa******
*Cikin Labari*
Suna a wannan yanayin ne saiga Baban Nusaiba ya shigo gidan kamar an jefosa,tun daga zaure yake jin ihu da kururuwansu Umma Kande wanda hakan ne ya sashi saurin shiga gidan,samun Umma Kande yayi a zaune a ƙasa,ta wage ƙafafunta haɗi da saka hannuwa a kai tana ihu.cikin sanyin murya ya tambayi lafiya,Iklima ta sanar mishi Musa ne ya rasu,bai sake ce da ita komai ba ya fita daga gidan,fuskarsa babu yabo babu fallasa,shidai gashi nan,mutuwar ma ba damuwa yayi da ita ba,to baya cikin hankalinsa.
Tun safe Sa'eeda da Ummanta basa nan,ita Sa'eeda taje IT, ita kuma Ummanta daga shara ta wuce aikin biki a bayan layinsu,basu san da abinda ke faruwa ba.
Da sallama Sa'eeda ta shigo gidan,cak ta tsaya ganin ikon Allah,yau su Umma Kande ne ke kuka haka duk da lokacin rasuwar Zaliha tayi kuka amma wannan karon kamar hauka take,wai meke faruwa ne? Mai ya samesu haka?,tambayar kanta tayi,wanda babu amsa,taso ta buɗe ɗakinsu ta shiga ba tare da ta tambayi mai ya samesu ba,amma ina bazata iya ba,ita mai raunin zuciya ce ga mutane,haka tayi kasadar tambayar Iklima mai ya faru.Cikin kuka Iklima ta sanar ma Sa'eeda Musa ne ya rasu yanzu.
"Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un,Allahumma gafir lahu,warhamhu,wa'afi anhu,Allah ya gafara masa,yasa ya huta,yasa kuma aljanna ce makoma a garesa,Allah ya baku haƙuri tare da juriyar rashinsa"
Iklima da Jummalo ne suka iya bata amsa,amma Maman Jummalo tare da mai gayya mai aiki wato Umma Kande basu san mai take cewa ba tsabar tashin hankali da ruɗun daya samesu.Ɗaki Sa'eeda ta wuce wanda bata jima ba saiga Ummanta ta dawo,itama tambayarsu tayi mai ya faru,Iklima ce ta bata amsa,salati tayi tare da yi mishi addu'ar Allah ya gafarta masa ta wuce ɗaki.
Haka su Umma Kande suka ci-gaba da zaman makokin Musa wanda har ƴan uwanta da Maiduguri saida sukazo ta'aziyya,yanzu kullum da hijabi zakaga Umma Kande haɗe da carbi saikace tasan me ake cewa😂😂😂,bayan anyi arba'in ɗin Musa wanda ba'a kawo gawarsa ba kasancewar ƙurmus ya ƙone,Umma Kande ta yaki ce saka hijabi haɗi da riƙe carbi,wannan karon Nusaiba batazo ba saidai kira a waya tai musu ta'aziyya saboda yanzu bata samun lokaci sosai,tauraronta ƙara haskawa yake a harkar luwaɗi da kuma lesbianism,wanda bata wannan ƙasa bata waccan.
Bayan rasuwar Musa da wata biyu su Iklima da Jummalo suka shiga islamiyar da Sa'eeda tayi sauka,ajin matan aure suka shiga saboda babu wani abun kirki da suka sani dangane da addinsu su.Wannan kenan
@@@ @@@@@@@@
*Bayan Wata Shida da Sati Biyu*
A ɓangaren karatun Sa'eeda kuwa,sun kammala IT yanzu kuma sun shiga shekarar ƙarshe a karatunsu wato 400 level,yawanci lecturers ɗin da suke ɗaukarsu sababbi ne,masu zafi babu wasa a tattare dasu.Farkon shigarsu ajin wata sabuwa lecterer ƴar gayu ta fara ɗaukarsu wani course,shigowanta ajin tayi tozali da Sa'eeda, cak ta tsaya tana kallonta babu ko ƙyafta ido,kowa a ajin kallansu suka komayi ganin wannan ikon Allah, mata daga zuwa aji ta kafe Sa'eeda da kallo babu ko ƙyartawa,kusan seconds 20 sai kuma lecterer ta ƙarasa cikin ajin still idanunta akan Sa'eeda, kasa haƙuri matar tayi ta tambayeta da harshen turanci
"Young Lady what's your name please? "
Sa'eeda da tunda ta haɗa ido da wannan sabuwar lecterer ƙirjinta ya fara duka,gashi taga matar sai kallonta take babu ko ƙiftawa,miƙewa tayi cikin ladabi ta amsa mata cikin hatshen turanci
"My name is Sa'eeda Sulaiman"
"From which State"
"From Kaduna"
"Alrght seat down"
Ba haka ran matar yaso ba domin akwai abinda takeso ta tabbatar akan garinsu,saboda wani abu take ji a zuciyarta game da wannan yarinya,amma ya zata tabbatar tunda ta ce ita ƴar Kaduna ce,sha re zancen tayi,tazo gaban Allon haɗi da gabatar da kanta cikin harshen turanci wanda take magana cike da ƙwarewa
"Good morning class,My name is Dr.Nabila Abubakar Kabir Dikko,nice to meet you all"
Duka ajin suka amsa mata cike da murna saboda matar ta gama tafiya da imaninsu,ga turancin da takeyi daga ji kasan ba'a Nigeria tayi karatu ba,saboda yadda take amfani da phonex wurin lanƙwasa harshenta.Cike da ƙwarewa Dr. Nabila take musu karatu,gashi ta iya bayani mai gamsarwa,lokaci-lokaci idanun Dr.Nabila na kanta Sa'eeda wanda har yanzu ta kasa gasgata abinda zuciyarta take ayyanawa game da yarinyar,haka ta kammala musu lecterers ta fita,kamar jira ƴan aji suke tana fita kowa ya fara yaba Dr. Nabila saboda ƙwarewa da gayunta.
Haka suka ci-gaba da karatunsu a 400 level first semester cikin nasara,a semester ɗin ne aka rarraba ɗalibai ga project supervisors nasu,luckily Sa'eeda aka bama Dr.Nabila, haƙiƙa Dr Nabila taji daɗin bata Sa'eeda da akayi a matsayin project student ɗinta,koba komai zata samu damar tambayanta abubuwa da dama wanda suke cikin ranta tun a ranar da tayi tozali da ita.
Sa'eeda ma haka abin yake a wurinta domin har labarin Dr Nabila take ba ma Ummanta,saboda tanada kirki sosai gashi tunda Dr.Nabila ta zama supervisor ɗinta take taimakonta da kuɗi ko wasu abubuwa,duk da Sa'eedar bata son amsa amma babu yadda ta iya saboda jan idon da Dr. Nabila take ma Sa'eeda idan taƙi amsa,ƴan aji sunyi gulmar har sun gaji musammam squad ɗinsu Maryam wai Sa'eeda na shisshigema Dr.Nabila saboda taga tanada kuɗi sosai,ga sabuwar Land Cruiser baƙa wanda take hawa,haka dai suka gaji da gulmar suka sa musu ido.
A ɓangaren ƙawancen Sa'eeda da Iman baza muce komai ba saidai muce maa shaa Allah,domin ƙawancen da sukeyi na tsakani da Allah ne babu hassada balle ƙyashi,ba ƙaramin daɗi Iman taji ba ganin yadda Dr.Nabila take son Sa'eeda, hakan na mata daɗi a rai koba komai ganin ƙawarta cikin farin ciki na daɗaɗa ranta.Wannan Kenan
@@@@@@@@ @@@@
A ɓangaren LOVE BIRD🕊️🕊️🕊️ wato Sauban da Maryam,tunda ya ce ma Maryam taje gidansu gyaro hali tare da koyan girki har yanzu bata dawo ba kusan wata biyar kenan,gashi har sun koma makaranta amma taƙi dawowa hasalima acan take tafiyarta makaranta abunta,tunda iyayenta sun ɗaure mata gindi akan sai Sauban yazo da kansa ya bada haƙuri kafin ta koma gidansa,shi kuma ya rantse koza ta shekara a gidansu ba zaije bikonta ba,domin laifinta ne ba nasa ba.Maryam nasan komawa gidan mijinta amma bata samu fuska gun iyayenta ba saboda sun kafe akan lalle-lalle-ilalla sai yazo ya bada haƙuri da kansa.
Shi kuma Sauban yanzu ya fita a harkarta musamman shawarar da Mom ɗinsa tazo mishi dashi wanda ya aminta sosai akan shawarar da ta yanke.
Yau ne ya shirya zuwa gidansu Captain Fu'ad domin yanason ya bashi shawara tare da ƙara bashi haƙurin abinda ya faru a gidansa kasancewar Captain Fu'ad auransa ya matso saura sati ɗaya,kuma ya samu hutu a wurin aikinsa Port harcourt.Bayan mai gadi ya buɗe ma Sauban gate ya shigo da motarsa yayi parking tare da nufar part ɗin Captain Fu'ad, da sallama ya shiga falon kasancewar ƙofar a buɗe take, amsa masa Captain Fu'ad yayi tare da miƙewa yana sakin wani shegen murmushi babu gaira babu dalili,tunda Sauban yaga yana mishi wannan munafikin murmushin yasan mugunta ya gani,cikin ɗaure fuska Sauban ya ce
"Malam ya da shigowa na ka mike tare da sakin murmushi"
Dariya Captain Fu'ad yayi tare da cewa
"Haba Angon Mairo kuku,kyau naga ka ƙara shiyasa ni sakin murmushi ganin aminina kuma ɗan uwana na samun kwanciyar hankali"
Eh tabbas! Yau naga ta kaina da Fu'ad, nasan kashina ya bushe,badai yazo gidana yaga yadda muke rayuwa ba shikenan ai na kaɗe ni Sauban, katse mishi tunani yayi da cewa
"Ka zauna mana Angon Mairo kuku,kana hutawa fa"
"Oooo God!!! Haba Fu'ad wani irin iya shege ne haka,ko ruwa baka bani nasha ba amma ka wani cikani a surutu marasa ma'ana"
Dariya Captain Fu'ad ya tintsire dashi harda riƙe ciki yana nuna Sauban yana sake tintsire dariya,ɓacin rai iya ɓacin rai Sauban yake ƙololuwa.Cike fusata yace da Captain Fu'ad
"Wallahi zanbar maka ɗaki naje na gaida Mom tunda naga alama ƙwaƙwalwarka ta taɓu"
"Sorry friend wallahi yadda ka koma ne yasani dariya"
"Ok nagane wato ga mahaukaci yazo ko? "
"A'a fa Sauban,why are misunderstanding my words,ummmm wallahi ba haka bane"
"No hakane mana,ga angon Mairo kuku ba wacca kaja girkinta harda amai da shan gorukan ruwa har biyu,ai dole kamin dariya Fu'ad"
Dariya Captain Fu'ad yayi tare da yima Sauban waƙa harda rawa yana cewa
"Da so samu ehh!!! Ace ta iya girki,ƴar fara first lady mai kyau sannan ace tanada kirki ehh,inba kasamu ehh! Inba kasamu ehh!! Inba kasamu ehh ehh ehh habawaaa!!! "
Dafe kansa Sauban yayi yana cewa
"Kai kai kai yau naga ta kaina,shikenan ai tunda kasan sirrin gidana na kaɗe,don Allah mubar wannan shirma,muyi abinda ya dace Fu'ad"
"Tohhh Angon Mairo kuku,ina sauraranka"
Baza yayi da abinda ya ce don idan ya biye halin Captain Fu'ad sai su shekara a haka,cikin muryar damuwa Sauban ya fara magana
"Fu'ad wallahi ina cikin matsala babba"
With serious voice Captain Fu'ad ya ce
"Subhanallah,meke faruwa Sauban"
" Ai komai ma ya faru Captain, Mom ce tazo min ta wata shawara a lokacin Maryam nace taje gidansu gyaran hali akan na ƙara aure,duk da nima inada wannan burin amma ba'a nan kusa ba,kwata-kwata yaushe akayi bikinmu ace har na ƙara aure, gashi Maryam duk yadda naso ta natsu tasan hakƙin mijinta amma ya gagara,idan na lanƙwasota ta nan saita ɓalle ta can,tana da matsaloli masu yawa wallahi,rashin iya girki,baƙar magana,rashin girmama na gaba da ita,ga uban ƙazanta,gayu kawai ta iya amma duk abinda matar aure ya dace ta sani babu abinda Maryam ta sani,could you imagine pads ɗin da tayi amfani dashi after her mensturation a toilet ta barshi saidai ni dana shigo toilet ɗin na ɗauke tare da jefarwa,how did you think i can tolerate her stupid atitude Fu'ad, common gyaran ɗaki Maryam bata iya ba,balle akai kan uwa uba girki,inaa inaa dole na samo ma kaina mafita wallahi,don bazan iya jurar halayanta ba,gashi tunda nace taje gidansu gyaran hali har yau taƙi dawowa,kuma na rantse babu inda zani bikonta"
Shiru Captain Fu'ad yayi yana kallon aminin nasa cike da tausayi duk da shi yajama kanta tun farko,sauke ajirar zuciya Captain Fu'ad yayi kafin ya ce
"Kaga illar dana hango maka tun a baya kaƙi ganewa,irin wannan matsalar na hango maka Sauban amma ina sai kayi burus da shawarata,ka irinta nan Sauban kwata-kwata yaushe kayi auran amma har ka fara fuskantar matsalolin da ko wa'inda suka shekara goma basu fuskanta ba,i told you from initial not just by mere looking zaka san wacca ta dace ka aura ba,shi aure da kake ganinsa akwai features da mutum yake bi kafin yasan wacca tafi cancanta ya aure,amma kai ina kyau da gayu haɗi da social life ya ruɗeka,kai kafi son mace very social,beautifuland classy bayan the most impotant features ɗin aure ka barsu,like addinin mace,kamewarta,natsuwarta,tsaftarta,ɗabi'unta da dai sauransu,duk da wannan baka duba ba sai kyau da wayewarta kawai,taya zakuji daɗin auran bayan turbar da kuka ɗauka kaida ita ba mai ɓulle muku bane,alhakin Sa'eeda ne tun kan aje ko'ina Allah ya fara saka mata,mace mai hankali, natsuwa,ilimi,ga uwa uba tarbiyya