Showing 6001 words to 9000 words out of 55707 words

Chapter 3 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt

31 May 2024

8052

ba🙃).


@@@@@@@@@@@@@@


Alhaji Sagir zama yayi kusa da ita haɗe da rumgumota sannan ya ce"My sweet honey kinsan wani irin goron sallah nakeso kibani kuwa?
Nusaiba tace " Wanda nasaba baka mana ko akwai wani goron na daban ne?
Ɗan murmushi yayi sannan yace" Sosai ma kuwa my sweet honey"
cikin zaƙuwa Nusaiba tace "To sanar min naji sugar na"
Gyara kwanciyar Nusaiba yayi a ƙirjinsa sannan yace " Nusaiba inaso in ɗaga darajarki a duniya,zaki samu kuɗi kamar ba gobe,in har kika bani haɗin kai"
Ɗagon kanta Nusaiba tayi daga ji yace zai ɗaga darajarta a duniya sannan zatayi kuɗi, har ta fara harsaso yanda zata fantama da kuɗi ita da familinta wayyo daɗi
"Na yarda sugar na kuma zan baka haɗin kai"
murmushi yayi a zuci yake faɗin 'ai nasan zaki yarda mayyar kuɗi '
Ɗan lunfasawa yayi sannan ya cigaba da cewa "Inason in biya buƙatata dake ta baya ma'ana ba yanda na saba kasancewa dake ba kamar yanda kika sani, ta duburarki nakeson biyan buƙatana dake,sannan zan turamiki dubu ɗari biyar #500,000 in kin yarda kuma zan haɗaki da abokaina suma masu irin wannan harkar, wallahi Nusaiba kin gama kuɗancewa in kin yarda amma"
Shiru Nusaiba tayi tana tunani ta yarda ko ko A'a, can da ta tuna mamanta zataji daɗi kuma sun kuɗance, kawai saita amince(Ya Salam, Allah ka tsaremu daga faɗawa halaka da kuma zugar shayɗan).
Jin ta amince yasashi sakin wani munafikin murmushi, don haƙarshi ta cimma ruwa.
Haka suka fada halaka ita dashi duk da tasha baƙar wuya saboda farkon yinta kenan, bayan sun kammala masha'arsu sukayi wanka, ita Nusaiba har da gashi tayi don taji maza(kwaɗayi ma muɗin wahala🙃🙃🙃), sai huɗu na yamma ta iso gida duk da yanayin tafiyarta ya sauya amma Umma Kande bata gane wani abu game da Nusaiba ba, hasalima murna ta ke tayi saboda Nusaiba ta siyo kayan abinci haɗe da wasu kajin duk acikin kuɗin da Alhaji Sagir ya saka mata a account, murna iya murna Umma Kande tayi harda yima Umman Sa'eeda gori ƴarta batada mashinshini. (Umma Kande anyi bagidajiyar Uwa🤔).


@@@@@@@@@@@


Tunda daga wannan ranar Nusaiba ta zama ƴar hannu don Alhaji Sagir ya haɗata da abokanansa suna sharholiyarsu da ita.
Duk fantamawar da Nusaiba ta ke da kuɗi ko ajikin Umma Kande hasalima gadara ta ke ƴarta nada farin jinin samari, haka suma ƴan uwan nata duk da basa sharholiya irin nata amma suna ɗan matse matse da taɓe taɓe a zauran gidansu su da samarinsu.
Sa'eeda dai hutunsu ya ƙare sun koma makaranta,yanxu tashiga SS2, samari sun fara kai mata hari kasancewar ta kyakkyawa ga sexy eyes farare tas, gashi tanada ɗan girman jiki, don duk halittar ƴa mace ta gama bayyana a jikinta duk da ƙarancin shekarunta don yanxu take cikin shekara na 16,amma Maa shaa Allah.
Sa'eeda ta ɗaukar ma kanta alƙawarin sai ta kammala secondary kafin ta fara soyayya saboda soyyaya bata cikin tsarinta kwata kwata.


@@@@@@@@@@@@@


ABUJA


Ɗaki ne mai duhu sai ɗan wani haske kaɗan da nake ɗan iya hangowa wanda bai wadaci ɗakin ba, ga tururin hayaƙi daya turniƙe ɗakin, ni kaina da kyar na iya shiga ɗakin haɗe da addu'a dan ɗauko muku rahoto, wasu surutai kamar suddabaru naji muryar wata tana faɗi wanda nakasa gane mai ta ke cewa, kwatsam naga wani haske kamar walƙiyar ya ɓullo ta cikin bangon ɗakin ya haska ko'ina, wani halitta nagani kamar mutum amma wada, kansa a ƙasa yake, shi baiyi ƙasa ba kuma bayi sama ba, yana a tsakatsaki, tsawansa bai wuce tsawan hannu ba, sai rangwajejan kai kamar ƙwarya,yanada idanuwa kamar na mage, da sharɓa sharɓan kafakuwa kamar na babban mutum, kai in taƙaice muku, halittar nan batada kyawun gani hasalima mai ciki zaka iyayin ɓari ganin wannan muguwar hallitta.
Matar da naji na surutai sanda babu haske a ɗakin na sake kai dubana gareta tsohuwace amma ba can can ba, zata kai kimanin shekara 78 a duniya saidai a idanuwa kaɗaine zaka iya ganewa amma jikinta mai kyaune kamar ƴar shekara 40 a duniya. Sujjada naga tama wannan halittar, (wa'iyazubillah)..............................






Daga alk'alamin
🖍️📚Narnarhh Bukar📚🖍️


Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[4/25, 1:38 PM] +234 814 129 2044: 🏵️ NACINA YAJAWOMIN🏵️



Narrnarhh Bukar✍️


🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨




Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:Narrnarhh002


7️⃣----8️⃣


Sujjada naga tayiwa wannan halittar tana cewa "yakai Sarkin Tsageru! yakai gagara badau!! , yakai buhun ƙara kafi ƙarfin danna!!!, ya kai Shugaban matsafan duniya!!!! , haƙiƙa ka cika alƙawarinka gareni akan bullowarka bayan shekara 43 da suka wuce, kuma ina nan ina bin dokokinka da ka sharɗantamin". (toh shikuma wannan nashi salon tsafin kenan sai bayan shekaru aru aru yake bayyana, babbar magana 🤔🤔🤔).
Wata dariya naji har ƙasa na girgiza ashe wannan halittar ne ke busar dariya, can ya tsagaita kamar ruwa ya ɗauke ya fara magana jikake kamar ƙasa zata tsage
"Haƙiƙa kinbi sharudɗanmu na ƙin sallatar Asr da Subh tare da ƙin azumin watan Ramadan haɗe da sadakar baƙaƙen karnuka 50 duk shekara, lallai ke tamu ce! Ke tamu ce!!!
Sai kuma ya fara kuka kamar ana ruwan sama can kuma ya tsaya,(fans nifa hallittar nan ta kusa sani fitsari tsabaragen tsoro, da ƙyar na iya tsayawa dan ɗauko muku rahoto 😖😖😭).
Sai can ya cigaba da cewa"Irinta basu gushe a doran ƙasa ba suna nan har yanzu, wasu na a cikin ƙasƙanci wasu na a cikin farin ciki ,tabbas sai sun dawo bada jimawa ba, wannan haka yake, he! he!! he!!!
A razane ta ɗago kanta zuciyarta na dukan tara tara cikin rawar murna da inda inda ta fara magana " Su..... Suss.... Sussa nan a ra.... raye da... daman basu mutu ba?
Daka mata tsawa yayi yana magana cike da amon muryar"Karya zamuyi miki,dole ne su dawo, munyi iyayinmu sun gagaremu, suna sallah biyar kullum arana, suna nafila, suna azkhar na safe da na rana, suna azumi, suna Tasbihi da Hailala"
Cak ya tsaya ya kuma sake fashewa da kuka wanda yafi na farko ko ita kanta ta razane matuƙa ainun, sai kuma ya dakata da kukan sai ya ɗora daga inda ya tsaya a magana " kullun sai sun karanta baqara mu kuma bamaso,ruhunsu baya zama wuri ɗaya,lokacin dawowarsu yayi dole su dawo!!!
Ita dai har fitsari ya soma zubo mata, can kuma ya ce"Mun muki alƙawarin halittar jikinki zata tsaya ahaka in har kika cigaba da bin sharudɗanmu, zan koma, zan koma sai bayan shekara 5!!!
Lokaci kuda hasken ya ɗauke kamar ɗaukewar ruwan sama, haka dai ta tashi jiki duk a sanyaye ta boye kayan tsubbunta a wani akwati mai shegen kyau sannan ta kuma sashi cikin wani akwati babba tasa a ƙarƙashin tamfatsetsan kadonta na alfarma wanda ko queen Elizabeth sai haka(🙃🙃🙃).
Duk wannan gyaran da ta ke yi bayan ta kunna bulb din ɗaki ne, dayake can cikin salisalin dare ne wanda alokacin bayin ALLAH suke ganawa da mahaliccinsu amma ita da shaydani ta ke ganawa dashi (ALLAH kasa mufi k'arfin zuciyoyinmu).


@@@@@@@@@@@@


Haka ta kwanta cike da tashin hankali duk da tawani bangare ya mata alƙawarin barin mata halittar jikinta batare da tsufaba, sai kuma kareta da familinta gaba daya, shi ne kadai yake sassuata mata zuciya.
Ta jima bacci ɓarawo bai saceta ba, sai gabanin sallar asuba bacci ya ɗauke ta.
Washe gari sai wurin ƙarfe 11:17am na safe ta tashi, ita daman ba sallar Subh ta ke yi ba. Ƙwankwasa kofar ɗakinta naji anayi, ko kala batace ba, sai kusan minti 8 kafin tace "A shigo" , wata mata ta shigo ƴar kimanin shekara 50,babu sallama saboda tasan halin Uwar ɗakinta, ta tsufa sosai hasalima tafi uwar ɗakinta tsufa, za kayi tunanin ko ita ƴar aikin ce yayar.
Shigowa tayi har wurin makeken gadon uwar ɗakinta kana durƙusa haɗe da gaisheta "Barkha da safiya Hajiya"
wacca aka kira da Hajiya dake kwance ta tashi zaune da faɗin "Barkha"
Mai aikin tace "An shirya abincin a dining room Hajiya ",
"To" kawai tace sannan ta wuce bayi don yin wanka.
Ita ko mai aikin karatun zuci ta fara'Toh wai lafiya naga yau batama son yin magana, meke faruwa ne', tunda babu mai bata ansa ta tashi ta fita daga ɗakin.
Hajiya ta fito daga wanka ta shirya cikin haɗadɗan boyel lace milk color wanda ya ɗinku wurin masana ɗinki kuma ya zauna mata a Jiki ɗas,takalmi ta saka wanda ya dace da kayan, sannan ta sauko zuwa ƙasa don yau batajin hawa lifter kasancewar akwai lifter a gidan.
Saukowa tayi zuwa dining room don karin safe, baya ta kammala ne ta fito falo, kallon falon nayi wanda ya tsaru iya tsaruwa, saikace falon shugaban ƙasa saboda yanda naga annarka dukiya a ɗakin kai in taƙaice muku gidan ma gaba daya ya haɗu don idan kashigo gidan zakayi tunanin a Dubai kake, zama tayi sannan ta kanna TV.


@@@@@@@@@@@@@


Ƙararrawar ƙofar aka danna, alamun ana son shigowa, bata tashi ba sai dai naji tana kiran"Saude zo ki buɗe"
Mai aikinta naga tafito daga kitchen da sauri ta nufa ƙofar, budewa tayi sannan da ɗan ja baya, wata budurwa nagani mai kimanin shekara 17 tashigo da gudu da faɗa jikin Hajiya tare da fad'in"Granny I really miss you alot, da ƙyar dad ya barni nazo Nigeria saboda rashin tsaro"
Magana ta ke ma Hajiya amma cike da shagwaba, murmushi Hajiya tayi don yau bata cikin good mood ɗin magana, shafa bayanta tayi tana faɗin"yanxu ai gaki a Nigeria koh"
murmushi budurwar tayi sannan tace "Granny bara naje nayi wanka I'm very tired" da "ok" Hajiya ta bita dashi.
Gaskiya a rayuwarta tana tsanani son ahalinta don zata iya komai don farin cikinsu, yaranta uku ne duk mata, biyu suna aure a cikin garin Abuja ita kuma ɗayar wacca ta ke ƙaramarsu tana aure a UK da yarinyarta ɗaya Fadila wacca tazo Nigeria hutun 1 week.
Amina itace babbar 6arta wacca ta ke da yara biyu duk mata amma sunyi aure da kuma yaransu,sai Jamila mai yaro daya shima yayi aure da yaro ɗaya.
Duk babbar sallah duka familin suke haɗuwa don yin shagulgulan sallah.Fadila bayan tafito ta wuce taci abinci sannan ta dawo wurin grannyn ta don yin hira, a nan ne ta ke sanar ma Hajiya zuwa next year zata shiga Oxford University don karantar bagaren jarida.
Haka suka cigaba da hirarsu sannan kowa ya nufi ɗakinsa ita Fadila taje sallah duk da ba iya sallar tayi ba ita kuma Hajiya ta wuce ɗakinta don yin bacci,Wannan kenan.


@@@@@@@@@@@@@@@


KADUNA


Zaliha ce tafito da kayan wanki tanayi, sai taji an kwaɗa sallama, ɗagowan da zatayi tayi arba da Maman jummalo da ita Jummalon, haba sai ta saki wankin ta ruga da gudu ta rungume Jummalo, itama Jummalo rungume tayi tana murna, ƴar uwar sharholiya ta dawo, ji kawai sukeji ance "Ai saiki saketa ta huta mana, kin wani rirriƙeta sai kace za'a ƙwace maki ita"
Umma Kande ce tafito daga ɗaki jin Zaliha na ihu, Maman Jummalo ce ta nufi ɗakinta wanda yake kusa da na Umman Sa'eeda,ta buɗe ta shiga,Jummalo ma shiga tayi sai Zaliha tabisu da kayan da suka zo dashi tana murna.
Maman Jummalo ƙawar Umma Kande ce kuma ta hannun damarta, duk wani makirci tare suke ƙullashi,mijin Maman Jummalo ya rasu kuma abokin Abbansu Sa'eeda ne, shiyasa bayan mutuwarsa yaga ya dace ta zauna gidansa tunda daman a gidan haya suke kuma ƴan uwansu suna ƙauye da zama, wannan shi ne dalilin fara zaman Maman Jummalo a gidan.
Sai kuma akayi rashin sa'a halinsu yazo ɗaya da Umma Kande nan da nan suka ɗinke suna gallazama ma Umman Sa'eeda, batajin daɗinsu kwata kwata, sun haɗe mata kai. Tafiyar Maman Jummalo da Jummalo ƙauyen su ne Umman Sa'eeda ta ɗanji sassauci kaɗan.


@@@@@@@@@@@@@@


Kasancewar Umman Sa'eeda bata gida taje barka a maƙotansu wa'inda suke ɗan abun arziƙi yasa bata san da dawowarsu ba, itama Sa'eeda taje makaranta.
Umma Kande ce ta shigo da kula mai kyau da abinci sai kuma jug ɗin ruwa mai sanyi tana ƙara musu sannu da zuwa, Maman Jummalo ta amsa da fara'arta tana faɗin "Har da ɗawainya ƙawas"
Umma Kande tayi murmushi ta ce "Haba ƙawas ai babu komai, bari kedai gama cin abinci mufara chapter"
dariya Maman Jummalo ta kwashe dashi tana cewa " Haba dai ƙawas bara naci sai mufara sana'ar".
Haka dai Maman Jummalo da Jummalo suka kammala cin abinci, ita Jummalo ta wuce ɗakin Umma Kande don yin hira da ƴan uwanta Zaliha da Iklima Kasancewar manyan mata Nusaiba bata nan ta tafi nata harkokin(Ni kuma nace ta tafi tata sana'ar karuwanci ba koya kukaci my esteem fans🙃😂).
Maman Jummalo ce ta fara magana "ƙawas naga sauyi sosai a gidan nan, ko Babansu Nusaiba ne ALLAH ya buɗa masa ko ko Musa ne halan "
murmushi Umma Kande tayi sannan tace"Ai ƙawas duk basu bane hasalima Musa na Calabar kasuwanci ,Nusaiba ce ALLAH ya haɗata da wani attajirin mai kuɗi Alhaji Sagir, yana matuƙar sonta,kuma yana sakar mata kuɗi sosai, to shi ne ya gyara mana wannan gidan ai"
Ɗan jimmm Maman Jummalo tayi a zuciyarta tana faɗin 'zama bai ganni ba, dole Jummalo tasamo saurayi mai kuɗi wanda muma zamu fancama'
Umma Kande ce ta katse mata tunani da faɗin"Ni na kawo wata shawara yanzu, mai zai hana mu komawa wurin boka Sankeru ya samoma Jummalo, Zaliha da iklima samari masu kuɗi kamar yanda Nusaiba tasamu mai kuɗi kinga shikenan munyi sallama da talauci ko ya kikace ƙawas"
Shiru Maman Jummalo tayi tana nazari acikin ranta tana faɗin 'Kamar kin shiga raina aminiyar ƙwarai, nima nayi wannan tunanin saboda gaskiya bazan koma ƙauye ba'
Can ta fara magana "Gaskiya yau nasan kin cika aminiyar arziƙi mara baƙin ciki don da wata ce shikenan ta daina abota dani"
Murmushi mai sauti Umma Kande tayi tare da cewa "Ai a duniya banga abinda zaiza nabar abota dake ba, kin manta, kefa ce kika fara haskamin hanya har nazo wannan gaɓar kuma sai nabarki, a'a ba haka nake ba"
Ɗan dariya Maman jummalo tayi da cewa " Shiyasa nake yinki Over kawas".
Tare suka saki dariya haɗe da shewa harda tafawa, can Maman Jummalo tace" Wai ina waccan mayyar da ɗiyarta su ke ne, naga banji motsinsu ba"
dariya tasaki da faɗin"Ohon musu naga ɗazu ta fita ita kuma ɗiyarta ta tafi gantali wai acewarta makaranta, ni kinga yanxu wallahi basu a gaba na, don na gaba yayi gaba"
Dariya Maman Jummalo tayi sannan tace"Da kyau ƙawas kina wuta Ina binki ta petrol " tare suka sake kwashewa da dariya.
Umma Kande ce tace" Ranar lahadi saiki shirya muje wurin boko Sankeru ɗin", Maman Jummalo tace "To ALLAH ya kaimu".


@@@@@@@@@@@@


Haka suka cigaba da hirarsu, a nan ne sukaji sallamar Umman Sa'eeda amma babu wanda ya amsa, ita dama ta saba ko akwai mutane a tsakar gida babu mai amsa mata sallama ita da ƴarta ( Hmmmm wannan rayuwa🤔).
Ɗakinta ta wuce babu jimawa sai ga Sa'eeda ta shigo itama da sallamarta haka akai banza da ita, ta shiga ɗaki da sallama sai ta gaida Ummanta tare a rataya jakarta, ta ɗauki buta sannan ta nufi bayi da sauri saboda fitsari ya matseta tun a hanya.
Bayan ta fito daga bayi tayi kiciɓis da Maman Jummalo ta fito daga ɗakinta, sanin Maman Jummalo ta tsanesu yasata razana tare da ɗan russunawa da gaisheta.
Wani mugun kallo Maman Jummalo ta ke ma Sa'eeda a zuciyarta tana faɗin 'Haka wannan yarinyar ta dawo, ga kyau kamar mayya, ga diri saikace wata babbar mace,ko ƴan matan gidan duk tafisu kyau, gata da gashi kamar mamanta, ai dole na tsaneki tunda kinfi ƴan matan gidan nan kyau,gashi kyaunta yanxu yake ƙara bayyana'
Duk wannan zancan a zuci Maman Jummalo takeyinsa, ko amsata batayi ba ta wuce abinta, daman Sa'eeda tasan hakan zata kasance,tafiyarta tayi abinta tayo alwala ta wuce ciki.
A ɗaki kuwa Sa'eeda ke hira da Ummanta, tana cewa "Ummina mun kusa hutun babban sallar, mai zai hana muje ƙauyen Damari sallah, don mun rabu da zuwa tunfa banida wayo"
Shiru Umman Sa'eeda tayi tana sauraranta, can tace " Hakane kuwa, sai muje tunda kinason zuwa,babbar sallarma ai saura kwanaki yanzu"
Duk da Umman Sa'eeda ba son zuwa ta ke ba, saboda ba daɗin garin ta ke ji ba, haka suka cigaba da hirarsu.


@@@@@@@@@@@@@


Yau ta ke lahadi, su Umma Kande tun daren jiya suka kintsa tsaf saboda inda boko Sankeru yake akwai nisa don a machine ake zuwa wurin dajin sai a ƙarasa da ƙafa still shima ɗin akwai tafiya sosai, haka su ka ƙula sammako sai tasha,sai suka hau motar ƙauyen da dajin inda boko Sankeru yake,bayan sun sauka sai suka hau machine guda saboda k'arancin ƴan machine a ƙauyen , haka sukai ta tafiya har aka sauke su a wani gefen daji,Umma Kande ta biya mai machine sannan suka dosa dajin da tafiya a ƙafa.
Sunsha lafiya sosai kana suna isa wurin wata ƴan bukka wacca ta ke zagaye da manya manyan bishiyoyin kuka sunkai bakwai kana suka tsaya, dukkansu cire takalma sukayi sai suka fara tafiya da baya da baya har suka shiga bukkar(Fans kunsanni da ganin ƙwaƙwaf haka nabisu ciki don ɗauko muku rahoto🙃😇😇). Shigarsu keda wuya naga sun zube ƙasa suna mai kirayi kamar haka "Sankeru namu Sankeru na duk mai son ya dace,Shugaban matsubban duniya, Ka cire tuta,Kowa na bayanka, gamu yau munzo da ƙoƙon bararmu agareka mai share kukanmu", (Wa'iyazubillah,

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login