Showing 42001 words to 45000 words out of 55707 words
Chapter 15 - NACINA YA JAWO MIN book1 by Narrnarhh Bukar.docx.txt
zata sadamu har wajen gidan ba tare da mai gadi yasan da fitarmu ba,bara in tashi yanzu nan kar suzo don nasan suna hanya wallahi"
Ƙara rikice su Umma Kande sukayi jin ƙilama suna hanya,a gwale Ikilima take tafiya tana botsaro ɗuwawunka waje ta nufi gun drawers ɗin bedroom tana dubawa,suma tayata dubawa sukayi,daƙyar Iklima ta gano key ɗin,ai da sauri tabama su Umma Kande manyan hijabai kasancewar sun zubar da gyaluluwansu a sanda karnuka suka biyosu,harda zani Iklima taba Umma Kande, komai nata ta ɗauko har kuɗi masu yawa da mijin nata yasa a jaka ta ɗauko suka nufo ƙofar,cikin sa'a ta buɗe suka fito ta wani layin daban,samun mai keke napep sukayi babu ciniki suka shiga,sai a sannan ne Umma Kande ta sauke nauyayyen ajiyar zuwa tana da cewa
"Kaiiiii! Wannan bala'i haka,hmmmm"
Maman Jummalo itama ta sauke nata ajiyar zuciyar sannan ta ce
"Yanzu gidan Zaliha zamu nufa ko sai gobe"
"Sai gobe mana,yanzu direct zamu fara zuwa asibita a duba Auta,don gaskiya a yadda take tafiya ya nuna akwai matsala"
"Hakane "
Haka suka nufi asibitin da Iklima don a dubata,bayan likita ta dubata sai ta fito tare da cema su Umma Kande su biyota office rai a bace.Isarsu office keda wuya ko zama basuyi ba likita ta rufesu da faɗa akan ya zasu bar ƴar yarinya wacca bata girma cikin irin wannan halin,sannan suwa suka mata wannan muguwar aika-aikar.Tsuru-tsuru sukayi da idanu babu amsa,to wai me zasu ce bayansu suka siya wahalar da kuɗinsu,haka likita tayi masifarta ta gama ko ummm babu wacca tace a cikinsu.Likitar ce ta ce za'a ba Iklima gado saboda an illata ta sosai Allah ma ya rufe asiri bai kai stage ɗin da kashi zai dinga fito mata ba bisa ƙa'ida ba saboda afka matan da akai ta dubura.
Kasancewar akwai kuɗi a hannun Iklima wanda ta ɗauko na mijinta ,dashi suka biya kuɗin asibitin sannan aka bata gado,Maman Jummalo ce ta zauna da Iklima sai Umma Kande taje gida kiran Jummalo dan ta zauna da ita saboda gobe suke so suje gidan Zaliha suga ita wani kalan bala'i take a ciki.
Haka kuwa akayi,Jummalo ce ta zauna da Iklima,sai suka bata kuɗaɗan da zasuyi amfani dashi,sai suka tafi gida.
@@ @@@ @@@@ @@@@
Washe Gari
Kamar jiya har yau da safe suka nufi gidan Zaliha, amma a wannan karan basuyi kalle-kallan gida ba saboda wuyar da sukasha jiyan,bayan mai keke napep ya saukesu,sai suka sallameshi,gabansu na dukan uku-uku suka ƙwanƙwasa gate ɗin gidan,wani basamuden ƙato ne ya buɗe ƙofar gidan,ja baya su Umma Kande sukayi ganin wani gabjejan ƙato ga kwalli ya rambaɗa a idanunsa sai mazurai yake,cikin deep voice irin na manya-manyan gardawa ya ce dasu
"Wa kuke nema!"
Inda-inda suka fara yi,kowacce ta kasa magana,sai can Maman Jummalo tayi kasadar fara magana,wacca a rikice takeyin maganar haɗi da inda-inda
"Ammm amm amm dddamman wwwurinnn Zzzalihaaaa mukazo neeee yeeee"
"Ina zuwa"
Haka kawai yace musu ya kulle ƙofar,sauke ajiyar zuciya su Umma Kande sukayi a tare sai Maman Jummalo ta ce
"Oonii Hasfy!! Yara duk babu sa'a,Allah yasa gidan babu karnuka irin gidan Iklima"
"Ameen dai Maman Jummalo dako mun shiga uku"
Bayan mai gadin ya kulle ƙofar sai ya kira Ogansa akan iyayen Zaliha sunzo wurinta,dariya Ogan nasa ya tintsire dashi tare da cewa
"Aikin gama ya gama ai,barsu su shiga su ɗau sauranta"
"To Oga"
Katse wayar yayi sannan ya buɗe musu ƙofar suka shiga.Cikin sanɗa su Umma Kande da Maman Jummalo suka fara tafiya saboda tsoran kar suma sunada karnuka irin gidan Iklima. A haka har suka isa ƙofar ɗakin tare da ƙwanƙwasawa.
Zaliha dake a zaune a falon ta ce a shigo kasancewar ƙofar kodayaushe a ɓude take ba'a sa mata key,saida ta maimaita a shigo har sau uku sannan su Umma Kande suka shigo kasancewar Zaliha bada ƙarfi take magana ba,shigarsu ɗakin suka fara salati haɗi da sallalami,Umma Kande ce ta fara magana cike da ruɗewa
"Me zan gani ni Saratu! Zaliha haka kika koma,maiya sameki! "
Ɗan murmushin wahala Zaliha tayi sannan ta ce
"Kunzo ɗaukar gawata ne mama,Allah ya amsa addu'ana akan ƴan uwana suzo ɗaukar gawana saboda mutuwata tazo banaso in mutu a acikin ahalina ba,mama kin cuci rayuwata, kaicona da samun uwa irinki mai son abin duniya,gashi ta hanyar son abin duniyar zan rasa raina,don Allah mama ki roƙamin yafiya gunsu Umman Sa'eeda da ita kanta Sa'eeda akan su yafemin duk laifukan dana musu,son abin duniya ya kaini da halaka gashi mutuwata tazo"
Babu wacca a cikinsu bata zubda ƙwalla ba ganin yadda Zaliha jikinta ya koma kore shar ga idanunta sunyi yellow kamar wata aljana ba mutum ba,babban tashin hankali ma shi ne wani fari-farin ruwa yake fita a ta gabanta sai uban wari,cikin rawar murya Umma Kande ta ce
"A'a! A'a! Zaliha bazaki mutu ba,bazaki mutu ba Zaliha, muje asibiti Zaliha! Na shiga uku yau ni Saratu"
Girgiza kai Zaliha tayi tare da cewa
"Karku ɓata kuɗinku a kaina saboda ni tawa ta ƙare yannnnnzzzz......."
Tari ya saƙeta babu ƙakƙautawa a lokaci guda jini na fito mata ta baki ta hanci,da sauri su Umma Kande sukayo kanta tare da tallafota sukayo waje, sunci sa'a gidan a buɗe yake,direct sukayi hanyar waje,Maman Jummalo ce ta tarin musu keke napep suka shiga,cikin tashin hankali Maman Jummalo ta ce su tafi asibiti,a hanyarsu ta zuwa asibiti ne tari yasha ƙarfin Zaliha wanda a ƙarshe ta ce ga garinku nan.
Cak abubuwa suka tsayawa Umma Kande a ƙwaƙwalwarta,ji take kamar duniya ta juye babu sauran kows,lissafi ya ɓace mata kwata-kwata,wani ƙaramin hauka Umma Kande tayi a cikin keke napep ɗin tare da girgiza Zaliha wai ta tashi,amma ina rai yayi halinsa.
Haka akayi zaman makokin Zaliha wanda sai a lokacin Nusaiba ta dawo gida shima don kiranta akayi akan Zaliha ta rasu,da labarin abinda ke faruwa da ƴan uwan nata,tayi kuka tayi baƙin ciki sosai tare da godewa Allah da bata wanke fuskarta da wannan ruwan da boka Sankeru ya bada ba,da yanzu itama tana cikin tashin hankali.
Ko dayake hanyar da itama ta ɗauko ba mai ɗore mata bane,domin yanzu Nusaiba ta zama INTERNATIONAL HOMOSEXUALITY GANG STAR,tauraronta ne ke haskewa yanzu,bata waccar ƙasar bata waccan,har competition ɗin cin duri suke wanda yawanci ita ke ci,shiyasa bata cika zama gida ba saidai ta turo da kuɗi masu yawa,kuma Umma Kande da Maman Jummalo duk sun san mai take aikatawa amma ko ajikinsu tunda kuɗi na shigo musu babu ƙakƙautawa.
A haka a haka har akayi bakwan Zaliha sai a sannan ne Jummalo da Iklima suka dawo gida an sallamesu daga asibiti kasancewar yanzu Alhamdulillah sauƙi yazo ma Iklima,dan yanzu ta rage gwala ƙafa idan tana tafiya,kwana goma da rasuwar Zaliha Nusaiba ta koma ƙasar da tafito wato Germany,shi kuma Musa bai samu zuwa ba saida ya kira waya yayi ta'aziyya.Wannan kenan
@@@ @@@@@ @@@
A ɓangarensu Sa'eeda rayuwarsu na tafiya normal babu wata matsala,koda ma akayi rasuwar,tare dasu akayi zaman makokin,kasancewar Abban Sa'eeda ba'a hayyacinsa yake ba duk surutan da mazan layi suke masa akan yadda yaransa suka koma ko ajikinsa,hasalima idan ya tafi kasuwa bashi ke dawowa gida sai 8:00pm kuma yana dawowa yake wucewa turakarsa yayi kwanciyarsa,dayake yanzu lokacin rani ne baya zuwa gona,shidai rayuwa yakeyi gashinan gashinan dai.
Wasa-wasa lokacin exams ɗinsu Sa'eeda yazo kamar yadda tama Ummanta alƙawarin maida hankalinta kacokan a karatunta haka tayi,kwata-kwata ta daina tunanin Sauban aranta,gobe ne zasu fara exams duk shirin daya dace tayi duk tayi,a ranta take cewa
'I'm ready to face every single challenge in my life! I'm ready to face the battle with great speed! I want to become my own hero! Ready for whosoever come my way! I have change to a new version !!! '
Da wuri Sa'eeda taje hall ɗin exams ɗinsu,Iman ma acan ta sameta,shigorwa Maryam hall ɗin sai ƴan ajin suka kaure da ihun Amarya! Amarya!Amarya!
Sa'eeda taɓe baki tayi ko a jikinta,in fact ko kallon inda ake cewa ga Maryam ɗin batayi ba,focusing tayi ga summary dake a hannunta tana jiran su fara exams,haka suka fara exams,hall ɗin yayi tsit! Invigillators sai zagaye hall ɗin suka don tabbatar da tsakani da Allah ɗaliban suke rubuta jarabawan babu satar answer.
Bayan sun gama exams ne suka fito ita da Iman zasu nufo gida,Iman ce tama Sa'eeda raɗa a kunne tare da nuna mata wani abu da yatsa,Sauban ne yazo ɗaukar Maryam,kuma shiɗin Iman tama Sa'eeda raɗa a kunne ta kallesu.
Direct Sa'eeda fuska a ɗaure ta nufi inda su Maryam suke,Iman na kiranta amma inaaa,bata saurareta ba,saidai Iman ita ma ta biyota kar a samu matsala.Sa'eeda bata tsaya ko'ina ba sai a wurin inda Sauban yake,tsayawa tayi tare da kallonsa ido cikin ido ta fara magana cike da Izza wanda ba'a santa dashi ba
"To munafiki,mayaudari,annamimi,kai a tunanin zan mutu ne saboda soyayyar da nake maka ko! Never!!! Wallahi kayi kaɗan ɗan akuya,wato ka nunamin halinku na maza tare da waccan munafukar"
Nuna Maryam tayi wacca tayi mutuwar tsaye don jin irin lafuzzan dake fitowa daga bakin Sa'eeda wacca tasan bata magana,in fact ko yatsa kasa a bakin Sa'eeda bazata ciza ba amma yau gata tana magana cike da izza ta ƙasaita,katse mata tunani Sa'eeda tayi da cewa
"Ni Sa'eeda Sulaiman bana manta alkhairi haka zalika bana manta sharri, I hate deceivers in my life,ku jira ƙarshen ku ku ɗinnan"
Nunasu tayi sannan ta cigaba da cewa
"In shaa Allahu sai Allah ya sakamin tata-izan da gaggawa,wallahi wallahi wallahi idan inada da hakƙi daidai da ƙwayar zarra akanku sai Allah ya bimin hakƙina,sannan rashin asalina da kuke ta ja-inja a kai kusani,haka Allah yaso ya ganni kuma ina ji a jikina na kusa haɗuwa da ahalina,daga ƙarshe ina tabbatar muku da sai kunzo da ƙafafunku wurina kuna roƙon inyafe muku,trust me Sauban that time will surely come in shaa Allah"
Raf!Raf!Raf! Iman tayi da hannunta tare da jinjina ma Sa'eeda tabbas Sa'eedarta ta canja,Sa'eeda batabi takan mai zasu ce ba taja hannun Iman sukayi gaba.
Mutuwar tsaye Sauban yayi,saida ƙwaƙwalwarshi ta tafi wucin gadi na wasu seconds kana hankalinsa ya dawo jikinsa,Sa'eeda ce da wannan kalaman,yarinyar da batada magana,to yaushe ta fara zubo zance.(ba Sa'eedar da kasani a da bace ehe😏,ta yanzu bata ɗaukar raini🙃🙃🙃😂😂😂).
Juyowa yayi kan Maryam tare da hararta haɗi da cewa
"Uban me kike jira da baki shiga motar ba ehhhh!"
Da sauri Maryam ta shiga motar don yanzu tsoran Sauban take sosai,tunda ya mata dukan tsiya akan zagin Mom ɗinsa da tayi take shakkarsa,gashi ya hana a ɗauko mata ƴan aiki,ita take aikin gidan,har part ɗin Mom ɗinsa kasancewar a gidan suke da zama,babbar matsalar ma rashin iya girkinta,kasancewar ko a gida ƴan aiki suke musu girki shi kuma Sauban yace girkinta yakeso,kwaɓa takeyi wanda a ƙarshe saidai da zubar da abinci shi kuma waje resturant ya musu takeaway,sannan ya ce da ita zuwa resturant bazai fisshesu ba gwara ta koya girki ko kuma ya ƙaro wata(Tofa tun a first week of marriage an fara maganar kishiya,babbar magana su Maryam sai a gyara🤔🤔🤔).
Abu dayawa ga tsangwamawan da Mom ɗin Sauban take mata tun ran da ta zageta taji Maryam ɗin ta fitar mata a rai,sati guda da auransu amma tafara fuskantar challenges daban-daban.
Bayan Exams su Sa'eeda suka tafi IT a wajaje ma banbanta,sai bayan wata shida zasu dawo school kuma ajin ƙarshe wato 400 level.wannan kenan.
@@@@ @@@@@@@
ABUJA
Ƙarfe 2:30am na dare
Ɗaki ne mai duhu sai ɗan wani haske kaɗan da nake ɗan iya hangowa wanda bai wadaci ɗakin ba, ga tururin hayaƙi daya turniƙe ɗakin, ni kaina da kyar na iya shiga ɗakin haɗe da addu'a dan ɗauko muku rahoto, wasu surutai kamar suddabaru naji muryar wannan matar ta shekarun baya tana faɗi wanda nakasa gane mai ta ke cewa, kwatsam kamar wancan karon naga wani haske kamar walƙiyar ya ɓullo ta cikin bangon ɗakin ya haska ko'ina, wannan halittar nagani kamar mutum amma wada, kansa a ƙasa yake, shi baiyi ƙasa ba kuma bayi sama ba, yana a tsakatsaki, tsawansa bai wuce tsawan hannu ba, sai rangwajejan kai kamar ƙwarya,yanada idanuwa kamar na mage, da sharɓa sharɓan kafakuwa kamar na babban mutum, kai in taƙaice muku, halittar nan batada kyawun gani hasalima mai ciki zaka iyayin ɓari ganin wannan muguwar hallitta,sujjada tama wannan hallitar tare da cewa
"Yakai Sarkin Tsageru! yakai gagara badau!! , yakai buhun ƙara kafi ƙarfin danna!!!, ya kai Shugaban matsafan duniya!!! Haƙiƙa ka cika alƙawarin da ka ɗauka akan bayyanar bayan shekara biyar!!! "
Wata dariya naji har ƙasa na girgiza ashe wannan halittar ne ke busar dariyar, can ya tsagaita kamar ruwa ya ɗauke ya fara magana jikake kamar ƙasa zata tsage
"Karki yarda ayi auran!!! Karki bari ayi auran!!! Idan kuma ba haka ƙarshenki yazo Zulfa'u,yaaazoooo ƙarshenki Zulfa'u!!! "
Da saura ta ɗago kanta tana kallonsa don a gaskiya ita batasan da wani aure ba,to wani aure yake magana akai,kasa haƙuri tayi ta tambayesa cikin girmamawa tare da ƙan-ƙan dakai
"Ya kai Sarkin matsafan duniya, yakai Boka Burumbuɗu wani aure ne zan hana afkuwarsa"(daman sunan wannan halittar Boka Burumbuɗu,tabbb yaci sunnansa kuwa🤔🤔🤔😂😂😂😂)
Dariya ya tsintsire dashi har ƙasa na girgiza,sai kuma ya fara kuka ko'ina na ɗakin rawa yake can ya tsagaita tare da cewa
" Karki bari!!! Karki yarda!!! A hir ɗinki ki bari ayi auran..........
Mu haɗu a pages na gaba hmmmmm wuta kan wuta🔥🔥🔥🔥
****Auransu waye ne Boka Burumbuɗu yace kar Zulfa'u ta bari ayi????.......
****Shin su Umma Kande da Maman Jummalo sun tuba ko kohar yanzu basu saduda ba???........
****Yaya zamantakewar Maryam zata cika ba a gidan Sauban ganin tun a satin farko Maryam ta fara fuskantar ƙalubalai iri-iri???.........
Ku cigaba da zubo ruwan comments🤗🤗🤗🙃🙃🙃💝💝💝,Ni kuma bazan gaji ba wurin suburbuɗo muku da zafafan updates wa'inda zasu nishaɗantar,ilmantar tare da faɗakar daku🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️
Ina matuƙar alfahari daku my Esteem fans,Allah yabar ƙaunar🤗🤗🙃🙃💝💝🌹🌹🌼🌼🏵️🏵️💖💖💗💗💓💓
Daga alƙalamin
🖍️📚Narrnarhh Bukar 📚🖍️
Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah.
[5/23, 8:09 AM] Narnarhh Bukar: 🏵️ NACINA YA JAWO MIN🏵️
Narrnarhh Bukar✍️
🌹Perfect Essential Writer's
Association🌹
✨ P. E. W. A✨
Wattpad:@AISHAABUBAKAR812
Arewabook:@Narrnarhh002
Masu telegram zaku iya following ɗina ta wannan link ɗin🤗,🙃🏵️👇👇👇
https://t.me/+439Pdx2UbLZlOTNk
🌹🌹🌹I'm not born to be a writer but born to be a great professional writer✍️✍️✍️🙃🙃🙃🌹🌹🌹
🌼🌼🌼Special greetings to y'll my Esteem Fans,Ina ƙaunarku,ina alfahari daku domin da bazarku nake taka rawata🙃🙃🙃💖💖💖🌼🌼🌼
3⃣5⃣----3⃣6⃣
Wata dariya naji har ƙasa na girgiza ashe wannan halittar ne ke busar dariyar, can ya tsagaita kamar ruwa ya ɗauke ya fara magana ji kake kamar ƙasa zata tsage
"Karki yarda ayi auran!!! Karki bari ayi auran!!! Idan kuma ba haka ƙarshenki yazo Zulfa'u,yaaazoooo ƙarshenki Zulfa'u!!! "
Da saura ta ɗago kanta tana kallonsa don a gaskiya ita batasan da wani aure ba,to wani aure yake magana akai,kasa haƙuri tayi ta tambayesa cikin girmamawa tare da ƙan-ƙan dakai
"Ya kai Sarkin matsafan duniya, yakai Boka Burumbuɗu wani aure ne zan hana afkuwarsa"(daman sunan wannan halittar Boka Burumbuɗu,tabbb yaci sunnansa kuwa🤔🤔🤔😂😂😂😂)
Dariya ya tsintsire dashi har ƙasa na girgiza,sai kuma ya fara kuka ko'ina na ɗakin rawa yake can ya tsagaita tare da cewa
" Karki bari!!! Karki yarda!!! A hir ɗinki ki bari ayi auran jikarki da ɗa daga tsatson maƙiyiyarki,domin idan kika bari auran ya tabbatu,hooo hoo hoooo,asirinki na gab da tonuwa!!!
Tsuru-tsuru Haj. Zulfa'u tayi da idanu tana sauraransa,a zuciyarta tana cewa. 'Na shiga uku ni Zulfa'u daga wancan sai wancan,da wanne zanji,da farko ance karna bari muhadu da tsatsonta,yanzu auran da ma bansan da wanzuwansa ba ake cemin karna sake ayi auran,yau naga ta kaina'. Kamar Boka Burumbuɗu yasan mai take ayyanawa aranta ya ce
"Zulfa'u duk abinda muka sanar miki tabbatacce ne in har baki bi umarninmu ba! Kisani munyi iya yinmu domin mu halaka sauran ahalinta ammaa.....!!!
Wani irin gigitaccan kuka ya fashe dashi wanda duk ilahirin ɗakin na girgiza gashi shi kanshi ƙarar kukan babu daɗin ji,kai in taƙaice muku kamar saukan ruwan sama mai ƙarfin gaske haka kukan nasa yake.Yakai tsawan mintuna 10 yana wannan kukan,ita kuma Haj. Zulfa'u abin duniya ya mata katutu a yuwa,kanta a duƙe tana sauraran kukan nasa,sai kuma can ya tsagaita tare da cewa cikin amon muryarsa mai firgitarwa
" Basa wasa da sallolinsu biyar a duk rana,suna azkar ɗin safe da na yamma,suna nafilfilun dare,sun tsare yaransu da addu'o'i masu ƙarfi,mun kasa Zulfa'u!!! Mun kasa!!! "
Jinjina kai Haj.Zulfa'u tayi saboda abinda Boka Burumbuɗu zaice ya kasa to ba ƙaramin abu bane,tabbas ya zaman mata dole tayi taka tsantsan kar asirinta na shekaru aru aru su bayyana dako kashinta ya bushe,dole ta hana faruwan wannan auran duk da batama san dashi,wannan dole ne ta hana,haka tayi ta ayyana abubuwa a ranta kafin daga bisani Boka Burumbuɗu ya ƙara da cewa
"Zamu barki yanzu! Sai bayan shekara biyu wanda a lokacin zamu linka miki kariyar da muke baki sosai,domin lokacin abubawa zasu fara rincaɓewa,dole mu kareki Zulfa'u! Dole mu kareki domin kina mana biyayya tare da bin umarninmu haɗi da sharudɗanmu! Zamu tafi! Zamu tafi Zulfa'u! Sai bayan shekara biyu! Muna ƙara jajjada miki ki kula! Ki kula Zulfa'u kar iya auran jikarki da ɗa daga tsatson maƙiyiyarki Zulfa'u! Karki bariii!!! Karki bariii!!! Mun tafiii!!! Sai watarannn!!! "
Ɗif kamar walƙiya ya ɓace a lokaci guda hasken ya ɓace sai duhu ya mamaye ɗakin bayi ɗaga,a cikin duhun ne Haj. Zulfa'u ta lallaɓa ta kunna bulb ɗin ɗakin sannan ta harharɗa kayan tsafinta ta sakasu a cikin ƙayataccan akwati ƙarami mai kyawun gaske saita saka akwatin a wani akwati babba shima mai kyau saita maida a ƙarƙashin gadonta.Sannan ta hau tanƙameman gadonta na alfarma ta kwanta,ta kai tsawan awa ɗaya amma ɓarawo bacci yaƙi ziyartatta sai kusan sallar subhi bacci ya ɗauke ta,ba ita ta farka ba sai wuraran 11:23am na safe kasancewar babu sallah a tsarin rayuwarta hasalima tun tana da shekara 35 a duniya tayi sallama da bautar Allah hatta zuwa Hajji tun a wannan lokacin ta daina saidai bautawa aljan tare da zubar da jinin baƙaƙyan karnuka 50 a duk shekara.
Bayan ta farka daga baccin ta nufa hadɗan toilet ɗinta mai shegen kyau tayi wanka haɗi da brush sannan ta fito ta shirya cikin lafiyayyan atamfanta super holland wanda tasha duwatsu a duk ilahirin dokuwar rigan,ga gwalagwalen da ta saka a wuyanta da kunnenta harda