Showing 75001 words to 78000 words out of 94796 words
Chapter 26 - WA ZAI FURTA Book Complete by Zainab Dahiru Wawo.pdf
again, tunda an ce *Ina da rawar Kai*
Ta Kara kallon sa da sauri, ya Kara dariya.
Ya Mika Mata takarda ga Shi gobe gobe Zaki je kiga registration officer na nan University of
Abuja akwai abinda Zaki karasa, ta Kara zaro ido.
Me kake nufi?
Ya Dan Sha mur, Ina nufin na mayar da ke can anan Zaki gama.... Kai kuma fa?
Ni Zan karasa a dutsinma..... Wallahi ban yarda ba ta Mike tsaye.... Shima ya Mike, wannan
shine umurnin da na Baki Kuma abinda na zartar a matsayina na mijinki....... Akan meye zakayi
haka?
Saboda na nunawa kowa cewar ba sha'awar ki nake ba sonki nakeyi saboda Allah......Anwar....
Bilkisu kada Kija maganar nan, kada kuma ki sanar wa iyayen ki cewar nasan an daura Mana
Aure kawai Ina son ke ki amince da *Ni Anwar son da nake Miki na Aure ne ba na sha'awa
ba*.............✍
*Zainab wowo maman Abdallah*
Masu kirana waya kuyi hakuri ku aiko da sako ta whatsapp
[3/24, 8:50 PM] +234 706 188 4461: *WA ZAI FURTA?*
2⃣5⃣
*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( Hajia Rabi badawi Kano maman Ibrahim ), Allah ya Kara arziki ya
shirya Miki zuri'a ya Kara Miki tsawon kwana. Amin.*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*
*Domin ki...... beloved sister Khadija Dahiru wowo miji na gari I pray*
*RUKAYYA BAKO DAN BATTA I love you so much, remember this
always*.
******************
*ABUJA NIGERIA*
.... Na rantse da Allah ban aminta ba, sai dai kaima ka dawo nan mu gama tare .... What do you
take me for?
Bilkisu...... Da su mufeeda a school Zan Barka acan bana nan?.... Ya zaro ido...
Ta rike kugu billahil azim tare zamu koma FUDMA.... Abinda nake so ki fahimta..... I'll never
understand you, amma ka mayar dani shashasha.... Wallahi bazan aminta ba,
Ya harde hannuwa a kirji ji yakeyi kamar ya kamota ya rungume....
Ta banka mishi harara, yanda kake da kishi nima haka nake dashi, dole ka zaba ko nan ko
dutsinma Amma kafa ta kafarka....... Ya kyalkyace da dariya...
Ikon Allah Bilkisu ta dawo..... Ta banka mishi harara, Shi yasa ka daina kula ni ka kaurace
mun?
Kana son proving meye?, Wannan ne prove? Ai prove shine gani ga ka ba Ina can kana can
ba..... Naji maida wukar yanzu zauna ya kike so madam.....
Ta galla mishi harara kaje ka yo cancelling din komai mu koma FUDMA.... Ya maganar Sanya
nikaf???? Wannan ce damuwar ka?
Zan saka...... Ya kura mata ido.... Sai Kuma kunya ta kamata ta sunkuyar da Kai..... Ya yi
murmushi yace *Akwai chakwakiya*.......
Tayi shiru..... Watau kina son gani gaki ko?
Ni Zaki kure Bilkisu????
Kome zakace sai dai kace amma wallahi ba school din da zance ba tare da Kai ba, idan Kuma
ka dage na rantse da Allah sai dai a warware..... Dal!.. ya buge bakin da yatsa... Mutu ka raba
yarinya duk yanda kike so haka zanyi what next?
Ta zumbure baki shikenan....
Yayi murmushi yace *nawaoooo*
Har na siya Miki mota wallahi gata can awaje don bana son wani driver kawai da akwai masu
binki a baya da tsaronki Koda yaushe..... Sai ka koma da abinka su Kuma ka canza masu aiki....
Ya tuntsure da dariya.... Anya Baki fini kishi ba????
Ta Dan harareshi cikin kunya.
Ya Kama dariya, Watau bazaki yarda gani ga mufeeda bakya Nan ba ko?
Ta rufe fuska nidai ya Isa,
Ya Kara dariya anya wannan semester din Babu damuwa????
Ba wata damuwa,
Ba Kya Jin tsoron anything can happen bayan nasan ke matata ce Bilkisu?
Ta harareshi ashe baza ka iya ba daddyn mamaki ba...... Yayi murmushi Zan iya Mana.
To Kuma.
Ya bi ta da kallo, ya zuki iska ya fesar tare da sakin ajiyar zuciya.
Gaskiya rigimar ki tafi tawa... Ta dan harareshi, but I'll try my best ya karasa maganar Yana
murmushi.
Ta Dan sunkuyar da Kai, ya Mike Amma bazaki koma gobe ba sai next week ki fadawa daddy
Zan Aiko a daukeki Zaki hau private jet na from Abuja direct to katsina zamu tare ki a can kinji
ko?
Ta daga Kai kawai.
Yana Isa gida ya tarar da sadeeq a basket ball ground, ya chabe ball din .... Malam ya akayi ?
Ya rike kugu,
Wai kasan nayi wa yarinyar nan transfer taki yarda?
Ka mayar da ita Ina?
Wallahi nan Abuja , ya danyi dariya, could you imagine kishi ke damunta??.... Sadeeq ya
kyalkyace da dariya na fada ma miskilanci ke hana Bilkisu nuna maka so amma wallahi zaka
Sha wahalar ta idan ta goge ...Amma fa ta birgeni.
Kai ta birge ko Ni sadeeq kasan dai akwai rigima ko?
Babba ma kuwa suka kyalkyace da dariya tare da tafawa.
Ya wurga mishi ball din suka Fara bugawa cikin nishadi.
Yanzu ya zakayi kenan?
Zan siyi gidan nan Wanda naga angama sabo na darawa ko nawane yayi Masa kudin bala'i
Zan biya Mata,sai ta zauna ita da Aisha da Maryam Amma banda khausar don bana son
yarinyar... Daddy zai yarda?
Dolen sa ma, Zan Sanya Mata masu gadi sosai Nima na siya Mana gida bayan gidan redio
zamu bar hostel...... Sadeeq ya buga tsalle amma ka gama birgeni nawan suka tafa suna
dariya...
Na Kira VC na fada mishi ayi meeting wallahi duk lecturer din da ya Kara Kira mun Mata Zan
daure Shi..... Sadeeq ya zaro ido ai FUDMA sun gama shiga uku Yanzu...... Suleiman Kuma na
mishi text na fada mishi na auri Bilkisu kallonta idan yayi ya gama Jin dadi har abada don zai
Kare rayuwar sa a prison..... Anwar kada ka firgita makarantar can.... Yayi dariya kawai. Da mota zamu koma yanzu?
Ya kyalkyace da dariya Kai mota ce dakuwar ka Wai?
To motoci ba mota ba, Zan fito musu a mutum sak!
Nawaoooo... Sadeeq ya fada.
Bilkisu kuwa, Miskilancin ta da zurfin ciki ya hana ta fada wa mommy abinda ya faru ba.
Haka suka taru sukayi Mata nasiha cikin hikima na duk darasin maganar bai wuce ta kiyaye
tarayya da shi Kuma ta kula.
*******************
*Federal University dutsinma*
Aisha da Maryam abun ya daure musu Kai, gidan tsoro ma yake Basu, har basa son fita
saboda kattin da gewaye da gidan, komai an saka gida abinda ke gida ga masu aikin abinci da
gyaran gida.....
Da yake sun rigata komawa da kwana biyu shine yakai su ya masu bayanin anan zasu zauna
tare da Bilkisu ranar duk da suka gayyato wata kawa ko namiji wallahi sai yayi maganin su....
Su Kam sunyi tsuru tsuru gashi har yau basuyi waya da Bilkisu ba.
Misalain karfe shidda na marece jirgin ya ajiyeta motoci hudu an musu layi Yana tsaye ya goya
hannu a kirji ta Fara saukowa da zumbuleliyar hijab har kasa ya kura Mata ido tun kafin ta
karaso ya bude Mata kofa....
Tana shiga ya shiga suka rufe kofa aka fizgesu sai dutsinma.....
Ya kalleta ba gaisuwa hajia?
Ta danyi murmushi,
Kin gaji ko?
Ta ce hmm kawai,
Ya makarantar?
Ta tambayeshi tana kallon fuskar Wayarta,
Lafiya Lau, Amma fa ban shiga ba har yau sai gobe nima Zan Fara zuwa lecture... Ta Dan
kalleshi saboda me?
Ya Dan yamutsa fuska haka kawai.... Sai tayi dariya.
Dariyar me kikeyi?
Naga kana mun karairaya kamar mace... Ya kyalkyace da dariya Wai Ina son in birgeki.... Ta
dalla mishi harara.... Ya Kara dariya.
Su Aisha sun kagara ki dawo...
Kai meye hadin ka da Aisha???.... Ya zaro ido ya watsa hannuwa ba komai fa....
Sai tayi murmushi,
Anya Bilkisu???, Ya leka fuskar ta.
Ta rufe tana Yar dariya.
Kin iya mota?
Um.
Good, to na ajiye Miki tana nan, zaku zauna keda su Maryam, nima nabar hostel muna bayan
gidan redio nida sadeeq, idan daddy ya Miki magana kice ninayi Haka, akwai masu gadi da
ma'aikata Amma fa ki sani idan zakiyi mun abinci kada kisa kowa naki nake so kin gane ko?
Ta mishi banza.
Ko bakiji ba?
Karatu nazo ko girki?
Komai ma kinzo yi, kin sani cewa akwai Aure na akanki ko?
Gabanta ya bada ras!
A bakin gate ya fita yabar su suka shiga gidan driver ya fito yabar Mata motar tare da Mika
Mata key, ta zaro ido Wai wannan motar ce tawa?
Ya sunya eh Hajia, ta amsa kawai tayi ciki..... Su Aisha suka kwaso da gudu tana ganin su ta
fasa ihu itama sukayi ciki suna Murna.........Suka tsareta da tambaya Wai ya Haka?
Ta fada masu ya tura iyayen sa neman Aure Bata sanar dasu akwai Aure akanta ba.
Mufeeda kuwa hauka kadai ke batayi ba da taji Anwar ya siya ma Bilkisu gida ba.
Zuwanta biyu Amma ko layin gidan Bata iya kaiwa saboda body guard, shima ta gano nashi
gidan cikin Daren Nan ma securities ne gewaye unguwar.....
Ta dunga kunduma ashar tare da Shan alwashin gobe sai ta ji dalili.
Bakwai suke da lecture ta munafuki Richard, akayi sa'a Aisha ma nada 7am
Suka fito abin mamaki har an goge motar...
Ta kalli Aisha wallahi kunyar hawan motar Nan nakeji Aisha..... Meye na kunya?
Kuma ba ga nikaf kin saka ba?
Kai nasan yau na gama shiga uku makarantar Nan..... Ke muje ni ki ajiye ni kada na makara ta
bude motar ta shiga ... Ko Zaki ja mu....??? .... Ni??? Ta daki kirji.
Anwar yau ya mayar dani kauyen mu kike so ko?
Ba yanda ta iya dole ta shiga tare da bata wuta suma suka tayar da mota suna jiran ta fita su
bita ( securities biyu ),, ta fita gate din a hankali tana Hawa titi ta chilla da gudu saboda sun
kusa makara. Suma suka rufa Mata baya.
Duk da safiya ce duk tsiraren mutanen da wuce sai sunbi motar da kallo.....
Kai Anwar karshe ne, shida sadeeq kasa suka tako, a bakin gate ta wuce su, ya kyalkyace da
dariya Sadeeq yarinyar can gudu take da mota fa...
Dan ubanka mu ba ka hana mu dauko ba?
Ya Kara dariya suna ta sauri....
Ta tsaya Aisha ta sauka saboda ba hanyar su daya ba ita ciki zataje Aisha Kuma nan farko
farko.
Tana zuwa kowa yayo ma motar chaaaaaa..... Chinayye ta gane ta da gudu ta makale tana
fadin Bilkisu oyoyo.....
Ya akayi Kika ganeni?
Ta fada a hankali , haba ya bazan gane ki ba?
Wai kinyi Aure?
Inji waye?
Eh Mana ance you are married woman now....no, not yet. But am engaged... With Anwar??....
Shigowar sa yasa ta Kyaleta, ya rufe idanun sa da facing cap abin mamaki kawai ya wuce baya
yaki Zama kusa da ita.
Suleiman ya shigo sai kawai ya chanza layi ya koma can baya saitin Anwar din.
Sai mazurai yakeyi cikin facing cap.
Mugun na shigowa sai cewa yayi test... Hankalin kowa ya tashi, ko ajikin Anwar,
Nan da Nan Bilkisu ta Fara kyarma.....
Question biyu ce, ba Wanda ya sani Anwar kadai ya amsa da kyar Bilkisu tayi attempting ta
biyun sai kuwa su chinayye.
Yana fita ya taso da sauri... Kin amsa?
Ta zumburo Baki Ina na sani?
Bakiyi ba kenan?
To me Zan rubuta?
Ya buga tsoki this man .
Nan da nan Yan class suka Fara kallon kallo.
Shi kuwa Suleiman Richard na fita shima yabar ajin.
Ya zauna bisa table Yana kallonta, budo in Miki bayani ya saboda gaba... Ta Mika mishi book
din, duk nikaf din ta ishe ta ba yarda zatayi ne.
Ya Fara Mata bayani a hankali ya lura sai mutsu mutsu takeyi yace Wai ya akayi?
Nikaf din nan ta isheni wallahi Dan Allah in cire?
Ya danyi dariya cire Mana .
Ta kalleshi da sauri da gaske ko gatse?
Sai kawai yasa hannu ya cire mata..... Dai dai shigowar mufeeda.... Ta tabbata wallahi, kutumar
uba... Anwar da gaske An daura muku Aure da wannan banzar..... Ji kake tasssssssss!
Fassss.....ratssssss duk illahirin hankalinta ya bace ta gigice ta kidime shima ya razana ainun
ganin Bilkisu tsaye tana wanka Mata wadannan marukan.............na rantse da Allah Akan
*Anwar Zan iya kisa* don Haka ki kiyaye... Body guards suka gani cirko cirko nan da nan Yan
ajin suka fara direwa ta taga saboda firgici.......✍ Ayi hakuri da kadan.
*maman Abdallah*
*uwa Mai bada mama mom ( Maryam adamu tikau maman amannas) mom you are the best I
love you so much Mom*
Wadanda ke cewa ba ni ke rubutawa ba a fada wa Mai rubutawa ta ci gaba da kokari Nima Zan
dage wajen sharing.....✍
[3/25, 12:48 PM] +234 706 188 4461: *WA ZAI FURTA?*
2⃣6⃣
*Tukuici ne ga Aunty Rabi ( Hajia Rabi badawi Kano maman Ibrahim ), Allah ya Kara arziki ya
shirya Miki zuri'a ya Kara Miki tsawon kwana. Amin.*
*KINA RAINA MAMAN WEEDAD*
*Domin ki...... beloved sister Khadija Dahiru wowo miji na gari I pray*
*RUKAYYA BAKO DAN BATTA I love you so much, remember this
always*.
**************
*Federal University dutsinma*
.......Ta shako wuyanta ta buga da table, gyalen ta ya fadi hular gashin da ke kanta itama
tayo kasa, wani chukuikuyon kitso ya bayyana ba 'a ko ganin tsagar ga kegen can manne a
wuya.....kaiii Bilkisu kina hauka...mAnwar ya fada a firgice..... Ta nuna Shi da hannu daya korar
mun wadannan kattin ta kallesu tana zare ido.... *What the hell are you doing here*?????....
Wata Kara mufeeda ta saki ta dago ta da karfi goshinta ya Kara tsawo kamar wani bread da ake
Kira danbisije na funtua...
Ya yunkura zai riketa ta Kara buga kanta a table....Zan nakasa ta Anwar wallahi...... Ya daga
hannuwa sama okay ..okay... Ya kallesu kuje waje... Kofar class din da bakin tagogi students ne
makil ...... Idanun ta sun kada sunyi jawur tana magana tana zare mishi ido...... Kai bazaka iya
maganin ta ba ko? Zan ci ubanta yau saboda duk makarantar nan yarinyar nan ta tsone man
ido..... Zan yi..wallahi zanyi maganin ta please kada ki janyo mun bala'i kada kiyi kisan Kai
Bilkisu.... wannan cin fuskane ki barshi ta mayar da gyalenta please....Ta ingizata da karfi tayi
baya ta fada cikin sit bayanta ya daki kujera da karfi ta saki wata Kara.... Yayi wurinta da gudu a
firgice...... Tayi tsalle ta dira gabansa kana tabata Ina karairayata....... Chief security suka gani
da wasu securities subhanallah meke faruwa anan.... Yana ganin Anwar yace ranka ya dade da
kanka???
Dan Allah ku fita da mufeeda kuje da ita.... Magana yakeyi a harmutse duk ya rikice, Bilkisu
kuwa ya dake ta Sha mur Kai baka taba cewa ita ce tayi wannan tashin hankalin ba....... Ya kalli
security daya je da ita clinic.... Yallabai kuyi hakuri muje office... Ita ce tayi gaba...... Zuciyar ki
tayi yawa Bilkisu wannan yarinyar ta wahala me yasa Zaki.... Ta dalla mishi harara , ka Sanya a
daureni na daki sahibar ka kasa a kaini prison..... Ohh my God,
Da gudu sadeeq ya dawo cikin makaranta jin wannan mummunan labari,
Abin mamaki Bilkisu ta Sami shaidar lallai mufeeda ce ta Fara tsokanar ta..... Anwar ya shiga ya
fita case ya mutu. Suka fito duk ta chukuikuye fuska... Sadeeq yarinyar kaga zata yi kisan Kai
ko?
Bilkisu me...... Na rantse da Allah idan ka Kara mun maganar waccen Yar iskar Zan sameta har
dakinta na Mata tsinannen duka Wai Anwar kasan Hali na kuwa?
Na sani a yau, na sani wallahi Dan Allah kada ki Kara kula ta zan kawo karshen matsalar.....
Kada ma ka kawo zata ci ubanta.... Ya kalli sadeeq duk sukayi murmushi.
Kawo key din na dauko Miki motar sadeeq ku jira anan..... Ya wuce da sauri, sadeeq ya danyi
dariya, duk kin hargitsa mun Anwar kin San Shi baya son tashin hankali..... Tunda takai fagen
mufeeda ko? Ai Dole ya hargitse, wace irin masifa ce Suleiman ke bai gani ba?
Kasan Allah ka gaya mishi idan bai nesa da mufeeda ba sai na halaka ta...... Itama daga yau
Dole ta shiga taitayinta kuma Zan fada mishi.
Ya iso, ganin baida niyyar fitowa yasa ta fada baya ta zauna Dole sadeeq ya shiga gaba....
Suna fita yayi hanyar gidan sa Yana fadin Bari ki Fara ajiye mu tukun ta mishi banza kawai.
Har ciki ya shiga da motar suna tsayawa ta fito ya dan koma gefe ta shiga wani mugun ribos
da tayi sai da ta birge duk Wanda ke shiyyar.... Ya bita da murmushi kaiii sadeeq yarinyar can
karshe ce..... Suka kyalkyace da dariya Ina so na ce ta dafan abinci amma duk na tsorata da
ita.... Sadeeq ya kwashe da dariya Bilkisun kake tsoro???? .... wallahi tsoronta nake sadeeq, ya fada Yana dariya.
Kaga tsawar da ta daka mun Wai na ce su mustapha su fita???
Duk suka Kara kyalkyace da dariya.... sadeeq ya ce ko baba da babansa.
Mufeeda kuka kawai takeyi, ba dukan ya Mata zafi ba, irin yanda ta cire Mata hular gashi ta
tozarta ta gaban jama'a..... Ta kasa daina kuka, kunya ta hanata fitowa daga clinic din ta tafi
daki.
Hakuri kawai kawayenta ke bata, Asma'u ta ce Ina ga mufeeda ki shafawa kanki lafiya ki kyale
Anwar... Wallahi ko Zan rasa rayuwata bazan hakura dashi ba..... Duk suka zaro ido.
Amina ta ce wallahi matar