Showing 54001 words to 57000 words out of 184071 words
Chapter 19 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
registration din D.E ne,
karbar takardun yayi ya duba yace
"kaje waje daga lungu zaka ga wani office ka tambayi ina Hajiya farida, ka bata,
amsan takardun yayi hade da yi mishi godiya,
yana kokarin fita daga office din yaji an murda kofar wani office dake kusa da kofar fita,
dan saurayi ne ya fito fari kyakykyawa,
kallonshi yayi ya miko mishi hannu suka gaisa,
kallon sani Hafeez yayi mishi, tunanin inda ya sanshi ya shiga yi,
"Kai Jamal, ka dauki key din motar ne,
waigowa sukayi tare da Hafeez yace "yes Papy, kai fa ka miko min,
a wannan karan ba kallan sani Hafeez yayi wa dattijon ba,
kallon kamannin da yayi da mukusancin shi yayi mishi,
Allah mai halitta,
tabbas badan wannan fari bane tass babu abinda zai hanashi cewa shi bane......
Mrs Tijjani Shattimah......
[11/03 4:41 PM] Aysha Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣4⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Har kasa Hafiz ya tsuguna ya gaida dattijon,
bai kalli inda yake ba ya amsa yana magana secretary dinshi, Mikewa Hafeez yayi har lokacin idonshi nakan dattijon,
waigowar da zaiyi idanuwansu suka sarkafu cikin na juna,
nan take wani abu ya tsarga a jikin dattijon,
bai dauke idonshi akan Hafeez ba ya karaso kusa dashi yace "your face looks familiar,
wani level kake?,
cikin girmamawa Hafeez yace "yau na fara zuwa,
nazo registration ne, "Good, ya sunanka and wane course? dattijon ya tambaya har lokacin bai fasa kallon Hafeez yana nazarin inda yasanshi ba, "sunana Hafeez Adam, daga kaduna, computer science ne sir!
kauda tunanin inda yasanshi yayi dan ya kasa tunowa,
shi dai yasan yaron ya shiga ranshi daga ganin farko,
kuma a dan fisge idonshi na yanayi da Jamal,
kafadunshi ya dafa yace "All the best, Allah yasa ka fara a sa'a, Ameen.. Hafeez ya fadi ya bishi da kallo har ya fita daga office din....
Rashin nutsuwar da bai samu ba saboda registration shiyasa bai koma gurin directorn ba,
saida yayi sati uku ya samu nutsuwa har ya fara shiga lectures, a sannan ne ya fara tunanin konawa gurin mutumin dan jin ko yana da wani dan uwa, kamannin sunyi matukar yawa, badan tsufa da haske ba, babu abinda zai hanashi cewa su ba yan biyu bane,
saidai wannan ya fishi yarinta, da haske da kuma ilimi...
Yana gama cin abinci a cafeteria ya wuce masallaci yayi sallah, yana idarwa ya kama hanyar Academic planing,
meeting ya samu suna yi sai ya fita harabar gurin dan ya jirasu, saida yayi jiran awa 3 basu gama ba sannan ne ya hakura ya tafi gida,
zuwa academic planing ya zamewa Hafeez kullum,
wata rana har yaje sau biyu duk ba sa'a,
ko ace suna meeting ko kuma ace yana office din VC..
Ranar friday karfe 11 suke da lectures din Maths method,
tun tara na safe ya shiga school ya wuce office din,
zama yayi a gurin yana jiran ganin ta inda zai bullo,
daga can nesa ya hangoshi yana tafiya sauri sauri secretary dinshi yana binshi a baya da jaka,
mikewa Hafeez yayi ya iso gurinshi ya tsugana ya gaishe shi,
dafa kanshi yayi hade da mishi alama da ya dago,
sannan ya amsa, yace "malam Hafeez har ka gama settling ko?
Cike da mamakin rike sunanshi da yayi yace "eh ranka ya dade, kullum sai nazo bana cika samun ganinka,
tafiya ya fara yi yace "Allah sarki, schedules din nawa ne are very tight, muje in baka card dina kazo gida ka sameni......
*Kaduna*
Cikin ikon Allah Nadeeyah ta fara sabawa da yan ajinsu mata,
bata saki jiki dasu a farko ba saboda gudun wulakancin masu kudi,
da taga kowa na shige mata sai ta fara sakin jiki dasu musamman *Haifa* da *Amal* su biyun nan su suka zama kawayenta,
tun da suka fahimci Sabrinah na jin haushin shigowar Nadeeyah cikinsu sai suka dauke Nadeeya a sit dinta suka maida ita gabansu,
duk jan ajin Sabrinah saboda ganin tana da kyau ta saukeshi saboda ganin yanzu duk yan ajin sun raja'a akan Nadeeyah....
" *Badariyyah Kyari* sisternki tana da kyau sosai,
Rukky Mama ta cabe da cewar bari kedai Aliya,
in muna tsaye a assembly kallonta kawai nakeyi,
na rasa cikin jinsin da ta fito, fatarta kadai abar kallo ce,
uwa uba yatsun hannu,
kamar sun sokawa Badariyya Mashi tayi saurin cewa "ba sister na bace dalla,
she is an orphan, kawota gidanmu akayi dan ta dinga tayamu aiki,
u knw Daddy is very generous, kawai yaga tunda mate dinmu ce why nt ya sata a school tunda dama ss3 zata,
she is our helper kun gane ko!!
Kallonta Rukky tayi tace "kaii amma tayi sa'a, ga kyau, gashi ta dace gidan ruko,
wallahi in tana wucewa gaban staff room malamai har leke sukeyi,
uncle Tahir ne kadai bai wannan saboda class dinshi,
shi duk yadda ake koda sabrinah bata gabanshi,
shiyasa wannan ma bata d'ad'ashi ba,
gajiya Badar tayi da jin maganganu akan Nadeeyah tayi saurin mikewa ta wuce hade da ja musu tsaki...
bayanta suka bi da sauri saboda duk yan koranta ne.....
Tsaye yake gaban class yana kallonsu daya bayan daya,
cikin harcen turanci yace "Ba tambayarku nakeyi ba,
kun shirya ma presentation and drama?,
groups biyu suka mike suka ce sun shirya,
sauran kuwa sukayi kwala kwala da ido,
group 3 and group 6 meye topics dinku, ya tambaya fuska a murtuke, "*PLAGIARISM* "Khalifa ya fadi hade da mika mishi printed papers din da suka hada,
kallon dayan group din yayi yace and you?
Cike da rawar jiki Sabrinah tace *DRAMA, FICTION AND IMITATION*,
hannu ya mika ya karbi nasu takardar sannan ya kalli sauran yan class din yace "Kowa yasan dis is your first CA test,
to yanzu saboda kun nuna you are not serious na maida shi first nd second and is over 40 no attendance marks,
yana kaiwa nan yace duk class din su tafi school Hall su jirashi yazo su fara presenting,
cike da tsoro sauran suka fara ihu suna fadin sorry sir,
wasu a cikinsu kuma suka tafi cafe dan shirya nasu ko baiyi yawan na sauran ba....
Karfe goma daidai group 3 suka fara presenting nasu,
cike da kwarewar turancinsu mai dadi na butters suka gabatar dashi,
saida suka gama tsaff kowa ya tafa musu harda observers,
Shirye shiryen na dramar group 6 suka fara,
saida suka kammala komai sannan suka fara presenting, definition din drama sukayi sai dan short fiction story of Beggars da illolin da irin wulakancin da mabarata ke fuskanta,
a karshen labarin ne suka ce "Yanzu zamu yi muku drama akan labarin da muka gabatar...
Nan jikin Nadeeyah ya fara rawa saboda tsoron turancinta ba irin nasu bane,
Sabrinah da Ishaq sune masu kudi,
sai Nadeeyah, Haifa, da Abdulhameed sune maroka,
Nadeeyah itace Makauniya tana rike da sanda,
sai Haifah kurmah,
Abdulhameed kuma gurgu,
cike da burgewa suka fara dramar akan stage,
da fari Nadeeya taji tsoro,
sai da Haifa tayi mata wuzuwuzu ta tunasar da ita marks din da zasu samu sannan ta saki jikinta,
da sanda take shafa kasa tana fadin "a taimaki almajira saboda Allah da Annabi,
cikin harshen turanci take magana ta karasa daidai inda Sabrinah da Ishaq suke zaune kan dadduma suna shan fruits ta tsaya,
"Hajiya a taimaka min da sadaka saboda Allah..
tsaki sabrinah tayi hade da daukar ayaba tace "Mabaratan nan sunyi yawa a kasar nan honey,
kuma mostly hausawa, kallon Nadeeyah tayi hade da watsa mata bawon ayaba ta cigaba da cewa "ku ko kunya ma bakwaji, da wannan barar da kukeyi ba gara kuje ku zauna a gida ku jira ranar mutuwarku ba tunda baku da amfani,
katseta Ishaq yayi yana murmushi ya daga malunmalun ya fito da dari biyar yace "sweetie,
in ba irinsu ta yaya zamu samu kudin,
Allah na bamu kudin ne dan ya turo su suzo su amsa,
yana mika mata kudin Abdulhameed da Haifa suka fito daga mabanbantan guri suna kokawar kwacewa,
ana haka har suka tura Nadeeyah jikin Sabrinah kamar yadda suka tsara a labarin,
Sabrinah na ganin haka ta mike hade da manta drama sukeyi ta tura Nadeeyah da iya karfinta,
ihu Nadeeya ta saki saboda kafarta daya ta sauka akan stage ta rinjayi dayar,
ga tsakanin stage da kasa akwai yar tazara,
runtse idonta tayi ta sadakar ko kafarta ta karye ko kuma ta samu mummunan rauni,
Bude idonta tayi da sauri saboda jinta hannun mutum da kuma jin bugun zuciyarshi alamar tsoro,
kallonshi tayi ta hango manyan idanuwanshi cikin farin glass sunki daukewa a kanta,
ajiyar zuciya tayi ta fara kokarin raba jikinta da nashi,
sai a sannan ya sauketa ya koma gurin da yake tsaye har lokacin zuciyarshi bugawa takeyi,
Husnah da Haifa ne sukayi saurin isowa gurinta suna mata sannu hade da hawa kan stage din inda Abdulhameed da Ishaq suke ta ma Sabrinah masifa,
itama jikinta yayi sanyi dan bata taba tunanin Nadeeyah zata fadi kasa ba,
hakuri Nadeeyah tabawa su Ishaq tace "mistake aka samu kun sani, kuma faduwar is part of the drama dan a nuna yadda mabaraci ke wulakanta,
in Allah yayi muna da rabon marks zamu samu koda 30 ne,
kalaman Nadeeyah sunyi matukar yin tasiri a zuciyar sabrinah,
nan take taji ta shiga ranta,
a zuciyarta tana auno da ita akayi wa haka da sai ta kusa yi ma mutum illa,
nan dai sauran groups din suka fara presenting nasu..
Kallonsu kawai yakeyi ba tare da yasan me suke cewa ba,
duk kakalen shi na lura da yadda suke fadin words a wannan lokacin bai bi ta kai ba,
hankalinshi kacokan ya tafi can wani guri na daban,
"Sir here is our presentation, Amal ta fadi hade da mika mishi papers din,
glass din idonshi ya cire ya share zufar fuskarshi yace "ku je ku kara shiryawa zuwa next week,
ki fada ma sauran groups din,
wani tsalle Amal tayi ta wuce da gudu tana announcing,
nan Hall din ya kaure da ihun maza da mata,
da ganin haka observers suka miko mishi takardu hade da mishi sallama suka fita...
"Uncle dafatan munci 40/40,
dago kanshi yayi da jin muryar Sabrinah,
papers ya fara hadawa yace "ko 20 baku kai ba bare kusa ran 30,
Nadeeyah da Haifah dake can nesa dashi gabansu ya fadi,
nan Haifa ta taho gurinshi da sauri tace "plss sir karka mana haka, plsss ta karashe kamar zatayi kuka,
gurin da Nadeeyah take tsaye ya kalla ya kula da yanayinta yace "minus 5,
hada baki sukayi suka ce "wayyo uncle,
"minus 2 ya sake fadi har lokacin idonshi na kan Nadeeyah,
a hankali ta fita daga Hall din dan kar ta cigaba da jin kayan takaici,
tasan kaddararsu ce haka,
in ba dagewa sukayi a exams ba dakyar zasu samu C,
ganin ta fita yasa shi fara tafiya yana fadin ko A kuka kara cewa sai nayi minusing,
yanzu dai kuna da 15/40,
gum sukayi suna binshi a baya fuska dauke da kukan shagwaba,
Bai ko kallesu har suka fita yayi hanyar office dinshi,
jin zuciyarshi yake ta mishi nauyi,
duk inda ya wuce yan mata sai sun gaishe shi cike da yanga,
ko kallansu bayayi bare ya amsa, shiyasa suka mishi lakabi da mai girman kai....
Kallon kwallon sukeyi Ruwaida na ihu tana fadin "wayyyo zata fita waje,
bin kwallon tayi da gudu tana nishin murna ganin ta sakko kasa, tana karasowa gurin taga kwallon a hannun Hafeez,
gurinshi ta iso cikin command tace "bani abuna!
Dariya yayi ya mika mata,
har ta fara tafiya ta waigo tace "gurin Yaya Jamal kazo ko,
to bayanan,
kaje can farm house ka sameshi,
yau dai bai zauna a gida ba bare ku hadu ku hanani mosti a gidanmu,
tana karashewa ta murguda mishi baki ta wuce,
bayanta ya bi yana dariya har taa kai inda Papy da mami suke zaune,
tun daga nesa Papy ya hangoshi suka sakarwa juna murmushi,
har kasa Hafeez ya tsuguna ya gaishesu,
cikin sakin fuska Mami ta amsa sannan ta mike dan bude musu parlon baki...
Hafeez ya ga karamci a gidan Alh Abdallah,
saida suka gama yar hira yaje ya gaida Anni sannan suka dawo parlon,
kallonshi Alh Abdallah yayi yace "Dafatan dai lafiya, naji kace kullum sai kazo office,
sosa keya Hafeez yayi yace "lafy kalau sir, kawai dama dan in gaisheka ne,
dadi Alhj Abdallah yaji yace "gaskiya ka kyauta, nima tun ranar da fara ganinka naji kamar akwai bond da ya hadamu,
saidai kuma ni---- katse maganar yayi hade da cewa Allah ne kadai ya hada jinina da naka,
dafatan zaka dunga zuwa kana gaishemu,
in shaa Allah Hafeez ya fadi bakinshi dake dauke da maganar da tayi mishi nauyin tambaya,
"a ina ka sauka ne? Papy ya kara jefo mishi tambaya,
cikin girmamawa Hafeez yace "ina hotel nan kusa da school, har yanzu ban samu daki ba, wadanda aka samu nesa da school ne sai kuma 2 bedroom ni kuma yayi min tsada da girma, amma ana cigaba da dubawa in an samu zan koma can,
gyara zama Alhj Abdallah yayi yace "zama a hotel ai kashe kudi ne,
in zaka yarda kuma zaka iya ka dawo nan gida akwai dakuna sai ka zauna har ka gama karatu,
cike da farin cikin karamcinsu yace "Nagode sosai sir,
Allah ya kara daukaka,
Ameen papy yace yana kokarin mikewa,
tabe baki Ruwaida tayi tace Papy ka fada mishi ni ce princess a gidan nan,
in yana son ya dawo sai ya yarda da bazai dinga min fada ba, kuma zai dinga kaini yawo kullum,
dariya sukayi Papy yace "ai shima ya sani, karki damu ranki ya dade,
sallama yayi ma su Mamy sannan ya wuce cike da farin ciki,
yasan yanzu ya zama kusa dasu zai samu cikakken labarinsu,
dan shi al'amarin kamannin suna rikita kwakwalwrshi, ace kamanni har a cikin 'ya'ya, abun yayi yawa.....
Mrs Tijjani Shattima....
[13/03 9:18 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣5⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Watanni biyar kenan ina dakon soyayyar dalibata,
dalibar da a kullum take kuka dani saboda tsauri na a gareta,
juyi yayi akan kujerar da yake zaune bayan ya gama furta wadannan kalaman,
agogon office dinshi ya kalla yaga sam baya mishi gudu,
ya kosa goma tayi yaje ajinsu,
A da zuwa aji yana mishi wuya saboda samm teaching ba layin shi bane,
matsa mishi mahaifiyarshi tayi akan lallai sai ya kula da makarantar,
ganin ya raina turancin malaman yasa shi daukar literature dan yara su samu ingantaccen turanci da kuma sannin yadda zasu kirkiri wani abu kamar labari domin dogaro da kansu,
goma saura minti biyar ya cire medicated glass dinshi ya goge shi sosai, ya maida idonshi, kwantaccen sajenshi ya shafa da hannu hade da gyara zaman hularshi,
danyen voile ne a jikinshi baki wanda ya amshi farar kyakykyawar fatarshi,
fuskar nan tashi sai kyalli takeyi, Allah ya bashi wani irin sirrin kyau da ido mai narkar da zuciyar mata,
duk wanda ya ganshi zai iya sanyashi a jerin yan 30's saboda jikinshi yayi daidai da shekarunshi,
har ya kusa fita ya juyo ya dauki script dinsu na second term c.a test,
arranging dinsu yayi, yasa nata ya zama na karshe,
da gangan yayi failing dinta a script domin yaga yadda zatayi, amma a record dinta ya bata full marks din da taci, yana dosar class dinsu hanyoyin sadarwa na jikinshi suka fara charge,
ganin fuskarta kadai kan sanyashi manta ko shi wanene,
wani irin so yake mata marar fasaltuwa,
tun daga nesa Sabrinah ta hangoshi ta fito da sauri ta karbi takardun hannunshi,
gaisheshi tayi cike da kwarkwasa tana shishshige mishi,
dan sauri ya kara yi yana amsata cike da basarwa,
Bayan ya amsa gaisuwar yan ajin idonshi ya sauka gurin sit dinta,
ba yadda ya saba ganin ta ya ganta ba,
nan zuciyarshi ta shiga damuwa, yaso ta'allaka yanayinta da lokacin sanyi ne ya sanyata labta mai a fuska, ta kuma kunshe kanta kamar mara lafiya,
a gurguje ya dan yi musu bayani akan topic din da yazo musu dashi,
yana gamawa ya fito da script din ya fara rabawa,
wasu suyi murna wasu su kunshe abin su,
saida ya gama da kowa sannan ya kira sunan Nadeeyah,
kamar mai tausayin kasa ta fito ta karba,
tana budewa taga 10 duk sauran zeros,
kallon shi tayi idonta ya fada cikin nashi saboda tunda ya bata bai dauke idonshi a kanta ba,
kauda idonta da yayi narai narai tayi,
nan take kwalla suka ciko su, kafin ta karasa gurin zamanta ta fashe da kuka marar sauti,
har lokacin idonshi na kanta, ganin hawayenta ne ya sanyashi daburcewa,
A dan ya fara magana yana yabawa da kokarinsu,
sannan yace duk wanda yaga ba'a mishi marking daidai ba ya sameshi a office,
yana cikin class din aka buga karrawar break,
permission ya basu na kowa ya je yai break,
takardu ya fara hadawa yana kallon su ta cikin glass dinshi, Amal na karbar script din tana fisgewa,
fita yayi a ajin yasan dole in ta duba ta sameshi a office..
Babu yadda su Amal basuyi da ita akan taje ta nuna mishi baiyi mata marking wasu guri ba tak'i,
tace musu babu mamaki shi din yaga banyi daidai bane shiyasa,
zan dage a exams,
cike da masifa Haifa ta fisge takardar tace "ni bari in kai mishi,
sai shegen hakuri kamar damo, an fada miki ana hakuri da marks ne,
bayanta Amal tabi tace " muje wallahi,
sai ya gyara mata,
kwala musu kira Sabrinah tayi da karfi,
tana haki ta karaso gurinsu da yoghurt da bons a hannunta,
karbar script din tayi tace "ku koma class in kai mishi, may be marking ya mishi yawa ne bai gani ba,
da kamar su karba sai suka ga itace class rep dinsu suka bar mata hade da nuna mata gurin da tayi daidai..
Excuse sir..,
bai dago kanshi daga kasa ba yace yes come in,
da sauri ta shiga ta tsaya a gaban table dinshi,
tsaki yayi a hankali da yayi gamo da Sabrinah, "lafiya, ya tambaya hade da mikewa kamar yana neman abu,
makale murya tayi tace "Sir akwai script din da bakayi marking daidai ba,
yarinyar tana can tana ta kuka, kuma ta san ta amsa