Showing 174001 words to 177000 words out of 184071 words
Chapter 59 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
Allah cikin ikonsa mun haďu da abinda muka shekara da shekaru muna nema.....
Kamar dai yadda na faďa maka Alh Mukhtar,
Taheer ďana ne,
kanina ne ya haifeshi, mahaifinshi Allah yayi masa rasuwa shekarun baya da suka wuce,
to yana zaune tare da mahaifiyarshi acan Canada,
wannan zuwan da mukayi, alkhairi ne ya kawo mu,
a yanzu da na fahimci wacece Nadeeyah sai nakejin kamar yau dinnan a kaddamar da komai a hutar da kowa,
domin ita din 'ya ce ga kowanne a cikin mu,
duk da na fi kowa karfi akanta a al'adarmu da kuma musuluncinmu,
yanzu a gurina nine mutum marar karfi akanta dukkanku nan kun fini karfi,
ku kuka san komai nata tun tasowarta,
Saboda haka Alhaji Mukhtar nazo gareka ina nemawa ďana *Taheer auren ďiyarka Nadeeyah.... *
yana disa aya fadawa suka yi mishi kirari haďe da miko mishi ruwa yasha domin yin magana mai tsayi...
Ya ilahi... haskowa masu karatu halin da daukacin yan uwa da masoyan Musaddiq halin da suke ciki..
A kiďime Musaddiq ya mike da zaman da Papy ya tursasa masa yinsa,
domin yaso bin bayan su Anty Saude da kuma Nadeeyar da ya tabbatar tana kitchen din...
Cikin kaurarrar murya yace
"whatt a jo----
da sauri Hilal ya toshe mishi baki haďe da kokarin maidashi ya zauna,
iya karfinshi yasa ya hankaďa Hilal ya tafi tagaga zai faďi..
Daddy da a ganinshi yafi Musaddiq din shiga tashin hankali yayi saurin mikewa ya rike Musaddiq dake shirin sake magana,
"Da aka fara magana kaji an kira sunanka?
Ko irin tarbiyyar da ka samu kenan?,
a gaban bakin mu wanda yake kamar Mahaifi ga Nadeeyah kake kokarin nuna musu irin rashin mutuncin da ka koya cikin kankanin lokaci ko?,
to bismillah,
in ka gama dasu sai ka dawo kaina.....
'Dago idonshi da ya zama kamar gauta yayi ya kalli gefen da Taheer yake,
da sauri ya kauda kanshi haďe da fara takawa baya a hankali,
cikin rashin sani yayi muguwar buguwa da bangon bayanshi..
Da gudu Hilal ya doso inda yake, kafin Hilal ya karaso ya juya ya haye sama da gudun da taku uku kaďai yayi ya isa ďakin da yake...
Dafe kai Papy yayi cike da tausayi ya kalli Daddy da ya koma ya zauna yana magana cikin karfin hali..
"Mashaa Allah ranka ya daďe,
na baku Nadeeyah,
Allah ya sanya albarka a cikin auren,
karku damu da sakarcin Musaddiq,
yarinta ke damunshi..
Cike da jindadi Sarki yace
"To madallah,
sai a yanke mana sadaki domin muna da nisa,
munfi son ayi komai cikin lokaci...
Wannan karan duk wani kuzari na Daddy ya kare da kyar ya iya cewa
"Da kai da kaya duk mallakan wuya ne,
ranka ya daďe duk hukuncin da ka zartar daidai ne...
Kuka sosai Anty Raliya ta fashe dashi na tausayin dan uwanta da kuma halin da taga mahaifinta,
daki ta wuce da gudu Husna ta rufa mata baya itama kukan takeyi...
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun... shi kaďai take maimaitawa tana faďin duk laifi na ne,
a tunanina in Nadeeyah ta dawo zata komawa Little,
ashe wata kaddarar Allah ya shirya mana daban,
Cikin kuka take bawa Husnah labarin komai da tayi wanda yake neman jefa dan uwanta cikin barazanar rayuwa....
Wani irin wawan mari Anty Reemah da ta biyo bayansu taji komai ta wanka mata..
cikin masifa ta fara zaginta tana kiranta da marar imani,
tasan inda Nadeeyah take tabar kowa cikin zullumi musamman Mahaifiyarta dake fuskantar rayuwar ukuba saboda hakan,
ta inda take shiga bata nan take fita ba..
Durkusawa Anty Raliya tayi cikin kuka ta bata hakuri da kuma amsar laifinta,
ita tayi shi ne in a good faith dan Nadeeyah ta samu ingantacciyar rayuwa,
ashee inganta rayuwarta zaiyi sanadiyyar shigar rayuwar Musaddiq cikin wani rudanin..... ta karashe cikin matsanancin kuka.....
Zama sukayi su ukun suna cikin jimami suna zubarwa da dan uwansu hawaye...
Minti goma kaďai su Sarki suka kara sukayi shirin tafiya,
Kallon Hafeez Shareefah tayi tace anjima suzo shi da iyalanshi su sameta..
cikin ladabi ya amsa mata da "To,
Adress ta karba gurin Taheer ta bashi cike da farin ciki.....
Katse wayar dake shigowa cikin wayar Baffa yayi karo na biyar ya tashi ya tafi yin rakiyar su Sarki shima jikinshi ba kwari,
kawai dai basu da bakin bijire musu ne dan suna da dukkan iko akan Nadeeyah,
ga kuma taimaka mata da sukayi, ya zama dole suma su rama musu halaccin da sukayi mata...
Kallonshi tayi cike da tausayi bayan ya gama nacin Junior yazo gurinshi yaki,
A hankali tace "Bari mu tafi *KYARI*
in shaa Allah gobe da safe zan kawo maka shi,
baka bani phn numbernka ba,
kai dai har yanzu kana nan da miskilancinka akan mace,
to ni na tambaya a bani,
Dariya yayi wacce da gani yake ce, ya fara faďa mata number,
Shafa kan junior yayi yace "Takwarana sai gobe ko,
ka zo da kaya da yawa dan rikeka zanyi....
Saida suka ga fitar motocin sannan suka koma ciki dukkansu babu mai karfin yiwa dan uwanshi magana...
*DADDY*
sunan da ya bayyana a jikin wayar haďe da special ringing tone,
Dauka Husnah tayi ta nufi kitchen da wayar,
can baya ta hangota zaune tana wasa da yatsun kafarta,
dafata tayi haďe da zama a gefenta,
Idonta da sukayi luhu luhu ta dago ta kalli Husnah haďe da kakaro dariya, zatayi magana kenan wayar ta sake kara,
Ajiye mata wayar Husnah tayi akan cinyarta ta kauda kanta can gefe,
ganin sunan ya tabbatar mata da junior ne da aikin nan dan tare suka siyo sim din Nigeria dashi,,
Saida ta kusa katsewa ta dauka,,
"Mamma..
ya faďi kamar karamin yaro..
"Uhmmm Uncle,,
tafiya babu sallama ko?
Kwantar da kanshi yayi a jikin kujerar yace
"Na daga miki kafa ne,
nasan yau baki da lokacin mu ni da junior,
kinga yan uwa bayan dogon lokaci,
just call to tell yhu
"I love yhu alot..
Runtse idonta tayi tace
"Uhum,
"Uhummm, say it plss,
ya faďi cikin kaguwa,
"Same to yhu..
Dariya yayi yace
"Muna nan zuwa anjima bayan isha'i, take care plss...
"Ohk uncle, in shaa Allah bye.. tana kaiwa nan ta katse wayar...
"Husnah kun dawo kaduna ne ko kunzo hutu ne?
Hannayen Nadeeyah Husnah ta kama ta fashe mata da kuka,
"Dan Allah Nadeeyah karki auri Uncle,
dan Allah karkiyi sanadiyyar mutuwar Yaya Musaddiq,
Sake dawo mata da ainihin labarin halin da ya shiga bayan tafiyarta tayi,
sannan ta kara mata da irin halin rashin walwalar da ya ke ciki har yau dinnan da ya ganta..
Da sauri Nadeeyah ta share hawayenta tace
"Walwala?
wacce yakeyi da FAIDA matarshi fa?
"Faida?
Husna ta faďi cike da mamaki,
Faidar da keda 'ya'ya uku?
Faida ai tayi aure bayan rabuwarku da sati biyu,
ta auri abokin yaya Musaddiq Zubair..
Cikin sanyin jiki Nadeeyah tace "Na gansu tare a gidanshi suna tsaye cikin annashuwa da jin dadi..
"Kwarai kuwa zaki gansu,
basu da nisa,
kinsan bayan rabuwarku Daddy ya saki Mummy,
sai ya koma lagos da zama,
duk wanda yaje gidan ita ke kawo mishi abinci,
may be kin samesu ranar da baki a gidan ne..
Shuru Nadeeyah zuciyarta ta raunana matuka,
tausayin dan uwanta Musaddiq ya ratsa dukkan sassa na jinin jikinta,
saidai is too late... wata zuciyar ta faďi mata yayin da ta tuno da irin halaccin Taheer a gareta,
Shanye kwallar da ta taso mata tayi tace
"Husnah, Allah ya kaddara zamana da yaya Musaddiq na ďan lokaci ne,
rabon da ya haďa mu gashi nan ya fito duniya,
kinsan an ce Matar mutum kabarinsa,
a yanzu bana tunanin zan iya zama da kowani namiji in ba Uncle ba,
dan All---
da sauri Husnah ta bar gurin tana fitar da kuka mai sauti...
Rufe fuska Nadeeyah tayi itama ta fashe da kukan da ya daďe da tokare makoshinta.....
Tun Hilal na bugun kofar dakin Musaddiq har ya hakura da bugun ya koma ban baki..
"Look Kyari,
don't harm urself,
ka bude min kofar nan, everything will be alright,
trust me....
Kamar da dutse yake magana, dan Musaddiq bai ma san abinda yake fada ba,
tsaye yake gaban madubi hannayenshi dukka biyu ya daurasu kan table din yana fitar da numfarfashi kamar zakin da ya hangi nama,
Kalmar
"Daddy da yaji daga bakin gudan jininshi, da kuma kalamanshi,
har kawo furucin sarki, sai amsa kuwwa sukeyi a kunnenshi,
runtse idanunwanshi yayi saboda wani irin yanayi da yake ji a cikin jikinshi,
kaunar Nadeeyah dake adane a majiya mai tsafta ta taso mishi gadan gadan kamar guguwa mai karfin gaske,
da sauri ya buďe idanuwanshi wanda hakan yasa ya daki glass din mudubin dake dakin saboda yadda yaga idon kamar jini dan tsabar jaaa....
A firgice Little Nadeeyah ta farka da tsananin ihu tana waigen ta inda karan ya daki kunnenta,
hango Musaddiq tayi yana sake bin glass din yana farfasa su da hannunshi da jini ke zuba..
a tsorace ta nufi kofar fita tana ihu tana kiran sunan Mahaifinta..
Muryar Hilal taji yana magana cikin ihu yana umurtata da buďe kofar,
dakyar ta iya dabarar da ta murďa lock ta buďe da sauri ta faďa jikinshi tana ihun kuka,,,
Mika ma Maleekah da karar glass ya tarkato su zuwa sama yayi ya nufi Musaddiq da gudun gaske,
Hilal na ta'bashi yayi wurgi dashi ya cigaba yin wurgi da kayan gaban madubin yana faďin
"i'm useless,
Daddy is right i'm a fool nd a looser,
bani da amfani a gurin kowa,
gara in mutu kowa ya huta da mutum marar amfani iri na...
Cikin kuka yan uwanshin ke kiran sunanshi suna hanashi ji ma kanshi ciwo,
duk suna tsoron matsawa kusa ya illata su,
Mummy kuwa da tasan duk itace silar hakan zama tayi a bakin kofa tana kuka ririsss,
Cikin zafin nama Daddy ya karaso cikin ďakin ya isa gaban mudubin ya juyo dashi da karfi ya daukeshi da kyawawan mari har guda uku,
yana shirin sake yin na hudu Baffa da Papy suka hanashi..
Cire hannun Papy Musaddiq yayi a jikin Daddy ya kai hannun fuskarshi ya cigaba da marin kanshi,
"Slap me to death Daddy,
Dan Allah ka mareni har sai mutuwa ta riskeni,
i'm dead already,
numfashin ne kadai ya rage,
wallahi ko baka kasheni ba,
ni zan kashe kaina....
Da karfi ya janyo gudan jininshi cikin kirjinshi ya rungumeshi tsamm yana kuka mai taba zuciya,
Sai a lokacin zuciyar Musaddiq ta karye ya soma rero kuka mai cike da sambatu.....
Mrs Tijjani Shattima.......
[22/06 10:21 PM] +234 807 161 1811: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 7⃣5⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Jugummm jugummm..
sukayi a parlon kowa da abun da yake sak'awa a cikin ransa,
fitowar likitan da Hilal ne ya sanya su nufarsu da sauri,
"Doctor yaya?
Hope all is well?
Daddy ya tambaya cike da damuwa,
Guri likitan ya samu ya zauna haďe da ajiye akwatin taimakon gaggawarshi,
"Ka kwantar da hankalinka Alhaji,
komai lafiya kalau,
jinin da ya zubar ne kaďai ya sanyashi zama weak,
amma ya farfaďo, saidai ya samu bacci, yana bukatar hutawa da kulawa sosai..
yana kaiwa nan ya kalli mutanen dake zaune a parlon,
ganin rabinsu duk mata ne yasa shi mikewa yace
"Alhaji anjima ka sameni a office, akwai abin da zamu tattauna, Allah ya bashi lafiya ya karashe yana dafa kafadun Daddy haďe da yin hanyar waje....
Kasa zama Daddy yayi ya bi bayanshi da sauri dan baijin zai iya kaiwa anjima baiji abinda yake son su tattauna ba wanda ya tabbatar akan ciwon ďanshi ne....
Hilal kuwa zama yayi a can gefe, hawayen dake zarya a idanuwanshi sun kafe saboda tsananin tashin hankali
"Ta ina zai fara,
wace hanya zai bi dan ganin ya samar wa Musaddiq abun da yakeso ba tare da hankalin kowa ya tashi ba,
yafi karfin awa ďaya yana tufka da warwara amma bai samo mafita ba,
runtse idonshi yayi saboda yadda yake jin nauyi a kan kirjinshi, dakyar ya iya mikewa da taimakon Maleekah suka koma can dakin da Musaddiq yake....
Cikin kalaman hikima irin na likita, Doctor Lawal yake wa Daddy magana,
"Ya taba samun attack a yanda na lura,
saboda halin da na riskeshi a yau ban taba tunanin zai rayu ba..
Alhaji Mukhtar,
ďanka na cikin critical condition, zuciyarshi na iya bugawa at any time,
dan Allah ku kula a daina sanyashi cikin damuwa sannan a taimaka a samo mishi abinda yake so,
Cike da damuwa Daddy ya dubi Doc Lawal bayan ya gama mishi jawabi yace
"Samun abin da yake so wannan na Allah ne,
nidai zanyi kokarin ganin ya daina shiga damuwa da bacin rai...
Shawarwari Dr Lawal ya bashi kafin suyi Sallama....
Parlon ya koma jiki a sanyaye yana tunanin kalaman Doctor, yadda ya barsu a parlon haka ya dawo ya samesu saidai wannan karan suna dan tattaunawa da su Papy...
Bayan ya zauna ne suka shiga kum kum wannan na cewa wannan tayi magana suna ki,
a tare suka daure dan suna ganin hakan shine kaďai mafita ga rayuwar Musaddiq domin zaifi samun kula daga gurin uwa..
"Daddy dan Allah kayi ma Mummy afuwa,
ta gane kuskurenta,
dan Allah kayi hakuri ka sassauta mata...
Kallon 'ya'yan nashi yayi fuskar nan babu walwala zaiyi magana muryar Baffa ta katseshi....
"Me ya faru Rilwanu?
Me ya samu gidan nawa?
To to to gamu nan zuwa yanzu da yardar Allah ya karashe haďe da mikewa,
mikewa su Daddy sukayi suna tambayarshi ko lafiya?
"To nima dai ban sani ba,
Rilwanu yace inzo gida ba lafiya, a hanzarce suka fita dan zuwa gidan suga abinda ke faruwa..
Mummy dake can sama gurin Musaddiq itama tayi saurin mikewa ta biyo bayan Radiya da ta kawo mata rahoto...
Da sauri Malam Mato mahaifin Rilwanu ya debo ruwa ya mikawa matarshi dake tsaye kan Goggo tana taimaka mata,
wani irin ihu takeyi tana fisgar gashin jikinta haďe da firzar da ruwan da ake zuba mata a baki,
"Gishiri,
Gishiri,
hakan ta dinga faďi tana zaro harcenta da yayi fari tass kamar mayya,
Gishirin rilwanu ya debo a cikin buhu ya kawo musu dan a tunaninsu ciwukan jikinta zata sawa,
yana kawo mata ta yafa kusan rabin kofin a bakinta,
A firgice suka fara kokarin kwace kofin suka kasa saboda a wannan lokacin karfin ba ďaya bane,
ko jariri ne wanda bashi da zunubin komai sai ya fuskanci barazanar wannan rana bare mutum irin Goggo wacce ta naďi kayayyakin bil adama marasa adadi...
Sarketa gishirin yayi ta shiga tari kirjinta na ďagawa sama kamar zai rabu da jikinta,
yaye zanin jikinta tayi saboda tsabar azaba ta mike ta fara zubar da kayan dakinta tana ihu sosai..
Halacci da iyayen Rilwanu suke ganin an yiwa dansu shi ya hanasu barin dakin duk ko da irin warin dake fita a jikin Goggo...
Wasu gungun hotuna ta zubo har gaban malam mato, saura kiris glass din da ya fashe ya taba kafarshi,
da sauri ya matsa baya ya tsuguna ya fara tattara hotunan ya umurci Rilwanu da matarshi da su riketa,
yana gama tattara hotunan ya ajiyesu a kan table zai komo gurinta..
Tsayawa yayi cakk ya waigo da sauri ya sake duban hoton saman wanda bashi da kala samm, dauko hoton yayi jiki na rawa yace "Ma'un Ukari,
*Nankwat Manasir*
shigowar su Baffa ne yasashi mayar da hoton da bazai taba manta ranar da akayi shi ba,
"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun..
shi kawai yake maimaitawa cikin ranshi tare da tunanin inda mutanen nan masu matukar karamci suka san mace marar imani irin Ma'u...
Mummy ce ta karaso ciki ta dauko zani dan rufe mata tsiraicin jikinta tana kuka sosai,
Baffa kuwa hannunta ya rike yana faďin
"Ma'u zauna kiyi ta salati,
a yanzu ihu ba naki bane,
da karfinta ta fisge tayi hanyar waje tana ihun da ko gida uku ne tsakaninku zakaji ta,
da azama suka bita suka rikota suka maidata daki suka garkameshi dan yadda take jiyar da mutane ciwo....
Malam Mato kasa rike abun yayi a ranshi yace
"Marar lafiyar nan itace Ma'u wacce naga hotonta da kananan yara biyu?
Da sauri Baffa yace "Eh itace, ka santa ne?
Juyayi Malam Mato ya shiga yana tunanin ta yanda zai fara sanar dasu abubuwan da ya sani shekaru da dama wanda babu wanda yasan dasu sai ubangijin talikai sai shi da ita kanta Ma'un,
Nufar inda yake Baffa yayi zaiyi magana sukaji ihun Goggo tana faďin
"Na shiga uku,
ku kira min Bokan Ukari yazo ya tamaikeni,
yagar naman jikina akeyi,
wayyo,
wayyo,
ku kirashi yazo ya taimakeni,
yayi min alkawarin bazan mutu ba,
yayi min alkawarin karashe rayuwata har kowa ya mutu ya barni..
"Mai kashewa shi ke tsoron mutuwa,
shin akwai adalci a cikin wannan?
Malam ya Mato yayi tambayar ba tare da jiran amsar kowa ba,
da sauri ya nufi dakin ya buďeshi domin a yanzu samm ya daina tausaya mata...
"Ai bai kamata wanda yake da karfin zuciyar sanadiyyar rayukan mu'imunai da dama tsoron mutuwa ba,
*JUMMA'ATU BABBAN RANA*
Ranar yin katako daga kauyen ukari zuwa Gembu,
*Ma'u yar gidan Manasir*...
Tunaninki zai iya tafiya shekaru hamsin da doriya suka wuce,
in kin manta ni bazan manta ba,
zan fara tuna miki in yaso sai ki karasa da bakinki..
Tunda ya fara maganar azababben jikin Goggo ya saki,
maganarshi tafi ciwon azaba...
"Harďejo,
Musulman kauyen Gembu,
suna Sallar Jumma'a...
ko zaki iya tuna abun da faru a ranar,
cikin dabara yace
"Faďin ainihin abin da ya faru shine kadai zai taimaki rayuwarki ki dawo kamar yadda kike da, sannan babu zancen mutuwa har sai dan kanki kinji duniyar ta isheki...
Saboda jahilci da kuma tsabar son duniya, Goggo ta fara faďin dukkan labaran da suka faru a baya,
har kawo mutuwar Atika da yunkurin kashe Papy da kuma irin ukubar da ta bawa Mamma Suwaiba, har yadda tayi ta raba Daddy da Mamma suwaiba ta hanyar asiri,
wannan confession din tayi shi ne cike da sa ran ciwon zai barta sannan bazata mutu ba,
ta sa rai bayan ta rayu zata yi asirin da zai mantar dasu komai...
*Goggo dai tazo duniya zama ne, tazo ne kawai ta karaci rayuwarta cikin asarar da lokacinta gurin yiwa wasu sihiri domin kawai gamsar da zuciyarta*....
Ajiyar Zuciya Malam Mato yayi ya kalli duk mutanen gurin da suka mutu a tsaye saboda jin rashin imanin Goggo,
"Alhamdulillah da Allah ya taimakeni ta faďi da bakinta domin inata tunanin yadda zan gamsar daku,
a lokacin da Ma'u ta sanar da yan ta'addan nan cewa akwai Musulmai a kauyen Gembu, bani da bakin magana domin na riga na ce musu ni ba musulmi bane, bayan mun shiga garin na saukesu sai na nufi can wani