Showing 99001 words to 102000 words out of 184071 words

Chapter 34 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

a mazaunanta,
yaron dake kula da ita ne ya sa mata wani pillow a gurin ciwon,


saboda tausayin halin da Hajja ke ciki ya sanya Shareefah sharar kwalla,


Dakyar muryar Hajja ta iya fita tace "sannunku da zuwa,
da kai suka amsa hade da gyara zama akan daddumar da dogarai suka shimfida musu,


saboda son jin abun da ya kawosu ko kyankyamin dakin basu ji ba,


"Daga ina ranka ya dade?
Hajja ta fadi baki na rawa,


Shareefah ce ta fada mata sunanta da dalilin da yasa suka zo gurinta,
bude ido Hajja tayi sosai ta kure shareefa da ido,

*SHAREEFAH YALLO*

kece?

murmushi Shareefah tayi tace "nice,
ashe ma kin sanni,

kuka Hajja ta fashe dashi tace "farin sani,
ni na raineki tun kina tsumma,

nafi shekara ashirin a gidanku tun kafin a haifeki,

ashe zan sake ganinki,

rabona da ke inaga in banyi karya ba yakai shekara arbain, dan tun kina shekara goma sha biyu na bar agadez,
ashe ina da rabon sake ganinki ta karashe da kuka hade da tari,


Cike da kosawa sarki Tidjani yace "sai hakuri Baba,
dama haka rayuwa take,
kuma duniya fadi gareta, wata rana in da rai dole a hadu,
yanzu gashi sanadiyar mutuwar UMMU AYYU Allah ya kawo mu gurinki,
yanzu bamu da isashen lokaci zuwa mukayi ki fada mana labarin da Ummu tace ke kadai ce kika san dashi,
labarin YARIMA,


wani kukan ne ya kufcewa Hajja a zuciyarta tace

"yau labarin da yayi shekara da shekaru a kunshe, hali yasa zata bayyana shi,
labarin da ya zame mata tamkar kwai a cikin zuciyarta saboda riritarshi,
ajiyar zuciya tayi tace
"babu mamaki fitar labarin nan ya zama silar samun warakarta,


Nuni tayi ma yaron dake kula da ita wani gurin dake cike da kaya,

mikewa yayi ya dauko wata jakar saka ya mika mata,

hannu na rawa ta karbi jakar ta dauko wani ginin mutum mutumi wanda yake kewaye da kawunan mutane babu adadi,


Saboda tsananin tsorata saida shareefah ta rungumi kafardar mijinta,
abun ba karamin tsoro ya bata ba kuma ya daga tsigar jikinta matuka,

yadda aka yanyame shi da wasu abubuwa kamar kwari yasanya har sarki jin tsoro amma kadan,


wani guri ta daga a gefenta, inda take ajiyar abubuwa,
nan ta mike dayar ruwa nabin bayanta ta fita tsakar gidan ta daki wani dakali dake kofar dakinta,


nan take gurin yayi rami, hannu tasa ta ciro layu masu tarin yawa,

daga can kasa ta hango kurciyar da suka binne shekara da shekaru kwance babu rai ga layu kewaye da ita,

a gigice ta ciro kurciyar da duk wata sai ta bata ruwa ta mayar ta rufe,
tun da ta kwanta ciwo kusan watanni takwas bata kara bi takanta ba domin itama ba lafiyar gareta ba,

girgiza kurciyar tayi tana kuka tana fadin
*YARIMA ADAMU*

wayyo Allah Kunzo a kurarren lokaci,
nasan duk inda Yareema yake a yanzu to kasa ta rufe idonshi,


wannan kurciyar rayuwar Yareema ce,
Allah na tuba,
wayyo ni Allah,
haka ta dinga fadi hankali tashe,



Da karfi ta saki mutum mutumin hanunta ya tarwatse a tsakar gidan,
nan tabi kowane kai ta cire dabaibaiyin da aka mishi,
runtse ido Sarki Tidjani yayi saboda juyawa da yaji kanshi nayi,
dakyar Shareefah ta tallabe shi ya zauna a kasa ba tare da duban dattin gurin ba,
itama hakan ce ta kasance da ita, saidai ita ta kasa fahimtar komai,
sabanin Sarki Tidjani da komai ya shiga yawo a kanshi,
yadda abubuwa suka faru ya dinga tunowa kamar yanzu ake yinsu,

kusa dasu Hajja taje dan itama wani karfi taji a jikinta,
burinta ta sanar dasu komai da suka sani da wanda basu da masaniya...




"Nasan yanzu wasu abubuwan sun fara dawowa a kanku da kuma daukacin mutanen da suka san Yareema a Agadez,
to saidai abin da baku sani ba shine dalilin da yasa ya kaurace muku ya tafi can wani guri inda babu wanda zai ganshi bare har yasa shi waiwayen gida,


"Adamu Yallo... sarki ya dinga maimaitawa a bakinshi,
fuskarshi yake kallo kamar yanzu suka rabu cikin lambun *Shehrah Agadez*,

ina dan uwanshi ya tafi har tsawon wannan lokacin,
yana kallon fitarshi daga lambun lokacin bakinshi yayi mishi nauyi ya kasa kiranshi bare har ya tambayeshi inda zashi,
sai yau yaji tunanin ya dawo sabo dal game dashi,


Da sauri ya maida idonshi kan Hajja yace
"ina Adamu?
Me ya sami Adamu?
Innalillahi wa inna ilaihir rajiun, me ya shiga kaina har na manta da dan uwa kuma aminina,
Ya salam ya fadi hade da dafe kai..




"Ba laifinka bane Yallabai,
Laifin namu ne,
bakai ba ma kowa a garin Agadez a yau sai ya tambayin dalilin da yasa ya manta da Yareeman da suke matukar so fiye da sarkin Kanshi...
har ke ma Shareefah,
a karancin shekarunki zaki iya tunawa da
*Yeeman ki* ,

*Yeeman Pappalinto*

nan take mafarkinta ya dawo mata sabo,
sunan Yeema take yawan fadi cikin mafarkinta,

wani irin kuka ne ya kufce ma Shareefah ta dinga nanata sunan a ranta,
tabbas ta tuno kuruciyarsu saboda mafarkinta bai rage mata komai ba,


cikin kuka tace "Bani labarin Yeema nah!
Bani labarin dalilin da yasa yayi nesa dani.....





*TUNA BAYA.......*



**********

Ranki ya dade kici abinci dan Allah,
rashin cin abinci zai iya zame miki illa,
kuma kin sani sarki bazai fasa abun da yayi niyya ba,


cikin Kuka Fulani Ayyu tace "Hajjara yanzu anyi min adalci,
ace sarki ya rasa da wacce zai hadani sai da

*Kuyanga Rosalin* ,

kuyangar da na bawa yarda tasan sirrina fiye da kowa,
tayaya zan iya kallon mutanen gari,

wannan ai cin mutunci ne a gareni da masarauta baki daya,


Gabanta Jakadiyya Hajjara ta dawo tace "ki kwantar da hankalinki,
ki barshi yayi auren,
zamu san yadda zamuyi da ita,

da kalamai masu dadi Hajjara ta kwantar mata hankali har taci abinci....




Wata hudu bayan auren *sarki Abdallah Yallo* da Kuyangarshi mai kula da komai na alamuranshi *Rosalin Mujdaha*

mahaifinta shine mai bawa sarki kariya,
bayan rasuwar mahaifiyarta mahaifinta ya bawa sarki ita domin ta zama mai aikinsu ta jikinsu wacce zata kula dasu,
garin binciken shi na rashin haihuwa Rosalin ta fado ciki har malaminshi ya fada mishi alherin da ke tattare da aurenta,
bai damu da kalubalen da ya fuskanta daga yan uwa da matarshi ba aka sanya rana, har Allah yasa ta zamo matarshi,


kyakykyawar gaske ce doguwa sambal,
ga biyayya da hakuri,
hakan yasa yake matukar kaunarta,
babu irin asirin da Fulani Ayyu batayi ba dan taga bayanta amma Allah cikin ikonsa duk ta tsallake,



saboda tsoron Fulani da Rosalin keyi hakan yasa bata fita ko nan da can,
duk abin da zai hadasu tana neman hanyar kaucewa saboda bata san tashin hankali,
mugun hakuri gareta ga kawaici da sanin ya kamata,



Babu wanda keda masaniyar tana dauke da ciki domin tsakaninta da bayinta yar kallon fuska ce,
ko mikewa a gabansu batayi,


A ranar da cikinta ya cika wata tara ranar akayi haihuwa a gidan,
wazirin sarki wanda ya zamo kani ga sarki,
a gurin barka ne kowa ya fahimci ciki gareta,
ranar Fulani mutuwa ne kadai batayi ba,
gaba daya kansu ya kulle ita da Hajjara suka rasa ta inda zata bullowa al'amarin..




Ranar suna Yaro yaci sunan *TIDJANI*,

A daren ranar sunan Rosalin ta tashi da nakuda,
sarki da kanshi ya sa aka kira unguwar zoman gidan ta karbi haihuwar,

yana daga bakin kofa yaji kukan jinjiri,

wani irin kuka ya fashe dashi na murna wanda yaki dauke mishi har saida yaji dumin danshi a jikinshi,
nan gaba daya gari ya dauka Sarki Abdallah Yallo ya samu magaji.....,



kwana goma akayi ana buduri a garin,
gidan kuwa zama yayi kamar gidan gala, domin cike yake tun safe har washe gari,
babu abin da akeyi sai ciye ciye da raye raye,
ko ina ka zaga cikin garin farin ciki ke dauke a fuskar kowa saboda sarki ya zamo mai kyautatawa a garesu....





Shekarar Yareemah Adamu bakwai rikonshi ya koma gurin Fulani Ayyu da tayi sanadiyyar mutuwar Rosalin da karamin ciki bayan barin da ta dinga yi,


sarki yayi kuka yayi bakin cikin mutuwar Rosalin mace mai matukar nuna kula a gareshi....



Duk yadda Ayyu takai ga son kuntatawa Yareemah Adamu hakan yaki yiwuwa saboda sarki yana sanya ido sosai akanshi,

sai kuma matar waziri mahaifiyar Tidjani wacce yake yini a gurinta bacci kadai ke maidashi gida gurin mahaifinshi,



Albarkacin Adamu Allah ya azurta Fulani da samun ciki a lokacin da ta fidda rai,

saidai kashh tayi matukar bakin cikin ganin ya mace ta haifa,

haka nan tayi ta dakon kiyayyar Adamu a ranta,


shi kuma Allah ya daura mishi kaunar yarta Shareefah haka itama Shareefan,
ko ina zasu tare suke zuwa...




Yana shekara goma sha shida sarki ya fara barin mishi kujera yana ganin yadda yake gudanar da al'amuran sarauta,


Adalin sarki Abdallah, ashe a lokacinshi bai kwatanta adalci kamar yadda Adamu ke kwatantawa yanzu ba,


Izza ta mulki da kasaita gaba daya sun tabbata a jikin Adamu,


wani irin farin jini Allah yayi mishi wanda ya sanya ko ina a garin ake maganarshi da yabonshi,


A rana in baiyi abun alkhairi sau goma ba to zaiyi fin goman,

gaba daya kowa a garin ya tabbata cikin walwala saboda zuwan Yareemah Adamu....




*Mummunan Kaddara*


Ranar da ya cika shekara Ashirin ciff, ranar kaddara mummuna ta afka mishi,
a ranar al'amura marasa dadi suka faru a cikin garin agadez....


*Yadda Abun ya faru*


Cikin farin ciki Sarki ke sanarwa da fulani Ayyu ya game shirin komai na hutawa ya barwa Yareemah kujerarshi,
sannan ya fada mata an kawo mishi yaran sarakunan da zai aura mishi saboda cikar kamalar sarki,

nan ta nuna mishi farin cikinta sosai harda cewa zata tayashi zabe a cikin matan..


Tana barin gurinshi zuciyarta kamar zata buga ta kira Hajjara,
nan suka kulla duk shirinsu na kawar da Abdallah domin a cewarta in ta kuskura ta yarda aka nadashi sarki kuma yayi aure wasu familyn zasu zama iyalan sarki su kuma su zama yan kallo..



Makudan Silalla ta bawa Hajjara ta shirya tafiya can kauyensu Sassoun burum,


cikin sa'a, da kuma lokacin akwai wani boyayyen al'amari wanda Allah ya boye a rayuwar Adamu Hajja ta samu bokan da yayi nasarar yin aikin,
ya kuma bukaci auren Hajja,
a take ta yarje mishi domin dama tana bukatar yin auren,
bayan sun kammala aikin ta koma agadez ta karbo sha tara ta arziki daga gurin fulani Ayyu....




Cikin Kuka Hajja tace "kudi ne wadanda basu rufe shekara ba suka kare suka barmu da wahala,

saboda muhimmacin Amana naki yarda in watsa asirin, amma fa duk wata tana bibiyar asirin kamar yadda mijinta ya koya mata....



Shuru gurin yayi bayan Hajja tayi shuru,
sai kuka dake tashi a gurin,



Murya a dashe Sarki yace
"Bazan manta ranar karshe da na ganshi ba,
ranar muna tsaye a lambu muna hirar sarautar da za'a bashi,
yana tsinko ma shareefah yalon lambu,
a kasa ya zubar da yalon ya nufi kofar fita,
yana kurewa ganina na bishi na hango Haroun da abokanshi, suna Kallon Adamu ya gifta gefensu babu wanda ya gaisheshi bare ya tambayi inda zashi shi daya...


Ashe abubuwan da akayi mishi ba kanshi kadai ya tsaya ba har dukkan mutanen agadez,

koda na koma gida babu wanda ya tambayeni shi kowa harkarshi yakeyi har sarki bai damu da tambayar inda yake ba domin babin yareemah shafewa yayi a cikin garin agadez,

Ya Allahu ina zanga Adamu,
ina zan ganshi....




Ganin kukan bazaiyi musu ba suka fita a gidan Hajja domin babu wani hukunci da zasuyi ma musaka irin ta,
hukuncin Allah ma ya isheta,


Motocin sarkin sassounburum suka shiga suka je gidanshi suka sallemashi sannan suka wuce airport din katsina domin hawa jirgi zuwa agadez, saboda sassounburum tafi kusa da garin daura....


Shawara suka yanke na baza malamai ayi adduar da Allah zai kawo sanadin haduwarsu in har yana da rai,
domin basu yarda da maganar Hajja na ya mutu ba....




*Bawan Allah Adamu tun a cikin garin Agadez ya fara watangaliliya, duk inda ya wuce babu wanda ke ganeshi bare har ya bashi girman dan sarkin da suke matukar so, har ya samu motar da zataje zinder, a can ma saida yayi shekara biyu yana wahala, irin masu shigowa daga kawo kaya daga kano zuwa zinder su yabi zuwa nigeria, A kano ma saida ya shekara daya da watanni har Allah ya hadashi da Alh jogana, nan ya kaishi gidanshi dake kaduna dan yi mishi gadi, anan ne ya bude shago har kaddara ta hadashi da Suwaiba, barin agadez, zuwanshi kaduna, haduwarshi da Suwaiba, rabo ne na ya'ya, wanda Allah swt ya boye wasu al'amura a garesu, Tabbas haihuwar da namijin da suwaiba tayi a farko rubutaccen al'amari ne, mulki na Allah ne, shine yake bada aronshi ga wanda yaso koda kuwa almajiri ne.......*




*A gurguje na takaita muku labarin Adamu saboda mu kai inda muke san zuwa a kan lokaci*


_Akwai shagalin biki a page fifty...... ku cinka_


Mrs Tijjani Shattima....
[02/04 11:39 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 5⃣2⃣
By *Aysha Ya'u kurah*






A gajiye likis suka nufo motar Musaddiq,
sanye suke da white top kowacce da sunanta a jiki, sai bakin skirt mai tsagu da takalma masu mugun tsini suma bakake,
saman kayan sun daura graduation gown da hularta gashinsu ya kwanta a gadon bayansu,
bude gaba Husnah tayi ta shiga tana maida numfashin gajiyar rawar da suka tika,
ita kuwa Nadeeyah kwanciya tayi a baya hade sakin ajiyar zuciya,
dariya yayi yace "ina Badariyya? Ko ta wuce gida,


"Tana ciki zasuyi class party dinsu yanzu,
yaya dan Allah muje gida,
kamar zan mutu ta karashe fadi tana kwantar da kanta,
tada motar ya fara kokarin yi suka ji an kwala kiran sunan Nadeeyah,
da gudu sabrinah ta karaso tana haki ta mika mata waya,
"uncle Taheer ne, wai in kawo miki,

kallon Musaddiq tayi wanda ya kure ta da ido,
tana ganin ya maida idonshi gaba tayi saurin karbar wayar,


"Assalamu alaikum ta fadi a hankali,
"wa alaiki salam my omri ya amsa hade da lumshe ido,
congratulations,
kin kammala matakin farko na karatunki,
in shaa Allah kin fara takasu kenan har karshen rayuwarki, hope kina kula da kanki sosa?

"umm kawai tace tana wasa da hannun kofa,

"Good, take care kinji,
naji dadi sosai da naji muryar da na dade banji ba,
Ina fatan ganinki soon in shaa Allah...
love yhu bye,


Bata bashi ba ta kashe wayar hade da mika ma sabrinah,
karba tayi ta wuce ba tare da ta kawo komai a ranta ba...


"Kin gama?
ya fadi yana murda key,

"ta gama mana yaya,
muje plss,

tada motar yayi ya figeta da wani irin mahaukacin gudu,


ya rasa dalilin da ya sanya wani abu yayi mishi karan tsaye a cikin kahon zuciyarshi,
menene yake shirin faruwa dashi,
tun tafiyarshi lagos kome yakeyi ita ke fado mishi,
har sabawa yayi da tashin da take mishi da asuba,

komi nisan baccin da ya tafi in yaji karar wayarshi yasan ita ce,
dan ita kadai ke kula da tashin shi,
in ko yaje cin abinci babu wanda yake a gani a gabanshi in ba ita da daddan girkinta ba,
yana matukar kaunar ganin yanayinta a duk lokacin da ya tsokaneta,


wannan dawowar da yayi week end domin ta yayi shi saboda a matukar takure yake,
kewarta na addabar shi,

Tufka ya dingayi da warwara akan abun dake shirin faruwa dashi game da Nadeeyah,
har ya isa gida bai tufka komai ba bare ya warware...


Bakin motoci ya gani a harabar gidan shiyasa yayi parking daga can baya,
da sauri duk su biyun suka karasa ciki saboda lalurar dake tare dasu,


wasu lafiyayyun mutane suka gani su uku,
manyan mata biyu sai wata tsaleliyar budurwa black beauty, hannunta rike da katuwar waya mai fadi tana ta latsata tana taunar cingam,
gaishesu sukayi matan suka amsa da murmushi,

yafito Husnah Mummy tayi da hannu tace "zo ki gaida Anty Aliya,
takalmi ta cire ta karaso kusa dasu ta gaida su,
shafa kanta Anty Aliya tayi tana murmushi tace
"Husnah ta girma,
waccen fa ban gane ta ba?
daidai lokacin Musaddiq ya shigo parlon,

"Yar step sis dina ce wacce ta rasu,
Ayya,
yar me kyau da ita,
Allah ya jikanta,
Ameen Mummy tace hade dayi ma Nadeeyah nuni da ido da ta wuce daki,
juyawa tayi ta murda kofar dakin nasu ta shiga,
kan gado ta kwanta tana mikar gajiya,

karar shigowar sakon da taji a wayarta shi ya sanyata sakin wani irin Murmushi hade da daukar wayar,
a yanzu shakuwar da tayi da Hilal ta wuce misali,
har ta kanyi mamakin yadda ta saki jiki dashi sosai haka,

saboda dadin da sakon yayi mata har saida hakoranta suka bayyana...



*Congrats to my young Barrister, bigger yhu i pray, i'm very Happy, more grads are coming in shaa Allah....*



Kiranta barrister da yayi shi yafi komai yi mata dadi cikin sakon, tunda ta fada mishi abun da take son karanta shikenan kullum sakonsu ya koma akan lawyers,



_Thank you yayana, Allah ya biya maka bukatunka duniya da lahira, yhu are an angel......_



Wani irin juyi yayi a kan makeken gadonshi,
"will be ur life soon Nadeeyah,
ya Allah, i can't resist it,
i have to tell her,
wani irin faduwar gaba yaji da sauri sauri,
Soyayyar Nadeeyah kullum kamar kara hurata akeyi a cikin qalbinshi,
baya tunanin akwai abin da zaizo ya rabashi da ita sai dai ko mutuwa,
a kasalance hannunshi ya rubuta.



*Akwai wani sakon da zan baki zuwa anjima, kiyi ma sakon tanadi, domin yanada matukar tsada da kuma muhimmanci, take ur time daga yanzu zuwa dare dan sakon yana bukatar nutsuwa, domin a nutse za'a isar dashi, 10pm dot...*



Kokawa ya fara yi da zuciyarshi,
wannan tana ka tura wancan tana karka saba alkawarin da ka dauka na saita gama makaranta zaka isar mata,
wata tana fadin karka bari ya huce domin zai iya kawo rabon wani,
tunanin shi na karshe ne ya sanyashi saurin turawa,

kashe wayar yayi gaba daya dan gani yakeyi kamar in a kunne take zata iya ganinshi,

wani irin nishadi ya yake ji,
ya tashi ya fita parlor gurin su zainab,
wasan da bai saba yi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login