Showing 57001 words to 60000 words out of 184071 words
Chapter 20 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
daidai,
murtuke fuska yayi yace "script dinki ne?
Girgiza kai tayi tace "nooo na Nadeeyah Adam ne,
zama yayi yace "ajiye takardar anan kije ki kirata tunda she is sure of wat she wrote,
ajiyewa Sabrinah tayi ta fita tana girgiza ko ina na jikinta,
ita dai Allah ya daura mata son Tahir,
kasancewarsu makota yasa tare suke zuwa makaranta,
komawa ne ba tare ba saboda baya tashi da wuri,
ya dade da harbo jirginta shiyasa ya kama kanshi dan samm baya san macce mara kamun kai a cikin maza,
ita kuwa Sabrinah ko wani namiji a school din yasanta saboda tsananin kyawunta da rawar kanta....
Tirjewa Nadeeyah tayi tace ita Allah ya kashe ta baza taje ba, zata dage a exams,
bazata iya zuwa office dinshi yana kallonta dayday yana wulakantar da ita ba,
ga turancinshi ya mata tsauri bama ta gane abin da ya ke cewa,
haka nan su Haifa suka hakura sukayi banza da ita su a dole sunyi fushi,
har aka tashi a gida basu kalleta ba,
kamar bakinsu na ciwo suka ce "Nadeeyah sai gobe Allah ya kara sauki,
share majinar hancinta tayi tace "kuyi hakuri ku fahimceni,
basu ko tsaya saurararta ba suka fita,
school bag dinta ta rataya ta fito itama,
a gurin sauka kasa ta hadu da Husna,
riko hannunta tayi tace "ya muran kin dan ji saukinta,
gyada kai Nadeeya tayi tace "da sauki,
muje mu jira malam Ali ya dawo daga kai Badar,
walhi yau muna zuwa gida zan fadawa mummy duk abin da Badar ke miki,
yanzu ki dubi yadda sanyi yayi miki mugun kamu,
saboda tsabar bakin hali duk ta jike bargon da kike rufa,
ni na rasa irin halinta, yanzu dole saboda mugunta kullum sai mun jira an kaita a dawo a dauke mu,
ko tausayin malam Ali batayi,
murmushi Nadeeyah tayi tace "kiyi hakuri karki fada, wata rana sai labari,
babu abin da bai wucewa a rayuwa,
muje school shop in samu tom tom insha,
suna isa Husna ta siyan mata tom tom ta hada mata da biscuit da maltina mara sanyi,
nasan baki fita break ba,
muje mu zauna a can in kin gama sai mu koma gate...
Tun yana kallon kofar shigowa har ya gaji ya dubi agogo yaga lokacin tashi yayi,
tsaki yaja ya mike ya kashe komai na office dinshi,
yasan bazata zo ba,
a ganinshi tafi karfin tazo tayi rokon cewa tayi daidai ne,
rai a bace ya dauki mukullin mota hade da rataya jakar laptop dinshi ya fita daga office din,
jiki a sanyaye ya tada motar ya fara tafiya a hankali,
yarinyar nan tane neman zame ma zuciyarshi damuwa,
yana gab da fita gate din ya hangosu,
atishawa take yi a jere masu zafi, nan idonta ya kada yayi jajur hade da fitar ruwa,
daidai inda suke yayi parking, sauke glass yayi yana jiyo Husna na fadin "wani irin lalacewa kuma malam Ali,
haba dan Allah, kasan Nadeeyah ba lafiya gareta ba,
ga rana gashi babu motar haya, dan Allah ka koma gida ka karbi mukullin motar Mummy,
rai a bace ta kashe wayar tana ma Nadeeyah sannu,,
baisan sunan Husna ba saboda bai daukarsu komai,
yadai san Badar saboda rashin mutuncinta ga dalibai ana yawan kawo kararta, kuma yasan gidansu daya,
"Hey Kyari,
babu wanda baisan muryarshi ba kaf cikin makarantar,
da sauri ta iso gurinshi tace "Yes sir, Good afternoon! "Hw u ya fadi yana unlocking motar hade da cewa "baku wuce gida ba?
yamutsa fuska tayi tace "driver yaje kai Badar on his way back motar ta lalace, yanzu dole mu jira shi ya koma gida ya dauko wata, and my sister is very sick,
saida takai aya sannan ya dauke idonshi a kan Nadeeyah yace "ayya sorry, Allah ya bata lafiya, kuzo muje in kaiku gida,
cike da murna Husna ta janyo Nadeeyah,
zasu shiga motar Nadeeya taja Hannun Husna, tace "in wani guri zashi fa,
ki kyaleshi mu jira malam Ali,
fisgewa Husnah tayi tace dalla shiga muje,
anan zaki zauna ciwon ya karu,
baya ta bude ta shiga hade da cewa "ina yini,
bai amsata ba yayi saurin rage A.cn motar hade da tada ta,
sunan unguwar ya tambaya, Husnah ta fada mishi harda adress,
duk yadda Nadeeyah ta kai ga matse atishawa abin yaci tura,
a jere ta dunga sakinsu,
ta mudubin gefe yaketa kallon yadda idonta yayi,
A lokacin in hankalinshi yayi dubu to duk sun tashi,
hanyar dialogue pharmacy ya dauka,
suna zuwa ya kalli Husna yace "ku jirani in siyo magani,
bai jira amsa ba ya fita,
magunguna ya siyo na mura kala kala kamar zai bude shagon su,
bayan ya biya kudin ne ya dubi yawan maganin,
sai a sannan ya fahimci yawansu, murmushi yayi yace "cire min wadanda suka fi kyau, emergency,
karba yaron yayi ya cire mishi masu kyau hade da rubuta yadda za'a sha su,
barin mishi sauran kudin yayi ya fito ya shiga motar,
Mikama Husnah maganin yayi, kafin yayi magana wayarshi ta fara ringing,
tada motar yayi ya daga wayar,
"Sweet heart,
kunya ce ta kama Nadeeyah tayi saurin kunshe bakinta,
hirarshi ya dinga yi yana fada mata yadda yayi missing dinta,
cike da shagwaba kamar bashi bane mai mugun tsare gida yace "yaushe zaki dawo, gidan is empty witout u darling,
basu jin abinda ake cewa a daya bangaren sai ji sukayi yace "Noo i won't accept that from u,
in baki dawo ba this week zan bar school ba kowa in biyo ki,
ita dai Husna burgeta yayi sosai na yadda yake kula da wacce ta kyautata zaton budurwarshi ce ko matarshi,
kallon ledar tayi taga magungunan mura,
murmushi tayi ta kalleshi bayan ya gama wayar tace "Sir kaima mura kakeyi,
bai kalleta ba yace "ni lafiyata kalau,
na siyo miki ne in mura ta kamaki kisha,
murmushi tayi dan ta gane Nadeeyah ya siyo mawa tace "bana fatan Mura, saidai nagode sosai zan bawa yar uwata ita murar ta kamata,
gyada kanshi yayi yace "kin kyauta,
daganan bai kara magana ba har ya kai kofar gidan da ta nuna mishi,
godiya Husnah tayi mishi ya amsa yana dan mata murmushi,
cikin sanyin murya Nadeeyah tace "Mun gode Allah ya saka da alkhairi, Ameen yace a cikin zuciyarshi,
a fili kuma murya can kasa yace "baki da matsala in kinyi failing test ko? It's well, na lura ai karatun bai dameki ba,
yadda yayi maganar ba tare da ya kalleta ba ya dan bata mata rai,
murda kofar tayi ta dauki school bag dinta tace "nasan bazakayi failing dina ba, ni nayi failing, shiyasa zan duba mistakes dina in gyara a exams,
tana kaiwa nan ta rufe kofar ta fara tafiya,
murmushi Husna tayi tace "haka take sir, ko cutarta akayi zata dauki kaddara tace haka Allah ya rubuta,
mun gode sosai, itama ta bude kofar ta fita,
kallo yabi Nadeeyah dashi,
ji yayi kara samar mata special guri a cikin zuciyarshi,
zai tada motar kenan yaga sun tsaya jikin motar da tazo shiga gidansu,
dariyarta mai kyau ya hango, nan ya shagala da kallonta,
bai kula da maganin da Husna ta manta dashi ba saida ya tada motar,
yana gani yayi saurin kashewa ya fito da maganin yayi hanyar shiga gidan,
da yake gate din a bude yake ya hangosu tsaye da wanda ya shiga da motar,
sanye yake da uniform din Nysc,
akwatinshi Nadeeyah ta dauka yayi saurin matsowa kusa da ita yace "bani yayi miki nauyi,
kin bashi tayi tace "a'a yaya Musaddiq babu wani nauyi,
kama gefen yayi yace "to mu kama,
ni kaina yayi min nauyi bare ke,
har sun kusa shigewa parlon mai gadin ya kwala ma Husna kira,
a tare suka waigo suka ga Uncle Tahir a tsaye a wajen gate,
ledar ya mikawa mai gadin yace ya ba Husna ya juya ya tafi gurin motarshi,
haka kawai yaji zuciyarshi ta rike Musaddiq,
ya rasa dalilin da yaki alakanta mu'amalarsu a matsayin yaya da kanwa,
shiga motar yayi ya fara tukata a hankali kamar baya san barin layin.....
Mrs Tijjani Shattima.....
[13/03 9:58 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 3⃣6⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Magungunan Musaddiq ya karba yace "waye baida lafiya, "Nadeeyah ce yaya, Husnah ta fada tana tura kanta cikin parlon,
kallon Nadeeyah yayi yace "yaushe kika fara ciwo,
cikin muryar mura tace "jiya, akwatin ya kwace a hannunta yace "shan ruwan sanyi da kuma A.c, sam bakwa kula da lafiyarku, ga hancinki nan duk ya zuge yayi ja,
Husna da ta ji me yace tace "walhy yaya laifin Badar ne, kasan a kasa Nadeeyah take kwana,
kuma Badar ta kure a.c,
bargon da take rufa kuma ta jikashi,
da ta gane ina matsa ma Nadeeyah ta kwanta sai ta fara kwanciya tana cike gurin ta barmin guri kadan,
kasan ko school zamu bata hada mota damu,
saidai aje akaita a dawo a dauke mu,
cike da mamaki Musaddiq yace "kuma Mummy ta sani,
a'a bata san tana kwana a kasa ba,
amma tasan ba tare muke zuwa school ba,
ajiye akwatin yayi a kasa fuskarshi ta bayyanar da bacin ranshi,
kallonshi Nadeeyah tayi tace "dan Allah kar kayi ma mummy magana,
zaman lafiya yafi komai, wata rana zaka ga kamar ba'ayi ba,
tausayi ta bashi matuka na yadda take magana,
maganin ya mika mata yace "je ki ci abinci kisha maganin sai ki kwanta, sorry kinji,
gyada kai tayi ta wuce dakinsu, tun daga kofa tayi karo da takalmin Badariyya,
tattaresu tayi ta ajiyesu a mazauninsu,
sannan ta dauke jakar makarantar itama ta ajiyeta a gurin zamanta,
tana cire kaya ta hada da na Badar ta zuba a washing machine, sannan ta fito ta karbi na Husna, bayin Husnah ta bita ta tayata zuba ruwa da sabulu ta murda tace "suje suci abinci,
duk abinda sukeyi Badar na kallonsu tana game a waya,
tsaki taja tayi juyi ta cigaba da abin da takeyi, sam bata da masaniyar dawowar Musaddiq,
duk zatonta motar malam Ali ce ta shigo, shiyasa bata fito parlon ba,
Abinci suka zuba suka ci sannan tasha magani,
a parlon suka kwanta Husna ta kunna tv,
tun suna hira sama sama har bacci yayi gaba da Nadeeyah..
Yana gama shiryawa shima ya fito parlon,
bai nemi abinci ba saboda baya jin yunwa,
zama yayi kusa da Husnah yana tambayarta abubuwan da suka faru bayan tafiyarshi service,
labarai ta dinga bashi na yadda Badar da su Anty Raudha suka sa Nadeeyah a gaba,
ba kamar ma idan Anty Radiya tazo, ta dinga kakalo aiki kenan tana sata kuma mummy tayi ta kallonsu bata cewa komai,
Allah yaya abin da akeyi ba'a kyautawa,
abin haushin ma shine in mukaje gidan Goggo,
in kaga yadda suke mata sai kayi mata kuka,
sai fa in Daddy na nan ne take samun sauki,
Anty Rally ce kadai in tazo zata fita yawo damu ta siyan mana abu iri daya da Nadeeyah, yawancin kayan sawanta ma Anty Rally ke dinka mata,
jinjina kanshi yayi yace "ashe dai har yanzu wannan zumununcin namu bai daidaita ba,
ashe har yanzu bamu zama daya ba,
kallon Nadeeyah yayi cikin tausayawa yace "Ya Allah ka kawo ranar sauyi cikin rayuwar wannan baiwar taka,
taga jarabawa iri iri kuma duk ta dangana, ya Allah ka rangwanta mata...
Suna zaune a gurin har aka kira la'asar,
kin tashinta sukayi saboda kar kanta yayi ciwo,
masallaci ya fita dan zuwa yayi sallah,
ita kuma Husnah ta wuce dakinsu,
tana shiga Badar ta fito parlon, jin kamshin turarenshi ya tabbatar mata da dawowarshi, shekeke ta kalli Nadeeyah tana baccinta hankali kwance,
kitchen ta shiga ta dauko swan mai sanyin gaske a fridge,
ko dar bata ji a zuciyarta ba ta bude ruwan taje saitin kunnen Nadeeyah ta kwarara iya karfinta,
wani irin ihu ta saki wanda ya janyo hankalin Musaddiq dake dawowa daukar wayarshi da ya manta,
da sauri ya karaso parlon ya tadda Badariyya tsaye a kanta, tana ganin shi ta ajiye gorar ta fara cewa "ni bansan tana gurin ba,
ruwa nake sha ya zubar mata a fuska,
karasowa kusa da ita yayi yaga fuskar Nadeeyan a jike tana ta murza kunnenta ruwan ciki ya fito,
bai tsaya tambayarta ba ya dago kanshi hade da daga hannu zai mari Badariyya,
da sauri Nadeeyah ta shiga tsakiya hade da rike hannunshi tace "kayi hakuri dan Allah, bata san ta zuba min ba,
wani irin kishi ne ya tokare wuyan Badariyya ganin hannun Nadeeyah a jikin Musaddiq din da ta ke kira da nata ita kadai,
cikin bacin rai ta cire hannunta a jikin shi tace "karki sake taba shi, ina ruwanki,
ke zai mara da zaki wani rike mishi hannu,
turata tayi tace "dalla fita a tsakanin mu,
dankwalinta ta dauka zata wuce daki Musaddiq yaja tsaki yabi bayanta yace "in ruwan ya shiga kunnenki muje kiga yadda zakiyi, murmushi tayi tace "bai shiga ba, ina goge gefen ne,
bata san ta nuna mishi ya shiga dan kar ta kara janyo matsala a tsakaninsu,
daki ta shiga ta tarar da Husnah na sallah,
bayi ta wuce ta bude pampo ta zuba ruwa cikin kunnen ta karkata, nan take duk suka biyo sauran ruwan suka fito,
alwala ta dauro itama ta fito dan yin Sallah...
A parlor kuwa bin bayan Musaddiq Badar tayi tana cewa "nifa ba da gangan na zuba mata ruwa ba,
kasan sharri irin na matsi--- katseta yayi ta hanyar nunata da hannu,
yace "wallhi zagi daya kikayi ma Nadeeyah sai nayi miki dukan da ban taba yi ma wani irinshi ba,
Sosai ta tsorata da yanayinshi, dan bata taba ganin bacin ranshi ba sai sanyinshi,
baya taja tana kallonshi har ya karasa gurin motarshi,
wani irin sonshi takeji yana ratsa dukkan sassan jikinta,
kaff fadin duniya ita har yanzu bata ci karo da namijin da yayi mata 100% ba irin Musaddiq,
ganin yanayinshi na yau ya kara dasa mata soyayyarshi a jinin jikinta,
ko wani yanayi yana da shi kenan,
sanyi da zafi, saidai sanyin yafi yawa dan sam baya da saurin fushi,
zai dade yana tara laifi yana ma mutum uzuri, amma duk ranar da ka kureshi shima yanada nashi zafin,
bai taba gano hakan a tare dashi ba saida ya hadu da wasu yan rainin wayau a gurin service.....
Kasancewar lahadi ranar hutu ce ya sanya su shiryawa zuwa gidan Anty Rally,
dama tun friday ta nemi suzo domin su tayata aikin kwalema, basu wani yi kwalliya ba suka sanya dogayen riguna kimono da gyalensu kalar kayan,
babu yadda Mummy batayi da Badar ba taki binsu dan sam basa shiri da Anty Rally,
sallama sukayi ma Mummy suka fita gurin Malam Ali da kafin su fito ya juyar da kan motar,
shiga sukayi ya jasu suka wuce..
A tsaye suka samu Anty Rally a kitchen tana hade haden girki,
tana ganinsu taji dadi sosai tace "yauwa maza ku zo ku karasa, turo baki Husnah tayi tace "ai sai ki bari mu huta,
"iyyyeee Anty Rally tace tana kallonta,
Dariya Nadeeyah tayi ta daura gyalen a kanta ta cigaba da aikin,
cike da jin dadin yadda take komai tsaf tsaf yasa Anty Rally cewa "kai Allah yayi miki albarka, Allah ya kaiki gidan hutu inda zaki huta babu wanda zai sa miki ido,
Ameen Husnah tace hade da cewa tare dani,
rankwashinta Anty Rally tayi tace "Dalla can zo ki hada kayan cikin wancen basket din,
ki jerasu tsaff bari in dauko hijab,
jerasu ta fara yi tace "ina zamu,
liquid anty Rally ta tsiyaya a hannunta ta wanke hannunta tace "gidan Anty Saude,
jiya da daddare ta dawo daga Holland,
shine zan shiga gaisheta,
wacce Anty sauden,
Anty sauden Legacy?
Husnah ta tambaya,
Eh ita, matar akwai kirki, tana daraja makotaka, Anty Rally ta bata amsa hade da wucewa daki ta dauko Hijab,
kayan suka dauka Nadeeyah ta rike jug din kunnun Aya suka fito suka wuce gidan dake jikin na Anty Rally,
Gida ne kayatacce wanda za'a iya sanyashi cikin jerin 1st 5 din gidajen masu kudin layin,
kafin ka karasa cikin main house din ma sai kayi tafiyar 5mins,
babu abin da kake ji sai motsin flowers da karan water fountain din dake tsakar gidan,
suna karasawa kofar palon Anty Rally ta tura suka shiga ciki,
wani irin kurda kurda suka shiga yi suna hawa sama suna sakkowa cikin wani under ground,
sanyin A.c da daddadan kamshi ne ya tabbar musu da isowarsu parlon,
cire takalmansu sukayi suka shiga ciki hade da Sallama,
kyakykyawar mace wacce a kiyasi zatayi shekara Hamsin da biyar ta amsa musu,
murmushi ta saki tace "Raliya ce a gidan namu,
kusa da ita Anty Rally ta matsa ta sauke Fadil tace "ina wuni Anty,
daukar fadeel tayi tace "lafiya kalau Raliya,
Fadeel dina yayi wayau,
ina babanshi,?
murmushi Anty Raly tayi tace "yana nan lafiya,
Hada baki Nadeeyah da Husnah sukayi suka gaisheta,
kallonsu tayi tana murmushi tace "lafiya kalau, ina kika samo kyawawan yara haka,
nuna Husna tayi tace nasan waccen bayan kamannin da kukeyi nasan tana zuwa Legacy,
waccen fa ta nuna Nadeeyah da idonta yaki daukewa a kanta,
itama kanwata ce Anty, cousin sis dina,
ayya, mashaa Allah, tabarkallah dasu, ta fadi har lokacin bata dauke idonta a kan Nadeeyah ba,
zatayi magana kenan ta jiyo muryarshi daga can cikin daki,
"Momma nifa wahala kike bani, ban ganshi ba,
dafe kanta tayi ohh gosh *TEE*
a cikin blue trolly fa nace,
cikin shagwaba yace "shi fa na duba babu,
"anya Tee glasses dinka basuyi expire ba ta tambaya cike da tsokana,
rufe akwatin yayi ya fito yace "ni fa yanzu ko babu su ina gani,
bai kula da su anty Raly ba ya kwanto ta bayanta yace "kin gani sweetheart,
babu su ko yanzu a idona,
dariya tayi tace "gaskiya ne babyna,
hannu tasa ta dauki glass din tasa mishi a ido tace "to yanzu koma may be ka iya ganinsu,
dagowar da zaiyi yayi tozali da wacce ya kira da damuwar zuciyarshi,
da sauri ya gyara glass din ya sake kallon inda take ko gizo take mishi,
ita din ce zaune tare da Husna,
kallon Fadeel yayi yace "Boy ina Mummy,
dariya