Showing 132001 words to 135000 words out of 184071 words

Chapter 45 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt

da shi,
dan tasan zai tsani Mummy da tayi mata zagon kasa da sauran yan uwanshi,
sun fi awa hudu suna aikin kafin su iya samun nasarar aikawa gurin Faida da har lokacin suke tare da Musaddiq,



Wani abu ne taji ya soketa wanda ya sanyata dauke hannunta daga kan kafaďunshi,
a lokacin shi kuma wasu zafafan hawaye suka shiga fitowa da cikin idonshi,
tausayinshi ne ya ratsata taji bata kyauta ba da ta raba shi da matarshi sabon aure,
tasan yadda yakeji saboda tana ganin yadda masoya sukeyi a film,
sannan ta tuna da rabuwarta da masoyinta Zubair wanda iyayenta suka hanata aurenshi saboda bashi da kudi,


"Kayi hakuri Musaddiq,

kwantar da kanshi yayi kan sit ya fara kuka mai sauti,

"kamar wacce aka tsikara ta fara faďa mishi abubuwan da suka shirya tun kafin aurenshi da Nadeeyah, har zuwa na yau bata rage mishi komai ba, har marin da Nadeeyar tayi mata sannan ta karashe da cewa is not late Musaddiq,
Kaje ka dawo da matarka, dan bazan boye maka ba, zaiyi wuya ka samu mace irinta mai kawaici da hakurin shanye abubuwa...


Tunda ta fara magana yake mata wani irin kallo na mamaki,
tana kaiwa aya ya dubi agogon hannunshi, biyar saura ya gani, bai tsaya bata lokaci ba saboda bashi da ishashshen lokaci yayi saurin cewa

"Muje gida plsss,

tada motar da sauri,

Revrse tayi ta ja motar da gudu kamar zata tashi sama,
burinta ta isa akan lokacin domin shirinsu na su koreta ne sai suce ita ta tafi da kanta bayan ta zazzagesu,

wayarshi ya dauka ya dinga kiran Nadeeyah yaji wayar a kashe,

dangwarar da wayar yayi haďe da dafe kanshi yana ta hango wautarshi,
magiyar da ta dinga mishi ya ke tunonowa.,
runtse idonshi yayi sosai hawaye na artabu a cikin kwayar idonshi,

"Me ya sameni,?
ya furta a hankali kamar me koyon magana,


Faidah da itama ta rasa abinda yake mata dadi cikin ranta tace
"Babu,
influence din mu,
plss forgive me,
am going outta ur life yau dinnan....


Suna isa kofar gidan ya buďe kofar tun kafin ta tsayar da motar,

wani irin turi yayi ma gate din ya bude dukkanshi,
gudu gudu yayi ya shiga ciki,

Tun a harabar gidan yake jiyo shewar su Anty Raudha,
bai bi takai ba dan shi burinshi daga ya shiga yayi tozali da Nadeeyah,

suna jin an turo kofar sukayi gumm suka koma gurin Mummy suna danna kafaďunta suna bata hakuri,


Taku uku yayi ya hau sama ya murďa kofar ďakin da karfi,
jin karan ruwa a bayi yasa shi sakin ajiyar zuciya haďe da maida numfashi,
matakin da ya shirya dauka akan yan uwanshi da mahaifiyarshi mai karfi ne,
dan kiriss ya rage su rabashi da abunda yake jin so a yanzu fiye da komai a rayuwarshi,
bayin ya nufa da sauri ya murďa haďe da sakin fuskarshi,
ganin bata cikin bayin yasashi fara dube dube yana kiran sunanta,
kayanta dake cikin dakin ya duba yaga wayam ba komai sai kamshinta dake manne a gurin,
da sauri ya koma daya dakin dan duba ko tana can tana kwashe sauran kayanta,
nan ma babu ita sai tsirarrun kayanta,
faďin irin tashin hankalin da Musaddiq ya shiga a wannan lokacin bata baki ne dan kuwa babu inda a jikinshi baya rawa yana dube duben inda zai ganta,


Kasa ya sauko da sauri yana kwala kiran sunanta,

matsowa kusa dashi Anty Radiya tayi tace

"Ka bar neman wacce ta mari mahai-----

Don't u dare...
ya faďi da karfi wanda ya tsorata dukkaninsu,
wani irin yanayi suka gani akan fuskarshi wanda basu taba sanin akwaishi tattare da kaninsu ba,

bai dauke idonshi a kanta ba yace

"Ina Nadeeyah?
ja da baya Radiya tayi dan ga dukkan alamu Musaddiq na iya dukanta domin yadda idanuwanshi suka canza launi jijiyoyi suka mimmike akanshi,


"Ta tafi Musaddiq,
nasan batayi nisa da gida ba,
zo muje mu nemota kafin lokaci ya kure...


kallon mamaki su Radiya suka bi Faida dashi,
basu iya furta komai ba har suka bar parlon..



Duk inda ya kamata su duba sun duba basu ga Nadeeyah,
gaba ďaya hawaye ma Musaddiq nemanshi yayi ya rasa saboda tashin hankali,
gidan Hajiya Zubaida nan suka je a karshe bata can,
duk tashoshin kusa saida suka duba basu ganta ba,
ko wayarshi dake ta ringing bai duba ba bare yasan wanda ke kiranshi...



Sake kiranshi Hilal yayi a karo na goma sha hudu har lokacin Musaddiq bai dauka ba,

Zubair ya kira a waya yace
"yazo ya daukeshi a airport bazai gane gidan ba,
ya kuma rokeshi da yayi sauri dan tun jiya hankalinshi yaki kwanciya,
Minti talatin ce ta kaishi airport din saboda gudun da yayi, gaisawa sukayi Hilal ya faďa motar suka nufi hanyar gidan Musaddiq....




Wani lungu Nadeeyah ta zauna a nesa da layinsu kusa da 3stars luxury Hotel taci kukanta ma'ishi, wanda har ya saukar mata da zazzabi,

wayarta da zata kira Papy ma sun kwace mata,
haka suka tasota a gaba ba ko sisi tare da sharadin kar ta nemi Daddy tunda ba ubanta bane shi,
akwatinta ta dauka lokacin gari yayi duhu ta fara tafiya tana neman abun hawan da zai taimaketa ya kaita tashar da zata samu a kaita Gombe....





"Kusan fifty seven million Momma,
but zasu cire 5m na workers sai 5m a each shareholders na gwamnati,
yanzu ina driving ne kuma is late gobe da safe zanje bank inyi transferring zuwa acc dina,
hope kina kula da kanki?,

gyara kwanciyarta tayi cike da jindadi tace

"sosai ma,
ga kuma wasu kudin sun shigo na sake kula da kaina da kai,
Allah dai ya jikan Abbanka,


"Ameen Momma,
na kusa karasawa masauki in shaa Allah,
su Aman ma sun shigo lagos gobe zamu taho tare,


"To Mashaa Allah,
sai kun zo Allah yayi maka albarka, take care,

"In shaa Allah bye..



Ajiye wayar yayi ya cigaba da tuki hankali kwance,
yana karya sharp bend din da zai sadashi da hotel din ya fara latsa hon saboda ganin mace na tafiya a saitin inda yake bata waige bare taga abunda ke bayanta,


Duk irin kokarin da yayi brake din ya taku ya kasa dan ya kure da yawa,
sai da yayi mata mummunan buguwa ya daki ginin gabanta kaďan sannan motar ta tsaya,


kwantar da kanshi kan sitiyari yayi yana maida numfashi sannan ne hankalinshi ya dawo inda mutane ke ihu suna tururuwa,
buďe motar yayi ya fito a gigice ya nufi inda ya buge matar,


dakyar ya iya kutsawa yana faďin ku taimakeni in kaita asibiti dan Allah,
sam bai kula da fuskar ba shidai ya kinkimeta iya karfinshi ya nufi motar da wani mutum ya bude da niyyar taimakawa.....






Subhanallah....
me ya faru a can gurin?
Hilal ya faďi haďe da lekowa ta window,
wani saurayi ya tambaya abinda ke faruwa,

"Wallahi wani ne ya yayi accident har ya buge wata yarinya,
kaii abun ba kyau yarinyar ta bugu, dakyar in zata rayu,


"Ayya, Hilal ya faďi haďe da maida kanshi cikin motar,
Allah ya kyauta gaba,
muje Zubair,

jan motar Zubair yayi suna addu'ar Allah ya tsare dukkan musulmin duniya....





Mrs Tijjani Shattima....
[25/04 9:12 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣3⃣
By *Aysha Ya'u kurah*






Ohhh Musaddiq...
pick my call,
Abbati ya faďi haďe da buga hannunshi jikin siyitiyari...

Wayar Raudha dake cikin motarshi ya gani bayan ya idar da Sallar magriba, abubuwan da ya gani a wayar su suka razana shi matuka,

"How can some1 be so selfish, meye laifin Nadeeyah da suke shirin tarwatsa rayuwarta haka,
dama tun jiya da daddare yaga take takenta, in aka kirata a waya sai tace text me,
duk iya hangenshi bai hango abinda suke kullawa har ya kai haka ba,
in har Raudha zata iya kulla irin wannan abun ga ďan uwanta da matarshi wacce itama ta zamto yar uwa a gareta, to wa zatayi sparing,

wani irin kyamarta yake ji a cikin zuciyarshi,
bazai taba son 'yayanshi su kasance tare da ita da wannan mugun halin nata ba,
da yaga Musaddiq baida niyyar daukar wayarshi sai ya kira wani abokinshi akan su ajiye mishi ticket din zuwa katsina,
gara ya dauke 'yayanshi ya maida su gurin iyayenshi,
ita kuma Raudha ya riga ya gama yanke hukuncin da zai zartar akanta,
duk wanda yace tukunyar wani bazata tafasa ba to tasa ko huruwa bazata yi ba,
kafin Musaddiq ya saki Nadeeyah shi zai rigashi sakinta,
may be ta shiga hankalinta,

Shi laifin Daddy ma yake gani,
ya za'ayi ya bar 'yaya haka sakaka babu kwaba ba komai,
har mahaiifiyarsu nada ikon zuwa a haďu a bata rayuwar wata da ita,

"tirrr.. ya zama dole ya rabu da 'yar mace domin dama mugun hakuri yakeyi da ita....

Tada motarshi yayi ya nufi gidan Musaddiq dan ya sameshi ya fita hakkinshi akan abun da ya sani kafin hak'an su ya cimma ruwa....

*its too late....*




Da..dd..y......,
ya faďi cikin shashshekar kuka haďe da zuwan wani kukan mai karfin gaske...



Gaban Daddy ne ya faďi ya mike daga kan daddumar da yake haďe da fita a masallacin gaba daya,


"Me ya faru Saaaadiq,

Musaddiq bai bashi amsa ba sai kukan da yake tayi karamar yaron goye,
kuka ne mai cin zuciya wanda ya karya zuciyar Daddy ya sanya shi neman guri a dakalin masallacin ya zauna,
saida ya barshi yayi kukan sosai ba tare da ya katseshi ba sannan yace


"Bana san sakarcin banza,
ya isheni haka,
i have heard enough,
faďa min abin da yake damunka?


"Nadeeyah...
sun raba ni da Nadeeyah..

Mummy da su Anty Radiya sun rabamu Daddy,
na saketa da bakina Daddy,
dan Allah Daddy ka dawo min da ita,
i can't live...
i can't...
ya karashe cikin kuka mai tsanani...



"Innalillahi wa inna ilaihir rajiun kawai Daddy yake faďi cikin zuciyarshi,
ko a mafarki bai taba kawo abun da zai kai Mummy lagos kenan ba,
duk tunaninshi bai kai nan ba,
tunaninshi kawai taje ta zuga danta ya auri wacce take so ne,
ya barta tayi kidanta ne in maganar tazo gurinshi tunda shine wakili ya barta ta taka rawarta,


Ajiyar zuciya yayi yace

"Kar ka bar Nadeeyah ta je ko ina,
ku shirya gobe tun safe taho gida,
nasan matakin da zan dauka...



"Sun koreta Daddy,
ban san inda zan ganta ba,
na duba ko ina ban ganta ba..


Duk da Daddy bai iya fushi da Musaddiq,
a wannan lokacin saida yayi mishi gigitacciyar tsawa haďe da mishi kashedin lallai duk inda take ya nemota, in ba haka ba wallahi sai yayi mummunan saba mishi,


kalmar da Daddy ya faďa mishi a karshe ita ta sake assasasa hawayen idonshi,

"YOU A LOOSER,
U DOS'NT DESERVE A SPECIAL SOUL LIKE NADEEYAH....



Yana jiyo kalaman da Daddy ke faďa mishi wanda yasan shima ba'a cikin hayyacinshi yake faďinsu,
bai iya furta mishi komai ba dan yasan ya tafka babban kuskuren da ya cancanci fin wannan zagin...



Kasa tashi a gurin Daddy yayi har aka gama wa'azin bayan sallar isha'i wanda suke saurara a kullum,
mutanen dake fitowa a cikin masallacin ma daidai yake kallonsu,
yana ganin kamar duk matsalolin duniya a gidanshi aka tarasu,
bai san lokacin da hawaye ke bin idonshi ba,

"Yaso Suwaiba saboda komai nata ya zamo abun so ga kowani da namiji,
yana ganin rashinta shine mafarin shigar rayuwarshi cikin kowani irin kalubale...

Ya nemawa danshi auren yar da yake jin sonta fiye da 'yayan da ya haifa a cikinsa, saboda danshi ya samu zuri'a daga gareta kuma rayuwarshi ta inganta,
sun rabashi da ita, same mutanen da dalilinsu ya hanashi samun abun da yakeso a baya sune dai har yanzu dalilinsu zai kuma hana danshi abun da yake so,

*Tarihi ya maimaita kanshi*...

Hukuncin da zuciyarshi ta gamsu dashi shi ya yanke ba tare da duba tsufa da tarin yaran da suka tara dashi ba,
dakyar ya iya mikewa ya nufi gida zuciyarshi kamar ana soyata saboda gashin kumar da yakeji a cikinta......





Kashe motar Zubair yayi yace

"Muje dai tunda ka matsa,
dama amarya tamin gorin ban taba cin abincinta ba..


Dariya Hilal yayi ya saba jakarshi a baya suka wuce cikin gidan,


Tun kafin su karasa suke jiyo muryoyi ana maida magana kamar karnuka,


kalmar da ta da ta doki kunnen Hilal ita ta sashi yar da jakar hannunshi haďe da murďa kofar parlon...


*Da ya saketa ai ku kuka koreta, ku kuka ce zaku koreta kuma kuka ce mata kar ta sake shigowa cikin rayuwarku, saboda haka ku zaku nemota ko in tona muku asiri wallahi...*



Cikin rashin sani yake kallon wacce tayi maganar dan bai santa ba,

shakar da Raudha ta kai mata ita tasata sakin ihu sosai tana neman ceto,
dukkansu basu san Hilal da Zubair sun shigo parlon ba..


"Dan ubanki saboda wa mukayi?

Saboda ki aureshi muka sanyashi ya saketa kuma muka koreta a gidan,


Fisgewa Faida tayi tace
"Saboda kwaďayi dai,
kwadayin abin duniya da kuma kuna ganin Nadeeyah babu wani nata zai zame muku gata,
ni kuma kunsan waye mahaifina,
in banda son abun duniya waye zai ki Nadeeyah ya daukeni,
ta fini komai na dan adam,
ciki harda halin kwarai,
ranar da muka kwashe naman miya muka boye batayi yunkurin kare kanta ba saboda girmamawa kuma tasan ku kuka dauke dan ta ganshi daga baya,
hakan baisa tayi yunkurin tonaku ba,
ku kukayi ma kanku dan ni ko Musaddiq kadai ya rage namiji a duniya bazan aureshi ba, banason zama da mijin da baya sona,
gara in nemi wanda zai soni in soshi...


"Dan bakya son Musaddiq yanzu shine zaki faďa mishi duk abun da mukayi dan ki haďa ni da ďana?

Mummy ce tayi maganar cikin kunan rai da nadama,


"Gara in faďa mishi yasan lallai fa uwar da ta haifeshi bata kaunar farin cikinsa,
domin da kina kaunarsa bazaki rabashi da matar da ko sati biyu batayi a gidanshi ba,
kuma kinsan irin son da yake mata,

uhmm ni am out of this trash ku karata can,
gida zan wuce,
tana kaiwa nan tayi gaba abinta,


Bin bayanta Radiya tayi ta janyota haďe da ďaga hannu zata kwaďa mata mari,

kammm... taji hannunta alamun an rikeshi,

waigawa tayi dan ganin wanda ya rike hannun tayi tozali da Hilal wanda idanuwanshi suka zama kamar jini saboda tsabar jaa da sukayi,


wurgi yayi da hannunta wanda ya sanyata yin baya tagaga zata faďi,


Buďe fuska Faida tayi saboda rashin jin saukar marin a fuskarta,

ganin Hilal ya nufota yasata yin baya da sauri,

kamo hannunta yayi da karfi har ta kusa missing step zata faďi,


parlon ya dawo da ita ya zaunar da ita dabass kamar wanda yayi wurgi da kaya,
nan idanuwanta suka firfito waje tayi saurin cewa

"Waye kai?
In kaji min ciwo fa?
Akan me zak----


Shut up.... ya faďi da karfi har saida kirjin Mummy ya buga,

Zama yayi yana facing dinta haďe da daukar waya dan kiran Musaddiq yaji inda yake,
karar wayar yaji a parlor haďe da sakkowarshi daga sama a hankali kamar wanda aka zarewa laka...



Maida kallonshi gurin Faida yayi yace
"Bance ki rage min ko kalma daya ba,
bance ki mance komai ba dan in kin mance u will be in for it, komai da ya faru nakeson ji nd lastly...
ina Nadeeyah?




Kamar jira takeyi ya rufe baki tace
"cikin sauki ya kamata ka tambayeni ba sai ka kusa yi min lahani ba,
in dai wannan ne zan baka labarinshi, harda shirin gaba da mukayi....



"Ba kai ba,
uwarka ma bata isa ta shigo gidannan a yanzu tasan abun da ke faruwa ba,
Musaddiq ďana ne,
ni ke da ikon zaba mishi abin da nasan zai fi dacewa da rayuwarshi,
kai waye da kake tunanin zaka iya interfering cikin rayuwarshi a koda yaushe...



Runste ido Hilal yayi dan bashi da wani kuzarin da zai iya amsata,
sake duban Faida yayi zaiyi magana yaji sautin Muryar Musaddiq


"Ni ba danki bane,
karki sake taba ni,
babu uwar da zatayi ma ďanta haka,
a da ina ganin babu wata mace da ta kaiki son 'ya'yanta,
ashe ke din mace ce mai son zuciya,
i hate you, i hate u..
hakan yayi ta maimaitawa haďe da durkushe a gurin....




Share hawayen da ya ďigo mata tayi tace

"Taimakonka nayi,
bazaka gane hakan ba sai nan gaba,
yanzu nasan fushi ne da kuma shaukin dafin son da ta ďiga maka,
da sannu zata fita a ranka ka gane gatan da nayi maka,
kai kanka ka faďi
"bata da asali,
kasan kenan bata dace da mai cikakken asali irinka ba...




Hannayenshi duk biyun ya daura akanshi yana girgiza kanshi hawaye na bin idonshi,
kalmar *bata da asali* ita ta dinga yawo akanshi,
rarrafawa yayi ya isa kusa da Musaddiq,

"Nadeeyah bata da asali Musaddiq?
Kai da bakinka ka fadi cewa bata da asali?
To ina take?

Ina Nadeeyah take....
ya faďi da karfi haďe da shake wuyan Musaddiq..







Da sauri Zubair da tunda ya shigo yake tsaye cike da mamaki ya fara kokarin banbare Musaddiq daga hannun Hilal,
dukkansu hawaye ne ke zuba a idonsu,
ture zubair yayi da karfi yace

"He promised to take care of her,
ina ya korata?
Ina ya tura marainiyar Allah,
just 9days of their marriage,


Meyasa bai kyaleta ba tunda yasan bazai iya ba?
meyasa ya zabi ruguza rayuwarta at this early age?

he shud have lv her for me in yasan shi bazai iya ba,
shi kaďai ne wanda zan iya sadaukarwa da abinda na dade ina dakon so,
why did u do dis to her,
Why Musaddiq?

Ya karashe cikin ficewar hankali haďe da kwantar da kanshi a gurin....



Nan kallo ya koma gurin Hilal wanda ke kuka mai ban tausayi,


Share hawaye Musaddiq yayi jikinshi na rawa ya durkusa gaban Hilal yace

"Hilal----

Don't ask me anything Musaddiq, u are very useless,
baka da amfani a rayuwarka bare ka amfani wani,
you are a Coward...
Irresponsible human bei---


Toshe mishi baki Zubair yayi da sauri yace
"wannan abun da kukeyi bazai taimaka ba,
gara mu fita mu nemo ta kafin ta shiga wani hali...



Babu inda ďana zashi Mummy ta faďi tana rike hannun Musaddiq,


A hankali ya zame hannunshi yace

"Sau biyu kenan zan maimaita,
ni ba danki bane,
kin daina amsa sunan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login