Showing 129001 words to 132000 words out of 184071 words
Chapter 44 - ZUMUNCIN MU A YAU Complete By Aisha Yau Kura.txt
bakinta cikin nashi dan ta kwantar mishi da hankali...
A wannan daren da su Mummy ke kwance cikin farin cikin fara samun nasara,
a wannan daren su kuma ma'auratan suka sake samun shakuwa mai karfi a tsakaninsu,
wanda suke ganin in har wani abu yayi sanadiyyar rabuwarsu to fa zasu iya rasa rayuwarsu.......
Washe gari tun shida na asuba Nadeeyah ta shirya ma Mummy breakfast mai rai da lafiya haďe da farfesun kaza,
A kofar kitchen din ya tsaya yana kallonta cike da shauki,
sai a lokacin ya sake tabbatar da jiya matsala aka samu,
Haďe komai tayi cikin warmers, tana wanke hannunta taji ya kwanto ta bayanta,
murmushi tayi tace
"yauwa plss ka siyo kunun tsamiya sai a dama ma Mummy, kasan tana son karyawa dashi,
Lumshe idanuwanshi yayi yace
"nooo muje ki huta,
gobe sai kiyi mata kunun,
gyaďa kanta tayi tace
"ko dai kaima yunwar kake ji?
daukarta yayi yace
"sosai ma,
amma kinsan bana karyawa da wuri,
"Daukata baya maka wuya,
abinci zan fara ci inyi adding weight in ka daukeni kayi ta nishi, dan Allah ka saukeni kar wani ya fito ya ganmu,
tafiya ya fara yi yace
"in an ganmu ai da matata aka ganni,
ni bacci nakeji,
muje ki tayani,
Sun kusa step din karshe Mummy ta fito daga ďakin da ta kwana,
kokarin sauka Nadeeyah tayi ya sake riketa yana dariya,
"Wai kunyar ki take ji!
runtse ido Nadeeyah tayi tace
"Dan Allah ka saukeni,
a hankali ya sauketa yace
"Good morning maa,
Cike da danniyar maida danta bawa da taga Nadeeyah tayi tace "morning my dear,
"Ina kwana Mummy,
Nadeeyah ta faďi bayan ta tsuguna kasa,
"lafiya kalau Nadeeyah, ya gajiyarki,
"babu gajiya Mummy,
ga breakfast can ko nan zan hawo miki dashi,
"a'a barshi a can,
zan fi jin dadin karin a can,
Gefe suka matsa dan bata guri, ta wuce tana tunanin ta inda zata sake bullo musu,
ya zame mata dole tayi abun da zatayi yau zuwa gobe dan jibi zata wuce......
Ranar throughout Nadeeyah bata basu wata kofar da zasuyi complain ba,
kome zatayi a tsantsane take yinshi saboda bata san abin da zai kara sanya mijinta cikin bacin rai,
duk yadda Faida taso provoking dinta taki yarda ta kulata dan bata da lokacinta,
Cikin dare suka tashi suka shirya kulle kullensu,
sannan daga can wani bangaren da basu masaniya ana taimaka wa aikinsu.....
*(Kana Bacci ana maka nasari)*
Mrs Tijjani Shattima.....
[22/04 8:08 PM] Aysha Ya'u Kura: •• *ZUMUNCINMU A YAU* •• 6⃣2⃣
By *Aysha Ya'u kurah*
Kamar kullum yau ma tun uku saura ta farka dan yin sallar Nafila,
wata iriyar kasala ce ta sauko mata wacce ta hanata barin kan gadon,
zaune tayi tana gyangyadi har huďu ta gota,
da ta gaji da gyangyaďin sai ta ja pillow ta kwanta riris,
bacci mai nauyi yayi gaba da ita...
A kunnenta aka sallame sallah a masallacin kusa dasu,
mikewa tayi jiki ba kwari ta nufi bayi dan yin alwala,
sai da tayi minti goma akan toilet tana bacci sannan ta buďe ido da kyar tayi tsarki ta mike ta kunna pampo tayi alwala kamar me tsoron taba ruwan,
koda ta fito daga bayin zama tayi a kan kujera tana tuno mafarkin da tayi wanda ya kashe mata jiki matuka,
mafarkin ya taba ta sosai dan a iya saninta mafarkin dariya bai taba zama alkhairi ga mai yinshi, bare ita da taga dukkan wadanda suke nuna mata kiyayya kewaye da ita suna kuka ita kuma tana tsakiya tana kyakyata musu dariya mai sauti harda kaiwa kasa,
gefe kuma Musaddiq na zaune shima dariyar yakeyi yana kurbar juice,
dariyar da sukayi a cikin mafarkin kamar wadanda aka saukar musu da wahayin yinta, haka kukan da su Mummy keyi kamar wadanda suka rasa wani sashi na jikinsu,
Anty Reemah, Hilal, Hafeez da Husnah kuwa suna tsaye rai a bace suna masifa kamar zasu ari baki,
shigowar Daddy da Papy shi ya farkar da ita...
Tunda ya farka ya lura da yanayinta,
bai kulata ba ya nufi bayi yayi alwala dan yaga garin har ya fara haske,
a yadda ya barta haka ya sameta, wannan karan idonta a rufe yake wani baccin take son sake yi, gyara hannun jallabiyarshi yayi ya zauna a gefenta haďe da taba kanta,
a hankali ta buďe ido ta kalleshi,
"Har ka idar da sallah?
Kwantar da kanta yayi kan kafaďunshi yace
"yanzu zanyi,
shine baki tashe ni ba ko?
Cikin magagi tace
"Nima banyi sallah ba,
bacci ya hana ni,
zaunar da ita yayi sosai yace
"whatt,
ba dai bacci ba,
sai dai shaiďan,
tashi maza muyi sallah,
Mikewa tayi jiki ba kwari tabi bayanshi sukayi Sallar,
suna idar da sallar taji duk wani baccin da takeji ya tafi,
sai dai kasalar da ta kasa barinta,
Bayan ta gaisheshi ta fita dan zuwa kitchen haďa ma Mummy break fast,
karar tv da taji shi ya bata tabbacin akwai mutane a parlon,
a nutse ta karasa saukowa ta nufi parlon dan duk tunaninta Mummy ce ko Anty Radiya,
turuss... tayi tana kallon Faidah wacce ke kwance daga ita sai mini skirt da wata yar riga wacce iyakarta cibi,
kwanciyar da tayi bai boye komai na surar jikinta ba,
kirjinta kuwa ya bulluko kamar zai faso rigar kayan kirjin su fito,
Saman ta kalla taga ko Musaddiq ya biyota, ganin baya gurin yasata saurin karasawa gurin Faidah rai a bace,
gaba daya tsoron da takeji nata ta nemeshi ta rasa,
"Baiwar Allah,
gidan nan ba na mata bane zallah akwai maza, dan Allah ki tashi ki canzo kaya,
Mikewa Faidah tayi tana murmushi tace
"Ba matsala bane dan ya ganni a haka,
musulunci ma ya yarda in kana neman auren mace ta bayyana maka surar jikinta kafin ka aureta,
karki damu dani je kiyi cookun ki,
Ran Nadeeyah in yayi dubu to duka sun baci,
baki yin kanshi yakeyi,
bata san lokacin da bakinta ya furta cewar
"Ke bakiyi kama da tsarin matan mijina zai ruďe akan surarsu ba,
bance shi nawa bane ni kadai, amma fa ki sani ko zaiyi wani auren sai dai ya nemo wacce ta fini ba wai ya koma baya ya dauko wacce bata kaini ba...
"Ahayyyyyeee.....
Faidah ta faďi tana tafa hannu,
wacce ta fiki me?
kyau?
Kudi?
Asali ko me?
Ko dayake banda lokacinki,
nasan a cikin abun da kike takama dashi nafiki su 99%,
Asali shi kadai zaka fini ka cuceni,
Faďa min menene asalinki?
Waye mahaifinki wanda ya kamata ya zamto ado a gareki?
Waya sani ma ko irin yan fashin shanun nan ne aka buďe musu wuta suka arto nigeria neman maf---
Zazzafan Mari Nadeeyah ta sauke a fuskar Faidah wanda saida ta dauki lokaci mai tsawo tana tattaro confidence dinta kafin ta iya aiwatar dashi,
sauke marin yayi daidai da sakkowar Mummy daga sama...
"Kaii kaii,
me nake gani haka?
Mari fa?
Mummy ta faďi tana karasowa har tana missing steps kafarta na gurďewa,
ko kallonta Nadeeyah batayi ba dan a lokacin ji takeyi kamar ana hura wuta a cikin zuciyarta,
Kuka Faida ta fashe dashi ta rungume Mummy wacce ta rufe mata jiki da hijab din da ta sakko dashi,
"Subhanallahi.. Nadeeyah me yayi zafi haka harda mari,
in baki dubi cewa ba sa'arki bace ai kya duba cewa ita bakuwarki ce,
"Bakuwarku dai Nadeeyah ta faďi cikin ficewar hayyaci,
ranta yayi matukar baci,
ba'a taba aibata mahaifinta har haka ba,
abun ya haďe mata biyu ne,
ga kishi ga tabo iyaye,
mai hankali ne kadai yasan halin da zuciyarta ke ciki a wannan lokacin,
Sakin baki Mummy tayi tace
"Ni kike fadama bakar magana,
gefenta tabi ta haye sama ba tare da ta kulata ba zuciyarta na tafasa,
ta gaji da zaman nan na kaskanci da takeyi,
badan tana jin soyayyar Musaddiq har cikin jininta ba wallahi da babu abinda zai hana ta tattara kayanta ta gudu ta bar musu gidan,
to bazata iya rabuwa dashi ko na second ba dan tayi matukar sabawa dashi,
ta dai ďauki alwashin kwatar ma kanta yanci gurin duk masu neman muzanta ta,
dakinsu ta shiga ta sameshi yana baccinshi hankali kwance,
key tasawa ďakin ta karaso kusa dashi ta cire hijab dinta ta shige cikin jikinshi taja musu bargon,
rungumeta yayi sosai yace
"Har kin gama?
a shagwabe tace
"um um, bacci nakeji, in na tashi zanyi,
bai damu ba dan yasan yadda yaganta da ta tashi,
yadda jikinshi yayi mata rumfa yasata manta duk wani bacin ran da ta kwaso daga kasa tayi luppp har bacci yayi gaba da ita....
Karar waya ce ta tashi Musaddiq daga nannauyan baccin da sukeyi,
hannu ya mik'a ya lalubota a gefen gadon..
kokarin zare jikinshi yakeyi a hankali dan kar ya tasheta yaji ta kara kankameshi haďe da sake gyara kanta a kirjinshi,
hannunshi ya tura cikin gashinta yana squeezing dinshi a hankali,
kallon wayar yayi yaga sha ďaya saura sannan ya duba kiran da ya zama missed call,
bin bayan kiran yayi asap,
"Yallabai hw far
"Ango kasha kamshi,
daga ďaya bangaren Zubair ya amsa cikin zolaya,,
"Hutu dai ya kare,
ga kuma wani hutun zaizo,
tafiya Singapore 3month course kuma oga yasa sunanka,
kaga sai kayi honeymoon dinka hankali kwance,
"Woww Musaddiq ya faďi da karfi har Nadeeyah na farkawa a ďan firgice,
murmushi yayi a hankali yace "sorry baby,
"yaushe ne tafiyan Zubair?
Dariya sosai Zubair yayi yace "Kaji shi, dama aikin ya isheka ko, to next week ne,
"Mashaa Allah, bari mu fara shiri, gobe zan zo aiki tun 8 in shaa Allah,
"To Allah ya kaimu ango,
a gaida min amarya,
"Gata nan tana amsawa,
tace bakazo kaci abincin amarya ba,
Dariya Zubair yayi yace "kace mata har sai ta gaji da gwauro,
in na fara mata sintiri sai ta rufe min kofa...
Dariya sukayi dukkansu sannan suka koma wata hirar daban...
Daga Nadeeyah har Musaddiq basu san kalubalen dake cikin aure ba,
har gara Nadeeyah tasan Hakuri da juriya sune ginshiki a zaman aure,
shiko Musaddiq da ya tashi cikin gatan da babu fatawar komai sai ta sakarci duk daukarshi aure kawai jindadi ne da mace,
ka bata abinci,
ta kula dakai tayi maka duk wasu bukatu,
bai san ainihin tushen aure shine Hakuri da jajircewa ba,
bai taba hasaso wani tashin hankalin da zai sauya rayuwarshi na nan tafe cikin kankanin lokaci ba....
Jiyar da juna daďi sukayi a wannan safiyar saboda murnar zasu kadaitu da juna na tsawon lokaci ba tare da tashin hankalin yan uwa ba,
abun da basu taba yi tare ba shi sukayi ranar wanka,
Nadeeyah har mamakin yadda ta saki jiki dashi cikin kankanin lokaci take,
kwata kwata duk wata kunya tata ta rasa inda tayi balaguro,
sosai take son jinta like a jikinshi a koda yaushe,
Kananan kaya ya saka wadanda suka fitar da ainihin kyawunsa..
Hannunshi Nadeeyah ta kamo ta zaunar dashi akan madubi tayi brushing gashin kanshi da kwantaccen sajen gefen fuskarshi..
"Kayi kyau sosai sosai,
kewayeta yayi da hannunshi ya daura kanshi kan ruwan cikinta haďe da lumshe ido yace
" *I can't quantify my love for you, it's more than the sand under the sea. Like a snail cannot live nor survive without its shell, I cannot live without you cos with you, there is life....*
Bata san sanda ta sanya hannu ta rungume kanshi tana shafawa ba saboda daďin da kalaman sukayi mata,
"I can't live without u either,
Zaunar da ita yayi akan cinyarshi cikin raďa yace
"Sure?
Gyaďa kanta tayi haďe da kwanciya a jikinshi,
Oya muje muyi breakfast, to 12 yanzu, munyi latti,
Buďe bakinta tayi a firgice dan shaff ta manta bata yi ma Mummy abinda ya kaita kasa dazu ba,
abubuwan da suka faru ta shiga tariyowa cikin kwakwalwarta,
"Na shiga uku!
ta faďi a hankali dan tuno yadda tayi ma Mummy dazu wanda sai yanzu taga rashin kyautuwarsa,
Ganin idonta na shirin tara ruwa Musaddiq yayi saurin mikewa haďe da cewa
"Hey calm down,
ai ba yin kanki bane,
Mummy will understand,
nasan sun karya ma by nw,
Jiki babu kwari dan bata san abun da zata tarar ba in ta fita parlon tace
"To muje in haďa maka breakfast, sai inyi saurin daura lunch,
"Kindai kusa hutawa,
in mukayi tafiya ko cup bazaki dauke ba,
so nakeyi kafin mu dawo ki zama big madam,
"kaga nima sai in dinga daukarka a wuya na,
ta faďi tana dariya haďe da bude kofa,
dariyar shima yayi ya biyota yana cewa
"impossible,
ko hannuna bazaki iya ďagawa shi kaďai ba,
Ringing din da wayarshi keyi shi ya hanata bashi amsa ta sauka kasa tana dariya,
ganin ba kowa a parlon ya sa tayi tunanin ko suna daki ne,
kitchen ta wuce taga komai tsaff kamar yadda ta barshi da daddare,
bata kawo komai a ranta ba ta fara dafa mishi indomie dan itace mai sauki,
tana yanka albasa taji muryarshi a bayanta,
"Amm dazu da kika fito da safe wani abu ya faru ne?
Gabanta ne yayi mugun faďuwa ta cigaba da yanka albasa tace
"wani abu akace maka ya faru?
Wukar hannunta ya karba ya juyo da ita yace
"I trust u Nadeeyah,
daga bakinki kawai nakeson jin gaskiyar magana,
banason ki boye min komai,
Kasa ta sunkuyar da kanta hawaye ya fara sintiri a idonta,
"Uhmm tell me!
"Ni bansan yadda zan faďi maka ba,
duk yadda suka faďa maka daidai ne,
Zai sake magana yaji wayar ta sake ringing,
da yake suna gab da juna taji duk abun da Anty Radiya tace a wayar,
"Ka fito ne ko har yanzu kana like gurin wacce ta zagi mahaifiyarka har ta koreta a gidan danta?
Kashe wayar yayi jikinshi ya fara rawa yace
"Plss tell me Nadeeyah,
tafiya ta fara yi dan kukan da takeyi na neman cin karfinta,
"Kaje dan Allah,
duk abinda aka ce maka nayi nayi ne,
Ranshi ya fara baci da kalamanta ya juyota da karfi yace
"A bakinki nake son ji,
a harzuke ta ture hannunshi tace
"Ka tambayi zuciyarka in ta yarda zan iya aikata abun da aka faďa maka fine, sai ka dau mataki a kaina,
Rage murya yayi yace
"Yaushe kika canja Nadeeyah,
are u ok?
"very okk, ban canja ba,
saidai in kai ne ka kasa ganin abun da wasu da yawa ke gani a gurina,
"Wallahi Allah na gaji,
kullum cikin sharri,
da nasan hakan ce zata kasance dani wallahi da bazan taba yarda da aur---------
Mari masu zafi har biyu ya sauke mata a fuska haďe da kaita jikin bango da karfin gaske,
"Aaaaaa......
ta faďi tana rike kanta dan ta bugu sosai,
Yanayinshi gaba ďaya ya sauya kamar zaki,
babu abinda da yake iya furtawa sai wasu numfarfashi da yake fitarwa,
komai zai iya sauraronshi daga gareta banda batun rabuwa sai kuma yanzu da ta nuna favours tayi mishi da ta aureshi,
bacin ran da yake ciki a yanzu yafi na kullum,
murya a kausashe kamar wanda ake ingizawa yace
"Wacece ke?
Wacece ke da kike ganin kamar kin taimakeni ne da kika aureni,
badan zuciya me rore rore ba ke kin isa ki zamo matata,
kalleni da kyau,
kinsan nafi karfinki ta ko ina, babu abinda ban kere miki ba a rayuwa,
Wallahi badan tausayinki da ya rikiďe ya zame min soyayya ba da babu abinda zanyi da marar asa----
Cikin kuka ta katseshi a hankali dan kalamanshi sun kashe mata jiki matuka,
"Akwai wadanda suke so na, wadanda basu damu da sanin asalina ba,
me yasa baka barsu sun aureni ba?
meyasa baka bar wanda zai rikeni ya yarda da asalina ya aureni ba?
sai yanzu da ka koyamin sonka zaka bullo da cin mutunci a gareni,
why Yaya Musaddiq?
Hawaye ne ya zubo a idonshi amma zuciyarshi sam bata karaya ba yace
"I will free u,
kije ki auri wanda kike ganin zai fini baki kwanciyar hankali,
Toshe mishi baki tayi da hannunta haďe da shigewa jikinshi tana kuka sosai..
"Dan Allah kayi hakuri,
don't separate urself from me, plss....
Su Mummy dake tsaye a bayanta tun jin kararta na farko suka dawo cikin gidan ta fashe da kukan munafurci,
Shigowa kitchen tayi ta kashe gas din da ruwan ya kusa kafewa tace
"Bana san rabuwarku,
bansan me yasa kika tsaneni ba Nadeeyah,
har kika kai ga zagi da cin mutuncina,
har kina nuna min cewa ke ba son ďana kikeyi ba a idona,
wace uwa ce zata juri wannan,
waye yake zuga ki?
Waye shi inje inji dalili,
Dama harzuka Musaddiq din tazo yi aiko ya harzuka,
nan ya fara zagin Nadeeyah,
zagi na cin mutunci wanda a iya saninshi bai taba yinshi ga wani ba,
da taga ya tabo inda bazata iya jurewa ba ta share hawayenta ta fara maida mishi,
nan kitchen din ya gauraye da tashin hankali,
su Raudha da Radiya suka shigo suka haďu akan Nadeeyah,
Ganin har lokacin Musaddiq yaki furta kalmar saki ya sanya Mummy rike hannun Nadeeyah tace
"A idona kike cin mutuncina da 'yayana,
"a idonki 'yayanki ke cin mutuncin iyayena,
kin hana su?,
Rashin kunya sosai ta zubawa Mummy wanda dama shiryayye ne sun san dashi,
kafin ta rufe baki Musaddiq ya daka mata tsawa haďe da furta kalmar saki cikin rashin sani da tsananin bacin rai,
Yana furtawa Anty Raudah ta jashi waje dan ma kar kukanta ya karya mishi zuciya,
cikin mota ta tura shi tace ma Faida taja shi su tafi......
Tafawa sukayi haďe da sakin tsalle,
"zo "zo "zo
Badariyya,
akwai sauran rina a kaba,
kalli ki gani...
Hoton Faida ta nuno mata suna zaune cikin mota tana rarrashinshi cikin kwarkwasa,
Kallon marakisiyya tayi cikin tashin hankali tace
"Ya zamuyi da wannan?,
"Ina zuwa Marakisiyya ta faďi haďe da mikewa,
da dan gudu tayi dakinta ta dauko wata allura da naďin laya,
duk abun nan da sukeyi a idon Yareemah Suhail,
jiransu yakeyi su gama ya tarwatsa aikin sannan ya kwace duk wani sihiri da Marakisiyya ta mallaka,
Shiryayyen shiri sukayi ma Faida wanda zaisa gaba ďaya taji Musaddiq ya fita a ranta kuma ta faďa mishi duk irin shirin da sukayi dan rabashi da Nadeeyah,
ma'anar hakan shine Badariyyah naso in ta koma ya zamana ita kaďai ce wacce zata dinga kula