Showing 1 words to 3000 words out of 88777 words

Chapter 1 - SO NE KO KIYAYYA COMPELET BOOK BY MAMAN FAREESA.doc

??ࡱ?>?? ???????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????

 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Root Entry???????? ?F? WordDocument????1?0Table????????? Data
???????????????????? P??#KSKS?1?Ȏ????????????????????p p p p F \ h p r $??i*???F F ????p ????p ?p ??p p ?? =?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?


d'
=?%?=ؓ?SONE KO K'IYAYYA??=ؓ?d'
=?%?


=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?


It's rometic love story=؞?

Story & written
by mommyn fareesa

*GODIYA* godiya ta musammun ga Allah (SW)daya bani aron rai da lafiya har nafara rubuta wannan book"yah Allah yadda na fara lafiya Allah yasa na gama lafiya=?O?=?O?tsira da Amincin Allah sutabbata ga shugabanmu Annabi S A W.....

*GARGAD'I* wannan labarin k'irkirarran labarine ban yishi dan wata ko dan wani ba" aguji sauyashi ta kowace siga sbd hakk'in mallakata ne.....

dedicate to all my fans ina yinku totally guys>?p?>??

*tukwici ne agareki* hjy rahama garba bichi=?;?=ؖ?Allah ya shirya miki zuriya"Allah yabar mutum da masoyinsa=?O?

BISSIMILAHIR RAHAMANIR RAHIM

Free page 1&2

KANO STATE! *Anguwar nassarawa ( G R A)* .......Misalin k'arfe 6:11 pm na yinin ranar yau Litinin"gaba d'aya garin yayi lullumi sanyin iskan hadari na kad'awa gwanin dad'i da ban sha'awa"sbd yanayin garin damuna ne"ga hadari yayi bak'i k'irin Asararin samaniya....Aguje wata y'ar yarinya Fara kyakykyawa y'ar kimanin shekara 15 zuwa 16 ta tura get d'in wani katafaren gida Aljannar duniya"tana sanye da yunifoam light blue na islamiya ajikinta"gaba d'aya jikinta kirma yakeyi da alama fad'a ta jawo tana neman mafaka"bata nufi Ainahin gidan suba"saita shigo gidan dake kallon gidan nasu"saidai tana shigowa idanuwanta suka hasko mata wata had'add'iyar mota "Mercedes Benz kirar E350.....dam! k'irjinta yabuga"ta d'auke kanta dg barin kallon motar sbd bataso zarginta akan motar ya tabbata"k'ok'arin bin hanyar part d'in su nafee takeyi sukayi cin karo da nafeen"wacce itama irin yunifoam d'in jikin yarinyar ne ajikinta"kallo d'aya zaka musu kasan age mate ne dan kusan kansu guda.....fuska cike da Annuri nafee ta rik'e hannun *IN'AM* tana fad'in kinsan ko yarinya?yaya yadawo d'azun bayan mun tafi islamiya"nima yanzun dana shigo mommy ke sanar mun"gaban in'am yabuga!"ta d'aure fuska tana fad'in kina nufin da gaske *me tubarau* yadawo?? Eh mana gama motarsa can"ta fad'a tana nuna motar da hannunta"juya fararen idanuwanta in'am tayi tana tab'e baki tace"barama na koma gida"sbd nasan yana nan cikin gidan nan"yanzun mun shiga ukku da Azabarsa tunda yadawo"nidai in'am ki rufan Asiri kiyi shiru karma wani yaji koshi yaji kija mana"Ai nazata farin ciki zakiyi yaya yadawo?"nid'in ce zan yi farin cikin me tubarau yadawo?"lallai ma nafee"ta k'are maganar tana tab'e baki tana waiwayon bayanta taga babu kowa"waike in'am bazaki dena fad'in wannan sunan ba?"harara in'am ta gallah mata tana fad'in ke nifa fad'a mukayi da Amina bayan kin fito dg Aji"na fasa mata hanci"inaga takawo k'arata gida"shine na gudo nan"kin san wannan Al'azabatun yaji labari na shiga ukku Awajensa"nafee ta girgiza kanta tana fad'in nidai bbu ruwana "dama fitowa nayi in sanar miki yaya yadawo"to wai ni ina ruwana da dawowarsa malama?"ta fad'a cikin masifa"nafeesa ta gallah mata harara tana fad'in kar Allah yasa kiyi ruwa da dawowarsa d'in.... tana fad'in hakan ta juya tayi gaba"in'am taja tsaki itama ta nufi bakin get"dattijo me gadi nata tsokanarta ta masa banza ta fita"sbd wani irin haushi taji da akace *me tubarau* yadawo"zaizo yaci gaba da gana musu Azabar daya saba"musammun ita da yafi tsana"ta Ayyana hakan Aranta tana fitowa dg cikin gidan ta nufi gidansu dake kallon gidan data fito"tana tura k'ofar Auwal na kawowa zai fita"kusan bangazar juna sukayi"in'am ta banko masa harara cikin tsiwa tace dallah matsamun na wuce"shima da irin yonifoam nata Ajikinsa yadaka mata tsawa yana fad'in idan nak'i fa?"shiru tayi tak'i mgn"yaja tsaki yana fad'in banza k'azama"dama ummi ce ta Aikoni na kira....kuka in'am ta fashe dashi harda shashsheka zaka d'auka dukanta Auwal yayi"wanda sbd yakirata da k'azama takeyin hakan"sbd tanada tsafta ta fitar hankali shiyasa ta tsani Ace mata k'azama"Auwal kuwa ita dashi mabiyi da mabiyine"itace ke bimasa....aguje in'am ta zura cikin gidan tana ihun kuka"Auwal yasaki dariyar mugunta yabi bayanta"sbd Azatonsa in'am batada labarin yayansu yadawo....cikin rufe ido da borin kunya in'am ta shigo main parlour nasu bbu ko sallama sai kuka datakeyi shab'e shab'e da hawaye"sbd gudun kar Ayi zancen fad'ansu da Amina"tana shigowa ta fad'o Ajikin ummi dake zaune tana azkhar kafin akira magrib....tureta dg jikinta tayi tana fad'in zaki tashi ki nutsu kimun bayanin dalilinki na fasawa y'ar mutane hanci ko kuwa?"gaba d'aya ke baki girma Aduniya Autah?"burunki ki jawomun fitina Ana kamun kashedi.....kukan in'am yak'ara k'arfi tana duk'e gefen ummi......zaki tashi ki nutsu kiyi bayanin Abinda aka tambayeki ,ko saina fasa miki baki???...... Arikice in'am ta d'ago kanta y'an hanjin cikinta na hautsinawa"sakamakon Amon dakakkiyar muryar *dr Aliyu ibrahim mai tubarau* data daki dodon kunnanta"satar kallon gefen dayake zaune tayi kan 2 seeter yana danna waya"yadad'e da eye glass bak'i"ba'a ganin k'wayar idonsa Amma shi yana ganin kowa batare da Ansan yana kallon ba"saidai kyakykyawar fuskar nan tasa A had'e take, bbu alamar yasan meye wasa ko wani abu waishi dariya"yana sanye da farar k'ar d'in t shirt irin ta polo"da wondo 3 quarter bak'i"tun dg lallausan bakin sajensa zuwa sumar kansa k'yalli sukeyi sbd gyaran dasuke sha"gaba d'aya k'amshin turaren jikinsa yacika parlourn"acikin second 5 in'am ta k'are masa kallo"wanda gaba d'aya data shigo bata lura dashi ba saida yayi mgn"saima Asannan ta lura da yayunta maza 2 dake zaune Acikin parlourn"ta tabbatar sbd sunsan zai mata mgn shiyasa suka k'yaleta basu tankataba"Ahankali ta mayar da kanta Ak'asa tana b'ata fuska"cikin y'ar siririyar muryarta ta yarinta tace"ummi itacefa ta fara Jana"da wannan mugun uztaz d'in yashigo Ajinmu" sai yayita tambayata karatu"ina bada Amsa"Amma baya tambayar nafee da Aminar"ni kuma d'azun daya tambayeni sai nace ban saniba"sai takama yimun dariya"wai ina musu burgar inada k'ok'ari an tambayeni abu na kasa fad'i"saina barta sai bayan Antashi zata tashi tsaye dg kusa dani na chakumeta"nakuma sanar mata dg yau bazata koma zama sit namuba.....dg haka tayi shiru"yaya yusuf yaja tsaki yana fad'in wannan bashi bane hujjarki da zaki fitarma da y'ar mutane da jini ba.....yaya sulaiman ya k'arbe zancen da cewa ka barta jikinta zai gaya mata yanzun nan tunda batada hankali"sbd bakida mutunci malamin nakine mugu?"turo baki tayi tak'i mgn.....yayinda yaya Aliyu ke zaune zaka d'auka duk surutun da in'am keyi baya sauraro"saidai tsab yana jin komai kuma yana kallonta Acikin bak'in tubarau nasa"duka 2yrs yayi baya k'asar"sosai yaga in'am tayi girma"kuma da Alama rashin jinta na nan bata canzaba"saidai ya fahimci ta rage surutu"wanda Ayanzun surutun nata harma ya ishesa.....nidai dan Allah yaya sulaiman kuyi hak'uri itace fa ta fara Jana"kuma yanzun shine Auwal yacemun k'azama ko?......."shine kika shigo kina ihu haka?"cewar ummi tana hararanta"shiru tayi tak'i mgn sbd ganin wannan me tubarau d'in yana cikin parlourn"Allah ya shirya munke in'am"yanzun bakiga yayan kuba yadawo"sbd hankali yamiki yawa bazaki gaishesa ki masa sannu da zuwa ba??"ummi ta k'are maganar tana hararanta"yaya Aliyu kuwa wayarsa yakara Agefen kunnansa yana mgn cikin cool voice"da Alama da dr safwaan Abokinsa yake mgn"in'am kuwa turo baki tayi tak'i mgn"dan wani irin mugun haushi yaya Aliyu ke bata"sbd yanada tsatstsauran ra'ayi kuma yacika takura....tashi tsaye yaya sulaiman da yaya yusuf sukayi suna fadin ummi bara muje ankusa sallar magrib"nima dai bara na wuce ciki nayi Alwalah"ta fad'a suna fita"yaya Aliyu ya janye wayar yana tab'e baki"ummi na murmushi tace"my son sai kayi sallar zaka ci Abincin?"Eh ummi nayi missing girkinki sosai fa"ai yau na musammun ne nayi sbd kai"ta fad'a tana yin gaba"in'am dake zaune kamar ta kurma ihu tafara k'ok'arin satar kallon sa taga idan ba ita yake kalloba" sbd tasamu ta gudu dg cikin parlourn batare da mgn ta had'asu da shiba"saidai data saci kallonsa wayarsa taga yana dannawa"Aranta tace"bbu laifi al'azabatu yak'ara kyau"da alama london ta amsheshi"ta Ayyana hakan Aranta tana mik'ewa tsaye......K!gabanta na fad'uwa ta juyo taki mgn tana cin magani"zaka d'auka ba kallonta yakeyi ba"Amma sarai yana lura da Abinda takeyi....bece komaiba ya mik'e tsaye" masha Allah! Irinsu dr Aliyu Ake kira one in town"kyakykyawan dogon mutum karfaffa ne"me cike da kwarjini da kyawun haiba da kamala"kalar fatar jikinsa chacoolate colour ce"wacce ke wahalar samu"kallo d'aya zaka masa ka fahimci beda hayaniya da yawan mgn"ga wani abu dake tare dashi shine da yawan mutane yana musu kwarjini"ita kanta in'am duk tsiwarta bata iya kallon sa ta masa"wani abun tana yine sbd Azatonta be kallonta"saidai ta makara"tunda yace" K be koma mgn ba yanufi k'ofa cikin nutsuwa yana takunsa na isa da izzah yafita"in'am kuwa tasan muddin batabi bayansa ba tota shiga ukku yau"gashi Anutse yake tafiyar tasa Amma sai gashi yamata nisa"sadda suka fito Awaje har walk'iya Akeyi sbd hadarin yak'ara had'uwa"fatan in'am Allah yasa karya nufi part d'in umma"ganin har yashige cikin get d'in gidan su yasaka harda gudunta ta biyosa tana fad'in yaya! banza yamata"kaji yaya dan Allah kayi hak'uri"ita face ta fara Jana"kuma ni bansan kadawo ba"na bari sai Anjima zan gaidaka ko....shout up! yafad'a Atsawace cikin d'aure fuska batare daya kalletaba"tamkar takaima bayansa duka haka taji"saidai ta saki ajiyar zuciya dataga part d'in mommy yanufa"dukda yanzun fushi takeyi da nafeesa sbd Abinda ta mata d'azun yabata haushi...shine yafara shiga cikin parlourn"yayi sallama"mommy ta Amsa masa"fuska bbu rahama ya kalli nafeesa da mahmood yana fad'in kutashi kuje kuyi Alwalah lokacin sallah yakusa"da sauri sukabar parlourn"yayinda in'am data shigo ta tsugunna k'asa kan carpet tana raba ido"mommy ta kalleta ta kalli yaya Aliyu dake tsaye yana danna waya tace"Allah yasa y'ata ba laifi tayiba Aliyu?"ya d'auki kusan second 10 kafin cikin taushin muryarsa me cike da haiba da dad'in Amo" yace"gata nan mommy tayi sallah taci Abinci, sannan na bata hukuncinta....."yana fad'in hakan yayi gaba yabar musu daddad'an k'amshin turarensa......kuka in'am ta fashe dashi tana yiwa mommy rantse rantse ita bata masa laifin komai ba"ruwa baya tsami banza in'am"dg dawowarsa da hukun taki zai fara?"ke kuma gaki da shegen tsoron duk'a"Amma bazaki dena rashin jiba?"tana turo baki ta sanarwa mommy yadda sukayi fad'a a islamiya"hmmm! Ai na sanki Autar ummi baki barin saita kwana"yanzun ki tashi kije d'akin nafeesa kiyi sallar kizo kici Abinci"idan yadawo ki bashi hak'uri k'ilan ya k'yaleki"dukda nasan bazai dake kiba" zaidai miki hukuncin dayafi duka ciwo"sbd dama haka yake ma duk yaran nan in sun masa laifi"ni mommy na k'oshi ! dan Allah karki sanar masa banciba "ta fad'a tana tashi tsaye"bbu ruwana baza'ayi wannan k'aryar da niba"kije kiyi sallah An fara kira"kamar in'am tayi kuka haka taji"batace komaiba ta nufi d'akin nafeesa, ta sameta harma tayi Alwalah tana shimfid'a prayer mate zata kabbara salla"tab'e baki in'am tayi ta d'auke kanta"k'awata kenan ! ni banyi fushi dakeba kece zakiyi dani?"bansan meyasa kike nuna haka ga yaya Aliyu ba"bana jin dad'in hakan"karki manta kema fa yayankine?"niba yaya bane"garinma zan bari sbd matsawarsa"tafad'a cikin masifa tana nufar bath room ta shiga....nafeesa ta tab'e baki tana fad'in saiki sanya niya"dg haka ta kabbara sallarta..
Alh Ibrahim da Alh yakubu Abokan junane tun suna yara har girmansu"su haifaffun garin kanone kowa nasu na Acan"tun suna yara suke Abota"har Allah yasa sukayi Aure"da suka tashi gina gadaje sai sukayi Ajere ga gidan wannan ga gidan wannan"sukayi auren so da matansu hauwa(umma) da maimuna(ummi) "da farko zamansu lafiya suke cikin had'in kai matan"mazajensu na kasuwancinsu"shekarar su guda da Aure hauwa ta haifi d'anta Aliyu"Amma maimuna shiru bata haihuba"tunda Aka haifi Aliyu maimuna ta d'auki son duniya ta Aza masa" tana bashi kulawa kamar itace ta haifesa"sai hauwa na goyon d'ayyaba y'arta ta biyu sannan maimuna ta haifi d'anta sulaiman "shekarar sa biyu ta haifi yusuf"sannan mukhtar sai Auwal sai maryam Autah (in'am) "hauwa kuwa bayan d'ayyaba sai isma'il ,da ruk'ayya sai Auta Abdul hakeem"farkon Abinda yafara k'ok'arin had'a tsakanin hauwa wato umma da maimuna wato ummi"shine Alh ibrahim yanuna yana son k'awar maimuna da aure wato binta(mommy)"nanfa Akayita tashin hankali hardai Akayi Auren"hauwa da binta suna zaune kowa na harkan gabansa bbu ruwan kowa da kowa"hauwa ta k'ullaci ummi sbd a ganinta itace silar da Akayi mata kishiya"sunjima Awannan gidan "dg nan sukabar wannan Anguwar da suke sbd kowane yasami budi sosai"nassarawa G R A suka koma gidan Alh Ibrahim na kallon gidan Alh yakubu"wanda Alokacin itama binta ta haifi yara 3"saifullahi, zainab mahmood da cikin nafeesa suka koma"lokacin itama ummi nada cikin in'am"gaba d'aya umma da ummi basa shiri"danma ummi bata biye mata"sai Abin yazama mommy da ummi ke shiri"su kuma Abba da Alh hidimar gabansu sukeyi"gaba d'aya yaran gidan sun taso cikin had'in kai da girmama juna"zaka d'auka tamkar dangin junane na jini"kuma wannan zumuncin nasu yasaka Alh ibrahim (Abba) zai iya iko da d'an Alh yakubu(baba)shima zai iya iko danasa y'ay'an"gefe guda kuma Abba na tsawatarwa umma ta rage k'iyayya ga ummi Amma bata denawa"tunda yaran ummi dana umma suka tasa suka fahimci tsakanin iyayen nasu mata bbu shiri"Amma haka be damesuba zumuncin su sukeyi yasu yasu"tunda in'am ta tasa ta fahimci umma bata son y'ay'an umminta da ita ummin tata"sai tayi baya da zuwa part nata"idan sun had'u ta gaidata da k'yar take Amsawa"Ayanzun haka Anyiwa zainab da d'ayyaba Aure da ruk'ayya suna gidan mazajensu"yayinda Alh yakubu yarasu shekara 3 da suka wuce"wanda hidimar komai ta family d'in sa ta dawo wajen Alh Ibrahim"dukda yanada dangi da y'an uwa" wanda Alh Ibrahim yaso ya Auri ummi itace tak'i yarda"kuma mommy taso hakan sosai Aranta"Amma ummi sbd gudun Abinda zaije ya dawo sbd hjy hauwa ta hak'ura Amma badan bata soba.....hjy hauwa tanada k'anwa mai suna gaje uwarsu d'aya ubansu d'aya"yaranta biyu , Hamza da zubaida"Hamza zaiyi 24 yrs"zubaida zatayi 20yrs"mama gaje talakace lik'is Agidan haya suke zaune"da taimakon Aliyu da umma suka dawo gidan kansu"yakuma d'auki nauyin karatun hamzan"sosai hakan yayiwa mama gaje dad'i sbd macece ita mai son Abin duniya da had'ama da handama"ita kad'aice wajen mijinta mlm lawal dake sana'ar siyar da faskare"duk Abinda zai kamata bata godewa sai tayi hange"kuma mama gaje itace ummal aba'isin haddasa k'iyayyar ummi Azuciyar umma"tana tunzurata data ware kanta karta Amince da mommy kishiyarta da kuma ummi"yayinda Akwai wani buri da mama gaje taci Azuciyarta"wannan kenan.....yayinda hjy fatima maihaifiyar Alh ibrahim tana gidan zaune part d'inta daban" "kasancewar shikenan d'anta guda Aduniya...

In'am (maryam) wacce taci sunan kakarta"wato mahaifiyar Alh yakubu"tun tasowarta ta taso da k'iriniya da rashin ji"gata shagwab'abb'iya sbd Autace"saidai Allah yamata brain me d'aukar abu"tanada k'ok'ari boko da islamiya"tun last year sukayi saukar Alk'ur'ani me girma"yanzun SS 2 suke, sunyi exams suna hutu"dasun koma SS3 zasu shiga itada nafeesa"in'am batada k'awa konace Aminiyar data wuce nafeesa"dan sun shak'u da juna sosai"sai kuma wata sa'adiya da class nasu guda da ita"in'am bata shiri da yaya Aliyu"sbd kaf shine babba Acikin wannan zuri'a"yanada ikon hukunta kowa acikin y'ay'a kuma dole Amasa biyayya"kuma baya wasa da yaro"gashi gaba d'aya yafi yima in'am mugunta da takurata "tana jin haushinsa sbd hakan"tana kuma k'ok'arin nisantar Inda yake kodan sbd ummansa"shekara 2 da yayi baya nan ba k'aramin dad'i in'am tajiba"in'am farace ba jaba"kuma ba doguwa bace ba kuma gajera ba"batada jiki sbd batason cin Abinci sai kayan kwad'ayi"Allah yamata shan yajin tsiya"yaya Aliyu ne kawai ke tursasata taci Abinci"Adole zataci" tana kuka tana jin haushinsa"Ayanzun data fara girma kyawunta da baiwar surunta ke fara fitowa"dukda tana Ahaka da yawa maza na nuna suna sonta bata damuwa dasu"uztaz nasu yayi mugun mutuwa a soyayyar in'am shiyasa kullum islamiya yake mata tambaya sbd yaji siririyar muryarta yana kuma tsoron furta mata yana sonta"yayinda ita kuma haushi yake bata sbd sajensa irin na yaya Aliyu ne...Acewarta">?#?

Aliyu ibrahim mai tubarau matashin.....
'?

mu had'u a next page idan anyi zazzafan sharhi"tsaftataccen labarine me tsayawa azuciyar me karatu da sakq nishad'i=??=??hanzarta biyan naki ta wannan hanyar dan adama dake atafiyar bbu cizon yatsa sbd free page 5 ne kawai=?G?

wannan book d'in nakudine
Normal grp 300
Vip grp 1000
Special people 2k wato 3pages in a day

zaku biya kud'in ku ta wannan acc number=?I?2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK
Kituro shaidar biyanki what's app number d'ina 08100084251
300 kawai ake turo Kati idan bakida acc amma sauran payment d'in ta acc ne

banason transfer d'in Kati ko vtu photo d'in katin MTN zaki d'auka saiki turo dan Allah banda kiraL'

Y'an nijar kutuntub'i wannan n=?I? +227 88 01 90 50
Normal grp 500f
Vip grp 1000f
Special people 2000f

dan girman Allah da darajan iyayenki karkimun mgn idan baki shirya biyaba
=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?


d'
=?%?=ؓ?SONE KO K'IYAYYA??=ؓ?d'
=?%?


=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?=?>?


It's rometic love story=؞?

Story & written
by mommyn fareesa

Dedicate to zee h wada =?;?=ؓ?=ؖ?kiji dad'in ki ta wajena>??

Free page 3&4

........Aliyu Ibrahim mai tubarau matashin saurayine me jini ajika"wanda duniya ke damawa dashi sbd baiwar ilimin likitanci da Allah yabashi"d'an kimanin shekara 35 ne aduniya"tun yanada 32 yrs ya kammala karatunsa anan gida nigeria yafara aiki awata private hospital"dg baya kuma mahaifinsa da marigayi suka fara gina masa tasa asibitin"ba'a fi wata biyu da gama ginataba da bud'eta Allah yayima baba rasuwa"bayan rasuwar tasa da wasu watanni Aliyu yatafi london k'arin karatu"yanzun yazama babban likitan mata"kuma Alhmdllh takardunsa sunyi kyau sisai"Aliyu dogone wankan tarwada"kyakykyawa n gaske ne ajin farko"akwai cikar haiba da kamala atare dashi"beson surutu da hayaniya"sannan be cika yawan mgn ba sai akan Abinda yashafi aikinsa" miskiline na bugawa ajarida"da yawa na fad'in basu tab'a ganin murmushin saba"baya kula mata ko kad'an duk kuwa irin nacin mace dason ta shige masa"sannan baya Amsar haihuwa Atsarinsa"sbd baya son kallon private part d'in wata"Aliyu yanada hak'uri sosai da kauda kansa ga abubuwa"amma be iya fushi ba"bashida Aminnan da suka wuce Ahmed da safwan aduniya"safwan likitan kunne ne a Asibitin Dr Aliyu yake aiki"yayinda Ahmed lauyer ne me zaman kansa"safwan beda aure"Amma Ahmed yanada mata tasleem da yarinya guda hafsat"sunan me tubarau yasamo asaline tun sadda Aliyu ke yaro be wuce 12 yrs yake saka tubarau"kuma bawai wata matsala ce garesaba"ah ah kawai yana ra'ayine"har zuwa girmansa kuma be denaba"hakan yasa friends nasa ke kiransa da me tubarau"ak'allah baya rasa glasses 24 nasa ad'akin sa"Aliyu har yanzun be tab'a soyayya da wata y'a mace ba"tun bayan yagama karatunsa na likita Abba yamasa zancen aure yanuna ba yanzun"dg lokacin Abba yasa mishi ido kawai"yakuma sha alwashin sulaiman,yusuf, isma'il da saifullahi "duk idan sun sami matan aure zai musu aure tunda sun gama karatunsu suna aiki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login