Showing 60001 words to 63000 words out of 88777 words

Chapter 21 - SO NE KO KIYAYYA COMPELET BOOK BY MAMAN FAREESA.doc

ya mutu ummi"ta k'are maganar cikin gunjin kuka"wanda nafeesa data biyota taji komai"da hanzari ta juya ta fita"ummi kuwa salati tayi tana fad'in yana ina?"kafin In'am tayi mgn yaya sulaiman yashigo cikin parlourn da nufin yagaida ummi"yadda yagansu kuma yanzun yaga nafeesa tana tafiya da sauri bedai tsaida taba yatabbatar masa da cewar bbu lafiya....tun kafin yayi mgn koyayi k'ok'arin zama In'am ta iso gefensa ta rik'e hannunsa tana fad'in dan Allah yaya sulaiman muje ka kai yaya Aliyu Asibiti bashida lafiya"tafad'a tana kuka"be iya cewa komai ba"sai ummi datace maza sulaiman kuje can Asibitin nashi"dato ya Amsa yafita"In'am zata bishi ummi ta tsaidata"bata tsayaba ta fito Aguje"Atare da yaya sulaiman suka shiga d'akin yaya Aliyu"yana kwance Asume"yaya sulaiman yayi k'ok'arin gwada ya d'aukesa Amma yakasa"In'am dai na tsaye tana ta kuka gwanin ban tausayi"Ahaka sukaji muryar Abba da nafeesa zasu shigo cikin d'akin"Abba ne Agaba nafeesa na bayansa"yayi sallama yana fad'in subahanallahi! wai baya numfashi ne?"Eh Abba dama ummi tace nazo nakaisa Asibiti"na gwada d'aukarsa nakaishi cikin mota Amma yamun nauyi"to bara nakama maka"yafad'a suna d'aukar yaya Aliyun suka fita dashi" In'am ta fad'a jikin nafeesa tana kuka"kiyi hak'uri insha Allah zai sami lafiya"yanzun mu gyara masa d'akin kafin su dawo ko?"mudai gyara Amma ko saman Adaidaita ni sai naje nafeesa"bazan iya jure har sai sun dawo ba batare danasan wane Hali yakeba"yah Allah ka bama yaya Aliyu nah lafiya"nafeesa ta Amsa da Ameen tana jin tausayin In'am"Atare suka gyara ko ina"kowaccensu na lura da k'aton pic d'in in'am dake cikin bed room d'in basudai tankaba sbd suna cikin jimami"wayoyinsa In'am ta d'auka suka rufe d'akin ta Amshi key d'in"part d'in mommy sukaje ta d'auki hand bag d'in nafeesa da kud'in transport "sannan ta fito ta tari nafef ta shiga suka nufi Asibitin....
su yaya sulaiman na isowa Asibitin shida yaya yusuf Aka nufi emergency room da yaya Aliyu"yayinda Abba yana gida be biyosuba"tsai tsaye sukayi bakin k'ofar shiga emergency d'in"kusan mintina 45 da shigarsu ciki In'am ta iso wajen"kallo d'aya yaya sulaiman yamata ya fahimci taci kuka ta godema Allah"yaya sulaiman ina yaya Aliyun yake? ta fad'a Idonta cike da k'wallah"fuskarsa Ad'aure yace"suna ciki Ana dubasa"miye Abin ki wani kwaso jiki kizo mana nan?"wuce ki koma gida kina jina??"kukan data rik'e ta fashe dashi tabar wajen tana shan Alwashin bbu Inda zataje"Acan bakin get taje ta zauna ta lalubo number d'in tasleem matar brr Ahmed "bayan ta kirata tasanar mata idan yaya Ahmed na nan tafad'a masa yaya Aliyu bashida lafiya yana Asibitin sa"bayan sunyi sallama tayi tagumi..... doctor marwaan da dr Amaan sune sukayi tsaye kan yaya Aliyu kusan awa guda sannan numfashinsa ya daidai ta"suka masa Allurai aka kaisa wani room na mummunan suka d'aura masa drip"kafin doctor marwan ya kalli yaya sulaiman yace"idan babu damuwa ina son ganin wani babban makusancinsa"to shikenan insha Allah Abba zaizo sai kuyi mgn"daga haka dr marwan ya fita"shi kuma yaya sulaiman ya kira Abba yasanar masa komai"cikin y'an mintina ya iso Asibitin ya isa office d'in dr marwaan d'in"wanda yana ganinsa yafahimci mahaifin dr Aliyu ne sbd kama ta jini....bayan sun gama gaisawa dr marwan yayi gyaran murya yana fad'in zancen gaskiya Abba dr Aliyu yana cikin damuwa da fargaba daya saka Aransa"wanda binciken mu ne yasaka muka gano hakan"kuma ko shima idan yabinciki kansa hakan zai gani"yaka mata Abba kajashi Ajiki kaji meye damuwarsa dake barazanar shafar zuciyarsa??"sannan yanzun haka yakamu da ulcer"innalillahi wa inna ilaihir raju'un! cewar Abba yana tunanin tabbas zancen da yamasa jiyane yak'ara sakashi shiga damuwa"wanda yad'auka ya hak'ura da in'am d'in ma"suna cikin maganar brr Ahmed yashigo cikin office d'in fuskarsa d'auke da damuwa"d'uk'awa yayi yagaishe da Abba"kafin yaja kujera ya zauna yana tambayar meke damun dr Aliyu?"bbu wani b'oye b'oye Abba ya sanar masa yadda suka ganshi da zuwan su Asibitin da bayanin da dr marwan yamasa yanxun"shiru yayi yana tunanin Anya ciwon dr Aliyu beda Alak'a da in'am?"Amma sai yayi shiru yana jin yadda dr marwan ke rok'ar Abba Aji meye damuwar dr Aliyu Amagance masa ita"bayan sun gama mgn Abba da brr Ahmed suka fito"Amma Abba dan Allah babu wani Abu daya faru cikin gida na rashin jin dad'i ko kuma Angaya masa wata mgn data saka yashiga damuwa??"tabbas Akwai Ahmed"cewar Abba yana masa bayani"Ajiyar zuciya brr Ahmed yasaki yana fad'in wlh Abba sbd in'am ne"tunda yaji zancen za'a bama wani ita"yasha fad'amun sbd damuwar cikin gidan yake b'oye furtawa yana sonta"to Ai gashi yana neman rasa ransa ko lafiyarsa sbd zurfin ciki ko?"dama can nasan zancen saidai da baiyi mgn ba na d'auka ya hak'ura ne"sbd haka bbu damuwa indai mamana tana sonsa"gaskiya tana sonsa Abba"to saidai naji ta bakin nata tukum"dg haka sukayi sallama Abba ya shige mota driver yajashi"brr Ahmed yawuce d'akin da dr Aliyu ke kwance yanata bacci"lokaci guda duk ya zabge yayi y'ar fuska"saidai yak'ara wani irin mugun kyau"har yanzun be farkaba?"Eh gsky Amma sunce bazai jimaba"cewar yaya yusuf da yaje ya Amso break fast d'in da ummi ta shirya "idan yaya Aliyu ya farka yayi yasha magani"bara naje nadawo tunda be farkaba"okay yaya sulaiman ya fad'a yana tuba time kusan k'arfe sha d'aya na safe da wasu y'an mintina"brr Ahmed befi mintina 5 da fitaba"yaya Aliyu yafara matsa zara zaran eye lashes nasa"kafin yabud'e duka manyan idanuwansa da har yanzun Akwai jaa Acikin su"iya lab'b'ansa yayi salati yana k'arewa cikin d'akin kallo"yaya katashi kenan?"sannu ya jikin naka?"cewar yaya sulaiman yana kallon sa"maimakon me tubarau ya Amsa masa" sai yayi shiru yana tunanin ina In'am ta tafi??"da k'yar ya iya motsa red lips nasa yana fad'in ina my Angel??"d'an murmushi yaya sulaiman yayi yana fad'in na koreta yaya Aliyu"sai kawai tazo tayita mana koke koken gulma....dukda har yanzun bayajin dad'in jikin nasa hakan be hanashi had'e rai ba cikin sanyayyar muryanshi yace"maza kaje duk Inda take kazomun da ita"Akan me zaka koreta??"......yaya sulaiman na k'ok'arin mgn In'am da brr Ahmed suka shigo cikin d'akin"wanda bayan yafita ya ganta bakin get taci kukanta ta k'oshi idanuwanta duk sun kumbura"ta sanar masa yaya sulaiman ne yakoreta"tausayinta yaji yace"tazo suje yarakata d'akin"shine suka shigo a tare...In'am na shigowa sukayi ido hud'u da yaya Aliyu"wani kukan ta saki Aguje ta nufo gefen bed d'in"yaya Aliyu ya lallab'a yatashi zaune cikin k'arfin hali yana kallon ta bbu ko k'iftawa"saidai yatsorata da yadda yaga idanuwanta sunyi jajir sun kumbura"yaya Aliyu nah ka farka?"to ya jikin naka?ta fad'a tana duk'e gaban gadon ta kama hannun sa guda"beyi mgn ba sai jan hannun nata yayi ta dawo gefensa ta zauna"ya juyo Ahankali yana fuskan tarta yana jin kamar ya sanyata Ajikinsa "my Angel ina kika tafi kika barni??"yafad'a yanda itace kawai zata iya jin meyake fad'a"d'ago kanta tayi da nufin tayi mgn"sai sannan ta lura dasu yaya sulaiman da yusuf dake cikin d'akin"turo baki tayi tace"ba wancan yaya sulaiman d'in bane yakoreni& ... lallai Auta zaki koma gida zamu had'u ai ko?"kamata Abinda kayi niya"cewar yaya Aliyu fuska Ad'aure yana makama brr Ahmed harara dayayi tsaye ya jingina jikinsa ga bango yanata kallonsu cike da burgewa" Abokina bani nakashe zomon ba"gata nan tambayeta kaji zan tafi naganta bakin get"bayan ta sanar mun sulaiman yakoreta nace tazo muje nan"kai ina kasan bana lafiya?"In'am ce takira tasleem tanata kuka"Allah sarki my Angel na warke karki koma yin kuka kinjiko?"yafad'a yana kallon ta"yayinda yaya yusuf da sulaiman ke kallon yaya Aliyu suna mamakinsa"sbd sunsanshi beda sakin fuska ko yawan mgn Amma sbd mace gashi yanayi duk Akan soyayya"lallai SO mugun wasa....yaka mata kayi brush kaci wani abu saika sha magani gasu can"cewar brr Ahmed"okay"sulaiman Amsomun brush da toothpaste a shop"okay"yafad'a suka fita shida yusuf"brr Ahmed ya kallesu yaga in'am tayi k'asa da kanta tayi shiru shi kuma uban gayyar yanata kallonta"zan wuce gida Abokina"Allah yak'ara Afuwa zuwa dare nasan ka koma gida ko?"yaya Aliyu na k'ok'arin mgn Abba yashigo cikin d'akin"driver na biye dashi da ledoji manya Ahannunsa"brr Ahmed yama Abba sannu da zuwa sannan yafita shida driver"Abba na murmushi yace"mamanah yayanki yasami lafiya ko?"yafad'a yana k'ok'arin zama kan farar kujera"In'am ta Amsa da Eh tana masa sannu da zuwa"ya amsa kafin ya kalli yaya Aliyu dayayi k'asa da kansa yana fad'in Abba sannu da zuwa"yauwa Aliyu me b'oyemun damuwarsa"ka bani mamaki da sbd hauwa ka b'oye Abinda ke ranka game da y'ar uwarka In'am"meyasa bazaka sanar niba ni?k'irjin yaya Aliyu yabuga"yad'ago kansa yasaci kallon In'am datayi shiru tana sauraren kalaman Abba"mamanah! Abba yakira sunanta"na'am Abba"fad'amun kina son yayanki kamar yadda shima yake sonki??"kuma gaskiya zaki fad'amun karkimun k'arya.....
'?

wannan book d'in nakudine idan kina buk'atar siya serious normal grp 300
Vip grp 1000
via 2230373842 NABILA ALIYU UBA BANK

Ki turo shaidar biyanki ta what's app number d'ina 08100084251

Idan kika karanta mun book baki biyani hakk'ina ba ko kika siya kika fitarmun Allah ya isa ban yafe miki ba
d'?=ؓ? SONE KO K'IYAYYA =ؓ?d'?

55&56


...........kallon Abba In'am tayi yayinda ita kuma yaya Aliyu ke kallonta zuciyarsa na wani irin harbawa" yayi kasak'e yana jiran jin wace irin Amsa zata bama Abba"cike da yarinta tace"Eh ina sonshi fa Abba"sai kuma ta b'oye fuskarta da tafikan hannayenta Alamar jin kunya"yayinda yaya Aliyu yasaki wata iriyar Ajiyar zuciya Ab'oye yana furta Alhamdllh! Abba na murmushi yace"masha Allah! Ubangiji yayi muku Albarka yasaka Alkhairi Acikin wannan Alak'ar taku da juna"kan yaya Aliyu ak'asa ya Amsa da Ameen cikin tsantsar jin dad'in kalaman mahaifin nasa"yayinda kan In'am ke cikin cinyoyinta tanata murmushi..... Ahaka yaya sulaiman da yusuf suka shigo cikin room d'in"???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?Abba ya mik'e tsaye yana fad'in bara naje gida "to Abba insha Allah zuwa yamma zamu koma gida hardashi"cewar yaya sulaiman"yayinda yaya Aliyu ke kallon in'am tattausan murmushi shimfid'e Asaman kyakykyawar doguwar fuskarsa"murya can k'asa yace"my Angel d'ago kanki pls ki fad'amun yaushe kika fara son yaya Aliyu naki??shiru tayi tak'i mgn"ya mintsineta a hannunta guda dake gefen cinyarta"tayi saurin janye hannun nata ta b'oye tana dariya k'asa k'asa..... Abba yanufi k'ofa yana fad'in haba sulaiman kun zaunu da yawa Asibitin nan"kuje ku cigaba da hidimarku Allah ya muku Albarka yak'ara had'amun kanku"Ameen Abba"dama ummi tace"mu zauna mu kula dashi zuwa yamma"Amma shi yusuf yatafi nizan jira "dato Abba ya Amsa yana tunanin kyawawan halayen ummi"wanda yasan umma bazata iya saka Aliyu yayima sulaiman irin wannan abin daya masa yau ba"da wannan tunanin yafita dg cikin d'akin"yaya yusuf ya kalli yaya Aliyu daketa kallon in'am yace"yaya gashi kayi brush d'in"dato ya Amsa yana karb'an toothpaste d'in da brush"shi zai tafi ni ina nan A reception"cewar yaya sulaiman suna fita"okay kota wayane na kir.... Ashefa inaga wayar tana d'aki na mantata"In'am sai sannan ta d'ago kanta ta bud'e hand bag nata ta zaro masa wayoyinsa guda 2 tana fad'in yaya Aliyu gasu nan natafo maka dasu"kin kyauta my Angel"ban tab'a zaton haka kika damu dani ba?"I love you so much my Angel"murmushi tayi tak'i mgn ta rissinar da kanta ak'asa tana mik'a masa phones nasa"daya tashi saiya had'e da hannun nata ya rik'e"bazaki fad'amun yaushe kika fara sona ba my Angel?"yafad'a cikin wata iriyar muryar dabata sanshi da itaba"Atake In'am taji kasala da mutuwar jiki sun durar mata lokaci guda"batayi mgn ba tafara k'ok'arin zare hannunta"saidai yak'i cika mata hannun"wai rowar maganar ake mun kome?"idan bakiyi mun mgn ba bazan cika wannan hannun ba"yanzun kinga Addu'ar danace kimun ta cikar burinah Ajiya ta Amsu cikin sauk'i??maryam! kece duk wani farin cikin Aliyu"burunsa akullum ki zama tasa" ina sonki yanzun,ina sonki Anjima ,ina sonki jiya ,ina sonki gobe ,ina sonki har illah masha Allah"tun kina jinjira maryam yaya Aliyu yafara dakon soyayyar ki Azuciyarsa"kullum burinah shine na kyautata miki kiyi farin ciki"ko Abaya danake takuraki wlh SONE ba K'IYAYYA ba..... Allah sarki yaya Aliyu nah! ni kaina bazan iya fad'a maka yaushe ne nafara jinka Araina ba"kawa dai nasan daka dawo dg k'asar cairo d'in nan naji kana burgeni"shinefa sai nake sonka ko?"ta fad'a cikin shagwab'a tana y'ar dariya har dimple d'inta na lotsawa"still yana rik'e da hannun ta"saidai tak'i yarda ta kallesa"satar kallon sa tayi ai kuwa caraf suka had'a ido"ya d'age mata gira yana fad'in sai kincemun I love you my durling sannan zan cika hannun"wayyo Allah yaya Aliyu brush fa zakayi kayi break fast"muyi dai break fast"nasan kema bakici komai ba sbd ganin sweetie naki babu lafiya ko?"yafad'a Ahankali yana k'ara matsowa gab da ita"wai dan Allah yaya Aliyu yaushe ka iya surutu?"my mero ta koyamun"d'aure fuska tayi tana sakar masa mintsini me rai da lafiya Asaman hannunsa daya rik'e gudan hannun ta"bbu shiri yacikata yana yarfe hannun yana b'ata fuska"kamar wani d'an yaro"In'am data kallesa sau daya ta kama dariya tayi wuf ta sauka dg samqn bed d'in"bazan yardaba saina rama mintsinina da kikayi yarinya"wayyo yaya Aliyu kainefa kafara mun shine saina rama"kuma bbu kyau mugunta ko?"tsaye ya mik'e yana kallon ta yaja kwafa yana fad'in bazaki fad'amun kina sona ba my Angel?"turo baki tayi tak'i mgn"ya d'auki kusan second 10 kafin yanufi k'ofar toilet d'in yana fad'in idan na rik'eki zan miki muguntar datafi wacce kikamun yarinya"In'am ta masa gwalo"yatura k'ofar yashiga be kula taba.....
Abba na isowa gida yanufi parlourn sa ya zauna yana nazarin soyayyar Aliyu da maryam"yakuma san tabbas Alh d'ahiru yaji Aliyu keson maryam koda kud'in wani Aka kawo saiya mayar yabama Aliyu ita"to ballema ba'a kawo ba"yana wannan tunanin yaji sallamar umma"wacce gaba d'aya bbu ruwanshi da ita"saiya kama yake mata mgn"yana ganin itace ya had'e rai"zama nesa dashi tayi tana fad'in Alh yaya jikin Aliyu d'in?"tun jiya da baizo yamun saida safe ba nafara zaton bbu lafiya"toda safen nan sai nafeesa ta shigo ta sanarmun bashida lafiya yana Asibiti"ga kayan kari can na had'a zanje na dubasa.....hmmm! kin makara hauwa! domin dai ita maimunar wacce kika tsana itace zuri'arta kecan ke kulawa dashi"yanzun haka ta bayar da break fast yusuf yakai tun d'azun"inaso ki sani ciwon Aliyu nada Alak'a da maryam sbd irin son dayake mata"sbd tsoronki yak'i furtawa"yara nason juna mugun halinki zai sakq d'ana yaje yarasa ransa koya kamu da wata lalura"inaso kisani idan Allah yatashi zai iya d'aukar ranki maryam da Aliyu su rayu Acikin inuwar Aure"d'ana yakamu da ciwon zuciya ga ulcer dukdan sbd damuwa"yana kumayi danke"Amma ke baki san ciwon saba"miye ribar k'iyayyar da kike nuna wa maimuna da zuri'arta??"to Aliyu nasami labarin sbd in'am ya kwanta ciwo"nakuma tambayeta tana sonsa ta Amsamun"sbd zan iya komai sbd farin cikin d'ana"nanda sati 1 insha Allah zan sakq ranar Aurensu"ya miki dad'i kokar yamiki banida matsala"saidai inaso ki sani muddin kika tado mana fitinah wlh zan iya rabuwa dake har Abada"ko A kwanaki darajar mahaifiyata kikaci na barki"dubiya kuma kije bazan shiga tsakanin d'a da uwa ba" yana fad'in hakan yaja tsaki yatashi ya shige bed room d'insa"umma ta mik'e tsaye ta fita jikinta Asanyaye"yyinda kalaman Abba ke Amsa kuwa Acikin kunnanta"part nata ta koma ta d'akko hand bag nata da hijab tabar masu Aiki ta fita batare data d'auki Abin break fast data had'a ba" bayan driver yafito da motar umma ta zauna back sit suka nufi Asibitin"bayan sun iso ta fito ta wuce ciki"tana shigowa a reception taga yaya sulaiman zaune kan kujera yana danna waya"shi bema lura da itaba"saida yaji tace"sulaiman inane d'akin da Aliyun yake ne?juyowa yayi da sauri suka had'a ido"ina kwana umma?"yafad'a dukda bata cika Amsawa ba idan sun gaisheta"yana dai cigaba da gaishetane koda bazata Amsaba bisa bin umarnin ummi"lafiya qlau"mik'ewa tsaye yayi yace"muje ga d'akin can gaba"yafad'a yana yin gaba tana biye dashi Abaya"suna isowa bakin k'ofar d'akin yanuna mata shi kuma yakoma Inda yake zaune.....
yaya Aliyu na shiga toilet d'in in'am ta kama dariya taje ta tsugunnah gaban basket d'in"cikin nutsuwa da tunanin wai dama tun tuni yaya Aliyu ke sonta?"wanda ada ita tana ma Abinda yake mata kallon K'IYAYYA"da wannan tunanin ta had'a masa tea me kauri me zafi"ta Ajiye samqn loka"sannan ta zuba masa farfesun kayan ciki da doya da k'wai Agefe"itama kanta yunwar takeji Amma wata iriyar kunyarsa yanzun takeji"bata jin zata iya cin Abinci Agabansa"tana k'ok'arin zama gefen bed d'in yafito dg cikin toilet d'in"saida k'irjin In'am yabuga"tayi k'asa da kanta tana wasa da yatsun hannunta"yarfo mata sauran ruwan hannunsa yayi yana fad'in my Angel kinga jikin nawa da d'an k'arfi ba kamar jiyaba"saidai kan har yanzun yana mun ciwo"Ayya sannu"yanzun kaci Abinci saika sha magani zakaji normal "to dr maryam"yak'are maganar cikin zolaya yana zama gefenta"murya can k'asa yace"wai k'auyanci meye haka?"karfa Ace kunyata kikeji?....nidai kayi shiru kayi break fast dan Allah"ta fad'a cikin shagwab'a batare data kallesaba"bazan yiba bayan kema bazaki ciba" kuma bakice kina sona ba....wai haka yaya Aliyu dama yake?"matsowa gefenta yayi yana danna wayarsa yace"zo kiga pics namu na jiya"ka bari kayi break fast saimu gani"kuma banace I love you ba"tafad'a tana saka tafikan hannayenta ta rufe fuskarta dashi tana murmushi"yaya Aliyu yace"wow banyi zaton hakan ba my Angel"I love you too! nasan saura kiris ki zama matar yaya Aliyu"shi kuma yazama mijin ki....shiru tayi Aranta tace bashida kunya"ki tashi ki had'a wani tea d'in kinsan bansan musu ko?"batayi mgn ba taje ta had'a ta sheka yarage zafi"tana dg zaune ta bashi baya ta kafa kai ta shanye ta Ajiye cup d'in"sannan tajawo farar kujera ta zauna dg gaban gadon tana fad'in to yaya nika dena kallonah kaci Abinci ga magani nan najiranka...yana k'ok'arin mgn umma ta turo k'ofar d'akin ta shigo da sallama"Atare k'irjin In'am dana yaya Aliyu yabuga!"kallo d'aya ta musu ta d'auke kanta"yaya Aliyu ne yayi jarumtar Amsa sallamar tata yana k'ak'aro fara'ar dole"da sauri in'am ta duk'a ta gaisheta jikinta har kirma yakeyi"ta Amsa fuska bbu yabo bbu fallasa"In'am ta sauka dg samqn kujerar tana fad'in umma ki zauna"ita kuma ta nufi k'ofa da nufin taje reception ta zauna kafin ummar ta fito"yaya Aliyu yabita da kallo tamkar yatsayar da ita saidai yana shakkar umma"In'am dawo kiyi zamanki ni tafiya zanyi driver na jirana"juyowa tayi Ahankali tana mamakin yau umma ta Ambaci sunanta bayan da K take kiranta dashi"umma ina kwana?"lafiya qlau ya jikin naka?"Alhamdllh da sauk'i yafad'a yana kurban tea d'in"In'am ta d'akko plate d'in farfesun ta ajiye masa gabansa ta zauna can k'arshen gadon"yaya Aliyu na satar kallonta ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login