Showing 45001 words to 48000 words out of 60927 words

Chapter 16 - Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel By Billy Galadanci.txt

manga yakumayi

"Zandai kiraki nace baby karki damu" kashe wayan tai ga alama taji haushi, Manga juwa wayancewa tai ta kalleshi tana murmushi, kwanciya tai sannan ta janyoshi jikinta, cikeda shagwab'a tace

"Ni tausa zakamun jikina ke ciwo yau na gaji" kwantawa yayi saman ruwan cikinta,ya laquci hancinta

"Hilwa banda rigima plss kinji, yanzu bani mintuna biyu nai wanka plss" batace komai ba harya kammala yazo ya kashe fotila ya kwanta a bayanta, lalubar ta ya soma yi bata hanashi ba, hasalima ta saki jikinta sunyi wasa seda ya soma yi mata sambatu, seda taga ze wuce gona da iri sannan cikin dabara ta zare jikinta tabar dakin, dayan dakin taje ta rufe kanta tayi wanka ta kwanta abinta tana me dariyar shirin ta akan Ali Abbas lallai seya yabawa aya zaqinta sabida kullum haka zata masa, seta saki jiki ya yagal galata sannan ta janye jikinta setaga gidan uban daze kai ruwan ida yamai maqura wurin san zubar dasu.....

Mom Nu'aiym.
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*

*👑ALI ABBAS👑*

*Billy Galadanchi*

*Sadaukarwa gareki qawa tagari Fulany saddy*

*Wannan shafin tukwicine agareki fulani shamcy,nagode sosai da kulawa Allah yabar qauna*
                                         21
Wani irin ciwon kaine ya tasowa Ali Abbas tsabar sha'awa, yaje dakin datake ma yayi ta knocking tamai banza,wannan dare gabaki d'aya idanshi biyu be runtsa ba sam, yaci azabar sha'awa ko huddy data d'inga kiranshi kasa d'agawa tayi gabaki daya  ya gama shiga tashin hankali.....washe gari tun asuba manga ta sake caba sabon adon, kuma tayi kyau abinta matuqa, kai tsaye ktchn ta wuce waffles sandwitch ta musu da burger sannan se semolina pudding, a gurguje ta kammala komai ta baiwa masu kula da bangaren damar jere komai a dining sannan ta koma dakinta ta qara watsa ruwa ta kimtsa cikin wata lallausa doguwar rigar material ja me ratsin baqi a jiki ta gyara sumar kanta ta kwanta luf abinta, kai tsaye d'akin Ali Abbas ta nufa se tashin qamshi takeyi tako ina, zaune ta taddashi bakin gadon yana waya ga alama shida mahaifiyar shine sun jima suna wayar daga qarshe ya miqa mata suka gaisa

"Auta aini fushi nakeyi dake kuma shakka babu sena zaneki idan nazo garin, zanzo ne zuwa jibi dole na,naji abubuwan dake faruwa nakuma ji cewar ke jinina ce gaba da baya,dama nasan wannan qaunar danake miki akwai jini aciki inshaa Allah kuma zancen da kakan naki keyi baze ma faru ba, auren nan naki tunda Allah be rabashi ba babu wanda ya isa ya rabashi har abada kinji" murmushi tayi

"Ni ummu bazan ma koma Yamai d'inba, bansan da wannan zancen ba se kwanakin can, haka dai kurun bayan duk abinda yamun nataso tamkar baiwa yanzu kuma be daddaraba shine ze wani zo ya kashen aure" murmushi ummu tayi har ranta taji dadin maganar manga tace

"Yauwa auta,amma dai kidena xancen bazaki koma ba, aiko ba komai kakanki ne ya cancanci fiye da biyayya daga wurinki idan akwai so plss ki nustu" gyaran zamanta tayi ta shagwab'e fuska yanda tasaba wa ummu shagwab'a

"Toni ummu haka kurin kuma bema sanni ba daga sama ze wani ce ze takurani, ni ko yaa Alin anan zan barshi Allah idan kinzo qafana qafanki,garin ma ba maggie irin wanda nakeso niya isheni" sosai take birgeshi yanda take rero wa ummu shagwab'a

"Naji auta zanzo mana da maggie seme kuma kikeso?"

"Se tuwon madara da wannan carbin malam d'in dan Allah kuma ki sanya a soyamun aya, ki tahomun da garin dan wake duk babu anan" murmushi ummu tayi tasan dama indai Manga ce akwai shan zaqi

"Auta dan Allah ki rage shan zaqin nan,nidai a kayan zaqin nan ki zab'i wanda kikeso qwaya d'aya shizan zo miki dashi"turo baki tayi tamkar ummu na gabanta

"Nida d'add'ai da d'add'ai zan na riqa sha dan Allah ki tahomun da duka wlhy duk inaso" dariya yanzu kam ummu tayi

"To yayi zan taho da duka da yardar Allah, ki gayarmun da yar riqon taki" tsalle ta daka

"To ummu Allah ya barmun ke, sekin zo" sukai sallama ta baiwa Ali Abbas wayan

"Ummu dan Allah ki qyale zancen Manga zaqin ze mata yawa wlhy"

"Ba ruwanka yaro, ni kaga se anjima mayi magana ma" ta kashe wayan ita kuwa rausayar da kanta tana kallonshi idannan yasha kwalli

"Haba yaa Ali yazakace karta zomun dashi inasone fa yasa nace haka?" murmushi ya sakar mata me laushin gaske...."Manga rigima nida aka gwasale ma tace ba ruwana" gwalo ta masa tace tana kwanciya saman jikinshi

"kasan sarai ummu tafisona dakai miye na wani mana shishigi" jan hancinta yayi yace yana shafar sumar kanta da d'ayan hannunshi

"Mesa kika mun abinda kikamun jiya Hilwa? Kinsan kuwa tsinuwar Allah tana kanki kin gujewa shinfid'ar mijinki alokacin dayake tsananin buqatarki?" lumshe idanta tayi ta bud'esu akanshi a hankali

"Yaa Ali alqawari fa, alqawari kae cewar bazaka yiba, da kunnena naji kana daukar wannan alqawarin bawai wani yagayamun ba,dama ka dena wahalr da bakinka dan bazan maka wannan ba, seka sauke ruwan alqawarin a inda ya dace nina karbi ragowar" shiru yayi yana nazarin kalamanta lallai shima ya sani be kyautawa manga ba, ya zeyi da itane? In hakane ze qaurace mata ya kula bazata bashi hadin kaiba...murmushi ya qaqalo yace

"kiyi hakuri Manga bance bakiji abinda na fada ba amma ki sani sabida kurun na huta ne da rig8mar mata, ki yarda dani bekai zuciyata ba sam,banida burin daya wuce in kyautata miki in biyaki dukkanin bashin haqqin ki dana d'auka,Hilwa idan kikace zakimun haka baki damar wanke tarin laifukan dana aikata gareki ba, ke kanki shaidace banida macen danakeso sama dake kodan wannan kya sassauta mun wannan hukuncin, bana so ki dauki maganganuna a matsayin yaudara ko kuma sabida inada sha'awarki nake miki dad'in baki wlhy sam bako d'aya kece muradina Manga banida wata sama dake" kallon nutsuwa take dire masa harya kai aya,cikin murmushi tace

"Amma menene hukuncin mijin daya hana matarshi cin breakfast har 9 na safe" dariya yayi ya dauketa cak

"Ba laifin sa bane rigimar matar ne yayi yawa ai" suna dariya suka fita be direta ko ina ba se dininga,da kanshi yabata abinci taci sannan yaciyar da kanshi suka koma kallon TV.....

Daren dayazo kuwa Ali sam be nemi manga ba yasani sarai bawai yarda zatayi dashi ba, dan kanta ta kawo kanta be gujetaba sunsha wasanninsu sannan ta zame jikinta daga nasa ta rufe da duvet ta juya masa baya, yau kam manga waninirin azababben desire takeji har qasan ranta, taso sosai Ali Abbas yaci gaba da koda yi mata wasannin dayake mata ne amma ya mata banza, sunfi awa biyu idansu biyu kowa na zatan dan uwansa yayi bacci, itace taje tayi wankan tsarki tazo tazauna busar da kanta tasowa yayi a hankali yazo ya tsaya mata aka yace

"Manga wankan me kikayi acikin daren nan" kunya sosai taji amma seta dake tace

"Kawai haka nayi sha'awar yi" murmushi yayi yace

"Amma har wankin kanma se cikin dare zakiyi" wannan karon yasoma bata haushi ta juyo gaba daya ta fuskanceshi

"Ka soma aikin jari dane wai nikam yaa Ali? Ka soma damuna fa" murmushi yayi ya wuce toilet koda ya dawo batanan tabar d'akin gaba d'aya.....

*Bayan kwana biyu*

Kallon kallo aka tsayayi tsakanin Manga da huddy bayan dirarsu qasar Niger itada ummu, da jirgi sukazo wannan ya sanya su manga sukaje tararsu, bata zata tare da huddy suka zo ba, da qyar ta qaqalo murmushi sabida yanda taji qirjinta na dokawa

"Aunty huddy sannu da zuwa" murmushin ta sakar mata itama

"Yauwa Manga ya gida da qasar kuma" murmushi kurin tayi bata bata amsa ba sabida yanda jikinta ya mutu, ummu na shiga mota huddy da Ali Abbs sukai hugging juna, sannan da kanshi ya sumbaceta a goshi da sauri Manga ta kawar da kanta daga dubansu motar Ali Abbas suka shiga dukkansu yayinda ummu tabi driver shike tuqi yayinda huddy ke zaune agaba...manga na baya se cika take tana batsewa anzo da ita agabn mota gashi daga zuwan Huddy har an kaita gaba ita ta dawo baya.....bamewa wani magana har suka isa gidan.......

Se da dare yayi Manga na b'angaren su kurin taji knocking,wazata gani ba Huddy ba da luggage dinta a hannun hadima, kasa matsawa tayi su wuce seda huddyn tace

"Me martaba ne yace nazo nan sashin gun Ali Abbas" wani baqin cikine ya tarnaqe Manga da qyar tace

" 'yar china ki kaita d'ayan d'akin dame me amfani dashi karta takura" suna shigowa parlon huddy tace

"Manga amma naji ance zuhair baya nan gidan mezai hana naje gun Ali abbas kawai ba amfanin rarraba d'akunan ai inaga" wani kallo Manga ta wurga mata sannan kai tsaye tace

"Kowa da d'akinshi anan Aunty huddy, nima ba d'aki d'aya nake sharinga dashi ba" gyaran tsayuwa huddy tayi

"Inaga tunda yau nazo ya dace ace na k'arb' girkin tunda kin kwana biyu kinayi bana nan, shisa nace ba amfanin raba d'akin tunda kayana bamasu yawa bane" haushi dukya ishi bama kara a lamarin, idan tayi hakuri ai idan lokacin kwanciya yayi dama bame hanata zuwa gun mijinta amma wannan haukan har ina,manga bata qara Managa ba tadai nemi wuri ta zauna...Ali Abbas da kanshi yakirasu parlor ya kalli Huddy tace

"Hudaisa kece babba, sabida haka ki sani bazan raba kwana anan garin ba,semunje gida Nigeria kowa harni ku riqa kwana a d'akuna daban daban tunda kowa yanada nashi akwai yalwantar d'akuna amma nan matsayin baki muke har manga bazan so hakanan ba" turo baki tayi..

"Haba Abbi Ameer,yaushe rabona dakai indai za'ayi adalci,ba wani abu acikin raba kwana, nidai kasani gaskia ina buqatar mijina"

"Haba baby ki fahimceni mana,nan fa ba gida bane ba"

"kurun dai kace baka buqatana,ni zaka tauyen haqqina sabida bakasan ya nae misaing mijina ba" miqewa manga tayi cikin fusata

"Yaa Ali wannan maganar inaga tun farko be dace ni a sakoni aciki ba, indai ba wani abin ake nufi ba nason aci zarafina, kurin kuje kuyita kwanciyar meye aciki, shekaruna biyar ina matse k'afa sabida bansan dad'in mijiba, yanzu wanda suka san dad'in juna sunzo suna magana bandaida anasan cimun zarafi meye na kirana kune can ku qarata ni nan b'angaren ma zan bar muku" tayi hanyar waje da sauri Ali Abbas yaje ya riqota ..

"Haba Manga menene ma'anar hakan kuma?" warce hannunta tayi,yayinda huddy ke dariyan jin dad'in ta had'a fad'a dama haka ta shirya, se yanzu ita kanta ta fahimci tana tsananin kishin mijinta bazata barsu suyi zaman jin dadi ba ta qudurta

Masu karatu shin aganinku watafi gaskia? Anya Ali abbas ze iya da rigimar matanshi kuwa? Menene makomar wannan zaman kishin? Shin anya Manga batayi saurin manta halascin huddy ba kuwa? Anya manga batayi saurin nuna jin zafiba? Kodai tafisu gaskia shekaru biyar faa ba kwana biyar bane sam!!!!!

Vote! Vote!! Vote!!! Plsssss en wattpad kun iya karantawa amma bakwa voting mesa????

*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*

*👑ALI ABBAS👑*

*Billy Galadanchi*

*Sadaukarwa gareki qawa tagari Fulany saddy*

  *Kota yaya zan soma kwatanta kirkinki agareni pheey? na sani alqalamina ma bashida qarfin daze iya rubuta yawn alkhairanki agareni,Allah ya saka miki da alkhairi ya sanya alkhairi da albarka me tarin yawa arayuwarki*

                                        22
Har manga ta juya ta hango yanda huddy  ke murmushi seta juyo gaba d'aya ta had'e jikinta da nashi wuri d'aya,sumba ta manna masa a goshi sannan  tace tana riqe da hab'arshi

"Amma Boo kasan baze yiyu mu shiga hakkinta ba ko, kwana na nawa dakai? Idan dai ba rigima kakeso kamun ba kuma kasan yanzu banida maganin qishirwarka yana hannun Aunty huddy,nayi qoqarima kasani fa bawai sabawa nae ba amma haka nake daurewa,yau kuma Allah ya qwace ni seka zo da rigima,dan Allah ka ka tausayamun" tsororo yayi yana mamakin sauyawar akalar zancen lokaci d'aya ya gano wata wutar takeso ta kunna masa

"Amma manga dukda haka cikin gidan zasumin wani kallo ida.....bakinta ta had'e da nashi ta hau tsotsa tayi 1mnts tana aiki d'aya shiko yakasa komai kurun dai ya riqo qugunta ne, sakeshi tayi  tana murmushi

"Nasan wannan zakafi missing, ga shinan na d'an baka, yau Allah ya qwaci bakinnan nawa, da kake kwana kana dirxa" murmushin dai ya sakar mata ya gano ta rigada ta gama da matsalarshi hannunshi ta riqo

"Kayi hakuri na kwana a d'akinnan,bandani dakai se kuma huddy waye zesan an raba mana kwana, kaje ka bata haqqinta datake ta magana akai, sanin kankane cewar babu macen dazata had'a jiki dakai taso kuma ku rabu koda na wuni d'aya ne, banaso kayi tunanin ban damu dakai ba yanda zakayi rashina na kwana daya haka nima zanyi matuqar kewarka kaji" ta qarashe maganar tana me shafar sajensa ta langwab'ar dakai" murmushi ya sub'uce masa lokaci d'aya yaji gaba d'aya ta burgeshi yama manta da huddy a wurin, janyota yayi ta fad'a jikonsa yace yana shafar sumar kanta a hankali

"Tunda kin matsa ba komai, amma kiyi adu'a kafin ki kwanta plss,kuma ki riqa tunawa dani kima tabbatar kinyi mafarki na kinji Hilwa?" qayatacce murmushi ta sake masa sannan ta zame jikinta a nashi

"Ko tare dakai na kwana mafarkanka  ke cikashe faifan baccin danake boo,karka damu kaima sekayi nawa, ka tabbatar yau munyi komai damuka saba a mafarki" manna mai sumba tayi a wuya ta juya sannan tace

"Aunty huddy seda safe, yaa Ali acika alqawarin daka dauka yau plss" shiya gane inda Manga ta dosa na zancen alqawari yayinda huddy ta cika ta batse sabida ta zata alqawarin mafarkin dasuke Manga ke nufi, miqewa tai fuuuuuu ta wuce zuwa d'akin nasu kasa ma daurewa tayi ta sanya kuka, shi kuwa sun barshi sororo a wurin yana mejin dad'in qalaman Manga ya qurawa d'akin data shige ido ya kasa janyewa, matsawa yayi kusa da d'akin ya soma knocking a hankali, matsowa Manga tayi ta rungumi qofar sosai hawayen datake ta hanawa su zubo sanda sukayo ambaliya zuwa kuncin ta gashi tayiwa qofar key koda batawa qofar key ba bazata tab'a bud'e masa amma kam tanajin wani qaunarshi da sha'awarsa na fizgarta.....a hankali tace

"Waye?" cikin rarrashi yace

"Manga dan Allah ki bude sallama kurun zan miki" murmushi tayi me quna tace

"Yaa Ali kayi hakuri banaso in ganka zan shiga tashin hankali kasani na soma sabawa dakai gwara ka barni haka nan plss,kuma dan Allah karka kuma bud'e bakinka jin muryanka kad'ai bakasan kalan kasalan dayake saukar mun ba, indai kana sona ka juya abinka kawai" jiki a mace ya juya zuwa d'akin da huddy take a kwance ya tadda ita tana ruwan hawaye da sauri yayi kanta ya riqota yace

"Haba hudaisa,menene ya sanya kike so ki b'ata rawarki da tsalle? Yayana ana yabonki sallah zaki kasa alwala? Kinsan kuwa shirmen da kika tafka agaban qaramar yarinya, bansanki da haka ba yaya zaki bari kishi ya rufe miki ido ki janyowa kanki raini   awurin qaramar yarinya sabida qaddarar kishi ta had'aku, sam ki sauya tunani idan haka kika shirya yi" tsaki  taja masa ta miqe tana wurga masa wani kallo....

"Ni babu abinda zaka gayamun ka gama wulaqanta ni agaban qaramar yarinya, yanzu sabida Allah wannan cin mutuncin dakamun har ina? Agabana kake had'a jikinka dana manga,yanzu ka gayamun nice nakeso na janyowa kaina raini  kokuma kaine kake qoqarin janyomun rainin a wurinta, kasani wlhy wannan ne na farko amma idan kayi na biyu bazan haqura ba" qura mata ido yayi sabida a tsawon zaman shi da ita yaune rana ta farko data tab'a gaggaya masa maganganu haka,yakuma kula inma da laifin ta shima da nasa laifin sam be kyauta ba abinda ya aikata agaban ta, amma kuma ai bashi ne yayi ba, Manga ce shi miye laifin shi? Biye matan da yae? Dukda haka tallafo ta ya qarayi sosai

"Kiyi haquri huddy inshaa Allah bazan qara kwatan ta yi miki hakan ba, wannan ma kuskurene kuma na fahimceki sosai" batace dashi komai kurin dai ta rufe idanta ne ya kula ta rigada ta gama shaqa ba zancen kuma ya angwance dole haka ya qyaleta suka kwanta a mabanbantan gefe, kowa da abinda yake saqawa aranshi, banda sanjin Manga ajikin Ali ba abinda yakeso, se tunano moments da sukayi sharing tare yake yana sauke ajiyar zuciya lokaci zuwa lokaci yakan juyo ya kalli huddy ya kula ita ma ba bacci takeyi ba ranta a dagule yake.....

A b'angaren Manga ma hakan take, ta gama haqiqan cewa kanta lallai yanzu kam bazata rayu acikin farin cikiba inhar babu yaa Alinta atare da ita,sam bazata juri rashin saba na wani tsawon lokaci tun wuri gobe zata karbi girki inyaso kwana daya daya zasuyi bazata iya da rashin saba sam!!! Haka ta kwana tana dirzar kuka da asuba koda ta tashi gaba d'aya fuskar nan tayi ja idon sun kumbura sunyi luhu luhu dasu,cikin qarfin hali kanta yana sara mata taje ta alwaha tayi sallah, ta dade tana adu'an Allah ya rage mata zafin kishi sannan taje wanka ta sanya doguwar rigar atamfa kalar sararin samaniya da pink ba wani makeup data sanya se powder da lipbalm tayi kyau dukda haka daka ganta kasan bata cikin walwala, ktchn ta shige kai tsaye ta had'a musu chips kawai se meaty egg, yasha kayan qamshi da dandano, ruwan arabian coffee ta had'e musu gu daya sannan ta sanya akai komai zuwa dining.....da rausaya tamkar zata fad'a sabida kanta dake sara mata ta baro ktchn d'in zuwa d'akinta, cin karo tayi da Ali Abbas ga alama yanzu yafito wanka,jallabiya ce kurun ajikinshi sabida sumar kanshi ma a jiqe take sharkaf da ruwa, zuwa tayi ta kwanta a qirjinsa sam bazata iya hanawa kanta maganin ciwon dayake ba, rashin kwantawarta ajikin sa jiya shine ya janyo mata ciwon kan datake a hankali ta furta

"Yaa Ali banida zabin daya wuce na sanar maka nayi kewarka sosai jiya, bana fatan ganin abinda ze shamakanceni kasancewa tare dakai mijina, wlhy ina sanka, na tuba akan dukkanin abinda na aikata maka nidai roqona d'aya karka kuma cewa zakamun nisa yanzu kam idan hakan ta kasance lallai mutuwa kawai zanyi kowa ya huta" matseta sosai yayi ajikinshi

"Waye ya sanar dake zan gujeki Manga? Haba kema kinsan koda can ni ina tare dake

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login