Showing 51001 words to 54000 words out of 60927 words

Chapter 18 - Ali Abbas Part 1 Complete Hausa Novel By Billy Galadanci.txt

motsa ba, mahaifin shi ya mayarda dubanshi zuwa ga reshi yace

"Kayi hakuri zansan yanda za'ayi na karbo takardar sakin Manga batare daka saki Innoh ba, ka sani wlhy bazan bari su lalata ma rayuwa ba so yake ka auri er talaka in shiga uku na, yasani tunda ka gudu da mace babu wacce zata sake aurenka daga wata masarautar har abada, nize b'atawa suna ya sanya jinina ya auri er matsiyata yayi kad'an kuma" qurawa mahaifin nashi ido yayi,amma ya kasa furta komai aranshi yake mamakin hali irin na mahaifinshi wato shi sam beji wa'azi ba haryanzu beyi karatun ta nutsu ba, duk wannan abin daya faru beyi realizing cewar ya aikata mummunan kuskure ba, aranshi yace wannan karon sam bazan lamunci wannan rashin adalcin daga wurin mahaifina ba, a zahiri kuwa miqewa kurun yayi yabar fadar gaba d'aya batare dayace kanzil Ba....

  Kai tsaye jirgin sha biyu suka hau zuwa yamai, Ali Abbas kansa ya masa zafi, ya kasa gane inda dukkaninsu suka dosa,menene kuma ze sanya yarjejeniya tashiga cikin wannan maganar, manganshi akeso a had'awa zafi biyu lokaci d'aya akashe mata aure kuma akashe na uwar ta, yanadabyaqinin yanzu manga tasoma sansa ba ma kad'an ba, yana wayannan saqe saqen har jirginsu yayi landing a yamai.....

*Ina labarin Manga*

     Kallon kowa take da mamaki ta sanya wata baiwa ta mata kiran wani daga cikin dogarawan dasuke tsaronta

"Tambayar ka zanyi kabani amsa kai tsaye menene ya sanya aka kawoni nan kuma mesa aka kawo ni nan d'in?" sadda kanshi yayi qasa yace

"Ranki ya dad'e duk wanda kenan babu wanda keda masaniyar mesa aka kawoki nan, andaice mu tsareki tsaro me kyau karmu barki kije nanda can inji me martba" gyad'a kanta tayi cikeda gamsuwa da bayaninsa ta fahimci inda zancensa ya dosa,gyaran zamanta tayi tace

"Lallai kam da gaske me martaba nasona da hutu, tonan wane unguwa ne? Kallonta yayi bayaso ya sanar mata asamu matsala se sadda kanshi yayi qasa, ta gano baya so ya sanar mata setace

"Jeka abinka nasan zezo shise sanya a sanar dani ai" juyawa kurun yae, ita kuwa se hawaye shar, kallon akwatin kayanta tayi lokaci d'aya ta sak8 wani lallau san murmushi ta kalli hadimar dake d'akin tace

"Ki bani wuri bana san damuwa idan ina buqatar wani abin zan kiraki" ficewa tayi sumsum ita kuwa ta sauka da hanzari ta zuge zip din akwatin kayanta ta soma bincike, qaramar wayarta ta zaro wacce tunda sukazo ta ajiyeta sabida yanda idan takira ummu a Niggria ake zuqar katinta, Murmushi tayi sanda ta kunna taga cewar akwai caji a jiki, zuwa tayi ta datse qofar d'akin sannan ta dawo ta zauna kallon allon wayan take ta kasa tunano Number din Ali Abbas babushi a wayanta katin baze isheta ta kira ummu hartace ta sadata da Ali Abbas ba, runtse idanta tayi ta bude se yau take ganin wawtar ta ta qin haddacw digit din mijinta, Flashing tawa ummu dake can cikin tsananin b'acin ran cin kashin da aka musu, amma Mahaifin Innoh ya sanar musu hikima ce yanda yayi sabida me martaba baze tab'a bari Iro ya saki innoh ba,sabida kowa yasan yabar gida ba wata masarauta dazata baiwa iro aure shi kuwa baya had'a kanshi da talakawa, yanaso ne ya nuna masa kuskurensa.....tana dubawa taga Manga ta kira back da sauri dama tayita kiran number dinta bata shiga

"Ummu naa inasan nabar nan gidan ban gane me ake nufi da ajiye anan ba"

"Ki nutsu Auta gayamin kina ina yanzu?"

"Ummu nima ban sani ba wani gida kurun na farka na ganni ga gardawa da hadimai mata sunfi 30 a gidan hadda akwatin kayana, aciki ma na dakko wannan wayar tawa dana ajiye dan banga babban wayana ba"

"Tou ki saurara kiji,kakanki ne ya sanya aka b'oyeki sabida yanaso ya sanya lallai ALi Abbas ya sakeki, toki sani bazan iya haqura ba, bazan lamunci tarwatsewar rayuwar ku ba sabida haka nawa me martaba waya zezo gobe inshaa Allah, ki nutsu idan kakan naki yazo ki nuna masa sam ke bazaki komawa Ali Abbas ba, kema bakya so dama tsoro kike ji yanzu kuma tunda kinada gatanki abi miki haqqinki, zakiga ze saka a dawo dake cikin mutane ki nuna masa aje koma inane ke bazaki koma ba, ni kuwa kinga idan an kawo ki zansan yanda za'ayi in sace ki zuwa Niger dan na gano seda haka....."daganan ta kwashe komai na yanda akayi da mahaifin innoh dana baban manga ta sanar wa manga ta qara da cewar

"ko yanzu hankalin shi a tashe yake sabida bayasan sakin, kina addu'a kuma ki kula sosai kar wani yaga wayar hannun ki mu kasa gaisawa, zan saka yaro ya kiraki nanda mintuna biyar nasan kina buqatar hakan" da sauri tace

"Sosai Ummu,sosai nakeso inyi magana dashi ince ya kwantar da hankalin shi indai nice bazamu rabuba da yardar Allah" nisawa ummu ta qarajin tausayin su matuqa ta qudurta a ranta se inda qarfinta ya k'are.....

Manga na nan kwancen sega kiran Ali Abbas, dama kuma ta saka wayanta silent sabida tsaro, lumshe idanta tai tamkar yana ganin ta sannan ta sauke ajiyan zuciya datajiyo shi shima ya sauke fiye da nata kan yace komai ta soma kuka


"yaa Ali amma seda nace dakai zanbi Aunty ka barni na taho nan dabasa sona sam,yanzu gashi sun datse ni a wannan gidan sun hanani in ganka kuma nayi kewarka fa" ta qarashe maganar tana sheshekar kuka"

"Karkice zaki mun kuka mana Manga na, zaki qara d'agamun hankali ne fa,kinsan banasan b'acin ranki ko nan da can dan Allah ki kwantar da hankali, idan kikai yanda ummu tace qasar Nigeria ma bazani dake ba, Madina zan koma dake da zama gaba d'aya inda bame takurawa rayuwar ki kinji" shiru tayi ta tsagaita kukan tace

"Toni kamun labari bana jin dad'in komai kai kawai nakeso in gani" murmushi yayi ya soma mata wasa seda ta saki jikinta.....

Washe gari kuwa sega Shinan yazo da kanshi me martaba, cikeda da dabara Manga tagama ce masa batasan Ali Abbas bazata koma ba, ita koda ma su inno zasu koma nigeria bada ita ba dad'i kamar me ya dinga zabga mata albarka ya dauketa suka koma ainahin gidanshi...... Ba jimawa sarkin musulmi yazo daga sokoto da kanshi, en yamai ma sun qaraso aka zauna meeting akai akai yaqi amincewa da maganar su, haka aka kira ganin be yardaba ya sanya itama tace bazata koma ba, haka taro ya watse rayuka ba dad'i....Abinda be sani ba Manga daga fadar shi masarautar ta bari gaba d'aya ba tare da kowa ya sani ba, kai tsaye batare data dauki kayanta ko daya ba se wayarta babba da qarama da caja da jakar hannu.....tasha taje ta hau mota ta wuce Nigeria gaba daya abinta,message kurun tawa Ali Abbas akan tana hanyar Nigeria.....

Mom Nu'aiym
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*

*👑ALI ABBAS👑*

*Billy Galadanchi*

*Sadaukarwa gareki qawa tagari Fulany saddy*

                         25
Se washe gari su Ali Abbas suka bar garin gaba daya tare da me martaba, yayinda sargin yamai se masifa yakeyi akan sune suka sace Manga babu wanda yabi ta kanshi har Baban Manga suka had'o ba sallama suka sake baro masa gidan wannan karon baban Manga ya saka a rayuwarshi baze qara waiwayar gidaba ya kula sam mahaifinshi baze tab'a canjawa kuma yana shirin wargaza masa rayuwarshi data zuri'arshi baki d'aya,kuma mahaifin innoh ya bashi goyon baya a sokoto ya siya musu gida sannan yace tunda can Allah ya qaddari zaman nasu yaja jari abinsa yayi kasuwanci......

   Kallon kallo aka tsayayi tsakanin huddy da Manga bayan da Manga ta isa sokoto,

"Aunty huddy ina wuni?" shine  abinda ta furta bayan da taga kallon bame qarewa bane,wani sheqeqe huddy ta kalleta ta zubar sannan tace

"Lapia lau,me kikazo yimun agida?" Mamakin kalamanta Manga keyi ta juya kawai zuwa d'akin dayake mallakinta tuni batare data bata amsa ba, itama huddy batabi ta kanta ba sabida aiki zataje ta wuce tana mamakin dawowar ta ayau bayan Ali Abbas yace shise washe gari, haka ta fice zuwa gidan batare data kira shiba a zatonta tare suka dawo, tana mamakin mesa ze turo mata manga gidanta bayan itama mangar tanada gidanta mallakinta wanda aka kaita cikinsa matsayin matarshi? Haushi kamar me haka ta qarasa office se mita take a zuci.....

Dayake dawowar mota sukayi yamma likis suka dawo sokoto,dama koda su Baban Manga suka zo anrigada an siya musu gida sedai se andan masa gyara kasancewar anginane ba wanda ya shiga anan fada aka musu masauki kan a kammala gyara, kai tsaye Ali Abbas part d'insu ya wuce Huddy yaci karo da ita a parlor tana shirin fita zuwa office kawar da kanta tayi daga dubansa batai magana ba, da kanshi ya qarasa gareta,harga Allah Ali Abbas yana matuqar san huddy ya kasa gane inda ta dosa a en kwanakinnan, kyakyawar runguma ya kai mata ya sumbace ta a goshi,hannu ya sanya ya tallafo hab'arta

"Baby ni kuma yau fushin me ake dani? Tun jiya nake kiranki bakya daukar wayana mesa? Murmushi ta sakar masa najin dadin yanda taga ya damu da ita sosai

"Kaine baka sanar dami tun jiya zaku dawo ba ai,se manga nagani kuma baka kwaba a gida ba" murmushi ya sakar mata shima

"Huddaisa nine nace dake tun jiya na dawo wlhy ni yau na dawo gidannan,da garin ma gabaki daya Manga ma da kika gani da kanta tai tahowarta jiya bazata iya zuwa yauba tace" sauke numfashi tayi tace

"Ina call ne kuma an kawo emergrncy yanzu akamun waya ga ambulance can ma tazo ta daukeni,so zan tafi sena dawo" qara matseta yayi sosai yace

"ki dawo da wuri my baby,ina buqatar kulawanki fa" murmushi jin dadin kalamanshi tayi ta hade bakinta da nashi adaidai lokacin da manga ta doso parlor din tafito dakinta,lobbyn ta koma da sauri girjinta ya soma dokawa da sauri bayau ne karanta na farko ganinsu a haka ba, amma lallai yau taji wani azaba dabatasan da akwai irinshi a duniya ba,hankalinta ya tashi matuqa,wani qololon baqin ciki ke mata yawo tsakanin cikinta da maqogwaronta ta kasa had'yeshi ta kuma kasa fito dashi.... Tanajin ambude kofar alamun Huddy zata fita ta fito tattaro nutsuwarta tayi gu d'aya bataso ya gane tace tana me rugowa da gudu

"Oyoyo yaa Ali" wara hannayenshi yayi yana dari ta fad'a qirjinshi da gudunta tana dariya,d'agata sama yayi yana jujjuya ta

"Hilwa na an qara nauyi kiga yanda nake gumi sabida na daukeki" ya furta daidai lokacin daya direta a qirjinsa bayan sun kwanta qasa ta masa rub da ciki suna shaqar numfashin juna

"Ni Gaskia karkace ina qara nauyi sabida banasan nae qatuwa kaje ka auromun sirirya tazo tana mun yanga" Huddy dake tsaye kallon kanta tayi yanda aure ya mayar da ita wata irin qatuwa tamkar ba ita ba, shi kuma dariya yayi sunma manta da ita wlhy manga ma ta zata ta wucene shisa ta ware suka jin dadin ganin junan su

"Hilwa kome zaki zama arayuwa nime qaunar kine a haka, ni sam bana san mace bushsashiya nafiso wannan qaton d'uwawun naki ya qara girma yayi goman haka ma" turo baki tayi cikeda shagwab'a tace tana me dukan girjinshi

"yaa Ali sam bakada kunya agaban kanka tsaye kanka cewa wannan abin" tsunkulinta ya shiga yi suka ruga d'akin da gudun su atare suna qyalqyala dariya, huddy dake tsaye jikin k'ofa share qwallan daya kwaranyo mata tai ta wuce kawai zuwa wurin aikinta rai a b'ace, wani azalzalallen kishi takeji mara misaltuwa...office ta rufe ta sanya kuka bayan ta isa, tafi 10 mnts tana kuka gata da Emergency case tunda waya ne aka mata, mamanta ta kira a waya tana d'agawa tace da ita

"Mommy wlhy bazan iyaba,kin mayi haquri dama haka kishi yake,wlhy mommy idan naci gaba da zama Manga koba itaba indai kiahiyace mutuwa zan, dan Allah ki sanya ko bokanki ne ya kashe auren Manga da yaa Ali wlhy na gaji bazan iya jure waba" wani qasaitaccen murmushi Mommy tayi yaudai zatasha dadin ta gashi har er ta tasoma gane kan garin,tunda har da kanta take zancen aje gun boka

"Yauwa 'yata dama na sanar dake bazak8 iyaba,wani aikin se boka d'an murus,gunshi zamuje nida haj mariya gobe da safe in saka ya kashe auren murus,kowa ya huta kinji yarinyar kirki,Allah ya miki albarka da kika gane wa ennan dangin na mayu mallake miki miji zasuyi" sallama sukayi sannan ta wuce zuwa office.

*Yamai*

Tunda aka bincika ba Manga ba dalilin ta hankalin sarki ya tashi, koda ya nemi a kira masa iro aka sanar masa baya gidan shima tun safe seya qara rikicewa, ganin dai har dare ba labarin dukansu ga wayanshi bata tafiya, ya gano sarai sun gudu ne shida ershi in kuwa hakane iro be kyauta masa ba akaro na biyu ya nuna masa ya isarwa kanshi,yayi bakin ciki matuqa,yakuma qudurta aranshi baze taba qyalewa ba,seya bi bayansu ai masarautar ta sokoto ba b'oyayya bace....

Ammin huddy taci nasarar zuwa gun bokanta inda ta karb'o wani ruwan da idan har huddy ta saka shi a abinci yaci, takumayi tsarki da ruwan tabashi na tsarkin yasha to kuwa baze qara ganin wata mace a idanshi ba se ita kawai, zeji ya tsani kowa.....


Kwance a saman jikin Ali Abbas Manga take tana wasa da kwantacciyar sumar data yi luff a saman faffad'an qirjinshi,idanta a lumshe yake tana jinta daban bazata kwatanta kalar dad'in datakeji ba a wannan yanayin, shi kuwa hannunshi nakan sumar kanta yana shafawa a hankali,magana yake mata da wata murya wacce ita kad'aice kalar sautin ke fita idan yana magana da ita shida kanshi besan dalili ba.....

"Manga bana san kowa yasan cewar Madina zamuje, inaso in samu nutsuwa mafi dad'in gaske atare dake,ki sani muna tare da mahassada iri iri a kewaye damu,kuma akwai masu bibiyrmu da mugun sharri sabida haka kowa ki sanar masa zaki koma Niger gun kakan ninki, akan wata sabga ta daban haka muka tsara dasu Abbu, ni kuma zanje lagos idan na wuce da kwana biyu seki biyoni baya a lagos din daganan semuje dubai mu wuce madina bayan sati uku" murmushi tayi tace

"Tooh yaa Ali,amma kwana biyun dazakayi da tafiya ka barni zanta kuka ma ko" dariya ya sanya hannu ya shafi nonuwanta

"Nima zanyi missing komai daya shafeki Hilwa,musamman abokanan wasan nan nawa guda biyu ina qaunar su sosai kuma bana so suna mun nisa" fuskarta ta cura a cikin qirjinsa alamun jin kunya tace

"yaa Ali kaiko tam shi kenan" cakulkuli ya soma yi mata ta zille tana dariya tayi hanyar toilet,manyan mazaunanta da heeps ya qurawa ido yanda suke juyi ya lashi lps dinshi ya qosa ya gansu a qasar saudi da ake wuni bacci, sesun sheqe ayarau, idan ma sukaje har phones dinshi kashewa zeyi a huta....

Washe gari Huddy har tasha taje ta karb'o saqon mugun abin da suka shirya itada uwarta, tazo tayi nasarar sanya masa a abinci yakuma ci sosai, har lokacin manga agidan take zama acewar sa kota koma gidanta tunda tafiya zatayi wahala ne kawai, ruwan maganin ma ta shige ktchn dama kuma tayi tsarki dasu ta boye a wani roba dan haka sirkawa kurun tayi ta soma juyawa,Manga datazo dakko masa ruwan na kallon ta da sauri kuwa taje ta kusa dashi ta zauna tana jiran qarasowar huddy har Abbas ya kula da rashin nutsuwar Manga din, se kallonta yakeyi suna nan zaune huddy ta shigo da cup a saman qaramin tray,yasani ba'a kawo masa ruwa haka dole se'a roba se mamakin ganin ruwa a cup yakeyi, bece komai ba ya miqa hannu ya karb'a, Manga na kallonshi harya kai cup bakinshi ya soma kurb'a ta rasa dalilin daya sanya ta kasa cewa karya sha.......


Mom Nu'aiym
*HASKE WRITER'S ASSO. (Home of expert and perfect writer's)*

*👑ALI ABBAS👑*

*Billy Galadanchi*

*Sadaukarwa gareki qawa tagari Fulany saddy*

      26

Ganin fa ze zuqa da kyau ya sanya da sauri tace

"Yaa Ali karka sha wannan ruwan karka had'iye plss zubar da wanda kasa a baki" besan mesa ya miqe ya fesar da wanda ke bakinshi ba yakuma wurgar da kofin dake hannun shi ya tarwatse ya wurin ya mayarda dubanshi gareta

"Meya faru da ruwan Allah ya soni ban shaba"

"Banaso yaa Ali na gaya maka abinda ke faruwa kazo ka tashi hankalinka abanza tu da Allah yasa bakasha ba aishi kenan" kallon ta yayi

"Manga banasan raini sanar dani meke faruwa" kallon ta ta mayar zuwaga huddy taketa faman zare ido tana had'a gummi tace

"Aunty huddy kin yadda ingaya mai?" zaro ido tayi

"Mezak8 gaya masa kuma? Aibeje canba tunda besha ba,kinga malama kiyi iya abinda ke gabanki kinj8 ni ba" dariya tayi sosai sannan tace

"Bazan tsura ido ina kallo mijina ya cutu ba sam, bazan lamunci a cutarmun dashi ba,kaga yaa Ali kasan mena gani?" kan yace wani abu da sauri huddy ta rufe bakin Manga jikinta se rawa yakeyi

"Me kike shirin yi ne wai Manga? Bakida hankali ne ki bari zamuyi magana tsakanin mu amma ba a nan ba" gyaran tsayuwarshi yayi ya kasa gane inda suka dosa ga uban gumi da take narkawa naba gaira ba dal8li duk da zafin sokoto ya sani sarai wlhy wannan sanyin na AC be isa kasa baiwa bawa ni'ima ba,cikin nutsuwa yace

"Huddy ki shiga hankalinki kina jina ai,Manga ke kuma sanar dani yanzu yanzun nan menene?? Meya faru da ruwan"

Koda Manga ta kalli huddy harta soma kuka ta sani wlhy aurenta ya qare daga ranar abin ma tsoro yake bata yanda ya faru so fast

"Kaga yaa Ali bari kaji bafa wani abin bane dama dazan shiga kitchen ne" rufe bakinta huddyn ta kumayi da hannunta tana girgiza mata kai alamar ta rufa asirinta,wannan karon manga ta harzuqa bige mata hannu tayi da qarfi..

"Bansan irin hakannan wlhy, idan ke baki san darajar mijinki ba nina sani, idan kuma ke bakisan lafiyarshi itace gatanmu ba toni na sani, gwara na gayamai me kikai masa sabida gove idan kin kawo mai ruwa a kofi ya dena sha,kinata wannan rawar jikin sekace wacce ke shirin yin kisa, kokinji nace kinyi wani laifi ne? Ki nutsu kinji ba yauwa" kallon Ali Abbas tayi

"D'azu ina zuwa kithen na

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login