Showing 45001 words to 48000 words out of 72189 words

Chapter 16 - Jinah Complete Hausa Novel By Malik Ashtar.txt

17 Mar 2026

50

tunani kafin tace:

-Kuma fa kanada gaskiya.

-Ya kamata muyi masa magana.

-hakan za'a yi.

Neman mahaifin nasu suka shiga amma basu ganshi ba, yanke shawara su jirashi suka yi. Kafin nan suka wuce wajen mahaifiyarsu.

-Nan da ba da jimawa ba zaki warke mama.
Cewar Aya.

-Nayi kewar fadanki.
Cewar Ayu.

-Karya ne, Mama bata yi mana fada.

-Eh gaskiya ne, Tanti Sarah ce ke yi mana fada.

-Amma ita mama idan muka yi laifi, kawai zata ce : a'a rabin raina, ba kyau abinda kuke yi, ku daina kunji kuma kar ku kara sakewa.

-Sannan sai ta kara da ina sonku sosai, kyawawan diyana.

-Kuma abinda zamu yi matsayin hukunci, shine mu rungumeta.

-Kuma ba zamu saketa ba har sai taso hakan.

-Muna sonki mamamu !

Duk da halin da jinah take ciki, sai da ta jawosu jikinta ta kankamesu, sosai kalamansu suka tabata ta yadda hawaye suka kasa tsaya mata. Zuwa cen kuma ta fashe da kuka, sedai kukan nata kuma da nashi dalili, ba komai ba ta tuna face yanzu idan ta mutu a wanne hali zata bar 'ya'yanta, duk da ta tuna hakan hankalinta na matukar tashi ganin irin shakuwar dake tsakaninsu.

Jinah bata daina kuka ba har lokacin da Dauda ya shigo dakin. Tagwayen fita suka yi suka barta daga ita sai mijinta.

-Ni fa wannan koke koken naki sun fara isata!
Cewar Dauda a fusace, idanu Jinah ta fiddo cike da mamaki.

-Gaskiya na fara gajiya.

-Me.. Me yake damunka? Tsawa fa kake min?

Jinah ta fada tare da kara fashewa da kuka, ko sau daya mijinta bai taba yi mata haka ba.

-Kiyi hakuri, ki yafe min, ba a son raina ba, ki yafe min dan Allah. Kinsan ina sonki fiye da komai.

Mamaki ya kara dabaibaye Jinah ganin yanda ya koma yana bata hakuri. Zuwa cen Dauda kamar an bangajeshi yayi baya ya bugu da bango, yanayin fuskarshi ya fara canjawa, da ta nuna suffar mugun mutum sai kuma ta sauya zuwa ta nutsatsen mutum. Jinah bata ankara ba taji Dauda ya shaketa kamar zai kasheta, kokowar kwatar numfashi ta shiga yi, zuwa cen kuma ya saketa sannan ya rugumeta yana kissing dinta. Sosai Jinah ta tsorata da lamarin Dauda. Mikewa Dauda yayi, sannan ya fara buga kanshi jikin bango yana fadin :

-Ka mutu ! Eh amma kuma gangar jikina ce ! Ni kuma ruhina ne ! Ba zan barka ka cutar da ita ba ! Ni ban damu da ita ba !...

Juyawa Dauda yayi wajen Jinah sannan ya shiga juya kanshi hagu da dama, kuma duk lokacin da yayi hakan sai kamannin fuskarsa sun canja daga ta salihi zuwa ta mugu. Daga karshe dai ta muguntar ce tayi nasarar tsayawa, cike da mugunta ya dunfari Jinah kafin ya nausa mata wani naushin da yayi sanadin sumanta.

A wancen ranar Aljana Hindu da mataimakinta makabarta suka je, sunje da niyyar kawo karshen rayuwar wannan aljanin ne domin taso da Dauda. Tayi anfani da ruhin aljanin a gangar jikin Dauda. Hakan yasa aljanin ya koma mutum ba tare da ya manta da tunaninsa na aljanu ba. Hindu tasan idan ta aika aljanin directly, tagwayen zasu iya halakashi. Amma yanzu wannan hadin da tayi shine kadai hanyar da zata iya samun cikar burinta ba tare da wata matsala ba, sedai kuma wata barazana da zasu fuskanta a yanzu shine, tsananin soyayyar da Dauda yake wa Jinah, da kuma zaman gangar jikinsa a kusa da ita, yasa kwalwar asalin Dauda ta fara aiki, a hankali a hankali yana dawowa Dauda. Gangar jikin ta fara kokowa da ruhin, da ganin ta hanashi yin duk wani abu da bai dace ba.

A yanzu haka dai Aljanin ne ya dauki control din jikin ta yanda har ya sumar da Jinah, yanke shawarar zuwa ya samu uwar gijiyarsa yayi sai kuma ya tuna da yanda Hindu take ba zata yi jinkirin kasheshi ba domin bata son duk wani abu da zaya kawo mata cikas a cikar burinta.

Bayan wasu lokuta Jinah ta farfado taga Dauda kwance a gefenta yana ta sharar bacci, a tunaninta mafarki tayi, ajiyar tayi tare da cewa : wannan wane irin mummunan mafarki ne nayi.

(.....)

Sarah ce ta shigo gidan a kasalance, Nafisa da gudunta tazo ta taimaka mata ta zauna kan tabarmar dake shinfide a tsakar gidan, dan kishigidawa Sarah tayi.

-A ina kika je aunty Sarah ina nan duk na damu ?

Nafisa ta fada cike da nuna kulawa. Tsantsar nuna kulawar da Sarah ke yi masu yasa a kullum take kara sonta, kuma tana damuwa idan ta ganta cikin wani hali.

-Ganin likitoci sun kasa yin komai game da rashin lafiyar Jinah, shine na tafi neman mai maganin gargajiya.

Sarah ta fada da muryar damuwa.

-Kuma shine zaki tafi cikin wannan ranar, kema bakya tsoron wata rashin lafiyar ta kamaki ?

Abdul ne ya karaso wajensu, ba tare da ya yarda ya hada ido da matar babanshi ba. Duk da abinda ke faruwa tsakaninshi da ita ba zai so ganinta cikin wani hali ba. Yar uwar tashi ce tayi masa bayanin inda Sarah taje, shiga yayi cikin kayansa ya dauko magani doliprane, da taimakon Nafisa Sarah tasha maganin, kafin wani dan lokaci taje tayi wanka, sannan Nafisa ta danyi mata massage kafin ta kyaleta tayi bacci.

Haka gidan ya kasance tsit, kowa yayi bacci banda yan tagwaye dake jiran dawowar babansu. Bayan tsawon wasu awanni sai gashi ya dawo.

-Ina ka tafi baba ?

-Ina tunanin ai zaku iya sani.

-Ai ka hanamu anfani da tsafinmu ga mutanen dake cikin gidan nan, idan ba ya zama dole ba.

-Hakane.

Yau tsawon watanni kenan Fally yake son ko ta yaya yaga ya dawo da matarshi, yanzu kuma da ya samu hanyar ance masa duk cikin aikin ne matar take fama da wannan ciwon.

-Idan mama ta cigaba da rashin lafiya, ba zan taba yafe maka ba.

Ayu ke fadawa mahaifinsu da alamar kashedi, kafin ya bar wajen yar uwar ta rufa masa baya.

Shi Fally a tunaninsa ciwon nata na wani dan lokaci ne daga nan komai zai koma masu daidai. Abinda Dauda yace masa yayi shine : Sake yin wani alkwarin aure tsakaninsa da Jinah kamar a baya «Wata yar karamar wuka Fally ya dauko tareda yanka babban yatsanshi, itama haka Jinah tayi, sannnan suka hada yankakkakun yatsun nasu gu daya inda jinin nasu ya garwaya. Bayan sunyi hakan sannan Fally ya dauko wata kwarya mai dauke da wasu koren ruwa, ya fara sha sannan ya ba Jinah itama tasha.

Jinah cire zanin dake daure kugunta tayi, sannan ta kara cire wanda yake daure a kirjinta. Kwantawa tayi akan wani jan kyalle dake shinfide a gurin babu komai a jikinta. Shima Fally dama wani gajeren wando kadai a jikinshi ya fiddashi, sannan ya zuba wasu ruwa a jikin Jinah, bayan wani dan lokaci sai ga wani maciji ya bayanna a hannunshi, sakin wannan maciji yayi yanata bin jikin Jinah, ita kuwa ko a jikinta, dan ta san wannan yana daga cikin siddabarun alkawarin nasu, kuma daman ta iya sarrafa dabbobi kamar sauran aljanu, kuma kasancewar kyawun dake gareta irin na aljanu yasa tana iya yin wasu abubuwa sosai wanda cikakken dan mutum ba zai iya ba.

Macijin ya bace bayan wasu yan lokuta. Bayan wannan, cikin farin ciki Fally suka raya wannan rana kamar kowanne ango da amarya. Hakan zai nuna sun dau alkawarin zama na har abada a tare.»

Wannan shine abinda ya faru ranar aurensu, ranar alkawarinsu. Sai dai yanzu da yake son ya sake yin haka a cikin mafarkin Jinah, komai sai ya jagule, domin ita Jinah, ta kasa fahimtar komai, ta tsorata da ganin wannan mutumin yana tursasata shan wani abu da bata san ko meye ba, da kuma yanda taga maciji na tafiya a jikinta, kuma ta firgita sosai na ganin mutumin nan ta karfi yana yi mata fyade. Komai da ya kamata suyi cikin soyayya ita gani take ta karfi ne yake mata. Shi kuma ganin yake komai zai daidaita daga baya zasu zamo a tare kuma hakan shine muradinsa. Sam ya kasa bude ido ya farka ya kwaci kansa daga tarkon aka yi masa, ya gane wannan ba soyayya bace yake nunawa Jinah, kawai yana cutar da ita ne. Dadi da kari ma, kusan kullum sai ya bayyana akan idanunta sannan kuma ya bace, hakan ma bai san dab yake da haukatata ba.

A zahirance Fally bai san hakikanin abinda yake kokarin yi ba, bai san yana sanya rayuwarsa, ta Jinah da kuma ta 'ya'yansa a hadari bane.

Yayi nisan da ba zai iya gane abinda Dauda ya fada masa zai kaishi ga rasa duk wani farin

ciki nasa, kuma a hakan zai cigaba ba tare da yasan wadda yafi tsana a duniya wato Aljana Hindu yake taimakawa da kokarin cika mata burinta ba.

----------------------------------------------

Domin sanin abinda zai biyo baya kan abinda Fally yayi. Mu hade a Chapter na gaba.

Fatan wannan chapter ta kayatar daku ? Zan yi farin cikin ganin ra'ayinku.

Sannan ina bada hakuri akan kuskuren typing.

*©El_Ashtar*

Allez à la prochaine Readers 💪

💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️

On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5

You'd like this New ❤️ Story

CHAPTER 19

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

A wurin mutane soyayya ba wani dogon nutsatsen kogi bane a'a, a wurin mutane soyayya dogon kogi ne mai cike da igiyoyin ruwa masu saka kogin yayi sama yayi kasa. Haka a wurin aljanu, banbancin ba mai yawa bane, sai dai akwai muhimmanci mai tsauri a soyayyarsu, suna tsananin yarda akan wanda suke so, ta yanda zasu iya sadaukar da komai akan wanda suke so, nuna kulawa da muntuntawa da gujewa duk wani abu da zai cutar dashi, wannan kenan a cikin soyayyar aljanu. Amma kuma idan aka samu akasin haka daya daga cikin masoyan wani ya cutar da dayan, alakar dake tsakaninsu zata wargaje kuma dukansu biyun da wanda aka cutar da wanda ya cutar kowanne zai biya bisa laifin dan uwan nasa. Hukuncin kuwa ba komai bane face mutuwa.

Abinda Fally yayi kenan, bayan yayi magana da 'ya'yanshi, ya gano rashin lafiyar Jinah shine sila amma sai yace ai abu ne mai kyau domin dan ya gyara gobenshi ne. Bai san abinda yake aikatawa ba, a hankali yana wargaza muhimmiyar alakar dake tsakaninshi da Jinah ne kuma idan har ya cigaba dukansu zasu rasa rayukansu.

Hindu tana sane da hakan, kuma wannan shine plan dinta, da kanta ta tsara komai daki-daki, kuma abinda zaifi kayatar da ita shine yayin da Fally da Jinah suka mutu haka zai sa yan tagwaye suyi rauni, ta yanda ba zasu iya anfani da karfinsu ba. Daga nan zata sa a kamosu ta barka kirjinsu ta ciro zuciyoyinsu ta cinyesu danyu. Daga wannan lokaci babu wanda zai iya kwatanta karfinsa da nata, karfinta zai karu, kuma zai mayar da ita gagara badau ki mutuwa (Immortelle).

(...........)

A gidansu Sarah, alfigir ya keto, duka mutanen gidan idanunsu biyu tun awowi 3 da suka shude, suna kan Jinah, sakamakon farkawa da tayi da kara, ciwo mai tsanani da kuma sambatu, wanda yayi sanadin taso Sarah, diyan mijinta da kuma yan tagwaye. Kowannensu cikin tashin hankali yake, basu san me zasu yi ba, su kaita likita? Sun riga da sun san abinda likitoci zasu ce. Sarah bayan tayi iya kokarinta na ganin ta rarrashi Jinah. Da gudunta taje ta jiko ganyen maganin da wani mai maganin gargajiya ya bata, lokacin da ta bata ta sha, Aya da dan uwanta ta dalilin karfinsu, suka saka uwar tasu bacci, su kuwa sauran sai suka dauka ganyen maganin ne yayi aiki.

Fita suka yi suka barta ita kadai domin ta samu hutu. Yan tagwaye wajen babansu suka je, suka ce ya dakatar da abinda yake. Ce masu yayi, zata warke ne kawai idan ta tuna dani, a yanda na kusa cimma burina, ba zai yiwu na dakatar ba. Abinda ya fadawa yaran kenan.

-Ka cika son kai baba.

Cewar Ayu, kafin yaja hannun yar uwarshi su bar wurin. Shiga dakin mahaifiyar tasu suka yi, suka tarar har yanzu tana bacci. A bangare daya kuma na dakin, Dauda ne zaune a kasa hannuwansa dafe da kanshi. Matsawa suka yi kusa dashi, anan suka ji yana ta wasu sambatu. Aje hankalinsu suka yi domin fahimtar abinda yake fada. Anan suka ji yana fadar :

-Ba zan iya cutar da ita ba! Me yasa nake yin haka? Amma kuma ba ni bane! Zan yi fada domin ta! Ta dalilina ne ka dawo, zan fadawa shugaba, zata batar da kai har abada! Daga nan kuma wannan karamin ahalin naka zai biyo baya. Ba zan barka ka aikata hakan ba! Ba zan barka ka cutar da...

Maimata kalamansa na karshe yayi ta yi kafin ya fadi sumamme. Kallon juna yan tagwayen suka yi, ba tare da dayansu yace kala ba. Ayu ne ya saka hannunsa cikin rigar Dauda tareda dora hannun daidai kan zuciyar Dauda, shuru yayi na dan lokaci bayan ya janye hannunsa kafin yace :

-Bansan ko menene shi ba.

-Kamar yaya?

Yar uwar tashi ta tambayeshi da mamaki.

-Ban sani ba ko shi mutum ne ko aljani.

-Me kake fada ne? Mutum ne mana!

-Eh, da gani mutum ne, amma jin bugun zuciyarshi zai tabbatar maki da ta mutum ce kuma ta aljani ce.

Kasa yarda yar uwar tashi tayi, sai da itama tayi da kanta ta tabbatar.
Dukansu cikin rudu suka fada. Kokarin tayar da Dauda suka yi domin yayi masu bayanin meke faruwa dashi amma kuma yaki tashi. Kalaman Dauda ne ke ta lugude a kwakwalan yan tagwaye, kafin dukansu tunaninsu ya basu aljani ne ya shiga jikinshi. Daukar Dauda suka yi suka bace daga dakin nasu. Anan suka shiga bin duk wata hanyar da Dauda zai farfado, sai dai basu suka samu nasara ba sai da sanyin safiya. Kokarin karantar tunaninsa suka yi amma hakan ya faskara, wannan ya tabbatar masu shi ba aljani bane kuma shi ba mutum bane.

-A zahirance kai waye?

Ayu ne ya fara magana.

-Ruhina aljani ne, gangar jikina mutum.

-Ta yaya haka zai yiwu?

Cewar Aya.

-Ta karfin tsafin shugabata Hindu.

-Wacece Hindu kuma meye dalilinta?

-Hatsabibiya ce ita, Aljana mai karfin tsafi marar misaltuwa, kuma tana son kara zama gagarabadau ta hanyar samun naku karfin.

-Me? Ta yaya?

-Ta riga da ta fara, kuma sai ta karasa.

-Tanada alaka da ciwon mahaifiyarmu?

-Eh.

-Kuma da abinda babanmu ke yi?

-Eh. Zai yi sau 10 ne, a dare goma, daren jiya shine na dare na karshe.

Zuciyoyin yaran ne suka buga duum.

-Me zai faru bayan hakan?

-Iyayenku zasu fada doguwar sumar da zata dauke su tsawon wasu kwankaki kafin su mutu. Kuma da hakan ta kasance zata juyo kanku. Zaku fara yin rauni, ku kasa amfani da karfinku, daga nan zata kamaku ta ciro zuciyoyinku ta cinye.

Da gudu Aya ta nufi wajen iyayenta domin tabbatar da abinda Dauda yake fada, sai dai kuma da zuwanta ta tarar dasu sumammu, wurin mahaifiyarta ta durkusa ta fashe da wani azabataccen kuka wanda yayi sanadin jawo hankalin Nafisa, Abdul da Sarah. Ganin Jinah taki farkawa kuma bugun zuciyarta kadan kadan yake yi, yasa suka nufi asibiti da ita duk sun san ba lallai bane likitoci su iya yin wani abu.

Shi kuwa Ayu tsayawa yayi wurin Dauda domin sanin yadda zai iya wargaza plan din Hindu.

-Amma ta yaya zamu dakatar da ita?

-Ba zaku iya ba, amma akwai hanyoyi biyu da zaka iya daidaita wannan matsalar.

-Wanne hanyoyi ne?

-Zaku iya cire zuciyar Hindu kafin ku rasa karfinku, hakan zai sa kai da yar uwarka ku rayu, amma Iyayenku zasu mutu. Ko kuma hanya ta biyu, daya daga cikinku yaci ganyen Fula, itaciya ce dake kashe aljanu. Wannan itaciya guba ce da zata sa yayi rauni, daga nan sai yaje ya nemi Hindu, ganin halin da yake ciki zata dauka ko plan dinta ne yayi aiki, daga nan zata cinye zuciyar mai guba sai ta mutu shi ma mai zuciyar ya mutu.

Hakan zai sa Iyayenku su tsira, sannan mahaifiyarku zata tuna da babanku da duk wata rayuwa da tayi da aljanu.

Hawaye ne suka kwaranyo daga cikin Ayu kafin yace bana son mama ta mutu.

-Kuka kake yi Ayu?

Cewar yar uwarshi data bayyana kusa dashi. Jin bai bata amsa ba, ta cigaba :

-Ba zasu mutu ba, ba yanzu ba.

Goge hawayen fuskarsa yayi tare da rungume yar uwar tashi. Yaji dadin kalamanta sosai.

-Nayi miki alkawarin babu abinda zai faru.

---------------------------------------------------------

💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️

On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5

You'd like this New ❤️ Story

CHAPTER 20

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

Aya da Ayu sun shiga rudin tashin hankali na ganin halin da iyayensu ke ciki, babu wata hanya da ta rage masu ta ceton iyayen nasu. A tunanin Aya kenan, domin dan uwanta tuni ya yanke hukuncin abinda zai yi, ya yanke hukuncin tafiya ya sadaukar da rayuwarshi akan iyayenshi da yar uwarshi.

-Je ki ga mama, sannan ki tsaya kusa da ita.
Ayu yaba yar uwarshi umarni. Ya kara da cewa :
-Ni zan je wurin baba.
Sai dai karya yayi mata. Gyada kai yar uwar tashi tayi ba tare da bata lokaci ba tabi umarninsa. Shi kuwa sai ya dauki hanyar zuwa wurin Hindu tare da rakiyar Dauda. Kafin su karasa sai da suka biya ta cikin bakin tsibiri wanda mutane basu iya ganinsa, suka debo ganyen Fula, a take Ayu ya saka a baki ya tauna kafin ya hadiye. Bayan yayi hakan, suka dauki hanyar gidan Hindu.
Suna zuwa kusan gidan, Ayu yayi kamar ya galabaita. Koda Hindu ta tsinkayesu tayi wata kururuwar jin dadi. Ayu sai ganin yayi ta dira gabanshi. Kyakyawa ce sosai, ba za'a kwatanta gashinta da na mahaifiyarshi ba wajen kyau. Hakoranta har wata walkiya suke tsabar haske da kyau, batada siffar miyagun aljanu. Katse masa tunani tayi ta hanyar tambayar Dauda.
-Amma abin yayi sauri kuma ina yar uwar tashi?
Bata samu amsar tambayarta ba, sai dai wata mahaukaciyar dariya da Dauda yayi. Hindu da Ayu cike da mamaki suke kallonsa.
-Kayi tunanin na kawoka nan ne domin ka kashe shugabata? To ba komai nayi ba face saukaka mata shirinta.

Ayu ya fahimci

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login