Showing 24001 words to 27000 words out of 72189 words

Chapter 9 - Jinah Complete Hausa Novel By Malik Ashtar.txt

17 Mar 2026

37

da har ta fara bacci. Ta manta bata yiwa mijinta maganar Jinah ba. Sai dai akan wa zata gabatar da ita? Bata yi wannan tunanin ba ga kuma wadannan tagwayen. Zaune tayi tana tunani kafin Jinah ta bude ido.

-Lafiya dai? Me ya faru?

-Daya daga cikin kishiyoyina ce ta rasu, uwar gidan Kimba dake a Nigeria.

-Ayyah, Allah ya jikanta, ya kyautata makwancinta! Bata lafiya ne?

-Ban sani ba, amma rasuwarta ta taba Kimba sosai, dan nayi mamakin canjawarsa, wata kila dalilin rasuwarta ne, amma dai yau naga asalin Kimba da na sani kuma naso a baya.

-Masha Allah, Allah ya kara dorashi bisa hanya.

-Ameen, yazo tare da 'ya'yan marigayiyar, yace anan zasu zauna.

-To ya kike gani?

-Kema kin sani dole na karbesu hannu biyu sannan na kula dasu. Zan je in gansu, ko zaki rakani?

-Eh, me zai hana?

Fita suka yi daga dakin, suka bar tagwayen kwance suna bacci. Suna shiga dakin suka tarar da matasan zaune, macen ba zata wuce shekaru 15 ba, sai namijin saurayi ne da ba zai wuce 20 ba.

-Sannunku, kun wuni lafiya?

Sarah ta gaishesu, sai dai basu amsa ba, ko kallon tsiya bata samu ba. Kallon Jinah Sarah tayi da ta daga mata kafadu. Kara maimata gaisuwar tayi amma shuru basu amsa ba. Tashi suka yi, suka fita da tunanin wata kila har yanzu firgicin mutuwar mahaifiyarsu ne bai gama sakinsu ba. Bayan Sarah tayi wanka, itama Jinah ta shiga tayi. Kwantawa Jinah tayi gefen jariranta, ita kuma Sarah sai da ta tabbatar da diyan mijin nata sun samu wurin kwanciya sannan ta wuce dakin mijin nata.

Tarar da mijin nata tayi a kwance bisa gado, tunani tayi ko har yayi bacci. Kwantawa itama tayi gefenshi.
Cen cikin bacci taji hannunshi na shafa bayanta. Lebenta na kasa ta dan ciza, tana son ce masa a gajiye take, sai dai ba zata iya ba, ga halin da mijin nata ma yake ciki, kuma wannan shine karon farko da dadewa rabon da yazo mata cikin kwanciyar hankali. Juyawa tayi suna kallon juna, idanunta cike da sha'awa. Bata tsaya dogon tunani ba, ta biye mashi zuwa wata duniyar.

Washe gari, Sarah ta riga kowa tashi, gyara gidan tayi. Bayan ta idar ta nufi dakin da Jinah ta kwana domin tasheta tayi sallah. Kusan suman tsoro tayi, lokacin da ta tarar da yan tagwayen zaune suna kallon juna kamar wadanda ke tsaka da hira alhali ita uwar tasu bacci take ta yi abunta. Ido Sarah ta zuba masu, suma kuwa suka zubo mata nasu.

-Idan da ban sanku ba, to zan iya rantsewa aljanu ne ku!

Sarah ta fada tana kallon yaran dake ta yi mata murmushi.

-Gaskiya kuna da abin tsoro.

Ta fada kafin hankalinta ya koma kan Jinah da ta farka. Bayan ta fito daga dakin Jinah, ta nufi dakin yaran mijinta, tayi mamakin tarar da su suna sallah domin tuni suka tashi.
Fita tayi ta nufi tsakar gida inda ta ajiye gumba domin dama kokon karin kumallo.

(...)

Sarah na tsakar gida tana raba kokon da ta dama, sallama taji ana yi a bakin kofar gidansu. Amsa sallamar tayi tare da duba mai sallamar, da mamakinta taga Dauda, wani farin ciki ne ya lullubeta ganin Dauda a tsaye kan kafafunsa ya warke sumul. Tashi tayi da niyyar yi masa iso sai ga mijinta Kimba ya fito sanye da lafiyayyun kaya da jaka a hannu. Zuciyarta ce ta buga, ganin alamar tafiya zai yi.

-Kimba, ina kuma zaka je haka?

Ta fada da alamun tambaya a fuskarta.

-Ina ruwanki da inda zan je! Yaushe kika fara samun dokar sanin inda zan je?

Shuru tayi, domin ta tsorata da lamarin Kimba, mutum jiya take lafiya lau dashi, har ta fara tunanin zasu fara sabuwar rayuwa ganin kamar ya shiryu, ashe ba haka. Hawaye ne suka kwaranyo mata.

-Ina zaka je Baba?

Cewar 'Yarshi.

-Ba fa zaka tafi ka barmu a wannan gidan ba!

Cewar danshi.

-Ban son shirme, ba jimawa zan yi ba zan dawo. Kuma kar ku kuskura ku bar gidan nan. Kai kuma Samaila ka sake yi min magana haka, kaga yanda zan fasa maka baki, marar kunya kawai... Sai a yanzu ya lura da bakuwar fuska a wurin, yace: Kai kuma waye? Me kake nema anan?

-Sunana Dauda, kuma nazo wajenta ne, wato matata!

Dauda ya fada yana nuna Jinah da ta fito daga daki. Inda hannun Dauda ya nuna Kimba yabi da kallo, kwalalo ido yayi cike da tsoro, baki hangame kamar wanda yaga fatalwa. Duk wannan kallon ba kowa yake yiwa ba face Jinah. Sakin jakar dake hannunsa yayi, ya nufo inda take.

-Am..amma..ta..ta yaya.. kika dawo kyakyawa haka, ku..kuma kika mike tsaye kan kafafuwanki?.. Ya..yaya aka yi kika samu kafafuwa?..A'a ba haka kike ba, rarrafe kike yi a lokacin da nayi maki fyade.

"Nayi maki fyade" ita ce kalmar da kowannensu ya iya rikewa. Kimba jinsa yayi zube kasa sakamakon wani lafiyayyen naushi da Dauda ya aika masa a fuska. Sarah, kasa motsawa tayi, ita kuma Jinah ba ma zaka gane yanayin da take ciki ba...

(.....)

Kwance yake yana kallon sama, ya lula duniyar tunanin abubuwan da suka faru, yarintarsa, iyayensa, Mahaifiyarshi, Jinah... Tunaninsa tsayawa yayi ranar da zai rabu da Jinah, kuma a ranar ne aurensa da Jinah, murmushi yayi, murmushi mai ciwo. Zai iya cewa wannan ranar ita ce rana mafi dadi da ciwo a rayuwarsa, saboda bayan an rabashi da matarsa abar kaunarsa, mahaifinsa ya umurceshi da yaje ya dakatar da alkawarin da suka yi da Jinah, amma yaki yin hakan. Irin wannan umarnin sarkin aljannu ma yayi masa amma yaki yin hakan, wanda hakan yasa dole ya biya kin bin umarnin da yayi. Auren mutum babban kuskure ne a kabilarsu, mahaifinsa yace masa yaje ya dakatar da alkawarin shi kuma zai yi kokarin ganin ba'a turashi kurkuku ba. Fally shi bai shirya yin hakan ba, dan shi a ganinsa ba wani abu bane dan aljani ya auri mutum, sai dai bai san akwai kalubale da dama a cikin auren ba...

Fally yana ganin idan har ya karya alkwarinsu to dole Jinah zata auri wani, shi kuma abinda bai so kenan, yafi son Jinah tayi ta kasancewa tashi shi kadai. Kuma ma idan yayi hakan kamar yaci amanar Jinah ne, kuma ya karya alkwarin da suka dauka a tsakaninsu. Bayan awa 24 sun wuce wanda ya kamata ace cikinsu zai dakatar da alkawarin, Kaddararsa ta sauya, ya rasa duk wata kima irin ta aljanu.

Sarki ya aiko a kama Fally, a duniyarsu idan aljani yayi laifi ana zuwa kamunsa ne da wata azababbiyar sarkar wuta mai dauke da kananun kwari masu cin nama, idan wannan sarkar ta taba jikin aljani, shiga take har cikin naman jikinsa, ta sakar masa kwarin sun dinga cin naman jikinsa. Lokacin farko da ta taba jikin Fally, hannuwansa a daure suke ta yanda ba zai iya anfani da siddabarunsu na aljanu ba, Babu abinda ya iya yi face ihu. Bai taba jin matsanancin zafi a rayuwarsa irin na lokacin ba. A karo na biyu da za'a lafta masa ita, runtse ido yayi yana shirin jin saukarta. A maimakon yaji saukar bulalar, sai yaji an rungumoshi ta baya. Yana bude idonsa yaga bulalar ta sauka a bayan mahaifiyarsa da ta dantse hakori tare da runtse ido tsabar zafi. Ganin abinda mahaifiyarsa tayi yace:

-Me yasa kika yi haka mama? Me yasa kika zo nan? Me yasa kika bari bulalar ta tabaki?

-Kiyi hakuri ranki ya dade bamu ganki bane... kiyi hakuri.

Cewar Aljanun da suke bugun Fally cike da firgicin ganin bulalar ta sauka a bayan AYA mahaifiyar Fally. Domin babu aljanin da bai san da kwanan mahaifiyar Fally ba.

A wahalce mahaifiyar Fally tace:

-Idan har bakwa son ganin fushina, to ku gaggauta daina dukan dana, idan ba haka kuma kun san abinda zai biyo baya.

-Mun daina ranki shi dade, yanzu zamu maidashi cikin kurkuku.

-Karka damu Dana, zan fitar da kai daga wannan gun, nayi maka alkawari.

(...)

Girgiza kansa yayi domin dawowa hayyacinsa, a yanzu babu abinda ya rage masa face yin tunani domin kwanaki kadan suka rage masa. Kullum yana ji kamar ana cire wani bangare a jikinsa da wata wuta, da haka aljani ke fahimtar karshensa yazo. Juyawa yayi ya kalli inda abokin zamansa yake, tuni ya dade da mutuwa har wurin ya zama kamar sahara, babu komai da yayi saura a gawar sai kasusuwa. Shi ma lokacinsa kawai yake jira, duk da mahaifiyarsa tayi masa alkwari, amma ya riga da ya sare ba makawa sai ya mutu. Lokaci guda, idonsa suka fara yi masa nauyi, rufe idon yayi.

_Lokacina yayi Jinah._
_Ina matukar kaunarki Jinah._
_Na sani bayan mutuwata, zaki zama mai 'yancin kasancewa da wani, ni kuma idan haka ta kasance, zuciyata zata zama tamkar kwalbar da aka jefo daga kan bene mai hawan dari biyu._
_Nayi imani da soyayyarmu Jinah kuma zan cigaba da yin imani, tare da fatan kasancewa da ke a wata rayuwar._
_Ki cigaba da tunawa da ni, kamar yanda ba zan taba mantawa da ke ba, kema kar ki taba mantawa da ni, kar ki manta da ni Jinah!_

Fally ke fadar haka da tunanin maganarsa ce ta karshe. Domin ya gama sarewa cewa babu abinda zai hanashi mutuwa. Sai dai kamar almara, Fally yaji wani karsashi na kara bayyana a jikinsa, fatarsa na komawa daidai, wani karfi na kara shigarsa. Kasa yarda yayi, dan ya tabbatar, gwada bacewa yayi sai gashi ya bayyana a tsakiyar dokar jeji, Fally ya kubuta, Wani ihun farin ciki ya saki, ihun da yayi sanadin tsorata duk wata dabba dake cikin jejin.

*Libéré, délivré!*

A rayuwa, komai yanada dalili, a bayan kowanne al'amari akwai boyayyen sirri. Idan da Fally yasan me yayi sanadin fiddoshi to da zai gwammaci mutuwa.


--------------------------------

In cigaba ne? To na fara ganin likes da comments 😁

@El_Ashtar

💞 JINAH (Matar Aljani)💞
by Malik al-Ashtar ✒️

On wattpad 👉 https://my.w.tt/g6epSX3tJ5

You'd like this New ❤️ Story

CHAPTER 11

~*Wilaya Writers association of Nigeria*~
(Home of peace & hospitality).💦we are here to educate and entertain the heart of readers,we are the best among the rest💦

Visit to like our page:https://www.facebook.com/Al-wilaya-writers-association-of-Nigeria-113198586763490/?referrer=whatsappwhatsapp

Rayuwa akwai dadi, kasancewa a raye, shakar numfashi, kasancewa cikin koshin lafiya, abubuwa masu dadi da ban sha'awa a cikin rayuwa da kudi basu iya siya. Mai kudi a shirye yake ya sadaukar, a lokaci daya, duk wata dukiya da yasha wahalar tarawa shekara da shekaru, kawai dan ya kasance a raye. Haka ma talaka yana iya kokari ganin yayi fafutukar yakin kasancewa a raye. Wasu kuma duk dukiyarsu, adadin kwararrun likitocin duniya ba zasu iya kubutar dasu daga wata cuta da Allah ya dora masu ba, haka zaka ga kullum suna fadi tashin neman lafiya da tunanin idan sun kwanta bacci ba za'a wayi gari dasu ba. Sannan akwai wadanda a kullum cikin koshin lafiya suke kuma a kullum fatan dawwama a haka suke.
Duka wannan nau'i hudun na mutane mun kaddarantu ga mutuwa ne ko ba dade ko ba jima. Amma duk da haka muna fatan masu tsayin rayuwa, domin kamar yanda nace rayuwa wata aba ce mai ban sha'awa, kasancewa a raye wani iko ne na Allah kuma dole mu kasance masu yi masa godiya a kowanne hali. Iska daya ta numfashi da muke shaka ya fiye mana adadin dukiyar Karuna, mu kwanta da dare, mu wayi gari da safe wannan duk iko ne na Allah.
Sai dai Rayuwa takaitacciya ce, lokaci yana gudu ne tamkar haske. Kuma kowanne cikinmu yanada takaitaccen abin kirgen lokacinsa, dan haka muyi anfani da wannan takaitaccen lokaci namu, mu tunkari kaddarar dake gabanmu, mu kasance masu komawa ga Allah, dan mu kamar matafiya ne da muka yada zango a wannan duniyar.

A bangaren Fally a yanzu ya fahimci mecece rayuwa, domin halin da ya shiga da ganin mutuwa a kusa dashi. Yanzu kuma gashi ya kubuta, ya zama mai 'yanci sannan ya gujewa mutuwa a halin yanzu. "Nasan iyayena zasu yi farin cikin ganina idan naje gida." Ya fada a zuciyarsa cike da zumudin zuwa gida.

Sai dai da karasawarsa gida, yanayin kamshin gidan ya sauya, kamar akwai abinda ke faruwa, dan ba kamar yanda yake a baya ba. A kasalance ya karasa shiga gidan, mahaifinsa ya tarar zaune cikin yanayin bakin ciki. Ido suka hada, Fally yayi mamakin rashin ganin farin ciki ko mamakin ganinsa a fuskar mahaifinsa.

-Baba!

Cewar Fally.

-Kada ka kara kirana da wannan sunan! Kaga inda taurin kanka ya kaimu ko? Mahaifiyarka babu gwagwarmayar da bata yi ba ganin ta fiddoka, ganin cewa baka mutu ba. Gashi yanzu ta... A'a babu abinda ma zan iya fada maka dan bani da wannan karfin. Jeka! je ka kwanta kan gado.

Fally ya fahimci abinda mahaifinsa ke nufi, domin idan aljani ya mutu to yana barin wasiyyarsa ne kan gadon baccinsa. Kallon mahaifinsa yayi, bai ce dashi komai ba, ya nuna yatsa a take gadon marigayiyar ya bayyana a gabansu. Tafiya Fally yake kamar wanda kwai ya fashe ma, karasawa yayi kan gadon ya kwanta tare da rufe idonsa....

Dana, da farko, bana son ka dorawa kanka laifi akan abinda ya sameni, sam ba laifinka bane. Nayi kawai abinda ya dace ne. Naje naga Hindu... Nasan me zaka ce, kamar yanda mahaifinka yace min. "Bakida hankali ne, kinsan wannan matar shedaniya ce, kullum idan aljani yaje mata da neman taimako sai ta nemi wata sadaukarwa gareshi, ke kuma shine zaki je ki nemi taimakonta?" Itace aljanar da tafi kowanne aljani tsufa a wannan duniya tamu, ta rayu tsawon zamani da yawa, mace ce mai dogon sani da kuma karfin tsafi. Da yawan aljanu idan suka samu matsala suna zuwan wajenta ne neman taimako. Ban nemi taimakonta ba har sai da na tabbatar babu wata hanya ta kubutar da kai. Domin na kubutar da kai ka rayu, dole ni na kashe kaina, eh, na kawo karshen rayuwata. Lokaci mai tsawo kenan da take son taga mutuwata amma bata samu dama ba, ita da kuma da yawa daga cikin aljanu. Ba don komai ba, sai domin nice mai gadin Jinah kuma nice wadda uwarta ta bani amanarta kafin ta mutu. Shi yasa indai ina raye to basu taba cimma burinsu akan Jinah ba. Amma nayi imanin kai da mahaifinka zaku kare min 'yata Jinah, shi yasa na yanke ni na mutu dan kai ka rayu. Nasan mahaifinka zai yi fushi da kai, amma komai zai wuce.
Sannnan ina tayaka murna Dana, ka zama uba yanzu, Jinah ta haifi yan tagwaye kuma ta saka masu sunanmu, ni da mahaifinka. Yaran sun rayu, wannan wani ikon Allah ne dan hakan bai taba faruwa ba, idan irin haka ta faru yaran mutuwa suke. Wadannan yara suna tattare da wani karfin sihiri na aljanu, dan haka yanzu ba sai an jima ba rayuwar Jinah tana cikin hadari. Zasu bi kowacce irin hanya ganin sun mallaki waddan yara. Hindu ta dade da ganin wannan al'amari dake tattare da yaran shi yasa take son na mutu. Kar kayi bakin ciki dana, zan kasance kullum a cikin zuciyarka, ina yi maka ban kwana, ka kula min da 'yata Jinah da kuma jikokina. Mahaifiyarka mai kaunarka.

Wasu zafafan hawaye ne suka zubo ma Fally lokacin da ya gama jin wasiyyar mahaifiyarshi, hannuwa yasa ya dafe zuciyarsa sakamakon wani zugi da take masa. Mikewa yayi ya sauko daga kan gadon sannan ya nufi mahaifinsa tare da fadawa jikinsa yana kuka kamar wani karamin yaro. Yana ji da ba dan taurin kansa ba da har yanzu mahaifiyarsa na raye.

-Yanzu tunanin Jinah da ya'yanka zaka yi, ka daina kuka.

Take kuma wani farin ciki ya lullubeshi jin abinda mahaifinsa ya fada, yanzu kenan shi uba ne. Ana yawan basu labarin idan aljani da mace mutum, ko kuma aljana da namiji mutum suka samu haihu tare, yaron ba za'a taba haifarsa da rai ba. Amma gashi cikin ikon Allah nasu yaran sun rayu.

-Bamu da lokacin batawa, ya kamata muyi saurin tafiya kafin su farga da mutuwar mai gadin Jinah.

Cewar Ayu mahaifin Fally. Goge hawaye Fally yayi tare da daukar wata jaka ya saka wasu kaya da zai bukata, suka dauki hanya shi da mahaifinsa. Ba suyi tafiyar wasu kilomitoci ba, aka harbo wani mashi ya ratsa cinyar mahaifin Fally da tayi sanadiyar faduwarsa kasa.

-Baba!

Fally ya kwala kara tare da durkusawa kusan mahaifin nasa.

-Ka gudu! Suna nan!

Cewar mahaifin nasa da ya ankare da an biyosu.

-A'a baba a tare zamu je!

-Guba ce, ba zan iya anfani da tsafina ba.

Motsi Fally yaji, yana juyawa yaga mayakan aljanu sun kewayesu ta ko'ina.

-Ka ceci kanka dana!

Wasu kibiyoyin aljanun suka kara sakawo kafin Fally yayi saurin bacewa. Sai gashi ya bayyana a tsakiyar wani jeji, durkushewa yayi kasa tare da dafe kai, yana ji kamar yayi kuka, yayi kara ko kuma gurnani kamar zaki... Yanzu shi daya ya rage, shi daya, kuma dole ya kare matarsa da kuma 'ya'yansa...


(.....)


Jinah, Sarah, Dauda da kuma 'ya'yan Kimba ne zaune a tsakiyar gida, kowanne ya fada duniyar tunani. Duk wannan ta faru ne lokacin da Kimba ya furta shine ya yiwa Jinah fyade.

-Wannan ba fa zai taba yiyuwa ba, ba shi bane. Tagwayen da ba'a dade da haifa ba, lokacin da ya kamata a samu cikin yaran, Kimba yana Nigeria.

Sarah ce ke magana, kowannensu daga kai yayi yana kallonta, kamar tana maganar ne da niyyar kare Kimba, domin har yanzu kalaman mijin nata suna mata yawo a kwanya, sai dai ba yanda za'ayi ta gasgata hakan, abu ne marar yiyuwa ace Kimba ya yiwa Jinah fyade.

-Ba abu ne mai yiyuwa ba ace babana ne.

Cewar diyar Kimba. Jikin jinah yayi sanyi, ita kanta bata yarda shine ba, shi da ma baya cikin Nijar din, kuma bama tada hujjar cewar fyade aka mata.

-To me yasa zai ce shine idan ba shi bane?

Cewar Dauda.

-Gashi yayi tafiyarsa ba tare da ya bamu hujja ba.

Cewar dan Kimba.

-Bama shi bane, na tabbata.

Cewar Jinah.

-Kenan ke fyade aka yi maki?

Cewar diyar Kimba.

-Nima ban sani ba!

Jinah ta bata amsa.

-Mu manta da wannan yanzu, idan ya dawo, shi zai yi mana bayanin komai. Cewar Sarah tare da juyawa ga diyan mijin nata. Baku fada mana sunanku ba?

-Ni sunana Abdul.

Cewar namijin, ita macen kin magana tayi. Ya cigaba.

-Ita kuma Nafisa sunanta, amma muna ce mata Nafi zararra ko kuma kuce Nafi yar mahaukaciya.

Dariya dukansu suka yi, banda Nafi dake ta hararar yayan nata, shi kuma yayi kamar bai gani ba.

-Ina maku barka da zuwa gidan nan, kuma ina maku jajen rasuwar mahaifiyarku. Allah ya jikanta, yayi mata rahama.

-Ameen.

Fira suka cigaba da yi, kafin Jinah da Dauda su kebe zuwa daki. Da shigarsu daki

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login