Showing 12001 words to 15000 words out of 45490 words
saidai kamar takara dana zamani domin har wani jaja fatarta keyi balaifi tanada kyau, saidai batakai *Blue* ba domin shikam kyansa guri biyu yadauko da gurin Mom da gurin Dad itakam da alama mamanta tabiyo sab'ani *Blue,*
Shikam daka gansa kaga dad sak! harda tsawon da cikar zati, my *Bil* boy kana Ina tafad'a dai-dai lokacin data karasa shiga karamin falon
Abin mamaki *Blue* naganin ta yamike dasauri har yana zubar da dankalin gabansa, yanufi gurinta da ihun murnan ganin ta harda tsalle,
_Nikam nace toufa dama ance ko mahaukaci yasan nasa"_
Mutuwar tsaye Aunty Bebe tayi tana kallon sa yayinda *Blue* yarike hannun ta yana dariya, cikin rawar murya tace d...a...d haka my *Bil* boy yakoma?...kai ya gyad'a mata sai tasaki kuka tare da rungume shi tana fad'in Oh! my *Bil* boy me yasme ka haka?...
shima sai yasaki kuka harda buga kafa hakan yasa dad yace it's ok bebe, ahankali tayi shuru tana shafa kanshi shima shurun yayi cikin rawar murya tace Dad mutafi asibitin nan dai suka dunguma zuwa asibiti.
***""""***
Su *Beena* kam koda suka fita sun iske Ammu tagama had'a karin kumallo Wanda dumamen tuwon jiya ne sai kunu data dama masu,
Sannan tazuba masu akwano daya komar kodaya yaushe wato *Beena* itada *Bana* da *Banu*, sai *Bass* shi da *Bash* suma akwano daya domin tace masu cin abin tare da Dan uwa yana sa zumuci sosai, bayan tabasu nasu sai tadauki na Abbu taje kaimasa.
Bayan sun gama cin abinci sai *Bana* ta tattara kwanoni zata wanke ita kuma *Banu* takoma gurin Abbu don yasake fad'a mata karatu,
yayinda *Beena* tashiga wanka koda tafito har *Bana* tagama wanke-wanke, don haka sai itama tashiga wanka ko kafin tafito har *Beena* tashirya tana zaman jiranta, don haka da sauri itama tashirya suka fito,
Dai-dai lokacin da *Bass* da *Bash* suma suka fito ashirye, murmushi sukayiwa juna sannan suka shiga dakin Abbu don su sallame su inda suka iske *Banu* tagama karatun hartayi bacci kusada Abbu,
yayinda Ammu take matsama sa kafa nan sukace masu zasu tafi suka amsa masu dato tare dayi masu fatan nasara sannan suka fita, Ammu batabar dakin Abbu ba saida ta tabbatar yayi bacci sannan tamike tadauki *Banu* suka fito dakinta takaita takwantar,
Sannan itama takishin gid'a kad'an sai tafara tunani ahalin dasuke ciki wanda bata tab'a tunanin zasu shigesa ba arayuwa,
gashi yaya "Muda yaki yabata hakkinta haka kawai saboda tsabar mugunta ta yan'uba, ahankali tafurzar da iska me zafi tabakin ta, ranta ad'an bace tafurta inshallah Allah sai yad'orani akanka kabani hakkina,
Ahaka dai tayi ta tunani har sarkin barayin duniya ya dauke ta wato bacci.
*_Asibiti_*
******
Duk wani binciken da yadace ayiwa kwakwalwar *Blue* anyi amma wani abin mamaki babu abinda akagani, wanda zayanu na alamar yayi losing memory sane ko kuma yasamu tabin hankali ne,
Hakan ne yaba likitoci mamaki had'e da tsoro musamman Dad cike da tashin hankali, yace pls Dr Bamalli kusake bincikawa beyi musuba suka sake sakan *Blue* din acikin wani injindin bin ciken kwakwalwar mutu,
injindin sabo ne aka kawo masu kuma saida aka tabbatar da ingancin sa tukun aka kawo masu, amma abin mamaki results din da sauran injinan din suka bayar shima haka ya bayar, cike da tashin hankali dad yace no Dr Bamalli wannan ba gaskiya ba da alama injinan nan sun samu matsala,
idan kuma bahaka ba to kun kafara wasa da aikin ku amma tabbas kwakwalwar yarona tasamu matsala idan bahaka ba babu yanda za'ayi yadinga yin behavior like small kid, don haka kusace bincikawa don nasan maganin da zan d'ora sa akai, cike da bacin rai Dr Bamalli yace.....
Muje zuwa
_Alkalamin_
*_LUFHAT_*
๐๐๐๐
๐๐๐
๐๐
๐
๐ *_ZAUJUN-MAJNUN_*๐
_(miji mahaukaci)_
๐
๐๐
๐๐๐
๐๐๐๐
Page1๏ธโฃ5๏ธโฃto1๏ธโฃ6๏ธโฃ
WRITTEN
By
๐ *AMEENA UMAR FARUQ*๐
OR
๐ *MEENAT*๐
Marubuciyar
*_DA SANNU_*
*_ZUCIYATA CE_*
*_AFSANA_*
*_KYAUTAR ALLAH CE_*
and now๐๐ฝ
*_ZAUJUN-MAJNUN_*
SADAUKARWA GA
*_My lovely blood sisters ๐ฉโโคโ๐ฉHadiza (aunty)and Nana Firdausi out last bornnn, do u know what? sisters humm l really love love love yous irin babu adadin nan fa so muchhhhh love๐๐๐._*
Littafin nan na kudi ne duk me bukatar zaya iya turo katin MTN ko AIRTEL na 200 a wannan 08161850024, idan kuma tresfa zakuyi duk zaku iya tuntuban layin sai abaku account no ba nagode.
_____________________________
ยฎ _PEN : WRITERS ASSOCIATION_
_______________________________
~_only the exquisite and whizkid writers are opportune to be pen writers_~
https://www.facebook.com/groups/1061983803858837/
*_FREE PAGE_*
โ๐ผ
_*Bismilahirrahamaniraheem!*_
Haba dr L.U kamar ya injina sun samu matasala? kamar yanda kaji nafad'a, humm idan ko haka ne to kaine mutun nafarko dazaya tabbatar da hakan domin kuwa kana daya dagacin wayan da ke aiki da injina,
"au haka zakace?...eh to idan bance maka haka ba to me zance?....tunda agabanka ake komai ko ba haka ba, aibabu abinda bakasani akan aikin ba shine kake wani cewa mun fara wasa akan aikin mu wanda hakan yana nufin harda kai ke nan?..
"tunda aikin kenan guda dasauri yace a ah kudai domin nibana wasa da aikina jiya kwana nayi ina bincike, Wanda ya tabbatar mun dacewa tabbas boy yasamu matsala a akwakwalwar sa amma yanzu sai kununa mun wai kwakwalwar sa lafiya lau take wanna ai manakisa ne kawai za'ayi mun,
"Da sauri dr Bamalli yace a ah bamu muka nuna maka ba na'urori dai suka nuna maka, kuma kagani sannan mu babu wata manakisar da zamu samaka tunda duk abinda yasame ka yasame mu, d'anka ai d'an mu ne koba haka ba?....suka amsa da tabbas haka ne,
to kagani tabbas kwakwalwar *Bilal* kam tasamu matsala saidai bana tunani yashafi asibiti saidai k....da sauri dad ya katseshi dafad'in to idan baishafi asibiti ba me yashafa?... har dr Bamalli zayayi magana da sauri dr lb ya girgiza masa kai alamar ya kyale,
don haka dad yaci gabada cewa nidai nagane kawai bakusan taimaka mani ne dad'in abin banan bane kad'ai asibiti, so zan dauki yarona nakai shi inda kwararru likitoci suke su dubamun shi, dr Bamalli yace ashe kai dinma ba kwararre bane?....
Cike da jin haushi yace kune dai ba kwararru ba tunda kunkasa gano abinda yake damunsa, amma nikam tabbas na kware akan aikina tunda har nagano brain dinsa yasamu matsala, ok tunda kakware aida saika tsaya ka kagano abinda yake damun sa basai ka kawosa gurin wayan da ba kwararru ba,
Ai tun kafin kace na gano, kuma nafad'a maka idai so ne kawai nasake tabbatarwa ko bakaji abinda nafad'a ba ne?...eh naji to aiyanzu ka tabbatar don haka sai kaje kadora shi akan magungunan dasuka dace, yanzu kuwa yafad'i tare da kokarin daga *Blue* dayake zaune yanata faman wasa da filon gadon asibitin, dad kam sai fad'a yake kamar zaya ari baki sudai sauran likitocin sai kallon sa suke har suka fita daga d'akin.
Cike da mamaki dr bamalli yace ah! wai shi "Dr L.U wani irin murd'add'en mutun ne haka?...dr Ib yace humm! aikai dai bari halinsa sai shi yanada mugun ra'ayin rikau, saikace akansa akafara boko mtsw! wani dr yayi tare da cewa indai boko ne aimunga mangwafa kai! kaji mutun fa agaban safa akai komai, koba aikomai agabansa ba aishima dr ne yasan komai akan aikin,
humm! aikana wasa da "dr L.U yadauki boko da matukar mahimmanci arayuwar sa data iyalinsa, wani dr yace to aisai yamatsa kuma kunsan Allah tunda kukaga duk na'uronin nan basu nuna komai dangane da abinda yashafi brain dinsa ba, to tabbas ciwon sa bana asibiti ba ne,
Dr l.b yace inafa na asibiti nifa tun jiya nafahimci haka nigani nake kamar aljannu ne suka shafesa, idan kuma basu bane zato zunubi kilan anyi masa asiri ne tabbas cikin biyu za'asamu daya, idan ba haka ba babu yanda za'ayi yaro natsatse kamilalle cikin lokaci daya yakoma kamar *MAJNUN*,
wlh kaidai ni tausayi ma yake bani, ga Ubansa yaki yadda ya fahimci haka ah! to basai yaje yayi abinda zayayi ba gaskiya kam, Allah dai yasawake yakuma bashi lafiya duk suka amsa da ameen sannan suka fara firfitowa daga d'aki.
Dad kam yana fitowa su *Bulama* suka taresa da sauri Aunty Bebe takama hannun *Blue* tana cewa my *Bil* boy ya jikin?...be amsa mata ba saidai kwab'e fuska dayayi zayai kuka tare kokarin d'ora kansa akafad'ar ta,
yayinda papa da *Bulama* suka had'a baki gurin fad'ar me akace yasame sa?...cikin bacin rai yafad'a masu duk yanda sukai inda ya karashe dacewa kuji fa, maganar banza wai babu abinda yasamu kwakwalwar sa,
Da sauri *Bulama* yace in possible dad babu yanda za'ayi a ce wai babu abinda yashafi brain dinsa yake wannan behavior din kamar wani karamin yaro, aunty bebe tace gaskiya karyane basudai bincike sa dakyau bane....dad yace inafa suka bincika, kunga ku kyalesu" kawai mutafi gida muyi shirin tafiya,
Ke bebe muje ki koma gida ki kulada "mijinki da "yaranki kinji?...cikin sanyi murya tace pls dad mutafi tare, yace no baza aihaka ba Barr naji kace kanada important shari'a gobe ko?... kai papa yagyad'a wanda tunda yayi shuru bace komai ba azuciyar sa yanason yayi magana, akan lamarin nanfa bana asibiti ba ne amma yakasa koba haka bama yasan koya fad'a masa bazaya yarda ba,
Don haka bayada abinfad'a sai abinda dad yace, yayinda dad yaci gaba daya cewa yauwa kai kuma son muje kasama mana tickets guda uku na American Dani dakai da boy tunda already munada visa ko?...,yes dad yauwa idan munje anyi dace to shike nan idan kuma ba ayiba sai muwuce germany ko?..ok dad,
Sannan ya kalli papa tare da cewa koya kagani Barr?...,da sauri yace eh hakan yayi sannan suka shiga mota suka tafi gida,
Abu ga masu gidan rana wato raina inji malam ba haushe yace idan sunyi yawa sai inuwa,
Don haka cikin lokaci kankani komai ya kammala bayan dad yasanarwa da yan'uwansa komai, abin mamaki amma be sanarwa mon ba ko meyasa?.. haka nan jirginsu konace jirginmu yadaga zuwa
American domin nima dole naje dauko maku rahoto๐.
*_American_*
***""*****
Duk wani bincike daya kamata ayiwa kwakwalwar *Blue* din anyi mata amma babu abinda suka gano, sai allurai suke masa tare da bashi magungun wanda suke tunani Koda akwai wani matsala a brian din to maganin zasu iya bayyana wa saidai kuma babu abinda suka gano har tsawon sati uku, da kwana hudu don hakan ne yasa suka salleme shi yayinda suka kwasa zuwa Germany wani.
"A germany dinma dai bata canja zaniba results din kenan guda, kimani kusan sati uku ana bincike amma shuru gashi ciwon na *Blue* sai kara gaba yake abin gwanin tausayi, hauka tuburan baya be iyayin komai sai anyi masa tamkar yaro dan yaye,
Duk yarame yayi duhu hakan yasa dad sake shiga cikin tashin hankali fiye da tunani me karatu, hakama *Bulama* duk suma sun rame sunyi duhu tsabar tashi hankali, daga germany suka kwasa zuwa Spain acan dinma haka ne duk da na'urorin sai sunyi kamar zasu nuna wani abin sai kuma asamu akasin haka,
Nan ma dai sun kwashi tsawon sati uku da yan kwanaki ana binciken brian dinsa amma basuga komai ba, har papa da dad Lagos wato yayan dad suka kai masu ziyar inda papa yadaure yasake yin magana cewa ciwon nan fana *Blue* kamar shafar aljanu don haka bana asibiti bane, aikam dad yarufe ido yace shifa bayason yana danganta yaron sa da wasu aljanu don haka papa yayi shuru, tunda harda dad Lagos yagoyi bayan dad kwana uku sukayi suka dawo gida najeriya saboda duk kansu sunada shari'a me mahimmanci.
Yayinda suka bari ana sake binciken brian din *Blue* saida still basuga komai ba wanda hakan yaba likitocin mamaki don haka suka sallame su, mom ma ta ziyarce su tayi kuka sosai sakamakon yanda taga lilon d'anta yakoma, tace ma dad su dawo gida ayina gargajiya itama yatubure akan shibai san wannan zancen ba,
don haka suka rabu baran-baran haka tadawo gida najeriya zuciyar ta cike da kunci, saidai aranta tayi alkawarin yiwa d'anta addu'ar samun lafiya.
"Atakaice dai saida dad suka kwashi kusan wata biyu da wasu yan sittika suna ziyartar asibitoci kasa-kasa, kusan kasa biyar sukaje amma results din kenan daya don haka dad yace da *Bulama* sukoma gida yaje yafara aikin sa karsu taru aguri daya,
Kacan cewar dad da papa sun gina masu kamfani idan sun dawo zasu fara aiki to sai kuma ga laluran data samu *Blue* din, so haka akayi bayan sun dawo *Bulama* yafara gudanar da aiki akamfani su,
yayinda dad shima yacigaba da aikin sa bayan yasamar wa *Blue* masu kula dashi har mutun uku zaya dinga biyansu, tunda yakoma tamkar karamin yaro dan yaye irin masu shegen shagwab'a da saurin kuka baya iyayiwa kansa komai sai anyi masa harda abinci abaki ake bashi, wanka kad'a yakeyi dakan sa koshi facaka kawai yake da sabulu daruwa yafito,
"Wanda arana sai yayi wanka fiye da biyar domin har yanzu yana nan da mugun son tsafta bayason kazanta ko kad'an dotti yataba kayansa yadinga ihu kenan sai ancire masa ansa wasu, shiyasa kullun masu kula dashi cikin gyarasa suke Wanda inba kasan shi kagan shi saika rantse me hankali ne,
Allah sarki *Blue* gentleman duk yakoma wani iri gwanin tausayi๐ฅ.
*_Bayan wata uku_*
****"""*****
Sannun ahankali komai yake tafiya yanda Allah yatsara akuma lokscin da yaso,
Kamar su *Beenazeer* masuna nan suna rayuwa ayanda Allah yaso wato ba wuya ba dad'i, zance zuwa makaranta boko kam babu shi tunda basuda kudin biya don haka suka hakua saidai islamiya kam suna zuwa sosai,
Amma zance zuwa gurin kawu muda kuwa babushi domin duk yanda Ammun tayi yin kurin zuwan don karbo hakkinta, abbu yahana don haka ta hakura amman badan ranta yasoba saidai kawai don biyyyawa mijinta.
Misalin karfe 7:00am na ranan wata laraba wacce malam bahaushe kema kirari da laraba tabawa ranan samu, duk wanda yai samu acikin ta sai yakara, haka duk wanda yairashi aciki ta sai yakara to hakan ne takasance dasu *Beenazeer.*
Kamar koda yaushe bayan sun gama karatun su sund'an taya ammu aiki sai suka karya kumallo sannan suka shirya zuwa gurin aiki, har sun sallami iyayan su zasu tafi, sai Ammu takira *Beena* d'akin ta cikin sanyi murya tace idan kundawo baku iskeni ba natafi abuja....
Dasauri tad'ago kai ta kalli amman yayinda taji gabanta yayi mummunan fad'uwa, cikin tashin hankali tace Ammu yanzu abujan zaki koma gurin "kawu Muda?...kai ta gyad'a mata tare da cewa dole nakoma *Beenazeer* domin bazan iya cigaba da jure ganin mijina uban y'ay'ana cikin kun wannan halin ba,
Kuma gaskiya nagaji daganin ku zaune ba zuwa makaranta,
Cikin rawar murya *Beena* tace don Allah Ammu kiyi hakuri ki kyale "kawu muda tunda yaki baki, indai danmu ne mun hakura da karatun bokon tunda badashi zamu tafi lahira ba,
cikin rawar murya itama tace to naji idan harku kun hakura da karatun ku to shi Abbun ku haka zaya dauwama cikin ciwo?....kai ta gyad'a alamar a ah yayinda hawayen dasuka cika mata ido yazubo yasharrrrr!
tace to kingani don haka dole naje, cikin kuka tace Ammu kiyi hakuri karkije Allah fa yasan halinda muke ciki inshallah zaya yaye mana, cikin sanyi murya tace haka ne rokon danake kenan kullun saidai kisani nima dole zatasani zuwa amma nayi maki alkawari daga wannan zuwan idan har be baniba zan barsa da Allah, kedai kawai kiyimun addu'a keda yan'uwanki kinji ko?...
Cikin sanyi murya tace to ammu saikin dawo Allah yasa adace tace amin, to tashi kutafi don Allah ki kula da yan'uwanki sosai da Abbun ku kinji yar albarka murmushi tayi tare da cewa inshallah ammun mu sannan tafita.
Bayan ammun tashirya sai tashiga dakin abbu don ta sallame shi kasan cewar dama tariga taroke shi akan yabarta tasake zuwa gurin kawu muda, wanda dak'ar yabarta koshi saida tayi masa alkawari daga wannan zuwan idan har be bataba bazata sake zuwa, bayan ta sallame shi sannan tafito ta tafi,
Kamar koda yaushe Ammu ta'isa abuja lafiya saida agajiye ruwa kawai Safara'u ta bata, wannan lokacin ma bata iske kawu muda ba don haka saita tsaya jiranshi, can sai gashi yashigo yana ganinta yahad'e fuska kamar yaga mutuwar sa cikin sanyi murya tace inawuni yaya Mudassir?....
Cike da bacin rai yace bansani ba tace Allah yabaka hakuri, dama nasake zuwa karban hakkina ne... don Allah kayi hakuri kabani wlh muna cikin matsananci hali, zama yayi yad'ora kafa daya kan daya tare da fad'in kinyi kokari dakika sake dawowa so yau zakufita cikin halin dakuke, don haka bari nasa akawo maki hakkin naki yanxu,
Dasauri tad'aga kai ta kalle sa wani kila murmushi yasakar Mata sannan yasa hannun cikin aljinun rigarsa yaciro wayarsa, tare da danna lamba yakara akunne can yafara fad'in nomasi eh yauwa to Ina jiranku ok kuyi sauri ok sai kunzo sannan yakashe wayar,
Yana zubama ta wani mugun kallo sai karkad'a kafa yake hakan yasa Ammu jin fad'uwar gaba me