Showing 57001 words to 57616 words out of 57616 words
Chapter 20 - FAHIMAH Book 1 Complete pdf Writing by Takori kabara .txt
tsaga kirjinsa ya sanya ta. Ya yi kewarta yadda harshensa ba zai iya bayyanawa ba. Sai ya shiga nuna mata practically yadda ya yi kewan nata har abin ya bai wa Fahimah mamaki da tsoro. Tsoron nata bai je koâina ba ta ji Uwais ya sure ta bai aje ta koâina ba sai tsakiyar gadon dakinsa.
It was kind of gentle romance wanda ya motsa zuciya da ruhin Fahimah har sai da hawaye suka fito daga idanunta. Hawayen da ta tabbatar na farin ciki ne, farin cikin cikar buri, burin mallakar Uwais a rayuwarta, ta tabbata da ba ta samu Uwais ba rayuwarta ba za ta taba komawa cikakka, kuma mai dadi ba kamar yadda ta faro a baya.
A bangaren Uwais 100% satisfaction irin wanda bai taba samu a rayuwarsa ba. Da komai ya lafa a tsakaninsu ya koma gefe tallafe da kansa yana kallon Fahimah daga karshen idanunsa yana mamaki yana tuâajjibi a cikin ransa na yadda ta juya masa rayuwa cikin dan lokaci kalilan. Ya manta da asalin, ya manta da kalar fatar da ba ya son, ita din kadai yake son kasancewa da, fiye da kowa a halin yanzu. Ita ce sirrinsa marufar asirin sa. Inda yake jin zai iya sauke duk wani urge da bukatun sa babu shamaki.
Hannu ya sa ya janyo ta gaba daya ta dawo samansa. Ya ce, âFahhimah, yau hira za mu yi, madallah da Ammi na, uwata wadda ta fi ta kowa, da ta mallaka min this rare gem. Fahhimah ki ba ni labarin duk da ya shafe ki da na rayuwarki, ina kuma son sanin duk abin da ki ke so da wanda ba kya soâ¦â?.
Fahimah ta ce, âI have a very short biography wanda ka fi ni saninsa. Na tashi na gan ni a duniya ban san kowa ba bansan komai ba sai AMMI. Don haka na shiga tsananin kidima da Ammi ta dauke ni ta baka Ya Uwais, babu wanda zai so dansa ya auri mara asali, âyar da ba a da tabbacin ko shegiya ceâ?....â?.
Hawaye suka fito idonta, Uwais ya sa tafin hannunsa yana share mata ya ce, âYou are a darling (ke abar so ce) ko da kuwa a ce daga sama ne ki ka fado, ba dan Adam ne ya haife ki ba!
Ki yarda da ni Fahhimahâ? and I promise you LOVE and protection till my last breadth.
Ko kin ga iyayenki watarana, ko ba ki gansu ba har abada, Fahhima zan rayu da ke matsayin uwargidana kuma uwar 'ya'yan da zan haifa a gaba, daga gidan duniya har gidan aljannahâ?.
Kalaman Uwais sun narka zuciyar Fahimah, sai ta rungume shi sosai tana hawaye. Ta ce, âYa Uwais na dade ina sonka, ina son kasancewa da kai, your odd behaviours ba su taba sanya min tsanarka ba. Kullum gaya wa kaina nake I didnât deserve to be loved shi ya sa ka ke maltreating dinaâ?....â?.
Uwais ya sanya tafin hannunsa ya toshe mata baki yana girgiza kai, ya ce, âActually Fahhimahâ? iâ? Iâm jeolous of you. Sabida son da Ammi ta ke miki, bayan wannan sai kuma ganewa da na zo na yi Ammi daga gidan marayu ta dauko ki,
Iâm sorry Fahhimah, amma ki yarda soyayya ba ta yin kanta, sai lokacin da Allah ya nufa. A yau na samu kaina dumu-dumu a so da kaunarki, wanda nake fatan har mutuwa ta dauke mu tare, mu tashi tare a aljannah matsayin miji da mata ranar gobe kiyamahâ¦â?.
Fahimah sarkin kuka, kalaman Uwais sabida dadin da suke mata hawaye kawai suke sanya ta. Ba su suka bar gidan ba sai wajejejn karfe goma na dare, Amrah ta yi kira har ta gaji ba ta same shi ba don tun shigarsa gidan Ammi ya kashe wayar sa.