Showing 45001 words to 48000 words out of 70255 words

Chapter 16 - ALWASHI BOOK 1 COMPLETE by Ummi Aisha .txt

23 Dec 2024

3912

tayi masa tayi hanzarin barin wurin aranta tana tunanin yanda akayi yazama marar kunya tsakanin daren jiya zuwa yau,


Misalin karfe 10 nasafe suna zazzaune acikin falon sai ga khadija tashigo, tana sanye da orange colour din atamfa da mayafi kalar atamfar da yar karamar hand bag,


Duba yusleem tayi tatafi bayan sun gaggaisa, bayan tafiyar khadija mai gadi yashigo yace anyi baki wai masu siyan gidane suka zo, mamice tafita bayan ta dauki wasu takardu,


Wasu mutane guda biyu tasamu tsaye a compound din gidan suna jiranta amma yau babu dr sufyan,


"Sannu alhaji, wadannan sune takardun gidan gashi.."


Karbar takardun wani dan dattijon mutum yayi yafara dubawa, yajima yana nazarin takardun kafin ya dago yana kallon mami,


"Hajiya wannan wanda sunansa yake jiki shine mai gidan?"


Jijjiga kai mami tayi,


"Ehh shine yarona ne"


"Yana ina yanzu?"


"Yana ciki"


"Zan iya ganinsa?"


"Me zai hana, bisimillah zo mu karasa"


Yusleem yana zaune a falo ya tisa Hafsa agaba yana tsokanarta sai gasu mami sun shigo tashi yayi daga kusa da Hafsa yakoma wata kujerar ya zauna,


"Yusleem ga bakinka" inji mami, cikeda mamaki ya kalli mutanen nan yaga babu wanda yasani acikinsu, zama wannan dattijon yayi ya kalli yusleem,


"Yusleem baka ganeni ba ko?"


Daga kai yusleem yayi alamun eh,


"Zaka iya tunawa shekaru shida da suka wuce kaje neman aiki a wata ma'aikata ta yada labarai? A lokacin anyi maka interview daga baya kadawo akace maka baka samu aikinba"


Murmushi yusleem yayi alamun ya tuna,


"Ok sai yanzu natuna ai dayake shekarun an dan kwana biyu"


"To yusleem tun lokacin da kayi interview kasamu wannan aikin kuma abangarena wato department dina, nine nan nahanaka aikinka nace baka samuba amma gwamnati ta daukeka sannan duk watan duniya tana biyanka albashi na naira dubu hamsin da biyar banda allowances d sauran alkhairan da baza arasaba, nine na rinka rike kudin ina harkokin gabana dasu har lokacin da zaka samu promotion daga grade level 9 zuwa grade level 12,haka na rinka ninke kudinka ina kasafin gabana har saida naji wani malami yayi wa'azi akan mutane masu aikata laifi irin nawa, to tun daga nan nasoma binciken hanyar da zanbi insadu dakai inbaka hakkinka da aikinka amma kuma duk lokacin da nakira wayarka bata shiga, daga karshe danaga narasa yanda zanyi inganka sai narinka tara maka albashinka ina ajiye maka kuma ina juya maka acikin kudadena na kasuwanci wanda yanzu haka duk dukiyata tamuce nida kai, kayi hakuri yusleem ka yafe min domin na danne maka hakkinka kuma na cutar dakai..."


Jin maganar yusleem yayi kamar acikin mafarki, bashi kadaiba hatta su mami abin yabasu mamaki mutuka amma kuma duba da irin zamanin da muke ciki yanzu sai mamakin nasu baiyi yawa ba domin yanzu zalunci awurin mutane ba abune mai wahala ba,


"To ai alhaji ni banma san me zance ba domin gaba daya kaina yagama daurewa.." Yusleem yayi maganar yana kallon mami wadda ita dinma shi take kallo zuciyarta kamar kankara dan farin ciki domin arzikin danta da alama yakusa dawowa,


"yanzu tashi zakayi kazo muje inkaika kamfanoninmu da gidajenmu da kuma shagunanmu wadanda ake sayar mana da kayayyakin da kamfanin mu yake sarrafawa, yusleem wallahi kullum da kai nake kwana acikin raina inata addu'ar Allah yasa sai mun hadu nabaka hakkinka kafin na amsa kiran ubangijina, gashi yau burina yacika, zan sauke babban nauyi, zan baka albashinka na shekaru shida sannan kuma zan raba dukiyata gida biyu inbaka taka, haka kuma zamuje can ministry of information domin abaka office dinka wanda yake can yana jiranka.., yanzu tashi mu hanzarta mu tafi"


Farin cikine ya lullube Hafsa nan tasoma yiwa ubangiji godiya acikin zuciyarta, ji take kamar ta zuba ruwa akasa tasha dan farin ciki,


Alhaji musa mori bai bar yusleem yasake wata magana ba yasashi agaba suka fita yace zaije ya sauke nauyi,


Har tsakar gida mami da hafsat suka rakasu saida suka ga fitarsu sannan suka koma ciki cikeda farin ciki da murna, dan murna ko abincin rana kasa ci sukayi suna jiran suga dawowar yusleem amma har dare bai dawoba gashi kuma washe gari da safe zai tafi kasar Cairo,


Yusleem kuwa tunda suka fita basu samu zamaba suna can sunata yawo ana nunnuna masa filayensa da gidaje da shaguna da kamfanoni, basu suka samu Kansu ba sai karfe 9 nadare nan alhaji musa yagayyaceshi suje gidanshi suci abinci amma yusleem yaki yace gida zaije domin gobe da safe zai tafi kasar Cairo nan suka rabu da alhaji musa akan sai bayan yadawo sannan zasu karasa duk wasu abubuwa wadanda suka dace, suka kawoshi gida suka ajiyeshi.


Afalo yasamu su mami zaune suna sauraron zuwanshi kowannensu da gani babu tambaya yana cikin walwala da farin ciki, zama yayi agajiye kusa da hafsat yana murmushi,


"Wallahi yau nasha wahala mami, munyi tafiya sosai har wasu yan kauyuka mukaje.."


"Ikon Allah, Allah mai yadda yaso, Allah yasanya alkhairi dai" inji mami,


"Amin" ya amsa mata tareda kwashewa yadda akayi yasanar da ita, murna dukkansu suka rinka yi sai lokacin suka iya cin abinci, faten wake da kifi yaji albasa da manja, acikin faranti babba hafsat ta zuba musu suka hadu gaba dayansu sukaci harda mami,


Mamince tafara tashi tawuce bedroom dinta tabarsu awurin, kallon hafsat din yakeyi yanda taketa wani sussunne kai ita adole kunyarshi takeji, bai kulata ba yatashi yafita, wanka yaje yayi ya duba kayanshi yasa domin har hafsat ta hada masa yan kayan da zai tafi dasu,


Saida yashirya tsaf sannan yanufi part din mami, dakin da hafsat take ciki yatura yashiga, tana tsaye gaban mirror tana shafe jikinta da turare mai dan karen kamshi da dadi,


Abayanta yatsaya yana kallonta yana shakar kamshinta wanda yatasamma rikita masa kwakwalwa,


"Ashe nidinma dan gatane tunda gashi nan ana shirin yimin tarba ta musamman" yafada cikin tsokana,


Shiru tayi bata tanka ba, ji tayi yadauketa yayi saman gado da ita, rungumeta yayi yana bata labarin abinda yafaru tun daga fitarsa har Kawo dawowarsa,


"Yaya yusleem ai Allah yaga sadaukarwar da kayi kuma yaga irin tuban da kayi shiyasa bazai taba barinka katabe ba.."


"To ai da taimakonki hakan yafaru madam, Allah yayi miki albarka.."


Kasa amsawa tayi domin tuni taji yasoma yunkurin irin wasannin da yayi mata adaren jiya,


Duk da yanata maganar yagaji yagaji yau amma hakan bai sashi yayi barci ba, yanda sukaga rana haka sukaga dare har asuba tayi, saida sukayi salla sannan suka kwanta bacci.


Itace tafara tashi lokacin karfe 9 nasafe tayi wanka tafita wurin mami, bayan sun gama breakfast tana shirin taje ta tasoshi sai gashi yafito, kamar ta nitse dan kunya duk da tasan yanzu mami tagama gane adakin yake kwana, tagefen ido ta kalleshi lokacin da yana gaida mami,


"Yusleem karfe 11 fa zaku tashi, kayi sauri kashirya muje mu rakaka" mami tayi maganar tana duba agogon dake daure a tsintsiyar hannunta, tea kawai yasha yatafi shiryawa,


10:30 daidai yafito tsaf cikin shirinsa natafiya, yasha kananan kaya, iya hafsat ce kadai acikin falon tana jiran mami tafito tana tsaye gaban wani console tana ganin fuskarta, abayanta ya tsaya, yariko kugunta nan tayi saurin juyowa,


Murmushi yayi yakai mata kiss saman bakinta tayi saurin gocewa, hannunta yariko,


"Jiya baki ki ba yau kuma tsabar gulma ce tasaki kin yarda?"


Hannu tasa tarufe fuskarta, jin mami na kokarin fitowa yasashi sakinta nan suka dunguma suka tafi, motar mami suka shiga driver yaja suka fita daidai lokacin motar khadija ta Kawo kai nan tayi reverse tabi bayansu.....




_Gaisuwar fatan alkhairi ga Anty A'isha (mama 4),Anty Aisha (maman minal),Maman sultan, & Hawy yanmata_










*_Ummi Shatu_*👌🏻


© *HASKE WRITERS ASSO*








*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_








*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_






_DEDICATED TO MISS XOXO_








*45*








***Ta cikin mirror din saitinshi yake hango fuskar hafsat wacce ke kunshe da abubuwa guda biyu wato farin ciki da kuma sabanin haka,


Mami kuwa tamkar tafi kowa farin cikin wannan tafiyar ta yusleem domin zaka gane hakan idan har ka kalli fuskarta,


Tafiyar mintuna 15 zuwa 20 ne yakaisu airport din suna yin packing saiga khadija itama tayi packing din tata motar akusa dasu dan haka kusan atare suka firfito,


Cikeda fara'a ta karaso wurinsu tasoma gaisar da mami, cikin fara'a mami ta amsa domin acikin farin ciki take, dan kallon yusleem tayi taga hankalinsa ai bama anan yakeba domin yana tsaye shida hafsat suna yin magana,


Tsayawa dukkaninsu sukayi ajikin mota suna jiran su,


Hawayene suke kokarin zuba a idon hafsat yusleem yayi saurin kama hannunta suka bar wajen, can dan nesa dasu mami sukaje yafara rarrashinta,


Hannuwanta duka biyu yarike yana kallon fuskarta,


"Haba nanah karki zama raguwa, kiyi hakuri kinga da ace tun farko kudin nan sun fito dawuri to da tare dake zan tafi..."


Hawayen da taketa kokarin hana zubowarsu ne suka zubo sharr nan yakai hannunshi ya goge mata,


"Daina kuka, me kike so inkawo miki idan zan dawo..?"


Shiru tayi idanuwanta na kallon kasa,


"Abin dadi?, ko kayan kwalliya?", taji yasake tambayarta, girgiza masa kai tayi alamun a'a,


"To me kikeso?"


Nunashi tayi da dan yatsa,


"Ni kaina...?" Yayi maganar murya kasa kasa,


Kai ta daga masa,


Hannuwanta taji ya matse tareda janta zuwa kirjinsa bata fargaba tajita rungume ajikinshi,


"Yaya yusleem su mami..." Tafada tana kokarin zamewa, sassauta rikon da yayi mata yayi yana murmushi,


"Ki kwantar da hankalinki idan nadawo zaki sameni har sai ma kin gaji dani"


Murmushi tayi ta zame jikinta tana kallonshi, shi dinma kallon fuskarta yake yana murmushi, wurinsu mami suka koma yayi musu sallama ya dauki yar jakar kayanshi yawuce,


Saida sukaga tashinsu sannan suka bar airport din suka dunguma suka koma gida har khadija.




Bayan komawarsu gida harkokinsu sukai tayi amma da zarar hafsat tashiga daki sai taga kamar zataga yusleem, haka taitajin kewarsa har dare yayi, duk irin baccin da yacika mata ido amma lokacin da tazo ta kwanta sai taji ta kasa baccin kwata kwata, sai uban juyi data rinka yi tana tuno mijinta, dakyar tasamu bacci ya dauketa bayan dare ya raba.




Washe gari da safe bata samu damar fitowa da wuri ba sai wurin misalin karfe 11 lokacin da ta fito mami na shiri fita dama ita take jira,


"Hafsa ga breakfast can ni fita zanyi, ina son zanje gidan hajiya Sarah amma ba dadewa zanyi ba"


"To mami Allah ya kiyaye hanya sai kin dawo"


Fita mami tayi tatafi ita kuma ta nufi dining area, zama tayi ta karya duk da abincin bawani mai yawa taciba, falo tadawo tazauna ta kamo tashar b4u tana kalla domin zaman shiru babu dadi,


Har bacci yadan fara daukarta sama sama taji sallamar khadija wacce abisa dukkan alamu yanzu ta mayar da zuwa gidan kullum tamkar ibada,


Tashi zaune hafsat tayi tana murmushi,


"Sannu da zuwa.."


"Yawwa hafsa, ko mamin bata nan" inji khadija wacce ke sanye cikin wata doguwar riga ta atamfa,


"Ehh mami ta dan fita wallahi" hafsa tabata amsa bayan tatashi zaune,


Zama khadija tayi, bayan sun gaisa suka dan fara hira kadan kadan,


"Hafsa kowa yayi mamakin yadda akayi kika samu kan yusleem har kuka kai wannan lokacin tare, saboda yusleem baya iya zama da mace.."


Murmushi hafsa tayi,


"Baya zama da mace kamar ya? Aini ban san wannan labarinba ko a mafarki"


"To kuwa a lissafi kece mace ta fiyeda goma da ya aura, kuma saida ya sakeni sannan ya aureki, ni kinga bamufi wata biyarba tare"


Jijjiga kai hafsa tayi alamun tausayawa,


"Allah sarki, Allah yarufa asiri kin san ai dama lamarin aure sai hakuri domin shima rai gareshi..."


"Hakane amma nida ina zargin ko aljanu gareshi ko kuma da saninsa tsabar cin mutunci ne, shiyasa ma ni yanzu wallahi auren yagama fitar min daga raina domin kin san naji dadi shine gari bawai nasaba ba.."


"To ai ba duk aka taru aka zama dayaba khadija, sai kiga nan gaba kin samu inda zakiji dadin hankalinki ya kwanta..."


"Kayya hafsa, kin san ai duk wanda miciji ya sareshi to idan yaga tsumma gudu yake, hafsa arayuwar aurena tafarko ban tsinci komai ba face bakin ciki da bacin rai da takaici, shiyasa ko zan kara wani auren gaskiya ba yanzu ba sai zuciyata ta nutsu tukunna"


"Ubangiji Allah yazabi abinda yafi alkhairi, babu komai ai jarrabawa ce daga Allah"


"Amin.."


Haka sukaci gaba da yin hirarsu har azahar tayi sai lokacin khadija tatafi, tun daga wannan rana kuma kullum zatazo susha hirarsu da hafsat wani lokacin ma harda mami, ita hafsa tausayin khadija takeji domin irin labaran da take bata na kuncin rayuwa da rashin samun farin ciki wanda ta rinka fuskanta agidan aurenta nafarko, shiyasa take tausayinta domin tasan irin wannan rayuwar tunda itama tashiga makamanciyarta abaya, koda yaushe yanzu khadija tana gidan haka kuma idan bataje da safe ba to zataje da rana ko da yamma wani lokacin harda daddare ma zuwa take tamaida gidan mami kamar gidansu haka ta dauki hafsat a matsayin yar uwa kuma abokiyar shawara domin ko sabon bazawari tayi saita fada mata,


Yauma kamar kullum hafsa tana zaune tana tsifar kai ita kuma mami tana gyaran farcenta saiga khadijan tashigo da alama daga sch take domin karfe 2 saura narana,


Da mami kawai suka gaisa tahaye dining ta zubo tuwon shinkafa miyar zogale tadawo wurin hafsat ta zauna,


"To inbanda abinku kuma ga tsifar gashi ga abinci?" Mami tafada tana murmushi,


Dan kwali hafsat ta dauka ta rufe kanta, "bari inbarshi anjima na karasa idan tagama"


Tashi mami tayi ta shiga kitchen domin tajiyo buruntun kuku aciki,


Mami natashi khadija ta dubi hafsa dama da labari tazo mata,


"Hafsa inata son inbaki labarin wani guy Al'amin, saurayi ne fa amma yadage sai ya aureni duk da nace masa nataba aure"


Murmushi hafsat tayi, "to kibashi dama mana kigani, wallahi khadija kiyarda indai kinga baida problem"


Murmushi khadija tayi ta yanko laumar tuwo tasa abakinta,


"Shikenan zan gwada ingani, bari inyi sauri ma domin munyi dashi zaizo da yamma"


"To Allah ya tabbatar da alkhairi"


Saida khadija taji tayi nak sannan ta hada nata yanata tatafi, kullum hakace take faruwa domin acewarta dama gidan mami gidansu ne domin dama aminiyar mahaifiyarta ce.


Tunda yusleem yatafi basuji duriyarsa ba saida yayi sati biyu sannan yakira su murna ranar awurin mami da hafsa ba acewa komai, sun jima suna hira dashi yana yimusu bayanin abubuwan dake faruwa sannan sukayi sallama,


Haka da daddare ma saida ya kuma kira suka kwashe awanni shida hafsat suna hira, yanzu har tasan lokacin kiranshi domin kullum sai yakirasu da safe da daddare,


Satinshi 7 acan yafara shirye shiryen dawowa amma idan yadawo bayan wani lokaci zai sake komawa,


Hafsat tunda taji zai dawo tarasa inda zata cusa kanta dan murna wanda hatta mami saida ta fahimta, saloon mami takaita aka wanke mata gashinta aka gyarashi, bayan sun dawo gida mai kunshin dake yiwa mami tazo ta zane mata kafafunta da hannaye da bakin lallai mai adon ja,


Tarba ta musamman mami da hafsat suka shiryawa yusleem,karfe 3:30 jirginsu yasauka nan mami da driver suka tafi daukoshi banda hafsa wacce tazauna domin karasa girke girken da aka dora sabodayau tace itace zatayi girkin da yusleem zaici.....






_Gaisuwa da fatan alkhairi ga takwarata A'isha D/sabo..._










*_Ummi Shatu_*👌🏻




© *HASKE WRITERS ASSO.*










*ALWASHI....!*💍
_(Labarin Hafsat)_










*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_








_DEDICATED TO MISS XOXO_








*46*








***Lokacin dasu mami suka dawo gidan hafsat tana cikin daki tana shiryawa, saida ta kammala sannan tayi sallar la'asar domin lokaci yayi,


Tana tsaye gaban mirror tana gyara fuskarta bayan ta idar da sallar ta hango wulgawar mutum ta cikin mirror atsorace ta juya amma abun mamaki bataga kowa ba, tsorata tayi takama hanya zata fita daga dakin taje falo wurinsu mami,


Ji tayi anyi mata wata irin damka, tuni numfashinta yafara neman daukewa, ajikin mutum tajita anrugumeta tabaya tayadda bazata iya ganin fuskar mutumin ba, kara taso fasawa amma ina bata samu zarafin yin hakanba domin ji tayi anrufe mata baki da abinda bata san ko menene ba sai daga baya sannan ta fahimci cewar da bakinshi ne,


Wani sanyayyen kamshi ne mai dadi yake ratsa kofofin hancinta gaba daya,


Sassauta rikon da yayi mata yayi ya dago da fuskarta yana kallonta,


"Nanah hafsat..."


Firgigit tayi tabude idanuwanta akan fuskarsa ganinshi yasata daka tsalle ta rungumeshi na tsawon wasu mintuna,


Riketa yayi yana dan juyi da ita ahankali, dago da fuskarta tayi ta kalleshi, tabbas yaya yusleem dintane amma kuma tamkar wanda aka canjashi domin farar fatarshi tasake haskawa farin yakaru, gashi fatar tashi tasake laushi lubus kamar ta jarirai, kyakkyawar fuskarshi kuma tasake cika da kyau, annuri, da farin ciki,


Ji tayi gaba daya tagama raina kanta saboda yusleem yafita tako ina ita sai take ganinma ayanzu haka ai bata da wani abu atare da ita wanda take ganin zata iya jan ra'ayinshi domin yafita kyau yafita komai na rayuwa,


Hancinta taji yaja domin har lokacin tana dale ajikinshi hannayenta sakale awuyanshi,


Bude idanuwanta tayi daga dogon tunanin data lula ta kalleshi, ji tayi ya rike fuskarta yana kokarin sake saita bakinshi akan nata, shi kansa bakin nashi da lips din dake jiki da fararen hakoran dake jere aciki tasan abin kallone, lumshe idonta tayi tana jiran taji saukar lips dinshi akan nata amma sai taji sabanin haka maimakon yayi kissing din bakinta sai tajishi asaman kirjinta, saurin tureshi tayi tasoma kokarin kwacewa tana dariya,


Riketa yayi shidinma yana yin dariyar kasa kasa,


"Bakiyi min ko sannu da zuwa ba.."


Tana shirin yin magana suka jiyo maganar mami tana nufo kofar dakin,


"Hafsa har yanzu baki idar da sallar bane? Idan kin idar kifito ki hada salad din saboda nace kuku yahada yace kece kika ce karya taba sai kin fito..."


Bude baki tayi zata amsawa mami amma takasa saboda shakewar da muryarta tayi, rufe mata baki da hannunshi yayi yabawa mami amsa da,


"Mami har yanzu fa bata idar da sallar ba.."


"To idan ta idar kafada mata, sannan ku fito muci abincin..."


"To mami..."


Saida ta tabbatar da cewar mami tatafi sannan ta kalleshi,


"Kuma da tashigo taganmu fa gashi kace mata wai salla nake yi.."


Murmushi yayi ya lakuce mata hanci,


"Ai bazata ma shigo ba saboda tasan nidake yau tamkar tif da taya zamu kasance...."


"To kazo muje kar taga mun dade tayi zargin ko wani abu muke yi.."


Murmushi yayi ya dauketa nan tasoma mutsu mutsu, ajiyeta yayi ta fice shikuma yashiga toilet yayi alwala yafito yayi salla,


A falo ya samesu ita da mami sun baje

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login