Showing 12001 words to 15000 words out of 70255 words

Chapter 5 - ALWASHI BOOK 1 COMPLETE by Ummi Aisha .txt

23 Dec 2024

3910

_Dedicated to MISS XOXO_





*16*






***Haka rayuwar Hafsat taci gaba da tafiya akoda yaushe burinta shine taga ta taimakawa yan uwanta marayu wadanda basu samu gataba suke zaune acikin gidan marayu,


Rikon da hajiya kubra keyi mata kuwa rikone na tsakani da Allah wanda ko yar cikinta iya abinda zata iya yimata kenan,


Kasancewar Hafsat din ta maida hankali akan karatuttukan da ake koya mata yasa malamin dake koyar da ita fadawa Alhaji sa'id cewar lokaci yayi wanda yadace asata a makaranta duk da cewar bata faro karatun daga tushe ba amma yana kyautata zaton cewar zata iya, shawarar malamin Alhaji sa'id yabi aka sa Hafsat din awata makaranta ta day,


Zuwanta makaranta yasata sake samun gogewa da wayewa domin ta hadu da yan mata irinta wadanda suka fita wayewa,


Haka rayuwarta taci gaba da gudana sannan duk da ta shiga makaranta hakan bai hanata cigaba da yin saka ba tana saidawa idan ta hada kudin sai taje kasuwa tayi siyayya kamar yadda tasaba ta kai kayan gidan marayu.


Kwanci tashi har Amina kawarta ta samu mijin aure daya daga cikin ma'aikatan gidan marayun ne zai aureta,ba karamin dadi Hafsat tajiba domin Amina itama zata bar rayuwar kunci da talauci gamida maraici, tareda ita aka gudanar da komai aka daura aure suka rakata gidan mijinta wanda keda makobtaka da gidan marayun.


Akwana atashi ahaka Hafsat tashiga aji biyar na secondary domin dama a aji hudu aka sakata, kuma acikin wannan lokacin ne amal tazo gida hutu daga kasar Malaysia, kai idan kagansu kamar wasu yan biyu domin ko Alhaji sa'id dakyar yake iya banbance su musamman ma idan suka saka kaya iri daya domin hajiya kubra tun zuwan Hafsat gidan iri daya take yimusu dinki tareda amal bata taba banbantawa ba,


Saida amal tayi wata uku sannan takoma makaranta tana cike da kewar Hafsa domin komai tare suke yi gashi jininsu ya hadu sosai, itama Hafsat din tana mutukar kewarta.




***


Abangaren yusleem kuwa har yanzu bai fitar da matar aureba duk kuwa da irin Matsin lambar da Mami keyi masa akan ya zabo matar aure amma shiru to shi girman kanshi ma bazai barshi ya tunkari mace da maganar soba,


Kullum idan yaje gidan Mami sai ta tisashi agaba da tambayoyi amma sai dai yayi mata shiru daga karshe ma sai cemata yayi shifa har yanzu bai samu budurwar ba, kyaleshi Mami tayi ta zuba masa ido domin ta dade da sanin cewar aljana ce ta aureshi.




***


Misalin karfe 2:30 narana agogon hannunta ya nuna, dan karamin tsaki taja ta fito daga cikin motar tata ta kulleta ta tsaya bakin titi tana jiran adaidaita sahu,kallo daya kawai zaka yimata ka fahimci ko wacece ita domin sanye take cikin atamfa exclusive purple colour da mayafi shima purple sai takalmi da jaka duk purple colour,


Bakowa bace face Mami wadda ta dawo daga al hikima clinic dubiyar yar kawarta hajiya maryam wacce aka yiwa cs adaren jiya, ganin motarta ta bata matsala yasata tsayawa tanata kiran driver dinta amma bata sameshi ba wannan dalilin ne yasata barin motar awurin ta zabi tasamu adaidaita sahu yakaita gida inyaso daga baya sai drivern yazo ya dauki motar,


Adaidaita sahu ta tare tashiga yaja suka tafi, akan hanyarsu ne daidai queen ihsan restaurant akofar wata private school ta hangi wata yar budurwa tana tsaye sanye da uniform wanda yayi mutukar karbarta tana tare adaidaita sahun,


Da a niyyar Mami ta dauki drop yakaita gida kawai amma ganin budurwar wacce da alama itama agajiye take sannan ga rana yasa mami barin mai adaidaita sahun ya tsaya yadauki budurwar,


Lokacin da budurwar ta shigo ciki saida tagaida mamin, binta da dan kallo mamin ta yi tana yaba hankalinta,


"Hajiya ina zan saukeki..?" Mai adaidaita sahun ya tambayi budurwar,


"A titin fahad mangul zan sauka.."


"Ok to sai nafara sauke wannan hajiyar kenan saboda ita a madaci road zata sauka"


"Babu damuwa" inji budurwar,


Suna tafe dukkaninsu sunyi shiru saiko karar radio din da mai adaidaita sahun ya kunna dahaka suka karasa gidan mami, hand bag dinta ta bude ta fito da karamar jakar hannunta ta fiddo naira dari biyar ta mikawa mai adaidaita sahun, key din motarta da yafadi ta dauka ta fita tana gyara mayafinta,


Saida sukaje kofar gidan su wannan budurwar tana shirin fita bayan tabawa mai adaidaita sahu kudinsa sai kawai tayi ido hudu da yar karamar jakar hannun Mami wacce ta Jefarta aciki bata kulaba lokacin da zata dauki key din motarta,


Batayi magana ba tasa hannu ta dauki jakar tafita batareda tabari mai adaidaita sahun yaganiba....








*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_








*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_






_Dedicated to MISS XOXO_






*17*








***Tana makale da jakar acikin hijabinta ta shiga gida, afalo ta iske ummi tana lissafin wasu kayan yara da aka Kawo mata domin ta sara,


Ganinta yasa ummin yin murmushi,


"Hafsa na yau kam nayi miki laifi driver baije ya daukoki ba na aikeshi bakin kasuwa shagona yaje yakai kayan nan da aka Kawo jiya kinga shine har yanzu bai dawoba.."


Murmushi Hafsat tayi tazauna tana cire takalmi da safar dake kafarta,


"To ai babu komai ummi tunda gashi nadawo.."


"Ame kika dawo?"


"Adaidaita sahune dama kuma inada canji acikin jakata, kinga ma har na tsinci jakar wata mata wacce muka zauna tareda ita aciki" takarasa maganar tana nunawa ummin jakar,


"Yarwa tayi? To yanzu taya zaki ganta har abata, kodai cikiya zamu kai gidan radio?"


"Ai naga gidanta ummi, naga gidan data shiga koda ace ba gidanta bane tunda dai nan taje idan naje ai zan sameta"


"To shikenan tunda kinga gidan da taje sai kije ki kai mata koda gobe ne"


"To ummi Allah ya kaimu"


"Amin, kije kicire uniform din ki shiga kitchen akwai abinci yana nan"


"Toh" ta amsa tareda mikewa ta shiga bedroom dinta.


Washe gari da yamma ta shirya bayan tayi wanka, wani jan leshi tasa mai adon blue ajiki, farin hijab tasa tafito tana rikeda jakar data tsinta,


A balcony tasamu hajiya kubra zaune ta dan kishingida tana sauraren radio,


"Ummi bari inje indawo"


"To hafsa sai kin dawo, zaki gane gidan dai ko?"


"Ehh zan gane, to kije ku tafi da salisu driver sai yakaiki"


"Toh ummi" ta amsa tareda wucewa,


Abakin gate ta iske drivern yana zaune wurin mai gadi suna hira, ganinta yasashi tasowa domin yagane unguwa zasu fita, gidan baya yake kokarin bude mata taki tahanyar bude gidan gaba tashiga ta zauna.


Mami kuwa tunda ta koma gida take faman duba yar karamar jakarta domin makudan kudi ne aciki sannan uwa uba akwai muhimman abubuwanta aciki irinsu katin shaidar dan kasa, gashi ATM card dinta yana ciki,


Ganin bata ganta ba ya tabbatar mata da cewar jefarwa tayi, zama tayi tasoma kiran wayar yusleem amma shiru bai daga ba har takatse tasake kira, saida ta kirashi sau uku bai dauka ba,


Tana kokarin tashi taji shigowarshi domin shi shigowarsa cikin gidan ma daban banci dana kowa saboda awani hankali yake bude kofa ya rufeta,


Yana shigowa ko zama baiyi ba tafara magana,


"Kana inane haka nayita kiranka bakai picking ba? Nafita da mota ta dazu tabani matsala akusa da al hikimah clinic naje duba yar gidan hajiya maryam"


Saida ya zauna yadan jingina kanshi da jikin kujera sannan ya kalli mamin yayi magana,


"To amma mami meyasa zaki fita ke kadai? Meyasa baki tafi da driver ba? Saboda irin wannan na ajiye miki driver fa"


"Yusleem drivern ai baya nan yatafi gareji gyaran daya motar tawa shine naga basai na jirashi ba gara kawai naje nadawo"


"To meye matsalar motar?"


"Ina zan sani, tana can nabarta awurin ai saboda taki tashi, ni duk ma ba wannan ba, jakata na yar ahanya ko akofar gidan nan ko kuma acikin adaidaita sahun da nahau.., Kiran da naketa yi maka dama shine so nake kayi maza kaje bank kakai repot saboda ATM card dina yana cikin jakar"


"Mami shiyasa ai nace kidaina yawo dashi.."


"Babu komai, kai ai ba a ketarewa kaddara"


"To Allah ya rufa asiri, bari naje"


Tashi yayi yafita ita kuma ta mike zuwa cikin bedroom dinta.


Har mami ta fidda rai da samun wannan jakar kwatsam washe gari da yamma tana falo zaune tana kallo gabanta kuma snacks ne ajiye tana dauka jifa jifa tana ci taji sallama,


Amsa sallamar tayi tadan gyara zamanta tana jiran wanda keyin sallamar yashigo,


Wata yar budurwa tagani wacce kamar ta dan san fuskar amma dai bazata iya tunawa yanzu ba,


Ciki Hafsat ta shiga ta tsugunna tagaida mamin,


"A'a tashi mana, tashi ga kujera nan ki zauna" ita Mami ma duk tunaninta ko kawar surayya ce,


"Hajiya dama jiyane bayan mun saukeki a adaidaita sahu mun tafi yakaini gida sai naga jakarki kin mantata aciki shine nakawo miki yanzu..." Hafsat ta kammala zancen tana mikawa mami jakar.....






*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*








*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_








*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*






_Dedicated to MISS XOXO_






*18*








***Cike da mamaki Mami take kallonta bayan ta amshi jakar tata daga hannunta,


Tabbas wannan jakar tace nan tayi hanzarin bude jakar tafara duba kudinta da abubuwanta dake ciki,


Tsawon mintuna biyu tayi tana duban cikin jakar kafin ta dago fuskarta kunshe da mamaki saboda yanda ta yasar da jakar haka take babu abinda aka taba bare har acanja masa muhalli,


Ita kam Hafsat komawa tayi ta zauna bayan tabawa mami jakar, hankalinta kwance lokacin da taga mamin tana kokarin duba jakar saboda yanda ta tsinceta haka ta ajiyeta bata kara koda tabawa ba sai yau dinnan da zata Kawo mata,


"Yan mata ya sunanki?" Mami ta tambayeta fuskarta dauke da fara'a,


"Sunana Hafsat hajiya"


"Hafsat gaskiya kadanne irinku yanzu aduniya domin ba kowane zai tsinci makudan kudi da sauran muhimman abubuwa ya mayarwa mai kayanba sai wanda yake mutukar jin tsoron Allah, dama ni tun farkon ganin da nayi miki wallahi nayaba da hankalinki da nutsuwarki sannan lokaci guda naji kin shiga raina,nagode madalla..."


Dan murmushi hafsa tayi akaro nafarko domin jin dadin yabon da mami tayi mata,


"Ai babu komai hajiya, nima nagode Allah yabar zumunci"


"Ai nice da godiya hafsa, wallahi naji dadi mutuka domin ATM card dina yana ciki niduk dashi nafi damuwa ma wallahi saboda yarana sun koma makaranta last week to kuma yayansu account dinshi yadan samu problem babu damar ya tura musu kudi shine yasaka musu kudin a account dina inyaso sai atura musu tanan..."


"Ayya Allah sarki Allah yabasu sa'a"


"Amin amin, ai da har natura shi ma bankin yaje yakai musu report saboda kar asamu matsala sai gashi kuma kin Kawo min, wallahi nagode miki mutuka"


"Hajiya wallahi babu komai dama tunda naganta nace taki ce domin mu biyu ne aciki.."


"Allah sarki, kuma sai kika gane gidan nawa ma"


"Ehh dama nace koda ace banan ne gidan nakiba to zan Kawo saboda nasan kila idan nayi musu kwatance su ganeki.."


Murmushi mami tayi ta mike cikeda fara'a akan fuskarta,


"Allah sarki,Allah yayi miki albarka.."


Dining area taje,jimm kadan sai gata ta fito rikeda dan madaidaicin farantin silver,


Agaban Hafsat ta ajiye farantin tasake komawa ta dauko mata cup da juice na roba takawo mata,


Kallon farantin Hafsat tayi taga dambun nama ne da snacks,


"Ga lemo nan kisha kinji 'yata, ai ni danaga kin shigo nazaci kawar yatace surayya"


"Au Allah sarki ai inajin ma banma santa ba.."


"Ehh gaskiya bazaki santa ba saboda ba anan takeba tana can akasar Malaysia tana karatu yanzu haka saura shekara daya da yan watanni ta kammala, akwai kuma yayunta maza guda biyu Abdul da khalifa suma suna outside suna karatu sai babban yayansu shi yana nan anan.."


"Allah sarki" Hafsat tafada tana kallon agogon wayarta,


"Hajiya bari inje intafi saboda mamana tace kar injima"


"To ai hafsa bakici snacks dinba kuma ko juice dinma baki shaba"


"Babu komai hajiya, akoshe nake wallahi nagode madalla"


"To tsaya, ina zuwa" mami tafada tareda mikewa tashiga bedroom dinta tafito,


Kitchen ta wuce Jim kadan ta sake fitowa,


"Hafsat to ai sai ki fada min a inda gidanku yake ko saboda inason zan hadaki kawance da yata surayya, koda yake bari sai insa driver yakaiki kinga sai yagano min gidan ko"


Fuskar hafsa da murmushi tace,


"Hajiya nima driver ne yakawoni, kuma gidan namu ma bashida wuyar kwatance"


"To duk da haka dai zansa driver yabiku ya gano gidan naku"


"To shikenan hajiya nagode"


"Yawwa ga wannan babu yawa"


Dan tsorata Hafsat tayi saboda ganin girman ledar da mami ke mika mata,


"A'a hajiya bazan karba ba, nagode madalla amma kibarshi"


"Haba Hafsat karki maida hannun kyauta baya mana"


Dakyar dai mami tasamu har Hafsat ta karbi kayan, rakiya mami tayi mata har compound din gidan, nan sukayi sallama Hafsat tashiga mota drivern mami yana biye dasu suka fice daga gidan,


Kallon Salisu driver Hafsat tayi bayan sun hau titi sakamakon wasu kaya da tagani a sit din baya,


"Wannan kayan fa?"


"Nakine, daga ciki wannan matar tasa aka fito dasu tace asa miki acikin mota"


Sake waiwayawa Hafsat tayi ta kalli kayan nan taga katan din juice guda daya sai na biscuit shima guda daya sai snacks da dambun nama cikin wata leda mai dan kyalli, murmushi tayi tana yaba kirkin mami acikin zuciyarta wato duk abinda takai mata da bataci ba shine saida aka biyota dasu,


Har gida drivern mami yarakasu saida yaga shigarsu ciki sannan yajuya yakoma....










*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*








*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_








_*NA*_
*_UMMI A'ISHA_*






_Dedicated to MISS XOXO_






*19*








***Da murna akan fuskarta ta shiga cikin falon hajiya kubra, zaune ta sameta akan carpet tana goge wata doguwar rigarta mai dan santsi,


"Ah Ummi akan kibari nadawo sai ingoge miki shine kike yi da kanki?"


Hafsat tafada bayan tayi yozali da hajiya kubran,


"A'a Hafsat to ai bawani aiki ne mai yawaba, zaman kadaici ne ya isheni shine nadauko ina gogewa, abbanku ma kinga har yanzu bai dawoba nayi masa waya yace yana gidan abokinshi sunje meeting"


"To Kawo in karasa miki.."


Mika mata iron din hajiya kubra tayi tana cewa,


"Abinda yasa ban hada da ita acikin kayan gugar nanba bana so akona min itane tunda kinga tanada santsi..."


"Wannan kam sai anbita ahankali"


Bude kofa akayi aka shigo, Salisu driver ne yashigo bakinsa dauke da sallama,


Kayan da Mami tabaiwa Hafsat yashigo dasu ya ajiye yafita,


Saida Hafsat tagama goge duguwar rigar sannan ta tashi taje ta kinkimo kayan takawo gaban ummin tana fadin,


"Ummi kinga wai daga zuwa shikenan matar nan ta hadoni da wadannan kayan.."


Cikin fara'a hajiya kubra tafara bude babbar ledar da mami tabawa hafsan,


Manyan turarruka ne masu kamshi guda biyu irin na larabawa sai mansu da sabulai suma masu kyau sai abin hannu da sarka fation amma kuma mai mutukar kyauce,


Kallon kayan Hafsat keyi cikeda mamaki haka itama hajiya kubra mamakin ne ke bayyane akan fuskarta,


"Hafsa anya kuwa duk murnar mayar da jakar nan zatasa matar nan tabaki wadannan uban kayan? Anya kuwa?"


Murmushi Hafsat tayi ta gyara zamanta,


"Wallahi Ummi nima dai haka nace to amma yanda naga ta sake dani tanata yimin hira tana bani labarin yaranta sai nima nadan saki jiki domin harfa cemin tayi wai tanada yarinya budurwa tana kasar waje tana karatu idan ta dawo zata hadamu kawance.."


"Kawance...?" Hajiya kubra ta tambayeta tana dariya,


"Wallahi haka tace Ummi, kinga fa har drivern ta taturo ya biyomu wai yazo yagane mata gidanmu.."


"Allah sarki ai akwai mutane masu kirki a duniya, wasu sunada son jama'a.."


"Wannan kam tanada son mutane wallahi Ummi, kinga snacks din wai dan banci ba shine ta hado min dashi"


Jan kayan sukayi suka ciro suna dubawa, cake ne da meat pie da sauran tarkacen snacks,


Ajiyewa kayan sukayi har saida Alhaji sa'id yadawo suka nuna masa, tun daga wannan rana ita hafsa tama manta da batun mami amma ita kam mami Hafsat tana makale aranta,


Ranar alhamis da rana ta dawo daga super market siyayyar kayan amfanin gida ta biya ta gidansu Hafsat,


Hajiya kubra tana kitchen tana kokarin sauke girkin rana da tayi taji sallamar mami, da fara'a ta karbeta tamkar dama ta santa tayi mata jagora zuwa cikin falonta,


Ruwa da abinci da juice takawo mata sannan tazauna suka fara gaisawa,


"Hmm nace yarinyarki kuwa tana nan?"


"Wacce daga ciki?"


Murmushi mami tayi ta daga kanta takalli hoton amal wanda ke kafe ajikin bangon dakin wanda sak bashida maraba da Hafsat,


"Wannan, gata nan ajikin hoto" mami tafada tana murmushi,


"Ayya to ai tana makaranta, tatafi school tun watanni hudu da suka wuce"


"A'a, anya kuwa? Ai naga last week takai min jakata dana yar acikin adaidaita sahu.."


"To ai shiyasa nace miki wacce aciki domin su 2 ne kuma duk kamanninsu daya,wannan wacce kika nuna amal ce.." Hajiya kubra tafada tana dariya,


"Allah sarki to ba wannan nake nufiba, dayar nake nufi wacce taje gidana tace min sunanta hafsat"


"Ehh,itama tana makaranta amma karfe 2 zata taso.."


Kallon agogon hannunta mami tayi, karfe 12:30 narana,


"To gashi nikuma sauri nakeyi, idan tazo agaisheta, zanje intafi"


"Insha Allah zataji, gashi bakici abincin ba"


"Alhamdulillah, nagode sosai"


Tashi tayi tafita nan hajiya kubra ta bi bayanta ta rakata har bakin gate mami kuwa sai jaddadawa take cewar agaida Hafsat idan tazo,


Koda hafsat tadawo hajiya kubra tafada mata murmushi kawai tayi batace komai ba, ita harkokin gabanta kawai takeyi yanzu daga makarantar boko sai makarantar islamiyya kuma cikin hukuncin ubangiji duk tana fahimtar karatun nako wanne fanni,


Bayan sati biyu da zuwan mami tasake komawa ranar laraba da yamma amma ranar ma bata samu hafsat ba domin tatafi islamiyya,


Sam bataji dadin wannan sabanin da suke yiba wanda har hajiya kubra saida ta fahimci haka,


"Hajiya kiyi hakuri insha Allah zan turo miki ita gobe ko ranar juma'a, hafsan ce wallahi uzururrukanta yawa garesu amma insha Allah zata zo miki.."


Sai lokacin damuwar dake kan fuskar mami takau har ta maye gurbinsa da murmushi,


"To ina jira amma dai dan Allah hajiya kicika alkawari kuma ranar juma'a ma yakamata ki turo min ita yanda zamu dade muna hira.."


"To insha Allah zata zo, agaida mutanen gida"


Sallama sukayi mami

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login