Showing 69001 words to 70255 words out of 70255 words

Chapter 24 - ALWASHI BOOK 1 COMPLETE by Ummi Aisha .txt

23 Dec 2024

3906

makeup tafito, motar hajiya ta dauka tafita da ita, can tsohon gidansu yusleem tawuce kai tsaye B/Q din gidan tashiga inda malam hassan driver da matarsa Hadiza ke zaune,


Malam hassan baya nan domin har yanzu yana aiki dasu Mami sai matarsa ta samu nan tazauna suka gaisa ta gabatar mata da kanta,


"Malama Hadiza a iya tsawonki da Mami da yusleem mata nawa kikasan ya aura?"


"Gaskiya ban san adadinsu ba amma sunfi goma"


"Kuma duk shi yagansu yana so har ya auresu?" Hafsat ta jefa mata wata tambayar,


"A'a gaskiya duk mahaifiyarsa ce ke wahalar nemo masa"


"To meyasa yake sakinsu?"


"Saboda yace baya sonsu,ita kuma mamin bata hakura har sai ta sake yimasa wani auren"


"Wacece matarsa tafarko?"


"Wallahi namanta amma dai anan garin take"


"Daga cikin matan da ya aura waccece kike ganin kamar tafi sonshi?"


"Gaskiya duk suna sonshi shine dai baya sonsu"


"Zaki iya fada min guda uku daga cikin matan da ya aura?"


"Ehhh zan iya"


"Yawwa nagode"


Tsawon wani lokaci suka dauka suna tattaunawa sannan tayiwa Hadiza sallama tatafi, tana driving tana share zufar datake keto mata duk da cewar ta kunna air condition acikin motar,bata taba yin case mai kalubale irin wannan ba duk da cewar tajima tana yin cases daban daban to amma wannan yazo mata da wani salo daban,


Yanzu tunaninta shine inda zata samu matan da yusleem ya aura abaya domin amsa mata wasu tambayoyi, gida takoma domin magrib tayi, koda taje gidanma bata hutaba kwakwalwarta sai kaiwa da komowa takeyi domin gano ta inda yakamata tafara.


Washe gari gidansu kamal tayiwa tsinke wanda shine kukun da yake dafawa mami abinci, yana daf da zai fita taje,


Bayan tagabatar mata da kanta ne tasoma yimasa tambayoyi,

"Ranki yadade ni babu abinda nasani dangane dasu yusleem domin aikina shine kawai dafa abinci"


Murmushi Hafsat mori tayi,


"To amma kasan matarsa bata da lafiya ko?"


"Kamar yadda nafada miki nifa ban san komai ba"


"To shikenan nagode"


Sallama sukayi tafita tanufi motarta, chamber din Barrister Aminu ta tafi amma koda taje akofar office dinshi tasameshi yana kokarin fita alamun cikin sauri yake,


"Barrister da zuwa nayi kamin wani taimako"


"Gashi kuma barrister kin sameni akan hanya domin wata tafiya zanyi yanzu zanje bayelsa state domin yin wani case kuma gaskiya zanfi 1 month acan, amma abinda za ayi zan hadaki da barrister aiman insha Allah zai baki duk wani taimako kamar yanda zan baki"


Godiya tayi masa takarbi number din barrister aiman din tatafi amma duk jikinta yayi sanyi.


Tsawon 3 weeks ta dauka tana bincike amma har yau bata samu wata matsaya guda daya ba ganin lokaci yana kurewa yasata neman barrister aiman nan ta gayyatoshi gidansu domin bata sanshiba kuma bata taba ganinsa ba,


"Barrister narasa ta yanda zan bullowa case dinnan, wacce shawara zaka bani?"


"Barrister gaskiya case dinki yana bukatar dogon bincike, amma ke wakike suspecting?"


"To ai yanzu barrister kowa ma abin zargine harda ni kaina, yanzu bincike sai yabi takan kowa ciki harda ni, sannan ya auri mata da yawa abaya narasa tayanda zan samosu balle har inyi musu tambayoyi"


Murmushi barrister aiman yayi wanda kyawunsa ya bayyana domin kyakkyawan matashine wanda shekarunsa 32 kacal aduniya,


"Karki damu insha Allah zan taimaka miki, just give me 3 days i will find out duk wani information da muke bukata"


"Nagode barrister"


Hira suka dan taba daga nan yatafi, duk da barrister aiman yayi mata alkawari bata saki jikiba, itama cigaba yin nata binciken tayi cikin sa'a tasamu damar gano mata uku daga cikin matan da yusleem ya aura,


Lokacin da barrister aiman yadawo yazo mata da information masu yawa nan itada shi suka fara bibiyar tushen faruwar rashin lafiyar Hafsat amma sun kasa ganowa har bincikensu yaje karshe yanzu yarage iya gidansu yusleem kadai,sai ko kadan daga cikin matan da ya aura wadanda basu ganosu ba,


Samun barrister aiman tayi cikin sanyin jiki tace,


"Barrister nagama karaya, ina tunanin duk yanda akayi wanda yayi wannan abun nagida ne domin kaga yanzu duk mun gama bincikar kowa amma babu alamun laifi atattare dasu, yanzu kawai gidansu yusleem zanje inji yaushe abun yafaru,suwaye suke gidan alokacin,kai har ma wanda yashiga gidan aranar sai na bincikeshi koda kuwa dabbace.."


Dariya barrister yayi yace,


"Idan kikaje dakanki kuma ai magana ta lalace kibarni nine kawai zanje so sai muyi amfani da hidden camera kirinka ganin duk abubuwan da zamu tattauna dasu"


"Shikenan barrister amma fa ka binciki kukun nan dakyau domin ban yarda dashiba last time ma ni kin amsa min tambayoyi yayi"




Sallama sukayi tatafi, aranar da daddare tana tsaka da shiryawa barrister aiman tambayoyin da zaiwa su mami gobe taji wayarta na kara nan tadauka saboda ganin shine,


"Ansake samun wani information, akwai wata mata da ya aura guda daya bari zan turo miki massage ta whatsapp yanzu"


Katse wayar tayi tajira sakonshi, sunan da matar ke amfani dashi shine Big girl, nan tayi searching dinta a Facebook tayi adding dinta domin da pic da komai nata barrister aiman yaturo kawai matsalar sun rasa sunanta nagaskiya, creating din sabon account na facebook Hafsat tayi acikin wannan daren,


Friend request Hafsat tatura mata nan tayi accepting suka fara gaisawa, kamar yadda suka shirya da barrister aiman haka tayi tanuna mata cewar ita kawarta ce wadda suka dade basu haduba da ta tambayi Hafsat sunanta sai tace sunanta na'ima Abbas ashe kuwa big girl din nada kawa mai wannan suna nan tayita sakin baki suna hira har taturowa Hafsat sabuwar number dinta ta whatsapp,


Tsawon 3 days suna chaten nan Hafsat tafara tambayarta wurin wanne boka take zuwa yanzu, kamar wacce ke jira tafara fada mata cewar a Niger yake amma tabari sai zataje sai su tafi tare kuma abin haushi tun daga wannan rana bata kara ganin big girl ba ko a online gashi wayarta bata shiga,


Barrister aiman tasamu tafadawa yace sujira har big girl din tadawo online nan Hafsat ta girgiza kai tace,


"No barrister gaskiya bazamu jiraba, ni aganina muje office din masu sim din datake amfani dashi tana chat gaba daya atattaro mana chat dinta wanda tayi da kowa da kowa"


"Kuma fa kin Kawo idea barrister, tashi muje"


Office din masu layin da big girl ke amfani dashi sukaje nan aka tattara musu komai aka basu domin tunda sukayi bayanin kansu ma'aikatan suka karbesu hannu bibbiyu amma kuma wani abun mamaki hatta register sim din da take amfani dashi namijne yayi shiyasa babu damar ganin information dinta,


Gida Hafsat takoma tashiga daki tarufe ta nutsu tafara bincikar chaten din big girl daya bayan daya har tazo nakan wani malam Dahiru Niger, nan taga chaten dinsu, daukar number dinshi tayi dasafe takirashi tace kawarta ce ta turota wurinshi yayi mata kwatance zai musu wani aikine, nan yafayyace mata yanda zata ganshi idan tazo Niger, sallama sukayi barrister aiman nazaune yana jinsu daga nan suka fara tsara yanda zata shirya tafiyarta zuwa Niger.


Ajirgi tatafi aranar da taje bata samu ganin Malam Dahiru ba domin yana can maradi, saida ta kwana sannan washe gari tashiga mota tatafi maradi,
Bayan sun gaisa tayi masa bayanin cewar kawarta ce taturo ta akan asirin nan da tasashi yayi yakarya shi nan yarike kai yace,


"Ai nafadawa big girl din shifa wannan asirin bazai karyeba har sai mijin shida kansa shine yakona"


"Ehh tasani shiyasa ma tace kabayar atafi dashi akarya acan"


Tashi yayi suka tafi makabarta domin acan ya binne asirin, acan aka tono asirin yabata,duk abinda ke faruwa akan idon barrister aiman ne wanda ke zaune yana gani ajikin laptop dinshi domin hafsat tana makale da wata yar karamar hidden camera ajikinta,


Tana komawa hotel din data sauka ta tattara kayanta domin dawowa Nigeria saboda jikinta yabata cewar akwai abinda zai biyo baya......






_Gaisuwa da fatan alkhairi ga makiyan Hafsat mori domin nasan bata da fans ni kadai ke yinta..... Lol!_












*_Ummi Shatu_*👌🏻

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login