Showing 15001 words to 18000 words out of 70255 words
tafita tatafi, kamar yadda hajiya kubra ta alkawartawa mami haka ta cika alkawari ta hanyar saka driver yakai Hafsat gidan ranar juma'a da musalin karfe 1 narana,
Lokacin da Hafsat taje gidan mami tana cikin bedroom dinta zaune agefen gado suna yin waya da surayya jin sallama yasata fita ganin Hafsat dince tace ta karaso, har cikin bedroom dinta takaita tace ta zauna agefen gado amma fur hafsa taki zama sai akasa ta zauna kan dan madaidaicin carpet din dake shimfide akusa da gadon,
Wayar hannunta ta mikawa Hafsat,
"Ungo amshi ku gaisa da yar tawa surayya, ina zuwa bari inkawo miki ruwa kafin ku gama"
Karbar wayar Hafsat tayi tana murmushi tafara kallon screen din wayar saboda video call ne, surayyan ma daga can kurawa screen din ido tayi tana kallon Hafsat nan suka shiga gaisawa kamar dama can surayya tasanta domin hira sosai take yimata,
Mami tana cikin kitchen tana warming din abinci yusleem ya shigo yana sanye da farar shadda mai mutukar tsada kai idan kaganshi zaka dauka sabon ango ne saboda tsananin kyawun da yayi dama kuma shi haka ka'idarshi take baya taba saka manyan kaya sai ranar juma'a sai ko wani babban muhimmin abu,
"Har kadawo daga masallacin?" Mami ta tambayeshi tana kokarin sauke tukunya daga kan wuta,saida yaje yadan jingina da jikin bango sannan ya amsa mata da,
"Ehhh, ina kukun naku yake naga kina girki dakanki mami?"
"Ba girki nakeyiba dumame ne nayi bakuwa ne shine zan kai mata abinci"
"Ok" shine kawai abinda yace yajuya zai fita, dakatar dashi mami tayi,
"Bazaka shiga ku gaisa da bakuwar tawa ba?"
"Ina zuwa mami, ai ba tafiya nayiba" daga fadin haka yasaka kai yafice,
Filet mami ta dauko ta zubawa Hafsat abincin, macaroni da miyar danyen kifi sai abinsha da fruits, har mami takoma su Hafsat suna ta hira itada surayya wani dadi mami taji wanda ita kadai tasan ma'anarsa acikin zuciyarta,
Saida mami ta karbe wayar tace Hafsat taci abinci sannan hirar tasu ta katse, kasa cin abincin tayi saboda kunyar mami wanda har mamin saida ta fahimci haka, dakyar dai tadan ci ta tattara kayan zata fitar mami ta hanata,
Wuni guda tayi domin sai la'asar sannan hajiya kubra taturo driver yadauketa, mami kam wannan karon kaya sosai ta hada mata domin acikin kayan da take ajiyewa na auren yusleem ta dauko mata duguwar riga dark blue da takalmi da turarruka,
Kin karba Hafsat tayi amma mami saida tasaka mata acikin mota tatafi da kayan,
Lokacin da takoma gidan hajiya kubra taga kayan rasa abin cewa tayi sai can ta nisa tayi magana,
"Hafsat wannan matar haka zatayi ta miki hidima batareda wani abu aranta ba? Nifa ina tsoron rayuwar yau domin wallahi akwai ayar tambaya aciki"
Murmushi Hafsat tayi,
"Wallahi Ummi babu komai sai alheri domin yau munyi waya ma sosai da yartata.."
"To shikenan tunda hakane"
Koda suka nunawa Alhaji sa'id kayan fada yashiga yi sannan yace kar Hafsat takara zuwa gidan shi bai yadda da mami ba,
Tun daga wannan rana Hafsat bata sake zuwa ba amma da aka kwana biyu ita mamin sai gata tazo, ranar kuma tayi Sa'a Hafsat din nagida tana kan keken sakarta tana dinki,
Kyakkyawar tarba hajiya kubra da Hafsat din sukayi mata, ta dan jima agidan kafin tayi musu sallama tatafi, sai bayan tafita ne maigadi yashigo da kaya wanda takawowa Hafsat,
Kayan makulashe ne da turaruka masu tsada, ita kanta hajiya kubra yanzu tafara kuma wani tunani akan mami Wanda dai tabarwa zuciyarta bata furta ba.
Lokuta zuwa lokuta mami kanzo ganin Hafsat kuma duk lokacin da zatazo bata zuwa haka sai ta Kawo mata kayan makulashe irinsu biscuit, chocolate, sweet da sauransu banda mayukan shafawa da turaruka, akwai wani lokaci da taje dubai tadawo tsarabar da takawowa Hafsat abin ba acewa komai domin akwati guda medium ta ciko mata taf da kayan sawa,
Shiyasa tun su ummi na zargin akwai wani abu aran mami har sun dawo sun daina daga ita har Alhaji sa'id din,
Haka mami taci gaba da yiwa Hafsat hidima baji babu gani, lokacin da watan azumi yakama kaya sosai mami tabada aka kai mata kamarsu fruits, madara, sugar da dai sauran kayan hada tea da tarkacen kayan da akafi amfani dasu a lokacin azumi,
Ranar da aka kai azumi na 10 bayan ansha ruwa Hafsat ta shirya taje yimata sannu da shan ruwa, suna zaune ita da yusleem yatashi yafita, yana fita Hafsat ta shiga, ba karamin dadin ganinta mami tajiba nan ta cikata da kayan abinci iri iri,
Har Hafsat tabar gidan tatafi yusleem bai dawoba, da salla tazo kuwa mami kaya ta dinkawa Hafsat kala biyar daya materia, daya leshi daya shadda biyu atamfa super masu kyau da tsadar yan gaske kuma kowanne da takalminsa da mayafinsa banda turare da sarka da abun hannu, wannan sallar saida Hafsat tasamu kaya kala goma domin agida ma kala biyar Alhaji sa'id yayi musu itada amal,
Ranar salla kwalliya Hafsat taci bayan sun gama aikin Gida da hajiya kubra tace mata zataje gidan kawarta Amina nan tatafi mata da abincin sallar da Ummi tayi wainar shinkafa da miyar agushi,
Acan gidan Amina tawuni sai bayan sallar magrib driver yaje ya dauketa yamayarta gida tana zuwa taga wasu sabbin food flasks zama tayi tafara budewa tana gani, fried rice ce da kaza guda daya akai gasasshiya sai sinasir da miyar ganye wanda yaji kaji,
"Ummi wannan abincin fa?"
"Daga gidan mamanki hajiya siyama aka Kawo miki abincin salla"
Murmushi tayi ta mike,
"Allah sarki mami kinga ni namanta ma ban kai mata abincin salla ba"
"Gobe ai sai ki kai mata idan zaki mayar mata da kwanukanta"
Washe gari hajiya kubra tayi girki musamman saboda mami shinkafa da miyar kaji Hafsat ta shirya bayan taci kwalliya tatafi kai mata,
Da murna mami ta tareta tayi mata iso har cikin dakinta,
Zama tayi suka fara hira kamar yadda tasaba yi da Hafsat idan tazo mata, wuni cur Hafsat tayi sai yamma tatafi.
Ahaka rayuwa taci gaba da wakana mami tana mutukar kaunar Hafsat kuma tana kyautata mata wanda harsu hajiya kubra sun yarda da hakan adalilin hakanne ma zumunci mai karfi yashiga tsakanin hajiya kubra da mami domin kawance sukeyi sosai,
Sannu sannu Hafsat ta kammala makarantar secondary wannan dalilinne yasa yanzu bata zuwa ko ina sai makarantar islamiyya saiko dinkin sakarta wanda tasaka agaba,
Cikin weekend tashirya takaiwa mami ziyara,
"Hafsat ankammala karatu ko? Yanzu kuma me kikeda ra'ayin yi?"
Murmushi hafsat tayi,
"Mami karatu zanci gaba dayi"
"To hafsat banki ba amma dai da zakiyi aure shiyafi, idan kikayi aurenki sai kiyi karatunki agidan mijinki"
"Hakane mami amma to wazan aura? Nida ko zance banay.."
"Dana zaki aura hafsat, yarona nakeso ki taimaka min ki aureshi, dan Allah kiyi min wannan taimakon....!.
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
*_UMMI A'ISHA_*
_Dedicated to MISS XOXO_
*20*
***Cikeda mamaki Hafsat ta kalli mami saboda jin abinda tafada,
"Kidaina mamaki Hafsat sannan kuma narokeki dan girman Allah kada ki k'i amsar bukatata domin yin hakan na iya zama dalilin faruwar abubuwa da dama ciki kuwa harda dawwamar bacin rai da bakin ciki acikin zuciyata..."
Sunkuyar da kai Hafsat tayi tai shiru takasa yin magana acikin zuciyarta kuwa tunani takeyi shin shi yaron mamin da take burin hadata dashi shine yaganta yake sonta ko kuwa kawai mamin ce keda burin yin hakan a matsayinta na mahaifiyarsa domin ita tunda take zuwa gidan bata taba ganin daya daga cikin yaran mamin ba kuma surayya kadai ta sani har suke yin waya da ita,
"Hafsat ya naji kinyi shiru? Kodai bakya son dan nawa?"
Muryar mami ta katse mata tunaninta da takeyi,
"Mami to ai bai taba ganina ba kuma nima ba taba ganinshi nayiba.."
Murmushi mami tayi,
"Hafsat kenan ni awurina duk wannan ba wani abu bane kuma abune mai sauki domin na isa da dana duk abinda nasashi baya k'in bin umarni na, matsalar dai kawai kece idan baiyi miki ba,ga hotonshi nan akafe abango ta bayanki, juya ki gani..."
Waiwayawa Hafsat tayi cikeda mamaki ta kalli wurin domin tunda take shigowa bedroom din mami Allah bai taba bata ikon damar kallon wurinba bare har taga hoton,
Hadadden saurayi tagani zaune akan kujerarshi ta office wanda abisa dukkan alamu acikin office dinshi akayi masa hoton,
Farine kyakkyawa mai daukar hankali wanda baduk macece zata ganshi takau da idonta a lokaci guda ba,fuskarshi zagaye take da saje mai hadeda kasumba,bakaken suit ne ajikinshi wadanda sukayi mutukar amsarshi domin sun sake haska farar fatarshi,
Manyan idanuwanshi farare tatass ta zubawa ido har ta gangaro izuwa kan dogon hancinshi mai tsini wanda yake daf da bakinshi dan madaidaici mai dauke da zagayayyun lips wadanda suka kasance jajaye jur,
Ita kanta bata san tsawon mintunan data dauka tana karewa halittar yusleem kallo ba,
"Masha Allah, tsarki ya tabbata ga ubangijin halittu wanda ya kawata halitta da surar wannan bawan nashi.." Ta fadi hakan acikin zuciyarta wanda har lokacin takasa dauke idanuwanta daga kallon hoton,
"Hafsat..." Taji mami takira sunanta sai lokacin ta iya tunawa ma da ashe mamin na zaune wurin, cikin sauri ta dauke idonta daga kan hoton ta sunkuyar da kai cikeda jin kunya,
"Hafsat ko baiyi miki bane?"
Shiru Hafsat tayi bata amsaba tasake sunkuyar da kanta kasa,
Juyin duniya haka mami tayi tana tambayar hafsat amma taki amsawa tayi shiru,
Murmushi mami tayi,
"To Allah dai yasa hasashe na yazama gaskiya hafsat idan har kuwa hakan ya tabbata to nasan zanfi kowa farin ciki....."
Dan murmushi hafsat ta kuma yi cike da kunya,
"Insha Allah zanzo gidan gobe goben nan muyi maganar da umminki kafin asan ta inda za afara kuma"
Mami tafadi hakan cikin jin dadi, ita hafsat yanzu sai taji tana jin kunya da kuma nauyin mamin shiyasa taji duk zaman ta takura,
"Haba hafsat ai tsakaninmu babu yar surukunta, ki dauka cewa kece yata ba yusleem ba, ko aurenku ya tabbata karkiji kunyar sanar dani laifinsa matsawar yayi miki ba daidai ba.."
Shiru hafsat tayi takasa cewa komai,har mami takaraci maganarta ta gama bata iya daga ido ta kalleta ba daga karshe ma sai cewa tayi zata tafi duk kuwa da cewar ba wannan lokacin tayi niyyar tafiyar ba amma wannan maganar da sukayi da mamin itace ta tilasta mata barin gidan.
Ko drivern gidansu bata zauna zaman jiraba sai mami ce tasa drivern ta yakaita gida,
Hatta ummi saida tayi mamakin ganinta a lokacin saboda bata zaci zata dawo dawuri hakaba,
Tambayarta ummin taringa yi akan dalilin dawowarta da wuri haka bayan kuma ba haka tasaba dawowa ba idan taje,
"Hafsat ko unguwa hajiya siyaman zataje ne shiyasa kika dawo?"
"A'a Ummi babu inda zataje tana nan.."
"To meya faru?" Tasake tambayarta,
"Babu komai, tace zatazo wurinki gobe ma"
"Amma dai lafiya ko?"
"Ehh lafiya lau"
"To shikenan Allah yakaimu.."
Acikin zuciyarta ta amsa amin din bata bari ummin tajiba,
Ita kanta bazata iya fassara yanayin da zuciyarta ta karbi yusleem ba kawai dai tanajinta cikin nishadi wanda bata san dalili ba,
Daren ranar tayishi ne batare da tayi isasshen bacciba.
Washe gari da safe misalin karfe 11 daidai nasafe mami tayiwa gidan sammako lokacin Alhaji sa'id na nan ko fita baiyiba,
Jin zuwanta yasa Hafsat jin wata irin faduwar gaba duk sai taji jikinta yayi sanyi dan dakyar ma ta iya zuwa suka gaisa daga nan ta koma daki ta kule bayan ta gabatar mata da ruwa,
"Hajiya kubra yau dai zuwana yasha banban da wanda nakeyi ada domin dalilin zuwana yau shine neman auren yata nazo.. Wato Hafsat"
Murmushi hajiya kubra tayi ta kalli mami,
"To ai bakiyi min gwari gwari yanda zan ganeba"
"Kamar yadda nafada miki nazone in nemarwa dana yusleem auren yarki Hafsat idan har babu alkawarin wani akanta domin wallahi ina mutukar kaunarta kuma ina son inhada jini da ku.."
Murmushi hajiya kubra tayi,
"To ai kema yarkice, amma yanzu abinda nake ganin za ayi shine abbanta yana nan bai fitaba bari inje insanar masa"
"To shikenan"
Tashi hajiya kubra tayi tafita zuwa part din Alhaji sa'id mintuna Kadan sai gata tadawo,
"Hajiya to bismillah zo mu karasa wurin alhajin"
Tare suka shiga suka iskeshi zaune kan kujera hannunsa rikeda jaridar weekly trust,
Gaisawa sukayi da mami tayi masa bayani kamar yanda tayiwa Ummi nan Alhaji sa'id yace babu komai indai har Hafsat din ta amince domin ba za ayi mata doleba kawai abinda za ayi shine suje su daidaita ita da yaron,
Cikeda farin ciki mami tayiwa Alhaji sa'id godiya ta mike tafita acikin ranta tana ganin yanzu saura abu daya yarage shine tashawo kan yusleem....
*_Ummi Shatu_*👌🏻® *HASKE WRITERS ASSO.*
_(Home of expert & perfect writers)_
*ALWASHI...!*💍
_(Labarin Hafsat)_
*_NA_*
_*UMMI A'ISHA*_
_Dedicated to MISS XOXO_
*21*
***Falon hajiya kubra mami takoma tazauna tana jiranta zuciyarta cikeda farin ciki wanda kana iya gane hakan karara idan har ka kalli kan fuskarta,
Tana nan zaune har ummi tafito daga sashen alhaji nan sukayi sallama ta rakata tatafi, saida Hafsat taji fitar mami sannan tafito daga daki tazauna akusa da ummin tana dan kallonta domin jin karin bayani amma kuma sai dai kunya takeji,
"Mamin naku tatafi yanzu nakaita wurin abbanku sunyi magana akanki keda danta, abbanki yace yaron yazo ku daidaita mutukar kun amince kuna son juna to shi bashida wata matsala..."
Shiru Hafsat tayi ta dan sunkuyar da kanta kasa tana murmushi,
"Nida naso kema kiyi karatu kamar yar uwarki amal to amma kin san kowa da yadda Allah yake tsara masa rayuwarsa.., sai dai muyi fatan Allah yasa hakan shine yafi alkhairi"
Har dai ummi tayi maganarta tagama Hafsat bata iya cemata ko uffan ba.
Cikin farin ciki marar misaltuwa mami taje gida tana shiga ta nemi wurin zama ta zauna tafara lissafin abubuwan da ya kamata ta siyo ko ta hado domin bata bukatar bikin nan yawuce watanni biyu masu zuwa kacal,
Paper da pen ta dauko ta zauna tana rubuta abubuwan da takeso tasiyo da adadinsu,
Yusleem ne yaturo kofar falon ya shigo yana sanye da farar riga jersey da blue din trouser hannunshi rike da key din motarshi,
A kusa da mamin ya zauna ya jingina kamar yadda yasaba domin shi haka dabi'arshi take kamar wani mai sarauta akoda yaushe cikin iko yake,
"Mami ina kwana..?"
Dagowa tayi ta kalleshi bayan tacire farin medical glass din dake kan fuskarta,
"Sai yanzu katashi ko? In ba hakaba yaushe za akira karfe 12 da safiya..." Takarasa maganar tana murmushi,
"To ai mami weekend ne.."
"Ehhh tunda weekend ne sannan kuma kai kadaine baka da mata ai dole kayita bacci har rana ta fito"
Murmushi yayi yana shafa kasumbar dake fuskarshi,
"Mami yunwa nakeji wallahi dan yunwar ce ma tafito dani daga gida"
"To me zakaci?"
"Abani tea banda bread, soyayyiyar agada da dankali amma banda egg"
Murmushi Mami tayi tana kallonsa,
"Ai matarka zata sha tsaraba kai idan katashi karyawa baka karyawa da abu guda biyu kuma abin haushinma idan anbaka ba na kirki zakaci ba"
"Mami wallahi nima ina son infara cin abinci dayawa amma narasa meyasa bana iyawa, but ina tunanin nanda 2 weeks zanje london so zan biya ta chairo naga dr dina"
"Da dai yafi maka amma mutum yarinka cin abinci kamar wani karamin yaro..."
Bai kara maganaba yaciro wayarshi daga aljihu yasoma latsawa, mikewa mami tayi tafita takira kuku ta fada masa aikin da zaiyi tadawo wurin yusleem tazauna,
"Wai mami rubuce rubucen me kikeyi ne haka?"
"Ai zan fada maka, kwantar da hankalinka.."
Murmushi yayi yatashi yakoma kan 3 sitter ya kwanta,
Mintuna kadan kuku yashigo dauke da faranti wanda ya dorowa yusleem kayan breakfast din akai,
Akan center table ya dora mishi yajuya yafita, tashi yusleem yayi yaja table din gabanshi ya hada tea yasoma karyawa yanayi yana kallon mami wacce ta dukufa akan rubutun da takeyi,
Saida ya kammala sannan mami ta dago ta kalleshi,
"Yusleem ya maganar auren da nace ka nemo, har yanzu baka samo yarinyar da tayi maka ba ko kuma yaya?"
Dama tun shigowarshi saida jikinsa yabashi maganar aure mami zatayi masa,
Sai da yadan ja lokaci sannan yace,
"Mami meya faru kuma?"
"Babu abinda yafaru inaso ne inji idan har kasamo sai afara maganar auren idan kuma baka samoba to ni nasamo maka..."
Sunkuyar dakanshi yayi yana nazari batare da yace komai ba, tabbas shikam yanada farin jinin yanmata domin babu wahala yanzun nan budurwa tace tana sonshi sai dai kuma sam shi baya bukatar auren ne,
"Yanaji kayi shiru?"
"To mami ai nazaci mun gama maganar nan"
"Dawa? A'a bamu gamaba, nidai ina son kasani nasamo maka yarinyar da zaka aura nanda watanni biyu dan haka saika fara dukkan shirye shiryen da yadace amma wannan karon kasani banyi maka aure dan ka sakar musu yarinya ba,
Sannan kuma inaso ka sama mana visa mutafi umarah domin muje inyi maka addu'a akan Allah yarabaka da wannan aljanar da take tareda kai kuma yasa ayi auren nan cikin sa'a yasaka albarka aciki"
Tunda mami tafara maganar baice uffan ba har tagama,
"Ina fata kaji maganganun da nayi maka kuma sun shiga cikin kunnenka?"
"Ehh naji"
"Yawwa to Allah yayi maka albarka Allah yasa ayi cikin nasara"
Bai amsaba yatashi yafita mami tarakashi da ido,
Kamar yadda mamin tafada acikin lokaci kankani yasamo musu visa suka tafi umarah addu'a sosai mami tayi masa kan auren da zatayi masa bayan sun kammala umarah ne yawuce London yabarta anan bayan tafiyarshi da kwana uku itama tawuce dubai domin karasa hada lefenshi da siyan sauran abubuwan da za ayi amfani dasu abikin dan hatta kayan da amarya zata saka duk saida tasai mata,
Saida ta kammala siyayyarta tsaf sannan tadawo Nigeria shikuwa yusleem har lokacin bai dawoba, dawowarta babu jimawa tatura wakilan yusleem sukaje nemar masa auren Hafsat agidan Alhaji sa'id wanda basu tahoba saida ranarsu, domin Alhaji sa'id ya yanke ranar aure saboda ya fahimci cewar Hafsat din tana son yusleem,
Wannan abu ba karamin dadi yayiwa mami ba dan tsananin dadi aranar da daddare taje gidan tayi godiya,
Aminanta da kawayenta ta gayyato suka kai lefen Hafsat wanda tsayawa fadar kayan ciki bata lokaci ne, domin mami ta yiwa Hafsat lefe na alfarma irin lefen da tunda yusleem yake aure ba ataba yin irinshi ba,
Yanzu gidajen guda biyu ko ina shirin biki sukeyi gadan gadan, Alhaji sa'id ya sakarwa ummi kudi domin yiwa yartata siyayya, ita dai Hafsat bata katabus saboda har yau bataga angonba kuma shima