Showing 75001 words to 78000 words out of 133269 words
Chapter 26 - Dan Makaho Complete Document by Biebee Isa--.txt
ji ba, tunda tace da ke zaaje da ke zaaje din, sai ta san yanda zatayi da baba in ya kama mu, ki tashi dai kafin ya dawo muje mu dawo".
Dalo tace "in suka gaya mishi fa?"
K'amshi tace "i know how to shut them up, trust me".
Numfashi Dalo ta ja ta sake a hankali kafin ta bude Wardrobe ta ciro wani doguwar rigar da Mancy ta aiko mata dashi, gudun magana ne ya sa bata taba sakawa ba, Zaid yace "zan jiraku a waje" ya fita.
Sai da ta shirya suka fita tare gaban Hudu wanda yana ganin fitowar Dalo ya dauko waya don shaida ma yayarshi.
Zaid a gaba Dalo a baya Yesmin a seat din driver suka fita daga Gidan.
Wayar Dalo ke ringing ko da ta duba Aunty shafa ce, sai da hanjin cikinta suka kada, ba kasafai Aunty shafa ke kiranta ba, in har ta kirata to ita Aunty shafa ta fita kuka tana so Dalo ta mata wani abu sai ta kirata.
A daddare tace "donAllah ku maidani Gida bana son problem, ga Aunty shafa na kirana".
Yesmin ta cigaba da tuk'inta tace "answer and put the phone on speaker".
Bin umurnin Yesmin tayi ta kawo mata wayar daidai gemunta.
Muryan Aunty Shafa ya karade Motar "Ke Sadiya Gidan Uban wa kika tafi harda sa sabbin kaya, karuwancin da kika saba zaki ko?".
K'amshi tace "Wai ya Aunty Shafa? Dalo na tare dani, ko akwai matsala ne?"
Da sauri ta sauta murya tace "kingane Yesmin Babanta ne be so tana fita a gidan".
Yesmin tace "to muna tare ba wani wuri zataje ba".
Yesmin ta ma Dalo alamu da ta katse kiran.
Zaid na gaban Mota bece musu komai ba, ya san akwai wani abu da Yesmin ta sani wanda Shafa take tsoron a sani shiysa take daga mata tana kuma bari tana takata amma ko so daya be taba son sanin ko meye ba, abu daya ya sani shine ya yarda da Yesmin dari bida dari.
Chimex Shawarma ta nufa dasu, su ka bada order aka gasa musu guda biyar duk chicken and sausage ta biya kafin suka je Havillah Ice Cream.
Anan suka ci Shawarman bayan ta siya musu icecream.
Fira sukayi su uku cike da kaunar Juna, sukayi pictures kafin suka koma mota, yawo kawai sukai tayi a Garin Katsina, Girman Yesmin ya k'aru a idon Zaid, don ya dade be ga Dalo cikin farinciki irin na yau ba, sai da ta tsaya a Dadin Kowa ta siya ma Dalo Chocolates kafin suka koma Gida gab da Maghrib.
A kusan tare suka isa Gidan da Baba. Ganin Sadiya da Zaid a tare ya sa zuciyarshi nauyi, Yesmin tace "Ina wuni Daddy" ya amsa da murmushi "lafiya lau Yesmin yaushe aka zo?"
Tace "dazun da safe na zo, na zo muku weekends" yace "ayyah mungode sosai ina sukayi posting dinki bayan service?" Tace "General hospital na Kankia" "Allah ya taimaka" yana kallon Zaid da ya dauke kai ita kuma Dalo ta na jiran saukan fada ko duka a daddare, be ce musu komai ba, gaba yayi zuciyarshi na mai nauyi, yaranshi.. ya Allah".
Yesmin ta kallesu duka tace "muje ko?".
Tayi gaba suka bi bayanta.
Suna hanyar parlo sukaji muryan shafa'atu na cewa "Alhaji kaga Sadiya tun dazun ta fita, har yanzu ba ta dawo ba".
Nan da nan fuskar baba ya chanza " Ina Sadiyar, ba zata huta ba sai ta jawo min magana cikin Gidan nan ko? To kafin ta kasheni ni sai na kasheta".
Tuni Dalo ta koma bayan Yayanta a tsorace, shima Zaid ya tsorata da sudden change din baban, yanzu fa ya gansu, ya san tare suke, amma be ce komai ba, amma matarshi tayi magana duk ya koma wani zararre, matar nan ta maida masu mahaifi kamar wani toy.
Yesmin ta kallesu tace "Relax, ba abunda zai faru" parlorn ta k'arasa shiga ta wurga ma Aunty Shafa'atubwani mugun harara mai ma'anoni da yawa. Hajia Shafa ta dan tsorata tace "Laah kaga Alhaji na manta, ashe Sadiya da Yesmin suka fita, na ma manta, kar ka damu". Kamar wani pagal ya washe hak'ora yace "au haba dai? To to to ashe suna tare da Yesmin, ai ba damuwa, barin shiga daki" yayi haba Hajia shafa tayi saurin rufa mai baya don bata shirya haduwa da Yesmin ba.
Sai da suka kai Dalo har daki kafin suka fito a tare.
Hudu da Annah suna tsaye a Parlo.
Don Zaid ya k'ular da Hudu don ya san yana son Yesmin yace "Yesmin ayi rigegen zuwa dakina" da daria tayi saurin fita ya rikota ta fizge hannun ta arta a guje shima ya bita a gujen, bakinciki kamar ya kashe Hudu.
Yanzu shi ke gaba tana biye dashi a baya sukayi BQ.
Ita kuma ta fito daga dakinsu da Plates a hannu ta ga wata na bin Zaid suna gudu suna daria.
Zuciar Labiba ya halba.
Chak Zaid ya tsaya yana kallonta yanda itama take kallonshi, hakan yasa Yesmin chogewa itama don kallon abunda yake kallon.
Budurwa ce ta gani tsaye daga chan bangaren tana kallonsu, daga inda take ta hango fushi a idon yarinyar da bata wuce 18 ba, kallon Zaid tayi ta ga hankalinshi kacokam na gun yarinyar da wani expression a fuskarshi da ta kasa gane ko menene.
Yarinyar ta ga ta share wani abu a idonta kamar hawaye, ta wuce kitchen sauri sauri gudu gudu, a kan idonsu ta sake dawowa a guje ta fada daki.
Wani jijiya Yesmin ta hango a kan Zaid duk ya damu.
Jiki a sanyaye tace "Zaid who is She?"
Murya chan k'asa yace "Noone".
Kafin tace wani abu tuni yayi gaba ya wuce dakinshi tare da barinta tsaye.
Gidansu Labiba Yesmin ta kalla kafin ta tsaya wani nazari kafin ta shiga dakin Zaid ta ganshi kwance rigingine duk yanayinshi ya chanza.
Murmushi tayi tace "Yau ko ka tashi ka min Fira ko na je shagon Eskaley na zuk'i world".
Dariya ya fashe tare da mik'ewa yana fadin "Me zanyi in babu ke k'amshi?".
#1love
#DM
#anatare
#FWASonSo
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO 😉
BABI NA ASHIRIN DA DAYA 2⃣1⃣
(KISHI🤨😏)
Labiba ta katse tsaye ta kasa zaune, girgiza k'afa kawai take, binibini sai ta lek'a window amma ba wani alamun sun fito, har yanzu suna ciki.
Zaid na cikin daki tare da wata Macen da ba ita ba, sosai zuciyarta ke mata zafi da zugi.
Da ita ce tayi yunkurin zuwa dakinshi da yace mata Mara Aji, to ita wannan me za a kirata dashi? Tunda har yunk'urin taba shi take. Tsaki ta buga mai k'arfi tare da cuno baki cikin k'unar rai chan kuma ta tashi ta sake lek'awa.
Kiraye kirayen sallah taji na maghrib, hamdala tayi a zuciyarta ta na me murnan dole su fito suyi Sallah.
Shiru shiru har ta fito tayi nata alwalan bata ga sun fito ba, yayyafi aka fara dama garin tun bayan laasar hadari ya hadu, da sauri ta shige daki tana fatan ya fito ya je Sallah.
Har dai ta idar da Sallah tana ayyanawa a ranta sun fito a yayin da take sallahnTa na idar da sallah tayi tasbihinta a kan dardumanta take har aka kira Isha'i, ta tashi tayi Ishai ta hada da Shafa'i da Wutr.
Ta na ji yayanta ya shigo tare da kullo Gidan alamun yau ya gama fita, tashi tayi ta shiga dakin Yayanta da Sallama.
Zama tayi kusa da Amira ta sake gaidasu kamar yanda takeyi duk bayan sallahr da tayi sai ta gaidasu.
Yayanta da Aunty Aseeyah suka amsa.Ameerah da sabit suka gaidata.
Mallam Muhammad yace “nikam Labiba wani abu naji a cikin anguwa wai ko hatsaniya ya shiga tsakaninki da DanMakaho da ‘yan bencin eskaley” dumm gabanta ya yanke ya fadi, mak’ogaronta ya bushe da k’yar tace “waye kuma danmakaho?” Yayan yace “wannan yaron da ke nan Gidan Alhaji Zaki wanda ya samu matsala da matar babanshi kwanaki”.
“Tabb yo ni ina na ganshi balle in samu hatsaniya dashi” ta shirgo karyan da ita kanta tayi mamakinta, yayan yace “wallahi kin dainji abunda ke yawo a Anguwa, yanzu bayan Masallaci Mallam Na’abba ke ce min ya ga kanwata na sa’in sa da dan makaho da yan bencin eskaley, ni dai na sha mamaki sosai har ina cewa me ya hada labiba da DanMakaho?”.
Aunty Aseey ta chafe tace “wai baban Amira yanzu baka san gulman yan unguwan nan ba? Ana ganinta ta na zuwa makaranta har sun fara kawi ma gulma da k’arerayi, tunda kayi tafiyar nan ba fa inda muke zuwa, da ta dawo daga makaranta muna gark’ame a daki, to wallahi in ma sonta sukeyi su fito su fada ba wai su dinga hado k’aryan da bai da wani amfani ba, in banda k’arya mai zai hada Labiba da ‘yan shaye shaye?”.
Mukut Labiba ta hadiye bak’in miyau, hankalinta na dagawa a duk lokacin da akace me zai hadata da dan shaye shaye? Amma a fuska yak’e takeyi.
Mallam Muhammad yace “in ma gulma ya je musu kan har yau baa gyara bangon chan ba to inshaAllah zan gyara da na hada yan kudaden nan, bulo tsada yake shiyasa, amma ni k’anwata ba ruwanta da yan bencin Eskaley.
Cike da rashin sanin yanda zaayi ta tashi tace barin shiga daki.
Zuciyar Labiba na tsinkewa har yanzu hankalinta na ga dakin Danmakaho, zuciyarta na ingizata da taje ta ga su nan ko ba sa nan ko don hankalimta ya kwanta amma ina ba zata iya ba, Yayanta na gida, ba zata bashi dalilin gasgata maganganun yan Anguwa ba.
Yesmin na fashin Sallah, ganin an fara yayyafi ya sa Zaid yin Maghrib da Isha’i a gida, nan suka cigaba da fira har karfe 10:30.
Anty Aseeyah ta shigo da Sabit da yayi bacci dakin babansu, ta koma ta dauko Ameerah har zata fita ta tsaidata ta hanyar cewa “Aunty Asee” Aunty Asiya ta dan tsaya tace “yadai Aunty Labs?”.
Labiba tayi murmushi tace “wai dama Jawad mukayi waya yanzu wai yace zaizo gobe” hak’ora Aunty Aseey ta yashe tace “ahh Mallam Jawad, aikam sai yazo Allah ya kawo shi lafia, zan gaya ma Yayan naki yanzu kuwa”.
Murmushi Labiban tayi tace “to Aunty, in yace wayeshi? Kice mai cousin din besty Aisha ce” “kar ki damu, ki ba danuwan Aisha bane ai yasan wata rana dole a zo wurinki” murmushi kawai ta mata tace “sai da safe” “Allah ya kaimu Ameen” Aunty Aseey ta fita ta wuce dakin Mijinta.
Labiba kashe datanta tayi ta mike ta rage kayan jikinta zuwa kayan bacci, ta fita don zuwa toilet.
“Ki tashi na rakaki gida Yas dare na sake yi” fuska ta danyi tace “Zaiddd” girgiza kai yayi yace “Yesminnn to 11 fa, get up” a shagwabe ta tashi ya mik’e shima yace “oya” ganin tana niyyan sake zama ya sa shi rik’o hannunta ya ja, ita ko ta cigaba da bubbuga k’afa kamar ‘yar shekara4.
“Zanyi Mafarkinka” yace “nikuma zanyi mafarkin kinyi mafarkina daria sukayi gabaki daya.
Fitowarta daga Toilet saitin idonta kan su biyu, da taimakon wutan lantarkin da ke tsakar gidan da kuma hasken farin wata ya hasko mata Zaid da Yesmin suna tsaka da tsinkar fure a ganinta.
K’irjinta ke barzanar fitowa, kenan tun kafin mangariba suke tare har yanzu? Me suke cewa? Hawaye masu dimi suka cigaba da gangaro mata, kasancewar garin akwai sanyi don yayyafin be dade da tsayawa ba atishawa yazo mata mai k’arfi.
Da Zaid da Yesmin sukayi saurin kallon inda sukaji sautin Atishawan.
Ganin ita suke kallo ya sata saurin shigewa daki har da dan tuntubenta.
“Beebs” ya fada cikin wata irin murya wanda yake chan k’asan mak’oshi.
Yesmin ta kalloshi tace “Wa?”.
Be san maganar da yayi ba ya fito
Yesmin tace “Ehen? Wacece?”.
Zaid ya dan murji kanennen idonshi yace “Mak’wabtan mune”
Yesmin tace “eh ai nagani, sai me kuma?”
Bangon Gidansu ya fadi saboda ruwan da akayi kwanaki, to so kusan uku ana gyarawa ana sake wani ruwan yana rushewa-” Zaid “ba wannan ba cewa nayi wacece?” Kafadunshi ya daga sama yace “a gidan take, k’anwar mai gidan ce” yayi gaba, juywa tayi ta kalli Gidan, ta rantse tana ganin alamun mutum a daidai window din wani daki alamun kallonsu ake, ba ta da zabin da ya wuce tabi bayan Zaid din.
Har bakin Parlorn cikin Gidan ya rakota inda Hudu ke zaune yana kallo, da mamaki ya bisu da kallo, ya kalli agogon dake sak’ale kan bango, duk zatonshi Yesmin na daki, ashe tana chan suna iskanci da DanMakaho.
Yi sukayi kamar basu ganshi ba
Yesmin tace “Zaid, kamar ya kamata na san ko wacece”.
K’ura mata ido yayi sosai kafin yace “sunanta Labiba Ahmad, tana karatu a HUK Polytechnic, kina buk’atar sanin yanda tayi yarintarta ko abunda take so ta zama in the future?”.
Duk da faduwan gaba ya Ziyarci Yesmin amma sai da ta murmusa tace “hakan ya isa, Goodnight Zaid” shima murmushin yayi yace “Goodnight Yas Yas” ta juya ta shige dakin dalo don nan take kwana, be shiga ba don ya san Dalo ta yi bacci ya juya shima ya fita ba tare da ya kalli Hudu ba.
Hudu ya bi bayanshi ta zaguna marasa dadi amma beyi da karfi ba don ya san Mankas yanzu zai tada duk wanda yayi bacci a gidan da Tashancinshi.
WASHEGARI
Tunda yara suka tafi Tahfiz bata zauna ba, aiki takeyi, a ranar sai da ta cire duk yanar dake a saman ceiling, aka zo aka share Gidan.
Mallam Muhammadu ya fito don tafiya kasuwa yace “Ahh su Aunty Labs yau fa ba zama saurayi zaizo” kunya ya bata ta sa hannu ta rufe fuska” Aunty Aseey tace “ai dai ka dawo ku gaisa ko?” Yace “eh to bari dai muga kasuwan” addua suka mishi a tare kafin suka rakashi har bakin k’ofa.
“Labiba, kije kiyi baccin safenki, Abuja ba nan kusa bane”
Labiba tace “wani bacci Aunty Asee? Yace fa ya taho” “ahh to ai dai koma meye sai dai Yayan naki ya aiko da cefanen ko?” Hakane “amma bari dai na dora sobon in yaso sai na hada na saka a fridge don yau da alama rana zaa k’wala”.
Aunty Aseey tace “nidai barin je na kwanta” “to shikenan Aunty”.
Labiba ta kasa tsaye ta kasa zaune ta je nan taje chan, ta goge nan ta goge chan.
“Ki fito wallahi muje kan dining muyi breakfast” ta fada ta na jan hannunta.
Dalo tace “Aunty Yas donAllah ki bari nayi kalacina a daki yanda na saba”
Yesmin ta harareta tace “ba nace miki bana son musu ba, just standup muje muyi breakfast”.
Dalo ta numfasa ta san gardama da Aunty Yasmin ba amfani ya sa ta tashi suka fita.
Suna kan Dining table gabaki daya har Alhaji Alin. Kan dalo a k’asa suka isa bakin table, tunda suka fito idon Hudu ke kansu, sosai Hudu ke ganin kyaun Yesmin amma yau sai ya ga Yesmin tayi muni, ya ga Kyaun Dalo sosai ganin Yesmin da Dalo ya sa ya hango munin Yesmin a lokaci daya, ta fiye tsawo kuka tsohuwa ce, dalo kuwa bata fiye gajarta ba amma yarinyace shakaf, cikin seconds da ba su wuce 30 ba ya ayyano dalo a zahirance yana ayyana wasu abubuwa a zuciyanshi.
Aunty Shafa ranta ya baci ganin Yesmin ta tunkaro table tare da Dalo.
Da ido Yesmin ta mata magana ta jawo kujera ta zauna tare da cewa “Ina kwana Baba?” Alhaji Ali ya kalli Shafa ta galla mai harara yayi saurin kawar da kai ba tare da ya amsa gaisuwan dalon ba”.
Dalo ba ta damu ba ta gaida Aunty Shafa tace “sannu ‘yar sarki jikan galadima, sai yanzu zaa tashi ba aikin fari bare na baki, anzo an zauna zaa cika k’undu”.
Dalo ta daga ido ta kalli Aunty Yesmin, kamshi ta murmusa ta girgiza mata kai.
Yesmin tace “Daddy ina kwana?” Da fara’a Alhaji Ali ya amsa, ta gaida Aunty shafa itama ta amsa, Annah tace “ina kwana Aunty Yas”.
Aunty Yesmin tace “Lafiya lau Annah, ke kikayi breakfast dinnan hala?” Annah ta kyabe baki tace “ni zanyi abinci chabda, mommy ce tayi”.
Yesmin tace “auu na zata ke kikayi, ashe ba banbanci ke da Dalon, duk ba aikin fari bare na baki sai dai a dafa kuzo ku cika k’undu ko Daddy?” Ta fada tana kallon Alhaji Ali, Alhaji Ali yak’e kawai yayi don baida ikon magana.
Aunty Shafa ta san cewa bak’a Kamshi ta gaya mata tace “ku ci abinci kin tsaya jan mutane da surutu sarkin magana”. Dariya k’amshi tayi tace “Ok lets all eat”.
Yesmin ta zuba ma Dalo Dankali da kwai da sauce din k’oda ta tsiyaya mata ruwan tea a cup, dalo duk a tsorace take bata ko son daga ido, godia ta mata kafin ta fara tsakurar abincin a hankali.
Ba ka jin k’aran komai sai k’aran cokula, ji tayi wani abu na bi mata k’afa, ba ta biye ba ta cigaba da cin Abincinta.
Amma sai ta ji abun na yawa har wurin guiwanta, gashi kuma bata sonyi kwakwaran motsi tayi laifi wurin babanta ko aunty Shafa. Sai ta share duk yanda take jin abun na damunta bata yi motsi ba, ashe wai Hudu ne ke shafar kafarta, kasa cigabawa tayi da cin Abinci, ta mik’e tsaye.
K’amshi tace “yadai? Ina zaki?” Dalo ta kalli Hudu da sauri ta kawar da kanta don wani irin daniskan daga gira ya bi ta dashi tace “na k’oshi ne” Yesmin tace “come on my friend zauna kici Abinci” Dalo ta marairaice kamar zatayi kuka tace “dagaske Aunty Yas na k’oshi” Aunty Shafa tace “kema dai Yesmin tunda ta k’oshi ki kyaleta mana” kafin yesmin tayi magana Dalo tuni ta isa daki.
Yesmin ta dauki plate and Cup din Dalo ta bi bayanta dashi ta shiga ta ganta zaune tace “ke wai ya?” Dalo tace “wallahi kawai i wasn’t comfortable” Yesmin ta harareta tace “in har bakya zama kusa da Mahaifinki ta ya kike so ku saba? Ansa ki cinye”. Da sauri ta amsa plate din Aunty Yesmin kuma ta fita ta cigaba da kalacinta, ta riga su gamawa ba tare da tace da kowa komai ba ta fita daga Parlorn, sun san BoysQuaters ta nufa.
Tafiyarta takeyi wa ta hango? Labiba ce ke kai kawo tsakanin kitchen da wajen diban ruwa, tsayawa tayi tana kare ma yarinyar kallo, yarinyace karama, ba zata wuce shekarun su dalo ba, kishinta ya turniketa, a hankali ta fara takawa har sai da tazo boarder tsakanin gidaje biyun Labiba na waigowa ta ga mata tsaye.
Bata karasa ciki ba ta murmusa mata, labiba