Showing 123001 words to 126000 words out of 133269 words
Chapter 42 - Dan Makaho Complete Document by Biebee Isa--.txt
Ali na bayan tafin kafarta zata takashi ta murje hannunshi ba tare da komai ya faru ba.
Ita ba komai ya bata haushi ya bata mata rai ba irin yanda Hajia Er Rabi ta tona mata asiri gaban mutane, yanda Diyarta ta tsareta da tambayar in ita diyar bokace, ita Er Rabi zata ma haka? Aiko zatayi mugun nadama, don wallahi sai tayi maganinta.
Yana isa Gida yaga Motar Shafa'atu.
Lallai matar nan bata da kunya, mai ta dawo yi? Ko kayanta tazo kwashewa?".
Tsayawa yayi a bukka yana jiran Zuwan Dalo, kusan 20 minutes sai ga ta ta iso Driver ya sauketa.
Ta shigo tace "Baba ya baka shiga ciki ba?"
Ya murmusa yace "ke nake jira"
Tace "to mu shiga".
Yace "ina Matar Muhammadu?".
Tace "ta shiga dayan gidanchan kwaso yaranta".
Baba yace "Halimattus Sadiya".
Dalo ta kalleshi da sauri, da wayonta bata zaton ya taba kiranta da sunan nan.
Yace "Baba Mutumin Banza ne ko? Kin tsani Baba ko?"
Da sauri ta rufe mishi baki tace "Baba donAllah kar ka fara, kar ka fara".
Yace "Sadiya, ban kasance Uba nagari a gareku ba, na wofintar daku, na fiffita bare a kanku, na zabi wasu a kanku, na laanceku, na zalunceku, kuyi hakuri, ku yafe ma tsohon banzan nan".
Dalo na kuka tace "Haba Baba, meye haka kakeyi? Wallahi wallahi ban taba tsanarka ba a rayuwata, kai Mahaifinmu ne, mun son kai mai son mune, kar ka bari komai ya tsaya maka a rai, mun san komai da ya faru ba yin kanka bane, asiri gaskia ne, yayi tasiri a kanka, wallahi ko kadan ban rikeka a rai ba ko a da, na dauka hakan kamar fim ne a shafin rayuwata, fim din kuma ya kare, Babana ya fi na kowa kuma ina sonshi fiye da kowa".
Ta ja hannunshi suka shige Gida ba tare da barinshi yayi magana ba.
Suna shiga Gidan suka ga Shafa'atu zaune kan kujera tana karkada k'afa.
Tana ganinsu ta mik'e tsaye.
"Alhaji wani irin iskanci ne zaka dade a waje kuma yanzu ka dauki Sadiya? Uwar me zata mana? Ba ta koma gun uwarta ba".
Wani Mari da ya mata ta rantse taga taurari kusan dari lokaci daya.
Cikin k'unanrai yace "baki da kunya Shafa'atu, kunya bata isheki ba, har kina iya dawowa Gidana?".
A tsorace da fargaban da zuciyarta bata gama aminta dashi ba tace "ni zaka mara? Nan ba gidan aurena bane? Ina zani!".
Yace "Ke Jahila ce wallahi, to in sai na miki gwari gwari, daga lokacin da Asirinki ya tonu, aure ya kare tsakaninmu, ki fitar min daga Gida".
Aiko da sauri ta fita, ina ta ga ta zama? Ai chan zata nemo hatsabibin boka ya kashe mata Er Rabi, ya mallake mata Alhaji Ali, ba zata dawo gidan nan ba, sai ta mallake Alhaji Ali kaf dinshi".
Bata bi ta kan Annah ba da ke ta kwala mata kira.
Annah ko ta dinga binta kamar Jela.
^****^
Jawad kam tun da ya bar Asibitin bai koma ba, a daren rannan ya yanke ma kanshi hukuncin rabuwa da Labiba.
Aure? Ba zai iya aurenta ba ma, bayan ya san ga wanda take so, ai babu ma maganar aure, ba zai yiwu ace ya aureta amma zuciyarta da ruhinta suna wurin waninsa, gwara ya barta ta auri wanda take so, shima Allah ya hadashi da nashi, Allah ya hada kowa da rabonshi.
A Gidan Er Rabi.
Sam ya shiga dakin Uwargijiyarshi don yaji ta shiru, kwance ya ganta shameshame kan carpet kumfa na fita daga bakinta.
Ga wani magani a hannunta cikin er kwalba da alamu maganin ta sha.
Ajali ne yazo? Kashe kanta tayi? Lokacinta ne yayi? Allahu Aalam, ba wanda ya san mai ya kashe Er Rabi.m
Shi dai Sam ya bude Wardrobe dinta ya dau abunda zai dauka ya cika wa bujenshi iska.
Bayan Barinsu Gidan Alhaji Ali, Gidan k'awarta Hajia Clean suka tafi, ta gaya mata yanda Er Rabi taci amanarta, Hajia Clean tace karki damu, ni ai bana zuwa ma Er Rabi da matsalata, ina da bokana aikinshi kamar yankan wuka ne" donAllah muje ki rakani".
Tace "ki bari gari ya waye, dare yayi fa".
Tace "aa wallahi, da zafizafi ake bugun karfe, so nake na ci uban kowa wallahi".
Tace "kina da kudi?"
Tace "ina dashi a account".
Tace "kwaso su tas, yanda zai miki aiki da kyau".
Tace "Annah ta zauna a nan, zataje ta dawo".
ATM tayi ta zari makudan kudin a bankinta, tas ta kwashe kudin. Ta koma gida Hajia Clean.
Hajia Clean ta dauketa suka hau kauye chan gaba da Ajiwa.
Boka sarkin k'arya har bayan kwana sukayi wai yana aiki sai wurin karfe 12 na safe ya gama aikin, sai da ya karbe mata kudinta, ya bata wata 'yar hoda yace da ta shafa shi gaban goshin Alhaji Ali Zaki to ko kisa kika ce yayi sai yayi.
Da murna suka koma.
.....
A daren Jiya Alhaji Ali baiyi bacci ba, zuciyarshi zafi take, zai iya rantsewa ya kamu da hawan Jini.
Da farar Safiya aka kawo musu breakfast, Alhaji Ali ya umurci Dalo da tayi wanka zasu fita.
Bayan tayi wanka suka fita hannu rike da juna.
Gidan Mahaifanshi ya fara zuwa.
Da mamaki aka dinga zuwa daki daki aka tada masu bacci aka sanar dasu ga Yaya Ali yazo.
Nan da nan gida ya kaure da Yaya Ali ya dawo garesu, cikin lokaci k'alilan, dangi duk suka zo gidan, don yin barka.
Alhaji Ali ya ba 'yanuwanshi Labarin abunda ya faru.
Su Aunty furera sai da sukayi kukan jin dadi suka dinga tsine ma shafaatu.
"Wallahi Yaya da Police station ka sa aka kulleta, Shedaniya ce, barin irinsu masifa ne".
Yace "Bakomi, Allah zai mana Sakayya".
Ya nemi gafararsu suka ce bai musu komai ha, tunda ba yin kanshi bane.
Ya dade tare da Danginshi, ina zaa saka dashi da dalo akeyi, kowa na son ya burgeshi, nan da nan aka fara cika cooler don zuaa ganin Zaid ya gaya musu Zaid baiji dadi ba, suna ta yabon Zaid don yana zagayowa jefi jefi.
Nan aka sanar dashi Mijin Mariya diyar kanwar Mamarsu ya rasu.
Da mamaki yace "Mariya tayi Aure?"
Shiru sukayi, basu manta wulakancin da ya musu ba da sukaje neman taimako suna so ai mata kayan daki.
"Kai Kai, Allah ya tsine miki Shafaatu, ban yafe miki ba, kin shiga tsakanina da Yanuwana, Allah ya mana sakayya suka amsa da Amin".
Zuwa sukayi suka mata gaisuwa, Goggonshi ta kebe dashi tace "Mariya ta kusa fita takaba, in kana so ka nemeta".
Alhaji Ali yayi saurin kallon Dalo.
Dalo tayi daria tace "Allah Baba ka aureta, ai Aunty Mariya mai kyau ce".
Ya harareta, bai dai ce komai ba.
Goggo tace "Mariya na da hankali, da kuruciyarta, ko shekara 34 bata yi ba, yaruwarka ce, tun da kai ka ki auren zumunci, amma yanzu shi zamu maka, ko ka ki ko ka so".
Yayi daria yace "Ban ma k'i ba ina so".
Tayi daria tace ja'iri.
Bai bar Family house ba sai da aka kawo mus trailer na kayan abinci, ko wani gida sun samu buhu uku uku na shinkafa da kwalayen taliya, jarkan mai, har ta ashanar da zasu kunna sai da aka kawo
*****
Mancy ta iso Asibitin dauke da breakfast wanda Antisco tayi, bayan sun gaisa tace ya masu jiki, Baban Amira yace "ah jiki da sauki".
Ta kallesu tare da murmusawa bacci suke gabaki dayansu".
Tace "Mallam Muhammadu ka tafi gida kayi wanka, zan zauna dasu".
Yace "to ya tafi Mancy ta zauna ta jira har farkawansu".
Suka gaisheta Labiba tace zata shiga toilet Mancy ce ta taimaka mata har toilet, ta dawo da ita, ta basu breakfast, ta ba Zaid na shi ta hada ma Labiba tea ta na bata a baki, kunya duk ta kama Labiba. Zaid kam yaji dadin yanda ya gansu.
Ta isa Gidan maigadi yace ai sun fita, Asibiti ta nufa bata ga kowa ba sai Mancy.
Mancy tsoro ya kamata. Kar ta musu wani abu, waya ta kira Sadiya tace "ina Babanta? Ga Shafaatu nan tazo".
Aiko dalo na gaya ma Baba suka nufo Asibiti a sittin.
#1love
#DM
#anatare
#SonSoFWA
#nagode
Biebee Isa
[14/03 9:35 pm] Biebie: DAN MAKAHO π
ππ»AURE π
K'ARSHE
Zaid ya kalleta yace "me kike yi a nan?".
Tace "ashe baka mutu ba, naji haushi".
Yace "Ki fita daga dakin nan".
Shafaatu tace "Ubanka nike jira yazo, in yazo sai na tabbatar da ba zaku sake ganinshi a rayuwarku ba".
Mancy tace "Ashe abunda kika min da 'ya'yana bai isheki ba?"
Shafaatu tace "kar ki sake ki dameni, bari zan jira shi a waje".
Mancy ta basu labarin abunda ya faru jiya da daddare sosai sukayi Al ajabi.
Sai ko gasu sun iso da danginshi kusan su 12.
Tana ganinshi ta warwaro Powder din ta nufeshi gadan gadan zata shafa mai a goshi.
Tuni K'anin Alhaji Zaki ya tande mata k'afa ta fadi k'asa, kamar jira suke suka fara dukkanta Mazansu da Matansu, ko wannensu na fanshe bakincikin da suka k'unsa sanadiyarta. Ihu takeyi sosai.
Tuni sun mata Habo baki ya kumbura ido ya kumbura jini ta baki, ita burinta ta shafa mai Powdern nan a ka.
Rirriketa sukayi Alhaji Ali ya tako gabanta yace "Tsakanina dake sai Allah ya isa, ba abunda zance miki, sai tsinuwar Allah su tabbata a kanki, Allah ya saka mana tun a duniya, da ni da yarana ba zamu taba yafe miki ba, Allah ya sa ki wulakanta ki kask'anta anan dunia, Allah ya isa, mai sama mai kowa mai komai zai mana maganinki".
Wani daria ta fashe dashi wanda duk wanda yaji ya san bana lafia bane.
Chan sai taji muryan Mallaminta Baban Annah yace "ba na ce karki hada aikina da nakowa ba? Karshenki yazo".
Kamar an kunna mata battery ta fashe da daria "Hahahah, Alhajina, ni ce fa Matarka Shafaatu, ka manta ka tsani Dan makaho, ka tsine mishi ko zan ji dadi".
Da k'arfi kamar Lasfika ta fara tona ma kanta Asiri.
Nan dangin Alhaji Ali suka sake rufeta da duka kamar dama jira suke, mutane suka zagayesu suna kallo kamar film.
Daga dakin su suna jiyo duk abunda ke faruwa a wajen Amenity.
Ba me ce ma kowa komai, suna mamakin irin aikin sharrin da Shafaatu ta tafka.
Zuwan Alhaji Ahmad Dakata ne ya tsaidasu, yace "haba, ku kyaleta, so kuke ku kasheta? Kar ta mutu a hannunku, ku badata ga Hukuma".
Saketa sukayi, ko zafin da jikinta yakeyi bataji, mikewa tayi ta kakkabe jikinta tace "K'uran ko a jikina , ta musu gwalo".
"Alhajina tsaya in shafeka da hodar nan mana, boka yace "da ya taba goshinka zakayi duk abunda na saka".
Danginshi ka sa jurewa sukayi, wani k'anenshi mai zafin rai ya fincikota ya sata Mota, ya shiga ya Jata ya je ya yasar a wajen Asibitin kamar wata Bola.
Nan ta fara tsince tsince tana tattarawa a rigarta, chan sai ta ji wani shagon saida films na tashi da sautin kida, rawa kawai ta saka mai karfi, hankalin mutane ya dawo kanta, tunbur tayi haihuwar uwanta, wani maigadi ya biyota ta arta a guje, lokaci guda ta fita hayyacinta duk ta haukace ta susuce.
*
Hajia Clean aka gaya ma angs Hajia Shafaatu ba bin bololi a Hanya, Hajia Clean ta tsorata da taje ta gane ma Idanunta, dawowa tayi ta fattataki Annah tace ta fitar mata a Gida.
Annah taje ganin Mamarta a inda Hajia Clean tace ta ganta, tana ganinta ta kasa karasawa saboda warin da Mamarta keyi, Shafa ko na ganin Diyarta ta dinga binta da Gudu, Annah ta zabure ta ruga a guje tana kiran a taimaketa Mahaukacia na binta.
Annah ta samu wani shago ta boye, nan taji wani dan daudu na cewa yana da ikon sa yanmata yin kudi, Annah tace "ya taimaka mata" yace to baki da damuwa zakije ko ina ne? annah tace "ko ma ina ne zani wallahi".
Yace "kar ki damu, ni zan chanza miki rayuwa, zakiyi kudi".
Washegari Annah ta bi dandaudun nan Lagos tafiar Mota ce, dukta wahala.
Wannan shine Silar shigan Annah Dunia.
****
Kwanansu Zaid bakwai a Asibiti sosai suke jin dadin jikinsu, kullum zuwa ganinsu akeyi, har 'yan bencin eskaley sunzo, ana gobe zaayi Sallama Dr Ali ya bukaci a je a ma Zaid Xray a ga status dinshi.
Nurse tazo ta tafi dashi.
Akayi aka dawo dashi sai bayan 4hrs Dr Ali ya bukaci Labiba da Zaid a office dinshi.
**
Dr Ali yace "Zaid, na kiraku ne nan don na gaya muku status dinku duka".
"Labiba you are fit, amma kai Zaid akwai wata 'yar karamar matsala wanda in ka kiyaye to ba wani abu bane, ribs dinka is affected yayi bak'i, in baka bar hayak'i ba it can backfire anytime and you wont be lucky as you are now, amma in dai zaka dinga shan magani, kuma ka daina shan Sigari to lafia lau, and then zaka dinga samun frequent attacks, in dai kana shan magani, komai zai zo da sauki".
Zaid ya murmusa yace "Nagode Babana, na bari wallahi".
Dr Ali yace "Allah Sarki Yasmin, da kina nan da sai kin fi kowa jin dadi Zaid ya bar Hayak'i".
Zaid yayi murmushi mai ciwo yace "Yasmeeen, Allah ya rahamceki, Allah ya biyaki da Aljannah".
Labiba ta amsa da Ameen.
Dr Ali yace "barin je round"
Ya mik'e ya tafi ya barsu.
Labiba tace "kayi Missing dinta ko?".
Ya girgiza kai yace "fiye da tunaninki, nayi missing Yasmin, banda abunda zan biyata da shi, Yasmin ta mutu lokacin da ban taba zato ba, amma na ji mata dadin Shahadarta, Allah ka amshi Shahadar ka sa Yasmin na cikin walwala yanzu".
Labiba ta amsa da "Amin, sai ka mata takwara in mun haihu".
Zaid ya dan kalleta yace "Aure? Aure zamuyi?".
Ta daga mai gira tace "Yesss".
Yace "bakiji yanzu ance zan dinga samun attacks ba? I can die any time in nayi wasa da magani".
Tace "Sai mu jira mutuwarka, sai nayi takaba".
Ya kalleta confidence din na nan, sarcasm din na nan yace "i am serious, nifa ba zanyi aure ba, kar nayi aure na mutu at young age, na bar matata maybe da diyata ko yaro a karamin lokaci".
Labiba ta harareshi tace "aure kam zamuyi".
Yace "ba zan iya ba, zan ha'inceki na aureki yanzu, i am still sick wallahi, aurenki saura wata daya ke da Jawad".
Tace "to ka na nufin na baka Hantata a Banza? Kai tsaya ma kaji, wallahi baka isa ka zauna ba aure ba, ba kuma ka isa ka auri wata ba ni ba, Hantata a jikinka sai ka auri wata banza chan? Chabda, shi kuma Jawad ai he is not stupid, na san wallahi ba zai aureni ba, ya zaayi ya aureni bayan ya san abunda nayi, bayan ya san akwai wanda nikeso?".
Zaid ya kalleta cike da kauna yace "wa kike so?"
Tace "Zaid Ali Zaki nakeso".
Yayi daria yace "In Abbanki zai bani ke ina so".
Tace "Abbana zai baka ni InshaAllah, ehen Mallam, kadai ji ance ka bar shan hayaki ko? Wallahi duk randa na kamaka da ko lighter ne sai mun dawo Asibiti an sake budeka an ciro Hantata an mayar min cikina, ba zan yarda ka kona min Liver ba".
Yayi dariya yace "au Gori zaa min?"
Ta harareshi cike da k'auna tace "an maka goruba ma ba gori ba, kaidai ka kiyaye".
Yace "Yes Ma".
**
Suna fitowa daga Office din suka ci karo da Jawad.
Zaid ya dan kauda kai tare da yin gaba.
Jawad ya rik'o shi tare da cewa "Masoya, soyyayan har a office din doctor?" Ba wanda ya iya cewa komai.
Yace "Ya jikinka Brother?".
Zaid yace "Na ji sauk'i Alhamdulilah"
Jawad yace "Thanks to Labiba ko?".
Zaid yayi shiru kafin yace "Yes, thanks to Labiba kam, kar ka damu i know shes your wife to be".
Jawad yayi murmushi yace "Nooo, You can have her".
Sukayi saurin kallonshi ya gyada "kai yace kai take so, ko ba shi kike so ba ni kike so?".
Da sauri ta gyada kai "aa shi nakee so". Yayi daria yace "Allah ya barku tare, in an dauko maganar zan gaya musu na bar maka ita".
Zaid zai yi magana Jawad yayi gaba abunshi.
%%%%
A tare aka sallamesu.
Alhaji Dakata ya tattara Iyalanshi suka tafi Masaukin da Alhaji Ali ya basu.
Alhaji Ali ya kalli Dalo yace "zamuje gidan ne?".
Sadiya tace "Baba lets go on a date, ni da kai da Yaya Zaid".
Baba yayi daria yace "Ni Masoyinku ne da zaku date dani?".
Dalo tace "sosaii Ma".
Baba ya kalli Zaid yace "Muje?".
Murmushi yayi yace "Muje Baba".
Alhaji Abu yayi murmushi tare da mik'a ma Alhaji Ali hannu yace "to Alhaji a sha Soyayya da 'ya'ya lafia, mu bari mu isa gidan Hajia".
Yak'e kawai yayi tare da gyada kai.
Mancy ta ma yaranta byebye ta shige motar Mijinta, Jawad ya rufa musu baya.
Alhaji Ali yaga Mancy ta shige Motar Mijinta sosai ranshi ya sosu, ya kamata ya cireta a ranshi, ya san cewa ta mishi nisa, don yana da tabbacin ba zata rabu da Mijinta ba don ta dawo gunshi, abu ne da ba zai taba yiwuwa ba, ya san ta wuce mai nesa ba kusa ba, dole ya cireta a ranshi, ya zama dole ya hakura da ita
**^^**
Dakin ya zamana daga Labiba sai Maminta da Abbanta, tunda suka zo sai yau suka kebe.
Labiba cike da kunyansu tace "wallahi na san ban kyauta ba, wallahi Mami nasan na tada nuku hankali ranku bace yake".
Mami tace "Labiba baki da hankali, baki san ciwon kanki ba, ance miki So Hauka ne? Wani irin rashin tunani ne haka, namiji kike ma wannan zazzafan So? Baki san Namiji ba dan goyo bane".
Abba yace "Amina, godiar da zakiyi ma Allah kenan?"
Tace "dole fa a mata fada, bata kyauta ba, wani irin abune wannan? Yarimya ta task tundaga Edo State, tazo wai Katsina gun saurayi? Haba wannan rayuwa da mai tayi kama".
In akwai abunda Labiba bata so to fushin Iyayenta, nan tashiga basu hakuri tana kuka.
Tsakanin da da mahaifi sai Allah, nan suka yafe mata tare da mata fada sosai.
@@@
Zama sukayi a k'ayattacen wurin cin abinci, kowa ya fada abunda zai ci, a ka kawo musu, sai da suka gama ci kafin Baba yace "Zaid, ni fa kunyarka nikeji, ban san ta ina zan fara ba".
Zaid ya murza idonshi yace "Baba kunyan me fa?".
Baba yace "Zaid, ban kasance uba nagari wanda zakuyi alfahari dashi ba".
Zaid yace "Nagane inda ka dosa Baba, ba zan yarda ka nemi gafara na ba, ni wanene da zaka roki gafara na".
Baba yace "Zaid, na zalunceka, da bakina na laanceka, nine silar fadawan ka shayeshaye, na maka Illah".
Zaid yace "ba a hayyacinka ba, na san Babana na sona, a hayyacinshi ba zai taba furta min mummunar kalma ba, ban manta ba a da kana fada da duk wanda ya kirani da sunan DanMakaho, a cewarka sunan Banza ne, ta yaya zaka furta wani zagi da bakinka? Baba wallahi